ثلاثة الأصول وأدلتها
هذا الكتاب هو متن صغير أساسي يبين فيه التوحيد والدين والنبوة، يبين هذه المعاني الثلاثة الأساسية المهمة في فهم العقيدة، وفي دراستها دراسة سليمة وصحيحة. وهو كتاب مختصر، لكنه كتاب مبارك؛ لأنه سهل العبارة ومركز وموجه، وليس فيه أي تعقيد أو إشكالات. فالإنسان بمجرد أن يقرأ الكتاب يستطيع أن يفهمه، ويستطيع أن يعرف المعاني المتضمنة فيه. هذا الكتاب قبل أن يبدأ الشيخ في الأصول الثلاثة قدم لذلك بأربعة مسائل، ثم بعد ذلك بثلاثة مسائل أخرى، ثم شرع في الأصول الثلاثة، وهي التي يجب على كل مسلم أن يتعلمها، وهي التي يسأل عنها العبد في قبره: من ربك؟ وما دينك؟ ومن نبيك؟ ألفها رحمه الله للمبتدئين واجتهد في تسهيلها واختصارها حتى خرجت بأحسن حلة وأعظم فائدة؛ يفهم بها الصغير، ولا يستغني عنها الكبير فعم نفعها، وكثر خيرها؛ لعظم قدر موضوعاتها وشرف محتواها.
TUSHE GUDA UKU DA DALILANSU
Shiekh Muhammad Tamimi - Allah Ya yi masa rahama -
Da sunan Allah Mai rahama Mai jinƙai
Ka sani - Allah Ya yi maka rahama - cewa ya wajaba a kanmu mu koyi mas'aloli guda huɗu:
Ta farko: Ilimi, shi ne sanin Allah - Maɗaukakin sarki -, da sanin ManzonSa - tsira da amincin Allah a gare shi -, da sanin Addinin Musulunci bisa hujjoji.
Ta biyu: Aiki da shi.
Na uku: Kira zuwa ga Allah.
Na huɗu: Haƙuri akan cutarwa a cikinsa.
Dalili shine: FaɗinSa (Allah) - Maɗaukakin sarki -: Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jinƙai. {Ina rantsuwa da zãmani, 1. Lalle ne mutum yana a cikin hasara, 2. Fãce waɗanda suka yi ĩmani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, kuma suka yi wa juna wasiyya da bin gaskiya, kuma suka yi wa juna wasiyya da yin haƙuri (su kam, basu cikin hasara, 3}. [al-'Asr: 1-3].
(Imam) Shafi’i - Allah Yai masa rahama - ya ce: "Da a ce Allah bai saukar da wata hujja a kan halittunsa ba face wannan sura, da ta ishe su".
Imam Bukhari - Allah Ya yi masa rahama - ya ce: Babin: Ilimi kafin faɗa da aiki; kuma dalili shi ne: (Allah) Maɗaukakin sarki Ya ce: {Ka sani babu abin bauta a bisa cancanta sai Allah, kuma ka nemi gafara ga zunubinka...} (Muhammad 19). Sai Ya fara da ilimi kafin faɗa da kuma aiki.
Ka sani – Allah Ya yi maka rahama –: Lallai wajibi ne akan kowanne musulmi namiji da musulma mace, koyon waɗannan al'amura uku, da kuma aiki da su:
Na farko: Cewa Allah - Maɗaukakin sarki - Ya halicce mu, Ya azurta mu, kuma bai bar mu haka nan a zube ba; sai dai Ya aiko mana da ManzonSa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -; duk wanda ya yi masa biyayya, ya shiga aljanna, wanda kuma ya saɓa masa, ya shiga wuta.
Dalili shine: Faɗinsa (Allah) Maɗaukakin sarki -: {Lalle ne, Mũ Mun aika zuwa gare ku, wani Manzo mai shaida a kanku, kamar yadda Muka aika wani Manzo zuwaga Fir'auna15 Sai Fir'auna ya saɓa wa Manzon, saboda haka Muka kãma shi kãmu mai tsanani, 16} [al-Muzzammil: 15-16].
Na biyu: Lallai Allah ba Ya yarda a haɗa shi da wani cikin bauta maSa; ba wani mala'ika makusanci ba, ba kuma wani Annabin da aka aiko ba; dalili: FaɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Kuma lalle ne wurãren sujada na Allah ne, saboda haka kada ku kira kõwa tãre da Allah (da su, a cikinsu)18} [al-Jinn: 18].
Na uku: Cewa wanda ya yi biyayya ga Manzo - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - kuma ya kaɗaita Allah; ba ya halatta gare shi ya jiɓinci wanda ya yi adawa da Allah da ManzonSa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, ko da shi ne mafi kusa dangi gare shi.
Dalili: FaɗinSa Allah Maɗaukakin sarki: {Bã zã ka sãmi mutãne mãsu yin ĩmãni da Allah da RãnarLãhira sunã sõyayya da wanda ya sãɓã wa Allah da ManzonSa ba, kõ dã sun kasance ubanninsu ne, kõ ɗiyansu kõ 'yan'uwansu, ko danginsu. waɗannan Allah Yã rubuta ĩmãni a cikin zukãtansu, kuma Yã ƙarfafa su da wani rũhi daga gare Shi, kuma zai shigar da su a gidãjen Aljanna, ƙoramu na gudãna ƙarƙashinsu sunã mãsu dawwama a cikinsu. Allah Yã yarda da su, kuma sun yarda da Shi. Waɗannan ƙungiyar Allah ne. To, lalle ƙungiyar Allah sũ ne mãsu babban rabo22} [al-Mujadalah: 22].
Ka sani - Allah Ya shiryar da kai zuwa ga biyayyarSa -: lallai Hanifiyya - tafarkin (Annabi) Ibrahim - aminci ya tabbata a gare shi -: ita ce ka bauta wa Allah Shi kaɗai, kana mai tsarkake Addini a gare Shi; kuma da hakan Allah Ya umurci dukkannin mutane, kuma domin hakan ne Ya halicce su; kamar yadda Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma Ban halitta aljannu da mutãne ba sai dõmin su bauta Mini, 56.} [al-Zariyat: 56], ma'anar: "Suna bauta mini", wato: Suna kaɗaitani da ibada,
Mafi girman abin da Allah Ya yi umarni da shi shine: Tauhidi, shi ne: Kaɗaita Allah da bauta.
Kuma mafi girman abin da aka yi hani a kansa ita ce: Shirka, kuma Ita ce: Kiran wanin Allah - Maɗaukakin sarki - tare da Shi.
Dalili shine: Faɗinsa - Maɗaukakin sarki -: {Kuma ku bauta wa Allah kuma kada ku haɗa wani da Shi...} [al-Nisa'a: 36].
Tambaya: Idan aka ce da kai menene tushe uku waɗanda yake wajaba a kan mutum ya sansu?
Ka ce: Bawa ya san Ubangijinsa, da Addininsa, da kuma Annabinsa Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi- .
[GINSHIKI NA FARKO]
Tambaya: Idan aka ce da kai: Wanene Ubangijinka?
Amsa: To kace: Allah Shi ne Ubangijina, wanda Ya reneni ni, kuma Ya reni dukkan halittu da ni’imominSa, kuma Shi ne wanda nake bauta Masa, bani da wani abin bauta da cancanta sai Shi; dalili kuwa shine: FaɗinSa - Madaukakin sarki -: {Godiya ta tabbata ga Allah, Ubangijin talikai2} [al-Fatiha: 2]. Kuma duk abin da ba Allah ba, halitta ne, ni kuma ɗaya ne daga cikin waɗancan halittun.
Tambaya: Idan aka ce da kai: Da me kasan Ubangijinka?
To ka ce: Da ãyõyinSa da kuma halittunSa.
Kuma akwai daga ãyõyinSa, dare da yini, da rãnã da watã.
Kuma daga halittunSa: Sammai bakwai da waɗanda ke cikinsu, da ƙassãi bakwai da waɗanda ke cikinsu, da abin da ke tsakaninsu.
Dalili shine: Faɗinsa - Maɗaukakin sarki -: {Kuma akwai daga ãyõyin Sa, dare da yini, da rãnã da watã. Kada ku yi sujjada ga rãnã, kuma kada ku yi ga watã. Kuma ku yi sujada ga Allah wanda Ya halitta su, idan kun kasance Shĩ ne kuke bauta wa}. [Fussilat: 37].
Da faɗinSa - Maɗaukakin Sarki -: {Lalle ne Ubangijinku Allah ne, wanda Ya halicci sammai da ƙasa a cikin kwãnaki shida, sa'an nan kuma Ya daidaita a kan Al'arshi, Yanã sanya dare ya rufa yini, yanã nẽman sa da gaggawa, kuma rãnã da watã da taurãri hõrarru ne da umurninSa. To, Shĩ ne da halittar kuma da umurnin. Albarkar Allah Ubangijin halittu tã bayyana!54} [al-A'araf: 54].
Ubangiji Shi ne abin da ake bauta Masa; dalili: FaɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Yã ku mutãne! Ku bauta wa Ubangjinku, Wanda Ya halicce ku, kũ da waɗanda suke daga gabãninku, tsammãninku ku kãre kanku!21 Wanda Ya sanya muku ƙasa shimfiɗa, kuma sama gini, kuma Ya saukar da ruwa daga sama, sa'an nan Ya fitar da abinci daga 'ya'yan itãce game da shi, sabõda ku. Sabõda haka kada ku sanya wa Allah wasu kĩshiyõyi, alhãli kuwa kuna sane, 21-22}. [al-Baƙara: 21-22].
Ibnu Katheer -Allah Yayi masa rahama - ya ce: "Mahaliccin waɗannan abubuwa Shi ne wanda ya cancanci bauta".
Nau’ukan ibadar da Allah Ya yi umarni da su: kamar: Musulunci, da Īmāni, da Iḥsāni; kuma daga cikinsu har da: addu’a, da tsoro, da fata, da dogaro, da raghaba (burin kusanci), da fargaba, da nutsuwa da ƙanƙan da kai, da tsananin tsoro, da komawa ga Allah, da neman taimako, da neman tsari, da neman agaji, da yanka, da bakance, da makamantansu na nau’o’ikan ibadar da Allah Ya yi umarni da su - dukansu na Allah Maɗaukakin sarki ne; hujja kuwa: Ita ce faɗinSa Allah - Maɗaukakin sarki -: {Kuma lalle ne wurãren sujada na Allah ne, saboda haka kada ku kira kõwa tãre da Allah (da su, a cikinsu)18}. [al-Jinn: 18].
Duk wanda ya juyar da wani abu daga gareta ga wanin Allah; to mushriki ne kafiri; dalili kuwa shine faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Kuma wanda ya kira, tãre da Allah, waɗansu abũbuwan bautãwa na dabam, bã yanã da wani dalĩli game da shĩ (kiran) ba, to hisãbinsa yanã wurin Ubangijinsa kawai. Lalle ne, kãfirai bã su cin nasara, 117} [al-Mua'Minun: 117].
A cikin hadisi kuma: «Addu'a ita ce ɓargon (jigon) ibada».
Dalili: FaɗinSa Allah - Maɗaukakin sarki -: {Kuma Ubangijinku ya ce: "Ku kira Ni in karɓa muku. Lalle waɗannan da ke kangara daga barin bauta Mini, za su shiga Jahannama sunã ƙasƙantattu, 60}. [Ghafir: 60].
Dalilin tsoro: FaɗinSa Allah - Maɗaukakin sarki -: {...To, kada ku ji tsõronsu ku ji tsõro Na idãn kun kasance mãsu ĩmãni} [Aal- Imran: 175].
Dalilin kwaɗayi; FaɗinSa - Allah -Maɗaukakin sarki -: {...sabõda haka wanda ya kasance yanã fãtan haɗuwa da Ubangijinsa, to, sai ya yi aiki na ƙwarai. Kuma kada ya haɗa kõwa ga bauta wa Ubangijinsa}. [al-Kahf: 110].
Dalilin dogaro; FaɗinSa -Allah - Maɗaukakin sarki -: {...kuma ga Allah sai ku dogara idan kun kasance muminai}. [al-Ma'ida: 23]. Da kuma faɗiinSa (Allah): {...Kuma wanda ya dõgara ga Allah, to, Allah ne Ma'ishinsa...} [al-Ɗalak: 3].
Dalilin kwaɗayi, da tsoro, da halarto da ƙanƙar da kai shine: FaɗinSa - Allah - Maɗaukakin sarki -: {Lalle ne sũ, sun kasance sunã gudun tsẽre zuwa ga ayyukan alhẽri. Kuma sunã kiran Mu a kan kwaɗayi da fargaba. Kuma sun kasance mãsu saunar (aikata sãɓo) gare Mu} [al-Anbiya'a: 90].
Dalilin tsoro (wanda ya ginu akan ilimi): FaɗinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {...Kada ku ji tsõronsu kuma ku ji tsõroNa...} [al-Ma'ida: 3].
Dalilin inābah (komawa ga Allah) shine: FaɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Kuma ku mayar da al'amari zuwa ga Ubangijinku, kuma ku sallama Masa...} [al-Zumar: 54].
Dalilin neman taimako: Faɗinsa -Allah Maɗaukakin sarki -: {Kai muke bautawa, kuma Kai kadai muke neman taimakonKa, 5} [al-Fatiha: 5]. A cikin hadisi kuma: "Idan zaka nemi taimako to ka nemi taimakon Allah".
Dalilin neman tsari: Faɗinsa Allah - Maɗaukakin sarki -: {Ka ce "ina neman tsari ga Ubangijin safiya, 1} [al-Falaƙ: 1], da {Ka ce "Ina nẽman tsari ga Ubangijin mutãne} [al-Nas: 1].
Dalilin neman agaji: Faɗinsa -Allah Maɗaukakin sarki -: {A lõkacin da kuke nẽman Ubangijinku tairnako, sai Ya karɓa muku...} [al-Anfal: 9].
Dalilin yanka shine: FaɗinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Ka ce: "Lalle ne sallãta, da baikõna (yanke-yankena), da rãyuwãta, da mutuwãta, na Allah ne Ubangijin tãlikai, 162. Bãbu abõkin tãrayya a gare Shi...} [al-An'am: 162-163], Yana daga Sunnah: «Allah ya tsinewa wanda yayi yanka don wanin Allah»
Dalilin Bakance: Faɗinsa -Allah - Maɗaukakin sarki -: {Suna cikãwa da alwãshin (da suka bãkanta), kuma suna tsõron wani yini wanda sharrinsa ya kasance mai tartsatsi ne7} [al-Insan: 7].
[ASALI NA BIYU]
Sanin Addinin Musulunci da dalilai, kuma shi ne: Miƙa wuya ga Allah da kaɗaita Shi, da jawuwa gareShi da biyayya, da kuma barranta daga shirka da ma’abotanta.
Yana da matakai uku: Musulunci, da imani, da kuma kyautatawa.
Kuma kowane mataki yana da rukunai.
Rukunnan Musulunci guda biyar ne, sune: Shaidawa babu abin bautawa da cancanta sai Allah, kuma (Annabi) Muhammad Manzon Allah ne, da tsaida sallah, da bada zakka, da azumin Ramadan, da ziyartar ɗaki mai alfarma (Hajji).
Dalilin shahada: FaɗinSa -Allah Maɗaukakin sarki -: {Allah Ya shaida cẽwa: Lalle ne bãbu abin bautãwa fãce Shi kuma malãiku da ma'abũta ilmi sun shaida, yana tsaye da ãdalci, bãbu abin bautãwa face Shi, Mabuwãyi, Mai hikima, 18} [Aal Imran: 18].
Ma'anarta: "Babu abin bautawa da cancanta sai Allah.
Babu abin bauta dacancanta": yana kore dukkanin abin da ake bautawa komabayan Allah.
"Sai Allah" yana tabbatar da bauta ga Allah Shi kaɗai.
Bashi da abokin tarayya a cikin bautarSa, kamar yadda baShi da abokin tarayya a cikin mulkinSa.
Kuma tafsirinta wanda yake bayyana ta; shi ne faɗinSa Allah Maɗaukakin sarki -: {Kuma (ka ambaci) lõkacin da Ibrãhĩm ya ce wa ubansada mutãnensa, "Lalle nĩ mai barranta ne daga abin da kuke bautãwa, 26. Fãce wannan da Ya ƙãga halittata..} [al-Zukhruf: 26-27], da faɗinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Ka ce: "Yã ku Mutãnen Littãfi! Ku tafo zuwa ga kalma mai daidaitãwa a tsakã ninmu da ku; kada mu bauta wa kõwa fã ce Allah. Kuma kada mu haɗa kõme da Shi, kuma kada sãshenmu ya riƙi sãshe Ubangiji, baicin Allah." To, idan sun jũya bã ya sai ku ce: "ku yi shaida cẽwa, lalle ne mu masu sallamã wa ne, 64} [Aal Imran: 64].
Dalilin shahadar cewa (Annabi) Muhammad Manzan Allah ne; faɗinSa -Allah Maɗaukakin sarki -: {Lalle ne, haƙĩƙa, Manzo daga cikinku yã je muku. Abin da kuka wahala da shi mai nauyi ne a kansa. Mai kwaɗayi ne sabõda ku. Ga muminai Mai tausayi ne, Mai jin ƙai, 128} [al-Taubah: 128].
Ma’anar shaidawa cewa (Annabi) Muhammad Manzon Allah ne: Yi masa biyayya cikin abin da ya yi umarni, da gasgata shi cikin abin da ya bada labari, da nisantar abin da ya yi hani da barinsa kuma ya tsawatar, kuma kada a bautawa Allah sai da abin da Ya shara'anta.
Dalilin Sallah da Zakka da bayanin Tauhidi; FaɗinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Kuma ba a umarce su da kome ba fãce bauta wa Allah suna mãsu tsarkake addinin gare Shi, mãsu karkata zuwa ga addinin gaskiya, kuma su tsai da salla kuma su bãyar da zakka, kuma wannan shi ne addinin waɗanda suke a kan hanyar ƙwarai, 5} [al-Bayyinah: 5].
Dalilin azumi: Faɗinsa Allah - Maɗaukakin sarki -: {Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! An wajabta azumi a kanku kamar yadda aka wajabta shi a kan waɗanda suke daga gabãninku, tsammãninku, zã ku yi taƙawa, 183} [al-Baƙara: 183].
Dalilin hajji: FaɗinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Kuma akwai hajjin ¦ãkin dõmin Allah a kan mutãne, ga wanda ya sãmi ĩkon zuwa gare shi, kuma wanda ya kafirta to lalle Allah Mawadãci ne daga barin tãlikai, 97.} [Aal-Imran: 97].
Mataki na biyu: Imani; shi: Tsagi saba’in ne da wani abu, mafi falalarsu faɗin: Babu abin bautawa da cancanta sai Allah, kuma mafi ƙasa shine kawar da ƙazanta daga hanya, kuma kunya wani tsagi ce na imani.
Rukunan imani guda shida ne: Yin imani da Allah, da mala'ikunSa, da littattafanSa, da ManzanninSa, da ranar lahira, da ƙaddara alherinta da sharrinta.
Dalili a kan waɗannan rukunan shida: FaɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Bai zama addini ba dõmin kun jũyar da fuskõkinku wajen gabas da yamma, kuma amma addini shi ne ga wanda ya yi ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira da malã'iku da Littattafan sama da Annabãwa...} [al-Baƙara: 177].
Dalilin ƙaddara: FaɗinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Lalle Mũ, kõwanne irin abu Mun halitta shi a kan tsãri49} [al-Kamar: 49].
Mataki na uku: Kyautatawa - rukuni ɗaya ne -; shi ne: Ka bautawa Allah kamar kana ganinSa, idan kai ba ka ganinSa, to Shi Yana ganinka.
Dalili: Faɗinsa Allah - Maɗaukakin sarki -: {Lalle Allah Yanã tãre da waɗanda suka yi taƙawa da waɗanda suke sũ mãsu kyautatãwa ne, 128} [al-Nahl: 128].
da faɗinSa (Allah) Maɗaukakin Sarki: {Kuma ka dõgara ga Mabuwãyi, Mai jin ƙai127 Wanda Yake ganin ka a lõkacin da kake tãshi tsaye, 218 Da jujjuyãwarka a cikin mãsu yin sujada, 219} [al-Shu'araa: 217-219].
Da faɗinSa - Allah Maɗaukakin Sarki: {Kuma ba ka kasance a cikin wani sha'ani ba, kuma ba ka karanta wani abin karatu daga gare shi ba, kuma ba ku aikata wani aiki ba, fãce Mun kasance Halarce a lõkacin da kuke zubuwa a cikinsa...} [Yunus: 61] Zuwa ƙarshen ayar.
Dalili daga cikin Hadisi: Hadisin Jibril shahararre, daga Umar - Allah Ya yarda da shi - ya ce: "Wata rana muna zaune a wurin Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - sai wani mutum ya ɓullo mana, mai tsananin farin tufafi, mai tsananin baƙin gashi, ba a ganin alamar tafiya a tare da shi, kuma babu wanda ya san shi daga cikinmu, har ya zauna a gaban Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, sai ya jingina gwiwoyinsa zuwa gwiwoyinsa, ya ɗora tafukansa a kan cinyoyinsa, ya ce: Ya Muhammad!
Bani labarin game da Musulunci?
Sai Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Musulunci shi ne ka shaida cewa babu abin bautawa da cancanta sai Allah, kuma Annabi Muhammadu Manzon Allah ne, ka tsaida sallah, ka ba da zakka, ka azimci Ramadan, ka yi hajjin Ɗakin Allah idan ka samu ikon tafiya zuwa gare shi." Ya ce: "Ka yi gaskiya" - sai muka yi mamaki da shi, yana tambayarsa kuma yana gaskata shi -.
Ya ce: To ka bani labari game da imani?
Ya ce: Ka yi imani da Allah, da mala'ikunSa, da littattafanSa, da ManzanninSa, da ranar lahira, kuma ka yi imani da ƙaddara alherinta da sharrinta. Ya ce: Ka yi gaskiya.
Ya ce: To ka bani labari game da kyautatawa?
Ya ce: Ka bautawa Allah kamar kana ganinSa, idan kai ba ka ganinSa, to Shi Yana ganinka.
Ya ce: bani labari game da al-ƙiyama?
Sai ya ce: Wanda ake tambaya bai fi wanda yake tambayar sani ba.
Ya ce: To, ka bani labarin alamominta?
Ya ce: "Baiwa za ta haifi uwargidarta, kuma ka ga marasa takalma, matsiraita, talakawa, makiyayan tumaki, suna yi wa juna gasa wajen gina manyan gine-gine.
Ya ce: Sannan ya tafi, sai na zauna ɗan wani lokaci, sannan ya ce da ni: "Ya Umar, shin ka san waye mai tambayar?" Na ce: Allah da Manzonsa ne mafi sani, ya ce: "To, lallai Jibrilu ne ya zo muku don ya sanar da ku addininku".
[ASALI NA UKU]
Sanin Annabinku Muhammad ﷺ, kuma shi ne: Muhammad ɗan Abdullahi ɗan Abdul Muɗɗalib ɗan Hashim; Hashimu daga Kuraishawa ne, Kuraishawa kuma daga Larabawa ne, Larabawa kuma daga zuriyar Isma’il ɗan Ibrahim Khalil ne – tsira da aminci ya tabbata gare su da Annabin mu –.
Kuma shekarunsa sittin da uku – ciki har da shekaru arba'in kafin Annabta, da shekaru ashirin da uku a matsayin Annabi kuma Manzo.
An yi masa annabta da "Karanta", kuma aka aika shĩ da "mai lulluɓa", kuma garinsa shine Makka.
Allah Ya aiko shi da tsawatarwa daga shirka, kuma yana kira zuwa kaɗaita Allah; dalili kuwa shi ne abin da Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Yã wanda ya lulluɓa da mayãfi, 1 Ka tãshi dõmin ka yi gargaɗi2 Kuma Ubangijinka, sai ka girmama Shi, 3 Kuma tutãfinka, sai ka tsarkake su, 4 Kuma gumãka, sai ka ƙaurace musu, Kada ka yi kyauta kana nẽman ƙãri, 6. Kuma sabõda Ubangijinka? Sai ka yi haƙure, 7) [al-Mudathir: 1-7].
Kuma ma'anar Ka tsahi ka yi gargadi Yana tsoratarwa daga haɗaShi da wani a cikin bauta, kuma yana kira zuwa kaɗaita Allah.
{Kuma Ubangijinka, sai ka girmama Shi} Ma'ana: Ka girmamaShi ta hanyar kaɗaitaShi.
{Kuma tutãfinka, sai ka tsarkake shi} watau: Ka tsarkake ayyukanka daga shirka.
{Kuma gumãka, sai ka ƙaurace musu} Ar-rujzu: gumãka. Kuma ƙauracewarsu shine: barinsu, da baranta kai daga gare su da ma’abotansu.
Annabi - tsira da aminci - ya shafe shekara goma yana kiran mutane zuwa ga Tauhidi, bayan wannan goma kuwa aka Mi’iraji da shi zuwa sama, aka farlanta masa salloli biyar, ya yi sallah a Makka shekaru uku, sannan kuma aka umarce shi da yin hijira zuwa Madina.
Hijira: ciruwa (tashi) daga garin shirka zuwa garin Musulunci.
Hijira (ƙaura) wajibi ne akan wannan al'umma daga garin shirka zuwa garin Musulunci, kuma tana nan har sai alƙiyama ta tsaya.
Dalili shine: FaɗinSa Allah - Maɗaukakin sarki -: {Lalle ne, waɗanda malã'ĩku suka karɓi rãyukansu, (alhãli) sunã mãsu zãluntar kansu, sun ce (musu): 'A cikin me kuka kasance?' (Su kuma) suka ce: 'Mun kasance waɗanda aka raunana a cikin ƙasa.' Suka ce: 'Ashe ƙasar Allah ba ta kasance mayalwaciya ba, dõmin ku yi hijira a cikinta?' To, waɗannan makõmarsu Jahannama ce. Kuma tã mũnana ta zama makõma, 97. Fãce waɗanda aka raunana daga maza da mãtã da yãra waɗanda bã su iya yin wata dabãra, kuma bã su shiryuwa ga hanya, 98} [al-Nisa'a: 97-98].
Da faɗinSa Allah - Maɗaukakin sarki -: {Yã bãyiNa, waɗanda suka yi ĩmãni! Lalle fa ƙasãTa mai yalwã ce, sabãda haka ku bauta Mini, 56). [al-Ankabut: 56].
al-Bagawi - Allah Ya yi masa rahama - ya ce: "Dalilin saukar wannan ayar: Game da musulman da suke Makka ne waɗanda ba su yi hijira ba; Allah Ya kira su da sunan imani.
Dalili a kan ƙaura daga Sunnah: Faɗinsa - Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: "Hijira ba ta yankewa har sai tuba ta yanke, kuma tuba ba ta yankewa har sai rana ta ɓullo daga mafaɗarta".
Lokacin da Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya zauna a Madina, an umarce shi da sauran hukunce-hukuncen shari’ar Musulunci, kamar: Zakkah, da azimi, da hajji, da kiran sallah, da jihadi, da horo da aikin alheri, da kuma hani daga abin ƙi; sai ya kasance a kan haka tsawon shekaru goma.
Kuma - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya rasu alhali Addininsa yana nan yana wanzuwa, kuma wannan shi ne Addininsa, babu wani alheri face ya shiryar da al’ummarsa zuwa gare shi, kuma babu wani sharri face ya gargaɗe ta daga gare shi.
Kuma alherin da ya shiryar da ita a kansa shine: Tauhidi, da dukkan abin da Allah Yake so kuma Ya yarda da shi.
Kuma sharrin da Ya gargaɗe ta daga gare shi shine: Shirka, da dukkan abin da Allah - Maɗaukakin sarki - yake ƙi, kuma bai yarda da shi ba.
Allah - Maɗaukakin sarki - Ya aiko shi zuwa ga mutane baki ɗaya, kuma Ya farlanta biyayyarsa akan dukkanin aljanu da mutane; dalili kuwa shine faɗin Allah - Maɗaukakin sarki -: {Ka ce: "Yã kũ mutãne! Lalle ne nĩ manzon Allah nezuwa gare ku, gabã ɗaya...} [al-A'araf: 158].
Allah Ya cika Addini da shi; dalili kuwa shi ne faɗinSa Allah - Maɗaukakin sarki -: {...A yau Nã kammalã muku addininku, Kuma Nã cika ni'imaTa a kanku, Kuma Nã yarda da Musulunci ya zama addini a gare ku...} [al-Ma'ida: 3].
Dalili a kan mutuwarsa: Faɗinsa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Lalle kai mai mutuwa ne, kuma su mã lalle mãsu mutuwa ne, 30. Sa'an nan, lalle kũ, a Rãnar kiyãma, a wurin Ubangijinku, zã ku yi ta yin husũma, 31). [al-Zumar: 30-31].
Kuma mutane idan sun mutu za a tashe su; hujja kuwa ita ce cewa Allah - Allah Madaukakin Sarki - Ya ce: {Daga gare ta Muka halitta ku, kuma a cikinta Muke mayar da ku, kuma daga gare ta Muke fitar da ku a wani lõkaci na dabam, 55} [Ɗaha: 55], da faɗinSa Allah - Maɗaukakin sarki -: {Kuma Allah Ya tsirar da ku daga ƙasa (kamar ganye) tsirarwa, 17. Sa'an nan Ya mayar da ku a cikinta, kuma Ya fitar da ku fitarwa, 18} [Nuhu: 17-18].
Bayan tashin Kiyama za a yi musu hisabi, kuma a yi musu sakayya akan ayyukansu; kuma hujja ita ce fadinSa Allah - Maɗaukakin sarki -: {...dõmin Yã sãka wa waɗanda suka mũnana da abin da suka aikata, kuma Ya sãka wa waɗanda suki kyautata da sakamakon da ya fi kyau} [al-Najm: 31].
Kuma wanda ya ƙaryata tashi (bayan mutuwa) ya kafirta; dalili kuwa faɗinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Waɗanda suka kãfirta sun riya cẽwa bã zã a tãyar da su ba. Ka ce: "Ni, inã rantsuwa da Ubangijĩna. Lalle zã a tãyar da ku haƙĩƙatan, sa'an nan kuma lalle anã bã ku lãbãri game da abin da kuka aikata. Kuma wannan ga Allah mai sauƙi ne, 7} [at-Tagabun: 7].
Kuma Allah Ya aiko dukkan Manzanni masu bayar da bushara kuma masu gargaɗi; dalili kuwa shi ne fadinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Manzanni mãsu bãyar da bushãra kuma mãsu gargaɗi dõmin kada wata hujja ta kasance ga mutãne a kan Allah bãyan Manzannin...} [al-Nisa'a: 165].
Na farkon su shi ne (Annabi) Nuhu - amincin Allah ya tabbata a gare shi -.
Na ƙarshensu shi ne (Annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, shi ne cikamakin Annabawa; babu wani Annabi a bayansa; dalili shi ne faɗinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Muhammadu bai kasance uban kõwa ba daga mazanku, kuma amma shĩ yã kasance Manzon Allah kuma cikon Annabãwa...} [al-Ahzab: 40].
Dalili a kan cewa na farkonsu shi ne Nuhu: Faɗinsa - Maɗaukakin sarki -: {Lalle ne Mu, Mun yi wahayi zuwa gare ka, kamar yadda Muka yi wahayi zuwa ga Nũhu da annabãwa daga bãyansa...} [al-Nisa'a: 163].
Kowacce al’umma Allah Ya aika mata da Manzo - tun daga (Annabi) Nuhu har zuwa (Annabi) Muhammad - aminci ya tabbata agare su -, yana umartar su da bautawa Allah Shi kaɗai, kuma yana hanasu bautawa Ɗagutu; dalili shi ne fadinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun aika a cikin kõwacce al'umma da wani Manzo (ya ce): 'Ku bauta wa Allah, kuma ku nĩsanci Ɗãgũtu...} [al-Nahl: 36].
Allah Ya farlanta a kan dukkan bayinSa: kafircewa ɗagutu, da kuma imani da Allah.
Imam Ibnul Kayyim - Allah Ya yi masa rahama - Ya ce: "Ma'anar ɗagutu ita ce: Abin da bawa zai ƙetare iyaka da shi daga abin bauta, ko wanda ake bi, ko wanda ake wa biyayya".
Ɗagutai suna da yawa, kuma shugabanninsu guda biyar ne: Iblis - La’anar Allah ta tabbata a kansa, da wanda aka bauta masa alhali yana mai yarda, da wanda ya kira mutane zuwa ga bauta wa kansa, da wanda ya yi iƙirarin sanin wani abu daga ilimin gaibi, da kuma wanda ya yi hukunci da abin da Allah bai saukar da shi ba.
dalili: FaɗinSa Allah - Maɗaukakin sarki -: {Bãbu tĩlastãwa a cikin addini, haƙĩƙa shiriya tã bayyana daga ɓata; Sabõda haka wanda ya kãfirta da ¦ãgũta kuma ya yi ĩmãni da Allah, to, haƙĩƙa, yã yi riƙo ga igiya amintacciya, bãbu yankẽwa agare ta. Kuma Allah Mai ji ne, Masani25} [al-Baƙara: 256], Wannan ita ce ma'anar "Babu abin bautawa da cancanta sai Allah", kuma ya zo a cikin Hadisi: "Asalin al’amari: Musulunci, ginshiƙinsa: Sallah, kuma ƙololuwar tozansa: yin yaƙi a cikin tafarkin Allah".
Allah shi ne Mafi sani.