موسوعة الإيمان
كتاب "الإيمان الذي فرضه الله على عباده مما ورد في القرآن الكريم والسنة النبوية" من تأليف أ.د. محمد بن عبد الله السحيم ود. سامي بن محمد الخليل، هو كتاب شامل لجميع أصول ومهمات الاعتقاد ومسائله. يتميز الكتاب بربط المسائل العقدية بالكتاب الكريم والسنة النبوية المطهرة، ويحرص على تأسيس العقيدة بطريقة مختصرة وشاملة باستخدام عبارات ميسرة. يتناول الكتاب مسائل الاعتقاد بعيداً عن المباحث الكلامية والفلسفية، ويهدف إلى تقديم موضوعات الاعتقاد بأسلوب يسهل على جميع المستويات العلمية فهمها واستيعابها.
BAKANDAMIYAR IMANI WANDA ALLAH YA WAJABTASHI AKAN BAYINSA NA ABINDA YA ZO A ACIKIN ALKUR'ANI MAI GIRMA DA SUNNAR ANNABI
(Wani kundi ne da ya tattaro tushe da muhimman AKIDAH da mas'alolinta, ya yi fice wurin alaƙanta mas'aloli na aƙida da AlKur'ani mai girma da Sunnar Annabi mai tsarki, tare da kwaɗayi akan dasa AKIDAH ta taƙaitacciyar hanya kuma gamammiya, daidai da sauƙaƙan jumloli a tsakiyar bayani, da bayyanin mas'alolin ƙudircewa, tare da tsaftace Bakandamiyar daga bincike-bincike na ilimin zance da kuma falsafa).
A gabanin shiga Kundin
Da sunan Allah Mai Rahama Mai jin ƙai
Godiya ta tabbata ga Allah Wanda Ya saukar da littafi ga bawanSa, bai sanya karkata a gare shi ba, ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Shi kadai Yake ba Shi da abokin tarayya, mulki naSa ne, kuma godiya ta tabbata gareShi, Shi Mai iko ne akan dukkan komai, ina shaidawa cewa (Annabi) Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa ne kuma amintaccenSa ne akan wahayinSa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -.
Bayan haka: Lallai ilimin Akida shi ne mafi daukakar ilimai kuma mafi girmansu; domin shi yana magana ne ga mafi daukakar abin sani - shi ne Allah tsarki ya tabbatar maSa -, kuma mafi daukakar abin nufi - shi ne kadaitaShi da yin imani da Shi - kuma mafi daukakar makoma - shi ne ganin Ubangiji Mai girma a gidan ni'ima, da bin Annabi mai girma - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, da bin hanya madaidaiciya; saboda haka muka yi kwadayi mu wallafa wani littafi wanda ya tattaro mas'alolin Akida wanda muke neman shiriya da shi a cikinsa da littafin Allah, da sunnar AnnabinSa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi, wanda ya yi nesa daga zantukan ma'abota zance fararru, da Ta'arifai da Rukunai da Sharudda, kuma zamu sanya shi a hannun kowa ta inda malami da dalibain ilimi a jami'o'i da waninsu zasu amfana daga gare shi , kai dama dukkan musulmai.
Dalilin wallafa littafin:
Hakika magabatamu na gari sun yi babban kokari a bayanin ingantacciyar Akidah, da kuma bayanin abinda yake kishiyantarta, da yin raddi ga wadanda suka saba. Hakika wannan littafin ya zo dan ya kusanto da abinda magabata suka wallafa ga daliban ilimi dama dukkanin musulmai; ta inda muka hado mas'alolin Akidah a cikin littafi daya wanda ya tattarosu, mun takaita tabbatar da ingantacciyar Akida banda kutsawa a cikin raddi, kamar yadda muka yi kwaɗayi akan yinsa da saukakan haruffa bayyanannu, da kuma jeranta shi irin na tsari mai ban kaye, muna fatan mu kasance da hakan mun tabbatar da manufofi biyu: Na dayansu: Bada gudunmawa a cikin kusanto da ilimummukan magabata. na karshen kuma: toshe bukata mai tsanani a dakin karatun Akidah, ita ce: Samar da sassaukan littafi mai sassaukan lafuzza, wanda ya tattaro dukkan bincike-binciken Akidah.
Tsarin da muka bi a wallafawar:
Bijiro da ayoyi da hadisan da suke da alaka da kowanne bangare daga bangarorin karatun Akidah, da tato shi daga garesu.
Bijiro da dukkanin bangarorin littattafan Akidu: Duk daya ne masu isnadi ne ko kuma gundarin abubuwa ko sharhohin matanin; dan tabbatar da cewa rairayowar da muka yi ga Akida daga ayoyi ne da kuma hadisai, kuma mai kunshe ne ga abinda mawallafan littattafan Akida suka wallafa.
Idan mas'ala ta akida ta zo a cikin AlKur'ani mai girma, ko a sunnar Annabi ta fuska daya; zamu isu da dalili daya ko dalilai biyu wanda ya zo a ambaton wannan mas'alar a cikinsu. Amma idan mas'ala ta zo a cikin AlKur'ani mai girma ko sunnar Annabi ta fuskoki da yawa - kamar siffar zance, da daukaka sama, da hannu, da ganin muminai ga Ubangijinsu a farfajiyar Alkiyama da kuma aljanna - to zamu lazimci ambaton dalili ta kowacce fuska daga fuskokin da suka zo, amma ba zamu lazimci kawo dukkan abinda ke cikin babinba.
Zamu iya bukatuwa da kawo sashin bangarorin mas'ala a wani babin, sannan mu sake kawota mu kuma cikata a wani babin daban, kamar yadda muka zo da labarin halittar Mala'iku a babin halitta, kuma muka cike zancen game da su a cikin babin imani da Mala'iku, muka ambaci wasu ayoyi masu nuni ta fuskoki (da dama) a cikin babin imani da samuwar Allah, kuma ita kanta ayar zata iya zuwa ababin Rubibiyya dan kusancinsu, abin nufi daga babin imani da samuwar Allah shi ne bayyanar da dalilan samuwar Ubangiji wadanda mai musun samuwar Allah Yake inkarinsu, yayin da abin nufi daga babin Rububiyya shi ne tabbatar da Rububiyya wacce ta lazimci Uluhiyyar Allah wacce mushrikai suke jayayya a cikinta, kamar yadda zamu iya kawo ayoyi masu girma ko hadisi madaukaki a cikin sama da guri daya, gwargwadan fuskar kafa hujja da su, da kuma bukatuwa zuwa garesu.
Yayin bukatuwa zamu iya ambatan wasu abinda aka cirato daga jagorori magabata wadanda suke bayyanar da abin nufi daga aya da kuma hadisi, kuma zamu takaita akan abinda yake bayyanar da gaskiya a cikinsu, ba tare da kawo shubuha ko zancen wanda ya saba ba; dan kada mai neman ilimi ya dauki shubuhar ko ya karkata ga maganganun wadanda suka saba kafin ya samu damar tabbatar da wannan ilimin a zuciyarsa da kuma fahimtarsa. Muna fatan mai karatu ya samu kariya daga tuntube a wannan mas'alar; saboda abinda yake kewaye da ita na sabanin akida da ya shahara, kamar mas'alolin siffofi, da kaddara, da wasunsu.
Ibnu Abi Zamanin Bamalike ne - Allah Ya yi masa rahama - ya ce: (Haƙiƙa na sanar da kai da faɗin shugabannin shiriya da ma'abota ilimi a cikin abinda ka yi tambaya game da shi, dama wanin hakan daga abinda ake tambaya game da shi daga tushen Sunnar da kuma ma'abota soye-soyen zuciya masu ɓatarwa suka saɓawa Littafin Allah da Sunnar annabinSa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, da badan a ce manyan malamai suna ƙin a rubuta wani abu daga zancensu ba a dawwamar da shi a cikin wani littafi ba, da na baka labari akan karkatarsu da kuma ɓatansu daga abinda zai ƙara maka kwaɗayin guje musu, muna neman tsarin Allah daga fitinarsu, Allah Ya tsaremu da kai daga fitintinu masu bayarwa, kuma Ya datar da mu ga abinda Yake yardar da shi a fada da kujma aiki, kuma Ya kusanto mu gareShi kusanci-kusanci). Usulus Sunnah na Ibnu Abi zamanin (shafi na 309, 310).
Da gangan mun nisanci ta'arifai da irin yarukan ma'abota zance fararru wadanda Allah bai saukar da wata hujja ba gare su.
Mun sanya littafin akan yanayin Kundi da babuka, kamar yadda mawallafa na farko suka aikata a ilimin shari'a, ba mu yi amfani da rabe-raben mutanen zamani ba; Mabhas da madlab, kuma mun jera shi akan tushen imani. Ibnu Abin izz al-hanafi ya ce: (mafi kyan abinda za'a jeranta littafin tushen Addini shi ne a jeranta akan amsawar da Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ba (Mala’ika) Jibril - aminci ya tabbata agare shi - lokacin da ya tambaye shi game da imani, sai ya ce: "ka bada gaskiya da Allah da mala'ikunSa..." Sai ya fara da magana akan Tauhidi da siffofi da abinda yake da alaka da hakan, sannan magana akan Mala'iku, sannan har dai zuwa karshe). (Sharhin Akidar Dahawiyya (2/689).)
Mun yi kokarin rairaya ga kowanne Kundi a farkonsa , zamu kawo dukkanin mas'alolin Kundin a cikinsa ba tare da dalilai ba.
A abinda ya kebanci fitar da hadisai, hakika mun yi kokarin fitar da su a takaice, muna farawa da littattafan nan shida a tsarin jerinsu da aka sani, sannan mu jerasu gwargwadan rasuwa, saboda kwadayinmu na gajarta girman littafin, hakika mun wadatu da fitar da hadisan ba tare da magana akan hadisan ba sai a mafi kuncin guri.
Abinda wannan littafin ya kebanta da shi:
Alakanta mas'alolin akida da AlKur'ani mai girma da Sunnar Annabi mai tsarki, ta inda rikon wadannan mas'alolin zai zama a bayyane baro-baro ga dalibi.
Zuzzurfan bincike da mas'alolin Akida da suke manya masu alaka da kowanne babi daga babukan Akida.
Kwadayi akan dasa akida ta takaitacciyar hanya kuma mai tattarowa daidai da sassaukan harshe a lokacin bayani da bayyana mas'alolin Akida; har hakan ya zama mafi saukin fahimta da gamewa.
Tsaftatar littafin daga bincike-binciken zancen ma'abota zance da falsafa, da kusanto da ibarorinsa, da nisanta daga lafuzan da suka zo a wasu daga littattafan Akidah bayan bayyanar soye-soyen rai.
Bama da'awar cewa mu mun nitsa sosai a mas'alolin Akidah; saidai cewa mu mun yi iya kokarinmu a hakan, kuma muna masu jiran dukkanin wani gyara ga wannan littafin ko daidaita shi ko karin haske; har mu amfana daga gareshi awasu bugu na littafin masu zuwa. Ya ishemu cewa mu mun gangaro magangarar wahayi, mun yi kokarin fitar da sakamakon daga gare shi na ayyukan mafi daukakar ilimai, mun gabatar da su zuwa ga daliban wannan fannin muna masu kafa hujja ga kowacce mas'ala da aya ko hadisi ko biyun gaba daya. Muna rokon Allah Ya sanya wannan aikin saboda Allah ne Mai girma, kuma mai dacewa da Sunnar Annabinsa kuma badadinSa kuma amintaccenSa akan wahayinSa, ya zama mai anfanar da bayinSa, kuma mai hujja mai shaida garemu ranar da zamu hadu da Ubangijinmu.
Kuma muna godiya ga Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya daukaka - wanda Ya sawwaka mana wannan ilimin, Ya kuma hore mana hidimar AddininSa, Ya shinfida mas'alolin rukunan imani da Allah, da bayaninsu da kuma ambatan dalilansu daga AlKur'ani da Sunnah.
Kuma muna godewa dukkan wanda ya kyautata mana, mafi cancantar mutane da godiya su ne mahaifanmu, to Ya Allah Ka gafarta musu Ka jikansu Ka yi musu sakayya saboda mu da abinda kake sakawa mahaifi ga dansa.
Sannan muna godiya ga manyan malamai waɗanda suka duba littafin kuma suka gabatar da tsokacinsu da gyararraki masu albarka sune: Yarima DR. Sa'ud Ibnu Salman Ibnu Muhammad al-Sa'ud, babban malamin Aƙida (Kuma Farfesa) a Jami'ar sarki Sa'ud, da DR. Sahl Ibnu Rifa al-Itaibi, babban malamin Aƙida (Kuma Farfesa) a Jami'ar Sarki Sa'ud. Da farfesa Abdullah Dan Saleh al-Barrak, malamin Akidah a Jami'ar Sarki Sa'ud, da DR. Abdullah Dan Abdul'aziz al-Angari, malamin akida matemakin farfesa a matsayin jami'a a jami'ar sarki Sa'ud, muna rokon Allah Ya saka musu da mu dama ilimi da ma'abotansa mafificin sakamako, sakamakon abinda suka gabatar na tatacciyar nasiha da madaidaicin ra'ayi.
Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai, Allah Ya yi dadin tsira ya yi aminci ya yi albarka ga mafificin halittatrSa, aminci ya tabbata ga alayensa da sahabbansa baki daya.
Makka abar girmamawa
Rana ta takwas ga Zul-hijja
A shekara ta dubu da dari hudu da talatin da tara daga hijirar Annabi.
Gabatarwa
Da sunan Allah Mai Rahama Mai jin ƙai.
Da shi ne muke neman taimako, kuma babu dabara da karfi sai na Allah Madauki kuma Mai Girma
Godiya ta tabbata ga Allah kamar yadda yake kamata ga girman zatinSa da kuma girman sarautarSa, ina shaida cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah Shi kadai yake ba Shi da abokin tarayya, mulki nasa ne, godiya ta tabbata gareShi, Shi mai iko ne abisa dukkan komai, kuma ina shaidawa cewa (Annabi) Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa ne - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi amnici mai yawa -, bayan haka:
Wannan wani littafi ne wanda a cikinsa zamu ambaci abinda imani da shi yake wajaba akan musulmi, daga abinda ya zo a cikin AlKur'ani da Sunnah, zamu iya ambatan wasu daga maganganun sahabbai da tabi'ai da masu biye musu, a sharhin aya ko hadisi, ko dan zuwa da wata maganar da zata iyakance abin nufi daga ayar ko hadi Hakika mun raba shi zuwa Kundaye da babuka, kuma mun lazimci takaitawa a cikinsa gwargwdan iko, da takaituwa akan mas'alolin da suka lazimta, mun nisanci kutsawa cikin abinda mutanen ’yan baya suka kutsa na maganganun da ba su zo a cikin AlKur'ani da hadisin Annabi - tsira da amincin su tabbata ga ama'abocinta da kuma mafi cikar sallama, Allah - mai girma da daukaka - yana cewa yana mai kwadaitarwa akan bin AddininSa, da riko da igiyarSa, da koyi da manzonSa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: {Kuma ku yi daidami da igiyar Allah gabã ɗaya, kuma kada ku rarraba. Kuma ku tuna ni'imar Allah a kanku a lõkacin da kuka kasance maƙiya sai Ya sanya sõyayya a tsakãnin zukãtanku sabõda haka kuka wãyi gari, da ni'imarSa, 'yan'uwa. Kuma kun kasance a kan gãɓar rãmi na wutã sai Ya tsãmar da ku daga gare ta, Kamar wannan ne Allah Yake bayyana muku ayõyinSa, tsammãninku, zã ku shiryu} [Aal-Imran: 103]. Allah - Mai tsarki da daukaka - Ya ce {Kuma ku bi mafi kyawun abin da aka saukar zuwa gare ku daga Ubangijinku, a gabãnin azãba ta zo muku, bisa auke, kuma kũ ba ku sani ba} [al-Zumar: 55].
Muna cewa - muna neman dacewa daga wurin Allah:
KUNDIN FARKON HALITTA
RAIRAYO ABINDA KE CIKIN KUNDIN
Muna imani cewa Allah Shi ne Mahaliccin komai, kuma Allah Ya kasance alhali babu wani abu da ya kasance, babu wani abu kafinSa, Al'arshinSa ya kasance akan ruwa, Ya halicci ruwa kafin Ya halicci sama da kasa, sannan Ya halicci sammai da kasa, alhali sun kasance da a manne sai Ya budesu.
Kuma muna imani cewa Allah Ya sanya wannan halittar mai shaida akan RubibiyyarSa mai lazimtar da UluhiyyayrSa, Shi ne Mahalicci na Gaskiya, wanda ba Shi ba to abin halitta ne - Ubangijinmu - alherinSa ya yawaita kuma Ya daukaka - Shi ne Allah na Gaskiya, wanda ba Shi ba bawa ne bai cancanci a bauta maSa ba, ko ayi kwadayi a gurinsa, ko a yi nufi gare shi.
Muna imani cewa Al'arshi mai girma halitta ne mai girma daga halittar Allah, kai shi ne mafi girman ababen halittarSa.
Muna imani da cewa Mala'iku sun kewaye Al'arshin Allah Mai yawan rahama ne, kuma cewa Allah - alherinSa ya yawaita kuma Ya daukaka - Yana saman Al'arshinSa, a saman sammanSa, Ya nisanta da halittatrSa.
Kuma muna imani cewa Allah Ya halicci alkalamin da ya rubuta abin kadarawar kowanne abu, kuma alkaluman kaddarawa masu yawa ne.
Muna imani cewa Allah Ya halicci Kursiyyi, shi ne mafi girman ababen halitta bayan Al'arshi.
Kuma muna imani cewa Allah Ya halicci sammai da kasa da abinda ke tsakaninsu a kwana shida daga kwanakun Allah, kuma cewa Allah Ya daga sammai ba tare da ginshiki ba, kuma Allah Ya halicci wadannan ababen halittar masu girma dan wasu hikimomi masu girma wadanda ba'a kewaye sani da su, hakika Allah Ya kyautata halittarsu da kuma aikatasu.
Muna imani cewa wannan duniyar da sammanta da kassanta da duwatsunta, kai da dukkan abinda ke cikinta zai zama wani hali na daban a ranar alKiyama.
Muna imani cewa Allah Ya halicci rana da wata da gaskiya, kuma Shi - tsarki ya tabbatar maSa Ya daukaka - Ya sanya su ababen horewa da umarninSa, kuma Ya halicci taurari dan wasu hikimomi masu girma, kuma cewa taurari ba sa anfanarwa ba sa cutarwa, kuma ba sa tasiri a faruwar wani abu a sammai da kassai, duk wanda ya kudirce cewa su suna tasiri da kansu to hakika ya kafirta, ko ya yi shirka.
Muna imani cewa Allah Ya halicci Mala'iku daga haske, kuma Ya sanya su masu ban-banta da Juna a halitta.
Muna imani cewa Allah Ya halicci aljanu daga tartsatsi na wuta, kuma halittar aljani ta riga halittar (Annabi) Adam, kuma cewa shugaban Shaidanu shi ne Iblis, kuma cewa shi shi ne wanda ya rudar da iyaye biyu (Adam da Hauwa'u) - aminci ya tabbata agare su - har ya fitar da su daga aljanna.
Muna imani cewa Iblis ya yi girman kai daga sujjada, sai Allah Ya yi fushi da shi, Ya la'ance shi, Ya kore shi, kuma aljanu ababen yi wa maganane da bin shari'u, kuma ababen dorawa shari'a ne.
Muna imani cewa Allah Ya bai wa Mala'ikunSa labarin cewa Shi zai sanya Halifa a kasa, dan rayata da ibada. Kuma Allah Ya bayyana cewa wannan Halifan shi ne (Annabi) Adam, kuma cewa shi Zai halicce shi ne daga turbaya, wannan turbayar Allah Ya sanyata tabo, sannan Ya halicce shi mataki bayan mataki.
Muna imani cewa Allah Ya halicci (Annabi) Adam da hannunSa Madaukaki, kuma Ya sanya Mala'ikunSa su yi masa sujjada, kuma Ya halittar masa mata daga jikinsa dan ya natsu da ita, ita ce Hawwa'u, Ya zaunar da su a aljanna, sannan Ya sakko da su kasa.
Muna imani cewa mutane gabadayansu daga zurriyar (Annabi) Adam ne, kuma (Annabi) Adam daga turbaya yake, babu fifiko ga wani akan wani sai da tsoron Allah.
Muna shaida cewa Allah Ya halicci mutane akan madaidaiciyar dabi'a.
Muna imani cewa rai daga al'amarin Allah ne, kuma mutane ba sa sanin wani abu daga sha'anin rai, sai dai abinda Allah Ya tsinkayar da su akansa, kuma rayuka Allah ne Ya haliccesu.
Muna imani cewa rayuka za su mutu, mutuwarsu kuwa ita ce rabuwa da jiki.
Muna imani cewa dukkan abinda yake tafiya akan kasa na dabba ne to wasu al'ummatai ne kwatankwacinmu.
Muna sanin cewa Allah Ya halicci kowacce dabba daga ruwa, kuma Ya sanya jinsi biyu namiji da mace a kowanne abu, dukkanin wadannan ababen halittar za su halaka sai dai abinda Allah - Mai girma da daukaka - Ya togace shi.
BABIN: ALLAH NE MAHALICCIN KOWANNE ABU
Muna shaidawa Allah ne Mahaliccin kowanne abu, Allah - Madaukakin sarki - Ya ce: {Wancan ne Allah Ubangijinku. Bãbu wani abin bautãwa fãce Shĩ, Mahaliccin dukan kõme. Sabõda haka ku bauta Masa kuma Shi ne wakĩli a kan dukan, kõme} [al-An'am: 102]. Allah Madaukaki ya ce: {Allah ne Mai halitta dukkanin kõme, kuma Shĩ ne Wakĩli a kan kõme} [al-Zumar: 62]. Tsarki ya tabbatar maSa Ya ce: {Kuma Shi ne wanda Yake fara yin halitta sannan Ya dawo da ita, kuma (dawowar) ta fi sauki a gare Shi} [al-Rum: 27].
Muna imani cewa Allah Ya kasance alhali babu wani abu waninSa, kuma babu wani abu kafinSa, Allah - tsarki ya tabbatar maSa - Ya ce: {Shĩ ne Na farko, Na ƙarshe, Bayyananne, Bõyayye, kuma Shĩ Masani ne ga dukkan kõme} [al-Hadid: 3].
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Ya Allah Kaine na farko babu wani abu kafinKa, kaine na karshe babu wani abu bayanKa, kaine zahiri babu wani abu birbishinKa, kaine badini babu wani abu koma bayanKa". (Muslim ne ya fitar dashi (2713), da Abu Dawud (5051), da Tirmizi (3400), da Ibnu Majah (3831).
Daga Imran dan Husain - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Ni ina wajen Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yayin da wasu mutane daga Banu Tamim suka zo , sai ya ce: "Ku karbi bushara yaku Banu Tamim", suka ce: Ka yi mana bushara to ka bamu. Sai wasu muta daga mutanen Yaman suka shigo, sai ya ce: "Ku karbi bushara ya ku mutanen Yaman, dan Banu Tamim ba su karbeta ba" sai suka ce: Mun karba, mun zo maka dan mu fahimci Addini, kuma dan mu tambayeka daga farkon al'amari: Meye ya kasance? sai ya ce: "Allah Ya kasance alhali babu wani abu kafinsa, kuma Al'arshinSa ya kasance akan ruwa, sannan ya halicci sammai da kassai, ya kuma rubuta kowanne abu a cikin Lauhul Mahfuz. (Bukhari ne (7418), da Tirmizi (3951).) suka ruwaito. A wata riwayar da lafazin: "Allah Ya kasance alhali babu wani abu waninSa, Al'arshinSa ya kasance akan ruwa". (Bukhari ne ya fitar da shi (3191)).
Muna imani cewa dukkan abinda ke tafiya a bayan kasa na dabba to su al'ummataine kwatankwacinmu, Allah - Madaukaki - Ya ce: {Kuma bãbu wata dabba a cikin ƙasa kuma bãbu wani tsuntsu wanda yake tashi da fukafukinsa fãce al'umma ne misãlanku. Ba Mu bar (bayanin) kõme ba a cikin Littãfi, sannan kuma zuwa ga Ubangjinsu ake tãra su} [al-An'am: 38]. Kuma muna sanin cewa Allah Ya halicci kowacce dabba daga ruwa, Allah - tsarki ya tabbatar maSa - Ya ce: {Kuma Allah ne Ya halicci kõwacce dabba daga ruwa. To, daga cikinsu akwai waɗanda ke tafiya a kan cikinsu, kuma daga cikinsu akwai waɗanda ke tafiya a kan ƙafãfu biyu, kuma daga cikinsu akwai waɗanda ke tafiya akan huɗu. Allah Yãna halitta abin da Yake so, lalle Allah, a kan kõwanne abu, Mai ĩkon yi ne} [al-Nur: 45]. Kuma Ya sanya jinsi biyu (mace da namiji) a kowanne abu, Allah - Madaukakin sarki - Ya ce: {Kuma daga kõme Mun halitta nau'i biyu, watakila zã ku yi tunãni} [al-Zariyat: 49]. Kuma Allah - Madaukaki - ya ce: {Kuma lalle Shĩ ne Ya yi halitta nau'i-nau'i, namiji da mace}. [al-Najm: 45].
Muna imani cewa wannan halittar - duk da rabe-rabensu da yawansu - a daidai suke, wani abu Ba zai yi shisshigi daga gare su akan wani abu ba, ko wani nau'i akan wani nau'i ba, Allah - Madaukaki - Ya ce: {Kuma ƙasa Mun mĩkẽ ta kuma Mun jẽfa duwãtsu tabbatattu a cikinta kuma Mun tsirar a cikinta, daga dukkan abu wanda ake aunãwa da sikẽli} [al-Hijr: 19].
Dukkanin wadannan abubuwan na halitta zasu kare, Allah - Madaukakin sarki - Ya ce: {Dukkan wanda ke kanta mai ƙãrẽwa ne * Kuma Fuskarar Ubangijinka, Mai girman Jalala da karimci, ita ce take wanzuwa} [al-Rahman: 26-27]. Sai wanda Allah Ya togance shi daga mutuwa a cikin fadinSa - Madaukakin sarki -: {Kuma aka busa a cikin ƙaho, sai waɗanda ke a cikin sammai da ƙasã suka sũma sai wanda Allah Ya so (rashin sumansa) sannan aka hũra a cikinsa, wata hũrãwa, sai gã su tsaitsaye, sunã kallo} [al-Zumar: 68].
Muna imani cewa Allah Ya sanya wannan halittar ta zama mai shaida akan RubibiyyarSa wacce ta lazimci UluhiyyarSa, wani lokaci Yana sanya halittarSa ga wannan halittar mai nuni a kan hakan, kamar yadda yake a cikin faɗinSa - Maɗaukakin sarki - {Wannan shĩ ne halittar Allah. To ku nũna mini, "Mẽne ne waɗanan da ba Shi ba suka halitta? Ã'a, azzalumai sunã a cikin ɓata bayyananna} [Luƙman: 11]. Wani lokaci Allah Yana ambatan cewa mafi girman abin halitta a cikin su - Shi ne Al’arshi - mai nuni ne akan hakan kamar yadda yake a cikin faɗin Allah - tsarki ya tabbatar maSa -: {Allah bãbu abin bautãwa fãce shĩ Ubangijin Al'arshi, mai girma} [al-Naml: 26]. Kuma Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Tsarki ya tabbata ga Allah gwargwadon adadin halittarSa. Tsarki ya tabbata ga Allah adadin yardar kanSa. Tsarki ya tabbata ga Allah nau'yin Al'arshinsa. Tsarki ya tabbata ga Allah adadin tawadar rubuta kalmominSa". (Muslim ya fitar da shi (2726), da Nasa'i (1351/1), da Tirmizi (3555), da Ibnu Majah (3808). To nauyin al'arshi shi ne mafi nauyin ma'aunai. Wani lokaci kuma Yana sanya ababen halitta masu girma dalili akan hakan, kamar yadda yake a cikin fadinSa - Madaukakin sarki -: {Shi ne Wanda Ya halitta muku abin da ke a cikin ƙasa gaba ɗaya, sannan kuma Ya daidaita zuwa sama,sannan Ya daidaita su sammai bakwai. Kuma Shi ga dukkan kõmai Masani ne} [al-Baƙara: 29]. Wani lokaci kuma Yana sanya wani abu ɗaya daga ɗaiɗaikun waɗannan halittun dalili ne akan hakan, kamar yadda yake a cikin faɗinSa - tsarki ya tabbatar maSa -: {Ba ka gani ba, lalle Allah Ya saukar da ruwa daga sama? Sai Muka fitar, game da shi yã'yan itãce mãsu sãɓanin launuka kuma daga duwatsu akwai zane-zane, farfaru da jãjãye, mãsu sãɓanin launin, da mãsu launin baƙin ƙarfe, baƙãƙe} [Faɗir: 27].
Wani lokaci Yana sanya mafi raunin abin halitta kuma mafi ƙanƙantarsa dalili akan hakan, kamar yadda yake a cikin faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Lallai ne Allah ba Ya jin kunyar Ya bayyana wani misali, kowanne iri ne, sauro da abinda yake bisa gare shi. To, amma waɗanda suka yi imani, sai su san cewa lallai shi ne gaskiya daga Ubangijinsu, amma waɗanda suka kafirta, sai su ce: "Menene Allah Ya yi nufi da wannan ya zama misali?} [al-Baƙara: 26]. Shi ne Mahalicci na Gaskiya, wanda ba Shi ba to halittarsa aka yi - Ubangijinmu alherinSa ya yawaita Ya daukaka -, Shi ne Allah na Gaskiya, wanda ba Shi ba to abin halitta ne, ba ya cancantar abauta masa ko a yi kwadayi gareshi, ko a nuface shi.
BABIN HALITTAR AL’ARSHI MAI GIRMA
Muna imani cewa Al'arshi halitta ne mai girma daga halittun Allah, kai shi yana daga mafi girman halittarSa, idan Mai girma Ya siffanta shi da cewa shi mai girma ne to shi - haƙiƙa - mai girma ne, sai tsarki ya tabbatar maSa ya ce: {Allah bãbu abin bautãwa fãce shĩ Ubangijin Al'arshi, mai girma} [al-Naml: 26]. Kuma Ya siffanta shi da cewa shi mai girma ne, sai Allah - sha'anin Sa ya daukaka - Ya ce: {Mai Al'arshi mai girma} [al-Buruj: 15]. Ibnu jarir - Allah Ya yi masa rahama - Ya faɗa a cikin tafsirinsa: (Makaranta sun yi saɓani a kan karanta faɗinSa: (Almajid) sai gabadayan makarantan Madina da Makka da Basra da wasu daga mutanen Kufa suka karanta shi da Rufu'ah (Almajidu) dan bada amsa akan faɗinSa: (Zul'arshi) akan cewa shi yana daga siffar Allah - ambatanSa ya ɗaukaka -. Kuma gamewar makarantan Kufa sun karanta da wasali ƙasa (Almajidi), akan cewa shi yana daga siffar al'arshi. Amma magana ta daidai a cikin hakan a wurinmu cewa su ƙira'o'i ne guda biyu sanannu, kowacce daga cikinsu mai karatu ya karanta to ya dace. Jami'ul Bayan (24/346). Shi tare da girmansa halittarsa aka yi bawa ne, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Ka ce: "Wãne ne Ubangijin sammai bakwai kuma Ubangijin Al'arshi mai girma} [al-Muminun: 86]. kuma Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "...Kuma Ya halicci Al'arshinSa akan ruwa} (Tirmizi ya fitar da shi (3109), da Ibnu Majah (182), da Dayalisi (1189), da Ahmad (16188), da Ibnu abi Asim a cikin Sunnah (625).) Kuma yana da ginshiƙai: Tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Mutane zasu suma a ranar alKiyama, sai in zama ni ne farkon wanda zai farka, sai ga ni da (Annabi) Musa yana mai riƙe da ginshi daga ginshiƙen Al'arshi". (Bukharine ya fitar da shi (3398), da Muslim (2374), da Abu Dawud (4668).)
Al'arshi a samman sammai yake, Allah kuma Yana saman Al'arshi, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Lallai Al'arshinSa yana kan sammanSa, kuma ya aikata da ɗanyatsansa kwatankwacin ƙubba akansa - kuma cewa shi yana nauyi daShi nauyin sirdi da mahayi". (Abu Daud ya fitar da shi (4726), da Usman Ibnu Sa'id al-Darimi a cikin raddi ga Jahamiyya (24), da Ibnu Abi Asim a cikin sunnah (587), da Ibnu Kuzaimah a cikin Tauhid (147).) A cikin wata riwayar: "Lallai cewa Allah Yana saman Al'arshinSa, kuma Al'arshinSa yana saman sammanSa". (Abu Daud ya fitar da shi (4726), da Usman Ibnu Sa'id al-Darimi a cikin raddi ga Jahamiyya (24), da Ibnu Abi Asim a cikin sunnah (587), da Ibnu Kuzaimah a cikin Tauhid (147).)
Muna imani cewa ƙarƙashin Al'arshi akwai taskokin Ubangiji babu wanda zai iya ƙaddar ikonsa sai Allah, haƙiƙa tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "An ba ni waɗannan ayoyin na ƙarshen Baƙara daga wata taska ƙarƙashin Al'arshi, ba'a bawa wani Annabi kafin ni ba". (Muslim ya fitar da shi (522) banda gurin mai shaidar, da al-Dayalisi (418), da Ibnu Abi Shaiba a cikin al-Musannaf (32306), da Ahmad (23251), kuma lafazin nasa ne. Da wasunsu).
A cikin Hadisin Abu Zarrin - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Badaɗayina - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya umarce ni da abubuwa bakwai, sai ya ambata daga cikinsu: "Ya umarceni da in yawaita faɗin: Babu dabara babu ƙarfi sai ga Allah, su suna daga taska ƙaƙashin Al'arshi". (Bazzar ya fitar da shi (3966), da Ibnu Abi Shaibah a cikin Musannaf (35491), da Hannad a cikin Zuhdu (1013), da Ahmad a cikin Musnad (21415) kuma lafazin nasane, da kuma cikin Zuhdu (401).)
Muna imani cewa Manzo - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - zai yi sujjada ƙarƙarshin Al'arshi ranar alKiyama har sai ya nemi babban ceto, acikin Hadisin ceto mai tsawo cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Sai in tafi, sai in zo karkashin Al'arshi, sai in fadi ina mai sujjada ga Ubngijina - Mai girma da daukaka -, sannan Allah Zai buda min wani abu wanda bai budawa wani a gabana ba, na nau'o'in godiya gareShi da kyakkyawan yabo gareShi, sannan a ce: Ya Muhammad, ka daga kanka ka yi tambaya abaka shi, ka nemi ceto a ceceka, sai in daga kaina, sai ince: Al’ummata ya Ubangiji, al'ammata ya Ubangiji...". (Bukhari ne ya fitar da shi (4712), da Muslim (194), da Tirmizi (2434), da Ibnu Majah (3307).)
Muna imani cewa rayukan shahidai suna zuwa wasu fitilu wadanda ke rataye a cikin inuwar Al'arshi, daga Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - Ya ce: "Lokacin da aka kashe 'yan uwanku a Uhud sai Allah Ya sanya rayukansu a cikin wasu korayen tsuntsaye, suna gangarowa koraman aljanna, suna cin 'ya'yan itatuwanta, kuma suna zuwa wasu fitilu na zinare wadanda ke rataye a cikin inuwar Al'arshi...". (Abu Dawud ne ya fitar da shi (2520), da Ibnul Mubarak a cikin jihadi (62), da Ibnu Abi Shaibah (19678), da Ahmad (2388).)
An ce wa Ibnul Mubarak: Yaya zamu san Ubangijinmu? Ya ce: "Cewa Shi Yana sama ta bakwai akan Al'arshi, Yana nesa da halittarSa". (Raddi ga Jahamiyya na al-Darimi (shafi na 47), da Sunaye da siffofi na Baihaki (2/336), da Fatawowin Hamawiyya babba (shafi na 333), da Sharhin al-Dahawiyya - bugun Darus Salam (shafi na 219).)
Imam al-Darimi - Allah Ya yi masa rahama - ya ce: "Allah - alherinSa ya yawaita kuma Ya girmama - Yana saman Al'arshinSa, a birbishin sammanSa, Yana nesa da halittarSa, duk wanda bai sanShi da hakan ba to bai san Ubangijinsa wanda yake bautawa ba, kuma saninSa daga birbishin Al'arshi a can nesa da halittarSa da kuma kusancinsu daya ne, kuma wani abu ba ya nisantarSa; Wani abu kwatankwacin kwayar zarra ba ya boyuwa gareShi a sammai ko a kasa} [al-Saba:3]. Tsarki ya tabbatar maSa daga abinda masu kore siffofinSa suke siffantaShi da shi daukaka mai girma". (Raddi ga Jahamiyya ( shafi na 4).)
Muna imani cewa Al'arshi Mala'iku ne suke dauke da shi, Allah - Madaukakin sarki - Ya ce: {Waɗanda ke ɗaukar Al'arshi da waɗanda ke kẽwayensa, sunã tasbĩhi game da gõde wa Ubangijinsu, kuma sunã yin ĩmãni da Shi, kuma sunã yin istigfãri dõmin waɗanda suka yi ĩmãni, (sunã cẽwa), "Yã Ubangijinmu! Kã yalwaci dukan kõme da rahama da ilmi to Ka yi gãfara ga waɗanda suka tũba kuma suka bi hanyarKa, kuma Ka tsare su daga azãbar Jahĩm} [Gafir: 7]. Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma malã'iku (su bayyana) a kan sãsanninta, kuma wasu (malã'iku) takwas na ɗauke da Al'arshin Ubangijinka, a sama da su, a wannan rãnar} [al-Haaƙah: 17].
Haƙiƙa annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bada labari game da wasu siffofin masu dauke da Al'arshi sai ya ce: "An bani izini in yi magana game da wani mala'ika daga mala'ikun Allah daga masu dauke da Al'arshi, lallai tsakanin fatar kunnensa zuwa wuyansa tafiyar shekara ɗari bakwai ce". (Abu Dawud ya fitar da shi (4727), da Dabarani a cikin al-Ausaɗ (1709), da Abu al-Seikh a cikin al-Azamah (476), da Ibnu Shahin a cikin al-Fawa'id (19).)
Muna imani cewa Mala'iku suna kewaye da Al'arshin (Ubangiji) Mai yawan rahama, Allah Ya ce: {Kuma kanã ganin Malã'iku sunã mãsu tsayãwa da haƙƙoƙin da aka ɗõra musu daga kẽwayen Al'arshi, sunã tasbĩhi game da gõde wa Ubangijinsu. Kuma aka yi hukunci a tsakãninsu da gaskiya. Kuma aka ce, "Gõdiya ta tabbata ga Allah, Ubangijin halittu} [al-Zumar: 75].
Al'arshi tare yake da littafin da aka ambata a cikin faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: "Lokacin da Allah Ya gama halitta sai Ya rubuta a cikin littafinSa, shi yana nan a wurinSa a birbishin Al'arshi: Lallai rahamaTa ta rinjayi fishiNa". (Bukhari ne ya fitar da shi (3194), da Muslim (2751), da Tirmizi (3543), da Ibnu Majah (4295, 189).) Kuma su ne mafi girman halittu, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "...Idan zaku roƙi Allah to ku roƙeShi al-Firdaus; domin ita ce mafificiyar aljanna, kuma mafi ɗaukakar aljanna, a birbishinta Al'arshin Ubangiji al-Rahman yake, daga gareta ne ƙoramun aljanna suke bubbugowa". (Bukhari ne ya fitar da shi (7423).)
Muna imani cewa Allah Ya daidaita akan Al'arshinSa daidaiton da ta dace da girmanSa, maɗaukakin sarki Ya ce: {Lallai Ubangijinku Shi ne Allah wanda Ya halicci sammai da ƙasa a cikin kwanaki shida sannan Ya daidaita akan Al'arshi} [al'Aaraf: 54]. Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Wanda Ya halicci sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, a cikin kwãnuka shida sannan Yã daidaitu a kan Al'arshi Mai rahama, sai ka tambayi mai bãyar da lãbãri game da Shi} [al-Furƙan: 59].
An tambayi Rabi'atu al-Ra'ayi game da faɗin Allah - alherinSa ya yawaita Ya ɗaukaka -: {Ubangiji al-Rahman Ya daidaita a kan Al'arshi} [Daha: 5]: To ta yaya ya daidaita? ya ce: "Yadda ya daidaita ba’a sani ba, kuma daidaituwa ba abin hankaltuwa ba ne, kuma imani da hakan gaba ɗayansa yana wajaba akaina da ku". (al-Asma'u wassifat na Baihaƙi (2/306), da Sharhin usulun Ahlus Sunnah wal jama'a (3/582).)
Wani mutum ya zo wajen (Imamu) Malik ɗan Anas sai ya ce: Ya Abu Abdullahi: {Ubangiji al-Rahman Ya daidaita akan Al'arshi}: to yaya ya daidaita? ya ce: Bamu taba ganin Malik ya ji wani abu a ransa kamar yadda ya ji a wannan maganar ba, kuma gumi mai yawa ya fito masa kuma ya sunkuyar da kai, ya sanyamu muna sauraren abinda zaiyi umarni da shi a cikinsa, ya ce: Sannan baƙin ciki ya yaye daga (Imamu) Malik, sai ya ce: "Ta yaya (ya daidaita) ba abin hankalta ba ne, daidaituwa kuma daga gareShi ba abin jahilta ba ce, kuma imani da shi dole ne, tambaya game da shi kuma bidi'a ne. Lallai ni ina jin tsoron ka zama batacce, sannan ya yi umarni aka yi waje da shi". (Raddi ga Jahamiyya na al-Darimi (shafi na 66), da Sharhin Usul i'itiƙadi Ahlussunah wal jama'a (3/441), da Hilyatul Auliya waɗabaƙatul Asfiya (6/325), da al-ITiƙad na Baihaƙi (shafi na 116), da Sharhus Sunnah na Bagawi (1/171), da al-Asma'u Wassifat na Baihaƙi (2/306).)
Imamu Ahmad ya kasance yana cewa a ma'anar daidaituwa: "Shi ne ɗaukaka, Allah bai gusheba Yana maɗaukaki kafin Ya halicci Al'arshinSa, Shi Yana birbishin kowanne abu, kuma Maɗaukaki akan kowanne abu, kawai Allah Ya kebanci Al'arshi ne dan wata ma'ana a cikinsa da ya sabawa ragowar abubuwa, Al'arshi shi mafificin abubuwa kuma mafi ɗaukakarsu, sai Allah Ya yabi kanSa da cewa Shi Ya daidaita akan Al'arshi: Wato Ya ɗaukaka akanSa...An hakaito daga AbdulRahman ɗan Mahdi daga Malik; Cewa Allah - Maɗaukakin sarki - Ya daidaita akan Al'arshinSa mai girma kamar yadda Ya bada labari, kuma cewa iliminSa yana kowanne wuri". (al-Aƙidah, riwayar Abubakar al-Kahallal (shafi na 108).)
Rububiyyar Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -ga Al-arshi dalili ce akan cancantar a bauta masa banda waninSa, sai Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Dã waɗansu abũbuwan bautawa sun kasance a cikinsu (sama da ƙasa) fãce Allah, haƙĩƙa dã su biyun sun ɓãci. Sabõda haka tsarki ya tabbata ga Allah Ubangijin Al'arshi daga abin da suke siffantãwa} [al-Anbiya'u: 22]. Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Ka ce: "Wãne ne Ubangijin sammai bakwai kuma Ubangijin Al'arshi mai girma} [al-Mua'Munun: 86]. Kuma Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Ka ce: "Dã akwai waɗansu abũbuwan bautãwa tãre da shi, kamar yadda suka faɗa, a lõkacin, dã (abũbuwan bautãwar) sun nẽmi wata hanya zuwa ga Ma'abũcin Al'arshi} [al-Israa: 42].
BABIN HALITTAR RUWA
Muna imani cewa Allah - Maɗaukaki Ya halicci ruwa kafin Ya halicci sama da ƙasa, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce-: "Allah Ya kasance alhali babu wani abu kafinSa, Al'arshinSa ya kasance akan ruwa, sannan Ya halicci sammai da ƙasa". (Muslim ne ya fitar da shi (2713), da Abu Dawud (5051), da Tirmizi (3400), da Ibnu Majah (3831).) Kuma Allah Ya sanya kowanne abu mai rai daga ruwa, Allah - tsarki ya tabbatar maSa - Ya ce: {Mun sanya kowanne abu mai rai daga ruwa} [al-Anbiya'a: 30]. Kuma Allah Ya sanya shi aya daga ayoyin RubibiyyarSa da UluhiyyarSa, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Wanda Ya sanya muku ƙasa a shinfide, kuma sama gini, kuma Ya saukar da ruwa daga sama, sannan Ya fitar da abinci daga 'ya'yan itãce game da shi, sabõda ku. Sabõda haka kada ku sanya wa Allah wasu kĩshiyõyi, alhãli kuwa kuna sane} [al-Baƙara: 22].
Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma a cikin ƙasa akwai yankuna mãsu maƙwabtaka, da gõnaki na inabõbi da shũka da dabĩnai iri guda, da waɗanda bã iri guda ba, anã shayar da su da ruwa guda. Kuma Munã fĩfĩta sãshensa a kan sãshe a wajen ci. Lalle ne a cikin wancan akwai ãyõyi ga mutane waɗanda suke hankalta} [al-Ra'ad: 4]. Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce {Kuma shĩ ne Ya gauraya tẽkuna biyu, wannan mai dãdi, mai sauƙin haɗiya, kuma wannan gishiri gurbatacce, kuma Ya sanya wani shãmaki a tsakãninsu da kãriya mai shãmakacẽwa* Kuma Shi ne Ya halitta mutum daga ruwa, sai Ya sanya shi nasaba da surukuta, kuma Ubangijinka Ya kasance Mai ĩkon yi} [al-Furƙan: 53-54]. Sai Ya sanya koguna biyu mabanbanta daga ruwa, kuma Ya sanya tsari da kariya a tsakaninsu, ɗayansu bazai zalinci ɗayan ba, kamar yadda Ya sanya mutum daga ruwa, kuma Ya sanya dangantaka da sukurtuka daga mutum, to Allah Mafi kyan masu halitta alherinSa ya yawaita, misalan waɗannan ayoyin suna da yawa.
Kamar yadda Allah Ya sanya shi dalili akan tashin bayan mutuwa, sai Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma akwai daga ãyõyinSa cẽwa lalle kai kanã ganin ƙasã ƙẽƙasasshiya, to, idan Mun saukar da ruwa a kanta, sai ta girgiza kuma ta kumbura. Lalle wannan da Ya rãya ta, haƙĩƙa, Mai rãyar da matattu ne. Lalle Shĩ Mai ĩkon yi ne a kan kõwanne abu} [Fussilat: 39].
Kuma Ya sanya shi runduna daga rundunoninSa, sai Ya taimaki masoyanSa da shi, Maɗaukakin sarki Ya ce: {A lõkacin da (Allah) Yake rufe ku da gyangyaɗi, ɗõmin aminci daga gare Shi, kuma Yanã saukar da ruwa daga sama, a kanku, dõmin Ya tsarkake ku da shi, kuma Ya tafiyar da ƙazantar Shaiɗan daga barinku, kuma dõmin Ya ɗaure a kan zukãtanku, kuma Ya tabbatar da ƙafãfu da shi} [al-Anfal: 11]. Kuma Ya tabar da maƙiyanSa da shi, Allah - Mai girma - Ya ce: {Sabõda haka, ya kira Ubangijinsa (ya ce), "Lalle nĩ, an rinjãye ni, sai Ka yi taimako* Sai Muka bũɗe kõfõfin sama da ruwa mai zuba * Kuma Muka ɓuɓɓugar da ƙasã ta zama idãnun ruwa, daɗa ruwa ya haɗu a kan wani umurni da aka riga aka ƙaddara shi} [al-Kamar: 10-12]. Zuwa wanin hakan daga halayen da Allah Ya sanya ruwa a cikinsu sababi ne dan taimakon masoyanSa ko tabar da maƙiyanSa.
BABIN HALITTAR ALKALAMI
Muna imani cewa Allah Ya halicci alƙalamin da Ya rubuta ƙaddara, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Farkon abinda Allah Ya halitta (shi ne) alƙami, sai Ya ce da shi: Ka rubuta, ya ce: Mezan rubuta? ya ce: Ka rubuta ƙaddarar kowanne abu har zuwa tashin Alkiyama". (Abu Dawud ne ya fitar da shi (4700), da Tirmizi (2155, 3319), da Dayalisi (578), da Ahmad (22705, 22707), da Ibnu Abi Asim a cikin sunnah (115).)
Muna imani cewa alƙaluma masu yawa ne, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce alhali shi yana bada labari game da Isra'i da Mi'iraji: "Sannan aka hau da ni har na bayyana a wani matsayin da nake jin ƙarar alƙaluma". (Bukhari ne ya fitar da shi (349), da Muslim (163).)
Kuma labari game da rubutawar mala'iku ga ayyukan bayi ya maimaitu a cikin Alkur’ani da Sunnah, kamar yadda yake a cikin faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Lalle ne, a kanku, haƙiƙa akwai matsara * Mãsu daraja, marubũta * Sunã sanin abin da kuke aikatãwa} [al-Infiɗar: 10-12].
Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {A lõkacin da mãsu haɗuwa biyu suke haɗuwa daga dãma, kuma daga hagu akwai wani (malã'ika) zaunanne * Bã ya lafazi da wata magana fãce a lĩƙe da shi akwai mai tsaro halartacce} [Qaaf: 17-18].
Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma idan Muka ɗanɗanã wa mutãne wata rahama, a bãyan wata cũta tã shãfe su, sai gã su da mãkirci a cikin ãyõyinMu. Ka ce: "Allah ne mafi gaggãwar (sakamakon) mãkirci." Lalle ne ManzanninMu sunã rubũta abin da kuke yi na mãkirci} [Yunus: 21].
Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Ko sunã zaton lalle Mũ, bã Mu jin asĩrinsu da gãnãwarsu? Na'am! Kuma manzannin Mu na tãre da su sunã rubũtãwa} [al-Zukhruf: 80].
A cikin "Ingantaccen Hadisi" cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Babu wani mutum a cikinku, kuma babu wani rai da yake numfashi sai an rubuta masa mazauninsa a aljanna da wuta, kuma sai hakika an rubuta cewa dan wuta ne ko dan aljanna". (Bukharin ne ya fitar da shi (4948), da Muslim (2647), da Abu Dawud (4694), da Tirmizi (2136, 3344), da Ibnu Majah (78).)
Ya ce kuma: "Idan ɗayanku ya kyautata Musuluncinsa, to dukkanin wata kyakkyawa da ya aikatata za'a rubuta masa goma kwatankwacinta zuwa ninki ɗari bakwai, kuma dukkanin wani mummunan da ya aikatata za'a rubuta masa kwatankwacinta" (Bukharin ya fitar da shi (42, 7501), da Muslim (128, 129, 130), da Tirmizi (3073).)
BABIN HALITTAR KURSIYYI
Muna imani cewa Kursiyyu shi ne mafi girman halitta bayan Al'arshi, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce Yana mai bayyana girmansa: {Kuma KursiyyunSa ya yalwaci sammai da ƙasa} [al-Baƙara: 255].
Kuma Kursiyyu a gaban Al'arshi, yana gurin diga-digai, Haƙiƙa Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su - ya faɗa a cikin tafsirin wannan ayar: "Kursiyyu gurin diga-digai ne, Al'arshi kuma babu wanda zai iya ƙaddara girmansa" (al-Daru ƙuɗniyyu ya fitar da shi a cikin as-Siffat (36) Marfu'i da Mauƙufi, kuma Usman ɗan Sa'id al-Darimi ya fitar da shi a cikin raddi ga Bishril Mirrisi (84, 89), da Abdullahi ibnu Ahmad a cikin Sunnah (586), da Ibnu Khuzaimah a cikin Tauhidi (154), da Abul-sheikh a cikin al-Azamah (216, 217).) Tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Sammai bakwai ba komai ba ne akan Kursiyyu sai dai kamar wata sarka ce a daji, kuma fifikon Al'arshi akan Kursiyyu kamar fifikon wannan dajin ne akan wannan sarkar". (Ibnu Hibban ya fitar da shi (361), haka a cikin majruhin (3/130), da Dabarani a cikin al-Kabir (1651), a cikin al-makarim (1), da al-Ajurri a cikin Arba'in (40), da Abu al-Seikh a cikin al-Azamah (259), da Abu Nu'aim a cikin Hilyah (1/18 da 166 - 168), da Baihaƙi a cikin al-Asma'u (shafi na 510-511), da cikin Shu'ab (4325 da 7668), da Ibnu Abdulbar a cikin al-Tamhid (9/199). Shi Hadisi ne mai tsawo, wannan Hadisin namu wata jumla ce daga cikin shi, Hadisin yana da Hanyoyi masu yawa, saidai dukkaninsu masu rauni ne ba su ingantaba, haƙiƙa Uƙaili ya ambaci wasu daga waɗannan hanyoyin kuma ya yi nuni da cewa masu rauni ne, kuma Ibnu Adi ya ambacesu ya ce: "Wannan Hadisi ne Munkari ta wannan hanyar daga Ibnu Juraij daga Ada'u daga Ubaidu ibnu Umair daga Abu Zarr, wannan Hadisin ba shi da wasu hanyoyi sai ta hanyar Abu Idris Khaulani da Kasim Dan Muhammad daga Abu Zarr. Na uku Hadisin Ibnu Juraij da wannan su ne mafi mumini riwaya.
Kamar yadda Baihaƙi ya fitar daga Abbas Ibnu Muhammad ya ce: na ji Abu Ubaid yana cewa: "Waɗannan Hadisan waɗanda yake cewa cikin su: Ubangijinmu Ya yi dariya saboda yanke ƙaunar bawanSa da kusancin kishinsa. kuma cewa Jahannama ba za ta cika ba har sai Ubangijinka Ya ɗora ƙafarSa a cikinta, Kursiyyu kuma shi ne gurin diga-digai. waɗannan Hadisan a cikin riwaya su a gurinmu gaskiya ne, wasu daga cikinsu sun ɗaukesu daga wasu, sai dai cewa mu idan an tambayemu daga bayanin su ba za mu fassarasu ba, kuma ba mu riski wani yana fassarasu (Tawili) ba". (al-Asma'u Wassifat na Baihaƙi (2/198).)
BABIN HALITTAR SAMMAI DA KASA
Kuma muna imani cewa Allah Ya halicci sammai da kasa da abinda ke tsakaninsu a kwana shida daga kwanukan Allah, kuma babu wata gajiya ko ƙaramar gajiyawa, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun halitta sammai da ƙasã da abin da ke a tsakãninsu, a cikin kwãnaki shida, alhãli wata ‘yar wahala ba ta shãfe Mu ba} [Kaaf; 38]. Allah - Madaukakin sarki - Ya ce: {Shin wadanda suka kafirta ba sa ganin cewa sammai da kasa da sun kasance a manne sai Muka buda su} [al-Anbiya: 30]. Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Ka ce: "Ashe lalle kũ, haƙĩƙa, kunã kafurta a game da wanda Ya halitta kasã a cikin kwanuka biyu, kuma kunã sanya Masa kĩshiyõyi? Wancan fa, shĩ ne Ubangijin halittu} Kuma Ya sanya, a cikinta, dũwatsu kafaffu daga samanta, kuma Ya sanya albarka a cikinta, kuma Ya ƙaddara abũbuwan cikinta a cikin kwanuka huɗu mãsu daidaita, dõmin matambaya * Sannan Ya daidaita zuwa ga sama alhãli kuwa ita (a lõkacin) hayãƙi ce, sai Ya ce mata, ita da ƙasã "Ku zo, bisa ga yarda kõ a kan tĩlas." Suka ce: "Mun zo, munã mãsu ɗã'ã * Sai Ya hukunta su sammai bakwai a cikin kwãnuka biyu. Kuma Ya yi wahayi, a cikin kõwacce sama da al'amarinta, kuma Muka kãwata sama ta kusa da fitilu kuma don tsari. Wancan ƙaddarãwar Mabuwãyi ne, Masani} [Fussilat: 9-12].
Kuma Allah - Maɗaukaki - Ya ce: Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta * Ya ɗaukaka rufinta, sannan Ya daidaita ta * Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta * Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta * Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta * Da duwatsu, Yã kafe ta * Domin jin dãɗi a gare ku, ku da dabbobinku} [al-Nazi'at: 27-33].
Muna imani cewa Allah Ya ɗaga sammai ba tare da wasu ginshiƙai ba, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Allah Shi ne wanda Ya ɗaukaka sammai, bã da ginshiƙai ba waɗanda kuke ganin su. Sannan kuma Ya daidaita a kan Al'arshi, kuma Ya hõre rãnã da watã, kowanne yanã gudãna zuwa ga lokaci ambatacce. Yanã shirya al'amari, Yanã rarrabe ãyõyi daki-daki, mai yiwuwa ne ku yi yaƙĩni da haɗuwa da Ubangijinku} [al-Ra'ad: 2]. Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {(Allah) Ya halitta sammai, bã da ginshiƙi wanda kuke gani ba, kuma Yã jẽfa duwatsu mãsu kafuwa a cikin ƙasã, dõmin kada ta karkata da ku kuma Ya wãtsa daga kowanne irin dabba a cikinta, kuma Mun saukar da ruwa daga sama, sannan Muka tsirar a cikinta, daga kõwanne nau'i biyu (namiji da mace) mai ban sha'awa} [Luƙman: 10].
Muna imani cewa Allah - Maɗaukakin sarki - Yana rike da sammai da ƙasa daga gushewa, Maɗaukain sarki Ya ce: {Lalle Allah Yanã riƙe sammai da ƙasã dõmin kada su gushe. Kuma haƙĩƙa, idan sun gushe, bãbu wani baicinSa da zai riƙe su. Lalle Shi Yã kasance Mai haƙuri, Mai gãfara} [Faɗir: 41].
Muna imani cewa Shi - Allah tsarki ya tabbatar maSa - Ya riƙe sama kada ta faɗo akan ƙasa sai da izininSa, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma Yana riƙe da sama kada ta faɗo akan ƙasa sai da izininSa} [al-Hajj: 65].
Kuma muna imani cewa Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Yana jujjuya al'amarin waɗannan halittun, kuma Yana kiyayesu, kuma hakan ba shi da nauyi a gareShi, Allah Ya ce: {KursiyyunSa ya yalwaci sammai da ƙasa, kuma kiyayesu ba ya nauyi a gareShi, Shi ne (Allah) Maɗaukaki Mai girma} [al-Baƙara: 135].
Muna imani cewa Allah Ya halicci waɗannan halittun masu girma dan wasu manyan hikimomi, da ba za’a iya sanin hakikanin su ba, Haƙiƙa Allah Ya kyutata halittarsu da kuma aikinsu, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma kanã ganin duwãtsu, kanã zaton su sandararru, alhãli kuwa sũ sunã shũɗẽwa shũɗewar girgije, bisa tsarin Allah wanda Ya kyautata kowanne abu. Lalle Shi, Mai lãbartãwa ne game da abin da kuke aikatãwa} [al-Naml: 88]. Tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya ce: {Kuma ba Mu halitta sammai da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu ba, alhãli kuwa Munã mãsu wãsã} [al-Dukhan: 38]. Allah - Madaukakin sarki - Ya ce: Kuma ƙasa Mun mĩkẽ ta kuma Mun jẽfa duwãtsu tabbatattu a cikinta kuma Mun tsirar a cikinta, daga dukkan abu wanda ake aunãwa da sikẽli * Kuma Muka sanyã muku, a cikinta, abũbuwan rãyuwã da wanda ba ku zamã mãsu ciyarwa gare shi ba * Kuma bãbu wani abu fãce a wurinMu, akwai taskõkĩnsa kuma ba Mu saukar da shi ba fãce kan gwargwado sananne} [al-Hijr: 19-21].
Haƙiƙa Allah Ya kafa hujja da halittarSa ga sammai da ƙasa akan RububiyyarSa wacce ta lazimci UluhiyyarSa, sai Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kõ wãne ne Ya halitta sammai da ƙasa kuma Ya saukar muku, daga, sama, wani ruwa, Muka tsirar, game da shi, gõnaki mãsu sha'awa, ba ya kasancẽwa gare ku, ku tsirar da itãcensu? Shin, akwai abin bautãwa tãre da Allah? Ã'a, sũ mutãne ne suna daidaitã (Allah da wani)} [al-Naml: 60]. Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Lalle idan ka tambaye su: "Wãne ne ya halicci sammai da ƙasã kuma ya hõre rãnã da watã?" Lalle sunã cẽwa Allah ne. To, yãya ake karkatar da su?} [al-Ankabut: 61]. Kuma Allah Tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya ce: {Kuma lalle idan ka tambaye su. "Wãne ne ya saukar da ruwa daga sama, har ya rãyar da ƙasã game da shi a bãyan mutuwarta?" Lalle sunã cẽwa, "Allah ne." Ka ce: "Gõdiya tã tabbata ga Allah." Ã'a, mafi yawansu bã su hankalta} [al-Ankabut: 63].
Muna imani cewa Allah Ya sanya ƙasa wuri ne dan jarrabawa, sai Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Shi ne wanda Ya halicci sammai da ƙasa a cikin kwana shida alhali Al'arshinSa ya kasance akan ruwa dan Ya jarrabaku, waye a cikinku mafi kyautata aiki?} [Hud: 7]. Kamar yadda Ya sanya ta gurin tabbata kuma gurin rayuwa da isuwa, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Daga gare ta Muka halitta ku, kuma a cikinta Muke mayar da ku, kuma daga gare ta Muke fitar da ku a wani lõkaci na dabam} [Daha: 55]. Allah - Madaukakin sarki - Ya ce: Ashe, ba Mu sanya ƙasa matattarã ba * Ga rãyayyu da matattu} [al-Mursalat: 25, 26].
Muna imani cewa wannan kasantacciyar (halittar) mai girma yana girmama Allah Ubanugijin talikai, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Sammai bakwai da ƙasa da wanda yake a cikinsu sunã yi Masa tasbĩhi. Kuma bãbu wani abu fãce yanã tasbĩhi game da gõde Masa, kuma amma ba ku fahimtar tasbĩhinsu. Lalle ne shĩ, Ya kasance Mai haƙuri ne, Mai gãfara} [al-Isra'a: 44]. Kuma yana ƙanƙar da kai ga girmanSa, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Sannan Ya daidaita zuwa ga sama alhãli kuwa ita (a lõkacin) hayãƙi ce, sai Ya ce mata, ita da ƙasã "Ku zo, bisa ga yarda kõ a kan tĩlas." Suka ce: "Mun zo, munã mãsu ɗã'ã} [Fussilat: 11].
Kuma wannan kasantacciyar (halittar) tana firgita, tana jin tsoro daga sabon da bayi suke Ubangiji - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka kuma sarautarSa ta ɗaukaka - Ya ce; {Sammai sunã kusa su tsattsage sabõda shi, kuma ƙasa ta kẽce kuma duwãtsu su faɗi sunã karyayyu * Dõmin sun yi da'awar ɗã ga Mai rahama} [Maryam: 90, 91].
BABIN HALITTAR RANA DA WATA
Muna imani cewa Allah Ya halicci rana da wata, Allah Ya ce; {Kuma shĩ ne wanda Ya halitta dare da yini da rãnã da watã dukansu a cikin wani sarari suKe iyo} [al-Anbiya: 33].
Muna imani cewa rana da wata suna gudana, kamar yadda Allah Ya bada labari game da hakan da faɗarSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka: {Kuma rãnã tanã gudãna zuwa ga wani matabbaci nãta. Wannan ƙaddarãwar Mabuwãyi ne, Masani * Kuma watã Mun ƙaddara masa manzilõli, har ya kõma kamar tsumagiyar murlin dabĩno wadda ta tsũfa * Rãnã bã ya kamãta a gare ta, ta riski watã. Kuma dare bã ya kamãta a gare shi ya zama mai tsẽre wa yini, kuma dukansu cikin sarari (guda) suke yin iyo} [Y. S̃: 38-40]. To tsarki ya tabbata ga Allah Mafificin Masu Halitta.
Daga rahamarSa ga bayinSa cewa Ya sanya su (rana da wata) ababen horewa da umarninSa; dan tabbatar da amfanin bayi, Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Kuma Ya hõrẽ muku rãnã da watã sunã madawwama biyu, kuma Ya hõrẽ muku dare da yini} [Ibrahim: 33]. Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Rana da wata da taurari ababan horewa ne da umarninSa} [al-A'araf: 54].
Haƙiƙa Allah - Maɗaukakin sarki - Ya halicci rana da wata dan wasu hikimomi masu girma waɗanda ba za’a iya hakikaninsu ba, daga cikin waɗanan hikimomin akwai abinda ya zo a cikin faɗin Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka -: {Mai tsãgẽwar sãfiya, kuma Ya sanya dare mai natsuwa, kuma da rãna da watã a bisa lissãfi. wannan ne ƙaddarãwar Mabuwãyi Masani} [al-An'am: 96]. Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su - ya ce: {Rana da wata a cikin lissafi} [al-An'am: 96], wato: Adadin kwanuka da watanni da shekaru. (Tafsirin Dabari (11/558).) Allah - Maɗaukakin sarki - Ya faɗa a cikin wasu daga hikimomin halittar rana da wata: {Shĩ ne wanda Ya sanya muku rãnã, babban haske, da watã mai haske, kuma Ya ƙaddara shi ga Manzilõli, dõmin ku san ƙidãyar shẽkaru da lissãfi. Allah bai halitta wannan ba, fãce da gaskiya, Yanã bayyana ãyõyi daki-daki dõmin mutãne waɗanda suke sani} [Yunus: 5].
Muna imani cewa Allah Ya sanya su daga ayoyinSa masu girma masu nuni akan RububiyyarSa wacce ta lazimci UluhiyyarSa, Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Lalle idan ka tambaye su: "Wãne ne ya halicci sammai da ƙasã kuma ya hõre rãnã da watã?" Lalle sunã cẽwa Allah ne. To, yãya ake karkatar da su?} [al-Ankabut: 61]. Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya ce: {Kuma akwai daga ãyõyinSa, dare da yini, da rãnã da watã. Kada ku yi sujada ga rãnã, kuma kada ku yi ga watã. Kuma ku yi sujada ga Allah wanda Ya halicce su, idan kun kasance Shĩ ne kuke bauta wa} [Fussilat: 37]. Ya zo a cikin ingantaccen Hadisi tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Lallai cewa rana da wata ayoyi ne biyu daga ayoyin Allah, ba sa kusufi dan mutuwar wani ko dan rayuwarsa, saidai cewa Allah - Maɗaukakin sarki - Yana tsoratar da bayniSa ne da su". (Bukhari ne ya fitar da shi (1048), da Nasa'i (1459).)
Muna imani cewa rana da wata suna sujjada ga Allah Ubangijin talikai - kamar yadda sauran halittu suke sujjada ga - Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce; {Ashe, ba ka gani ba, lalle Allah, wanda yake a cikin sammai da wanda yake a cikin ƙasa yanã yin sujada a gare shi, da kuma rãna da watã da taurãri da duwãtsu da bishiyoyi da dabbõbi, da kuma mãsu yawa daga mutãne? Kuma waɗansu mãsu yawa azãba tã tabbata a kansu. Kuma wanda Allah Ya wulãkantar, to, bã ya da wani mai girmamã (shi). Kuma Lalle ne Allah Yanã aikata abin da Yake so} [al-Hajj: 18].
Muna imani cewa rana tana sujjada ƙarƙashin Al'arshi a kowacce rana, kamar yadda mai gaskiya abin gasgatawa tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: Daga Abu zarr - Allah Ya yarda da shi - cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce masa lokacin da rana ta faɗi: "Shin kasan ina take tafiya?" Na ce: Allah da manzonSa ne mafi sani, ya ce: "Lallai cewa ita tana tafiya ne har sai ta yi sujjada ƙarƙashin Al'arshi, sai ta nemi izini sai a yi mata izini. (Lokaci) Ya kusa ta yi sujjada, amma ba za’a karba daga gareta ba, kuma ta nemi izini amma ba za’a yi mata izini ba, za'a ce mata: Ki koma ta inda kika zo , sai ta bullo ta yammacinta, hakan shi ne fadin Allah Maɗaukakin sarki: "Kuma rana tana gudana ga matabbacinta, hakan ƙaddarawa ne daga Mabuwayi Masani} (Bukharin ne ya fitar da shi (3199), da Muslim (159), da Abu Dawud (4002), da Tirmizi (2186, 3227).)
BABIN HALITTAR TAURARI
Muna imani cewa Allah Ya halicci taurari (manya) da ƙananan taurari dan wasu hikimomi masu girma, daga cikinsu a kwai abinda Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ambace shi a faɗinSa: {Kuma da waɗansu alãmõmi, kuma da taurãri sunã mãsu nẽman shiryuwa (ga tafiyarsu ta fatauci)}. [al-Nahl: 16]. Katadah - Allah Ya yi masa rahama - ya ce: "Alamomin: Taurari, kuma Allah - Maɗaukakin sarki - kawai Ya halicci waɗannan taurarin ne dan abubuwa uku: Ya sanya su ado ga sama, kuma Ya sanya su ana gane hanyoyi da su, kuma Ya sanya su jifa ga Shaiɗanu, duk wanda ya kutsa a cikin wanin hakan: To ya rasa hankalinsa, kuma ya kuskure rabonsa, kuma ya tozartar da rabonsa, ya ɗorawa kansa abinda ba shi da sani akan shi". (Tafsirin Dabari (17/185).)
Daga Abu Musa - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Mun yi sallar Magariba tare da Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, sannan muka ce: Da zamu zauna har mu yi sallar Isshai'i tare da shi. ya ce: Sai muka zauna, sai ya fito gurinmu, sai ya ce: "Ba ku gushe ba a nan?". muka ce: Ya Manzon Allah, Mun yi sallar Magariba tare da kai, sannan muka ce: Zamu zauna har sai mun yi sallar Issha'i tare da kai, ya ce: "Kun kyauta, ko kun dace" sai ya ce: Sai ya ɗaga kansa zuwa sama, ya kasance saudayawa yana ɗaga kansa sama, sai ya ce: "Taurari aminci ne ga sama, idan taurari suka tafi za’a zo wa sama da abinda aka yi mata alkawari, ni kuma aminci ne ga sahabbai na, idan na tafi za’a zo wa sahabbaina da abinda aka yi musu alkawari, sahabbaina aminci ne ga al'ummata, idan sahabbaina suka tafi za’a zo wa al'ummata da abinda aka yi musu alkawari zai zo musu". (Muslim ne ya fitar da shi (2531).)
Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Kuma lalle Mun ƙawata saman Duniya da fitilu , kuma Muka sanya su abin jifa ga shaiɗanu} [al-Mulk: 5].
Daga Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su - ya ce: wani mutum daga cikin sahabban Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - daga mutanen Madina ya bani labari, cewa su a wani dare suna zaune tare da Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai aka jeho wani tauraro sai ya yi haske, sai Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Me kuke cewa a lokacin Jahiliyya idan aka yi jifa da irin wannan?" suka ce; Allah da ManzonSa ne mafi sani, mun kasance muna cewa: An haifi wani babban mutum, ko kuma wani babban mutum ya mutu, sai manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "lallai su ba'a jifa da su dan mutuwar wani ko dan rayuwar wani, saidai Ubangijinmu - alherinSa ya yawaita kuma Ya daukaka -idan Ya hukunta wani al'amari sai mala'iku masu dauke da Al'arshi su yi tasbihi, sannan waɗanda ke sama su yi tasbihi waɗanda ke bin su, har tasbihin ya kai wa ma'abota wannan saman ta duniya, sannan ya ce: Waɗanda suke biye da masu dauke da Al'arshi su cewa masu dauke da Al'arshin: Me Ubangijinku Ya ce? Sai su ba su labarin abinda Ya ce, Ya ce: sai sashin ma'abota sammai su baiwa sashi labari, har labarin ya kai wannan saman ta duniya, sai aljanu su fauci ji, sai su jefa shi zuwa ga masoyansu, su jefa shi, abinda suka zo da shi akan yadda yake to shi gaskiya ne, sai dai cewa su suna ƙirƙirar (karya) suna yin ƙari a cikinsa". (Muslim ya fitar dashi (2229).)
Shaiɗanu sun kasance suna satar ji, lokacin da aka aiko Annabinmu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai aka hanasu mazaunansu na ji, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya faɗa Yana Mai bada labari game da hakan: {Kuma lalle ne mũ, mun kasance muna zama daga garẽta, a wurãren zama dõmin saurare. To wanda ya yi saurãre a yanzu, zai sãmi yũla, mai dãko dõminsa} [al-Jinn: 9]. Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Lalle Mũ, Mun ƙãwatãr da sama ta kusa da wata ƙawa, watau taurãri * Kuma sunã tsari daga dukan Shaiɗan mai tsaurin kai * Bã zã su iya saurãre zuwa ga jama'a mafi ɗaukaka (Malã'iku) ba, kuma anã jĩfar su daga kõwane gẽfe * Dõmin tunkuɗẽwa kuma sunã da wata azãba tabbatacciya * Fãce wanda ya fizgi wata kalma, sai yũla mai haske ta bĩ shi} [al-Saafat: 6-10].
Daga Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su - ya ce: "Aljanu sun kasance suna hawa sama suna neman jin wahayi, idan sun ji kalma sai su ƙara tara a cikinta, amma kalmar sai ta zama gaskiya, amma abinda suka ƙara sai ya zama ƙarya, lokacin da aka aiko Manzon Allah - tsira da amnicin Allah su tabbata agare shi - sai aka hanasu mazaunan su, sai suka ambaci hakan ga Iblis, taurari ba su gushe ba ana jifa da su kafin hakan, sai Iblis ya ce da su: Wannan ba wani abu bane sai wani al'amari ne wanda ya faru a ƙasa, sai ya aika da rundunarsa,(su binciko me ya faru ?)sai suka samu Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a tsaye yana sallah tsakanin wasu duwatsu biyu - ina zatan ya ce: A Makka - sai suka hadu da shi, sai suka ba shi labari, sai ya ce: Wannan shi ne abinda ya faru a kasa". (Tirmizi ne ya fitar da shi (3324), da Ahmad (2482), da Nasa'i a cikin al-Kubra (11562), da Abu Ya'ala (2502).)
Muna imani cewa taurari da ƙananan taurari ba sa amfanarwa kuma ba sa cutarwa, ba sa tasiri a abubuwan da suke faruwa a sammai da ƙasa, duk wanda ya ƙudirce cewa su suna tasiri akan kansu to haƙiƙa ya kafirta ko ya yi shirka, Daga Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su - ya ce: An yi wa mutane ruwa a zamanin Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, sai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce-: "Daga mutane akwai wanda ya wayi gari mai godiya, daga cikinsu akwai mai butulcewa", suka ce: Wannan rahamar Allah ce, wasunsu suka ce: Haƙiƙa tauraro kaza da kaza na cikin taurari ya yi gaskiya, ya ce: "Sai wannan ayar ta sauka: {To ba sai na yi rantsuwa ba da lokutan faɗuwar taurari ba} [al-Waƙi'ah: 75], har ya kai {Kuma kuna sanya arziƙinku (game da shi) lallai ku, ku ƙaryata (shi)} [al-Waƙi'ah: 82]. (Mauslim ne ya fitar da shi (73).)
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Mafi tsoron abinda nake jin tsoro ga al'ummata a ƙarshen zamaninsu shi ne imani da taurari, da ƙaryata kaddara, da zalincin shugabanni". (al-Rauyani ne ya fitar da shi (1245), da Dabarani a cikin al-Kabir (9113).)
kuma Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi hani daga duba a taurari, Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Wanda ya bincini wani ilimi daga taurari, to ya bincini wani yanki na sihiri, ya ƙara abinda ya ƙara". (Abu Dawud ne ya fitar da shi (3905), da Ibnu Majah (3726), da Inu Abi Shaibah (26159), da Ahmad (2000), da Abdu Ibnu Humaid (714).)
To neman sanin ilimin taurari ba ya halatta sai gwargwadan abinda za'a gane tudu ko kogi da shi; domin neman iliminsu yana kaiwa zuwa ga bokanci". Daga Sa'id Ibnu Jubair ya ce: "Wani mutum ya zo wurin Abdullahi Dan Abbas, sai ya ce: Ya baban Abbas, ka yi mini wasiyya, sai ya ce: Ina maka wasicci da tsoron Allah, na haneka da aibata sahabban Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -; domin cewa kai baka san abinda ya rigaya garesu na falala ba, kuma na haneka da aiki da taurari sai dai abinda za'a gane da shi a sarari ko a kogi, domin cewa su suna kaiwa zuwa ga bokanci. Kuma na haneka da zama da waɗanda suke ƙaryata Kaddara, duk wanda yake son a amsa addu'arsa, kuma a tsarkake aikinsa, kuma a karba daga gare shi , to ya yi gaskiya a zancensa, ya bayar da amanarsa, ya kubutar da ƙirjinsa ga musulmai". (Ibnu Baɗɗah ne ya fitar da shi a cikin al-Ibanah (1987).)
BABIN HALITTAR MALA'IKU
Muna imani cewa Allah Ya halicci Mala'iku daga haske ne, a cikin inagntaccen Hadisi daga A'isha - Allah Ya yarda da ita - ta ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "An halicci Mala'iku daga haske, kuma an halicci aljanu daga tartatsi na wuta, kuma an halicci (Annabi) Adam daga abinda aka siffanta muku". (Muslim ne ya fitar da shi (2996).)
Allah Ya sanya Mala'iku mabanbanta a cikin halitta, Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya ce; {Godiya ta tabbata ga Allah Mahaliccin sammai da ƙasa wanda Ya sanya Mala'iku manzanni masu fuka -fukai biyu-biyu da uku-uku da huɗu-huɗu, Yana ƙara abinda Ya so a cikin halitta, lallai Allah Mai iko ne akan dukkan komai} [Faɗir: 1].
Kuma Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bada labarin cewa shi ya ga (Mala’ika) Jibril, yana da fukafukai guda ɗari shida; Kuma yana da girman halitta; Daga Abu Ishaƙ Shaibani ya ce: Na tambayi Zirr Dan Hubaish game da faɗin Allah - Maɗaukakin sarki - {har ya kasance gwargwadan zira'i biyu, ko mafi kusa * sannan Ya yi wahayi zuwa ga bawanSa (Annabi Muhammad) da abinda Ya faɗa masa} [al-Najm: 9, 10]. Ya ce: Dan Mas'ud ya zantar da mu: "Cewa shi ya ga Jibrilu ne yana da fukafukai ɗari shida". (Bukhari ne ya fitar da shi (3232), da Muslim (174), da Tirmizi (3277).) Daga Nana A'isha - Allah Ya yarda da ita - ta ce: "Duk wanda ya riya cewa (Annabi) Muhammad ya ga Ubangijinsa to haƙiƙa ya girmama (magana), sai dai haƙiƙa ya ga (Mala’ika) Jibril a halittar sa, halittarsa kuma ta toshe abinda ke tsakanin sasanni". (Bukhari ne ya fitar da shi (3234), da Muslim (177), da Tirmizi (3068).)
Zamu yi cikakkiyar magana game da Mala'iku a cikin Kundin imani da Mala'iku da izinin Allah, zan taƙaita magana a nan kan abinda ya shafi halittarsu kadai.
BABIN HALITTAR ALJANU DA SHAIDANU.
Muna imani cewa Allah Ya halicci aljanu daga tartsatsi na wuta, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Kuma Aljani Mun haliccẽ shi daga gabãni, daga wutar iskar zafi} [al-Hijr: 27]. Kuma Ya ce: {Kuma ya halicci aljani daga bira daga wutã} [al-Rahman: 15]. Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "An halicci Mala'iku daga haske, kuma an halicci aljanu daga garwashin wuta, kuma an halicci (Annabi) Adam daga abinda aka siffanta muku". (Muslim ne ya fitar da shi (2996).)
Muna imani cewa Allah Ya halicci aljanu da mutane dan su bauta maSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -, Allah Ya ce: {Kuma ban halicci aljannu da mutãne ba sai dõmin su bauta Mini} [al-Zariyat: 56]. Aljanu a cikinsu akwai masu gargaɗi, amma babu manzanni a cikinsu, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma a lõkcin da Muka jũya waɗansu jama'a na Aljanu zuwa gare ka sunã saurãren Alƙur'ãni. To, alõkacin da suka halarce shi suka ce: "Ku yi shiru." Sannan da aka ƙãre, suka jũya zuwa ga jama'arsu sunã mãsu gargaɗi} [al-Ahƙaf: 29]. Dan Abbas - Allah Ya yarda da su - ya ce: "Manzanni daga banu Adam ne, kuma akwai masu gargaɗi daga aljanu" (Tafsirin Ibnu Kathir (3/340).)
Amma faɗinSa - Maɗaukakin sarki - {Yaku taron aljanu da mutane shin manzanni ba su zo muku ba daga cikinku suna karanto muku ayoyiNa}, abin nufi; Wato daga jumillarku ba daga dukkaninku ba, shi kamar faɗinSa - Maɗaukakin sarki - ne: {Kuma Ya sanya wata haske a cikinsu}, da faɗinSa; {Sai suka ƙaryata shi, sai suka soketa} tare da cewa mai sokewar ɗaya ne daga cikinsu.
Muna imani cewa halittar aljanu ta riga halittar (Annabi) Adam; saboda haka ne Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma Aljani Mun haliccẽ shi daga gabãni, daga wutar iskar zafi} [al-Hijr: 27]. Shugaban Shaiɗanu shi ne Iblis - Allah Ya tsaremu daga gare shi - Allah Ya halicce shi daga wuta kamar yadda Ya halicci sauran aljanu da Shaiɗanu, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya faɗa yana Mai bada labari game da Iblis cewa shi ya ce: {Ya ce: Ni ne mafi alheri daga gare shi, Ka halicceni daga wuta kuma Ka halicce shi daga tabo} [Aaraf: 12]. Kuma Iblis ya kasance daga aljanu, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Lokacin da mukace da Mala'iku ku yi sujjada ga Adam sai suka yi sujjada, sai Iblis ne kawai ya kasance daga aljanu sai ya saba daga umarnin Ubangijinsa} [al-Kahf: 50].
Kuma Iblis shi ne wanda ya ruɗar da iyaye biyu (Annabi Adam da Hawwau) - aminci ya tabbata agare su - har ya fitar da su daga aljanna, lokacin da ya yi musu waswasi, kuma ya yi musu rantsuwa cewa shi yana daga masu nasiha, sai ya rudar da su da ruɗu, sai suka ci daga bishiyar, Allah Ya ce: "Kuma ya Ãdam! Ka zauna kai da matarka a Aljanna sai ku ci daga inda kuka so; kuma kada ku kusanci wannan itãciya, har ku kasance daga azzãlumai * Sai Shaiɗan ya sanya musu waswãsi dõmin ya bayyana musu abin da aka rufe daga barinsu, daga al'aurarsu, kuma ya ce: "Ubangijinku bai hanã ku daga wannan itãciya ba fãce dõmin kada ku kasance malã'iku biyu ko kuwa ku kasance daga madawwama * Kuma ya yi musu rantsuwa; Lalle ne nĩ, a gare ku, haƙĩƙa, daga mãsu nasĩha ne * Sai ya saukar da su da rũɗi. Sannan a lõkacin da suka ɗanɗani itãciyar, al'aurarsu ta bayyana gare su, kuma suka shiga sunã lĩƙawar ganye a kansu daga ganyen Aljanna. Kuma Ubangjinsu Ya kira su: "Shin, Ban hanã ku ba daga waccan itãciya, kuma Na ce muku lalle ne Shaiɗan, a gare ku, maƙiyi ne bayyananne * Suka ce: "Ya Ubangijinmu! Mun zãlunci kanmu. Kuma idan ba Ka gãfarta mana ba, kuma Ka yi mana rahama, haƙĩƙa, Munã kasancẽwa daga mãsu hasãra} [al-A'araf: 19-23].
Muna imani cewa shaiɗan ya yi girman kai daga sujjada, sai Allah ya yi fushi da shi, Ya la'ance shi, Ya kore shi daga aljannarSa, kuma cewa shi ya nemi Allah Ya jinkirta masa zuwa ranar Alkiyama; sai Allah Ya jinkirta masa, kuma shi ya yi rantsuwa da buwayar Allah sai ya fitini dukkan 'ya'yan (Annabi) Adam sai bayin Allah masu ikhlasi kawai, Allah Ya faɗa Yana Mai bada labari game da kaidinsa: {A lõkacin da Ubangijinka Ya ce wa malã'iku, "Lalle Nĩ Mai halitta mutum ne daga lãkã * To idan Na daidaitã shi kuma Na hũra daga RũhĩNa a cikinsa, to, ku fãɗi a gare shi, kunã mãsu yin sujada * Sai malã'iku suka yi sujada dukkansu gaba ɗaya * Fãce Iblis, ya yi girman kai, kuma ya kasance daga kãfirai * (Allah) Ya ce, "Yã Ibilis! Mẽ ya hana ka, ka yi sujada ga abin da Nã halitta da HannayeNa biyu? Shin, kã yi girman kai ne, kõ kuwa kã kasance daga maɗaukaka ne? * Ya ce, "Nĩ, mafifici ne daga gare shi: Kã halitta ni daga wutã, kuma Kã halitta shi daga lãkã * Ya ce: "To, ka fita daga gare ta, dõmin lalle kai abin jĩfa ne * "Kuma lalle a kanka akwai la'anaTa har zuwa rãnar sakamako * Ya ce: "Yã Ubangjĩna! Sai Ka yi mini jinkiri zuwa rãnar da ake tãshin su * Ya ce: "To, lalle ne kanã daga waɗanda ake yi wa jinkiri * "Zuwa ga Yinin Lõkacin nan sananne * Ya ce, "To, inã rantsuwa da buwãyarKa, lalle, inã ɓatar da su gabã ɗaya * "Fãce bãyinKa daga gare su, waɗanda Ka tsarkake} [Saad: 71-83]. Shaiɗan ya ce kamar yadda Allah Ya bada labari game da shi: {Ya ce ‘’To akan halakarwar da ka yi mini, ina rantsuwa, lallai ne, ina zaune musu tafarkinKa madaidaici * "Sannan kuma haƙĩƙa, Inã je musu daga gaba gare su, kuma daga bãya gare su, kuma daga bangaran damansu da bangaran hagunsu; Kuma bã zã ka sãmi mafi yawansu mãsu gõdiya ba} [al-A'araf: 16-17].
Aljanu ababen yi wa magane ne da shari'u, kuma an ɗora musu shari'un, suna da iko akan jin wahayi da fahimtarsa daga manzanni da kuma masu gargaɗi, saboda haka ne suka ce lokacin da suka ji Alkur’ani, kamar yadda Allah Ya bada labari game da su: Kuma a lõkcin da Muka jũya waɗansu jama'a na aljanu zuwa gare ka sunã saurãren Alƙur'ãni. To, alõkacin da suka halarce shi suka ce: "Ku yi shiru." Sannan da aka ƙãre, suka jũya zuwa ga jama'arsu sunã mãsu gargaɗi * Suka ce: "Ya mutãnenmu! Lalle mũ, mun ji wani littãfi an saukar da shi a bãyãn Mũsã, mai gaskatãwa ga abin da ke a gaba da shi, yanã shiryarwa ga gaskiya da kuma zuwa ga hanya madaidaiciya} [al-Ahƙaf: 29-30].
Kuma muna sanin cewa akwai salihai daga aljanu akwai koma bayan haka daga cikinsu, wanda ya yi imani daga cikinsu to makomarsa ita ce aljanna, wanda ya kafirta daga cikinsu to makomarsa ita ce wuta, Allah - Maɗaukaki - Ya ce; {Kuma lalle ne mũ, akwai sãlaihai a cikinmu, kuma akwai a cikinmu waɗanda ba haka bã mun kasance ƙungiyõyi dabam-dabam} [al-Jinn: 11]. Sannan Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma lalle ne mũ akwai a cikinmu, waɗanda suka mĩƙa wuya, kuma akwai a cikinmu karkatattu. to, wanda ya mĩƙa wuya waɗancan kam sun nufi shiryuwa * Kuma amma karkatattu sai suka kasance makãmashi ga Jahannama} [al-Jinn: 14-15].
Allah - Maɗaukakin sarki - Ya faɗa Yana Mai bada labari game da tabbatar da Mala'iku za su yi wa fandararru daga mutane da aljanu a ranar (akan zuwan manzanni) al-Kiyama: {Yaku aljanu da mutane shin manzanni daga cikinku ba su zo mukuba suna karanto muku ayoyiNa kuma suna gargaɗinku gamuwa da yininku wannan?} [al-An'am: 130]. Kuma Maɗaukakin sarki Ya ce: {Ya ce ku shiga a cikin wasu al'ummatan da haƙiƙa sun shuɗe daga gabaninku daga aljanu da mutane a cikin wuta} [al-A'araf: 38].
Kuma Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya bayyana cewa sababin shigarsu wuta shi ne rashin jinsu ga shiriya ji na karba, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Haƙiƙa Mun halitta saboda Jahannama, masu yawa daga aljanu da mutane, suna da zukata ba su fahimta da su, kuma suna da idanu ba su gani da su, kuma suna da kunnuwa ba su ji da su} [al-A'araf: 179]. Waɗannan ayoyin sun yi nuni akan cewa aljanu suna da zukata da kunnuwa da idanu. Kuma shaiɗanu suna da muryoyi da suke rikitar da halitta da su, Allah - Maɗaukaki - ya ce: {Kuma ka rikitar da wanda ka sami iko akansa daga garesu da sautinka, kuma ka yi hari a kansu da dokinka da dakarunka} [al-Isra'a: 64].
Haƙiƙa Allah Ya gargaɗi mutane; da kada Shaiɗan ya ruɗesu kamar yadda ya ruɗar da iyayensu, Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya ce; {Yã ɗiyan Ãdam! Kada Shaiɗan, lalle, ya fitine ku, kamar yadda ya fitar da iyãyenku, biyu daga Aljanna, yanã fizge tufarsu daga gare su, dõmin ya nũna musu al'aurarsu. Lalle ne shĩ, yanã ganin ku, shi da rundunarsa, daga inda bã ku ganin su. Lalle ne Mũ, Mun sanya Shaiɗan majiɓinci ne ga waɗanda bã su yin ĩmãni} [al-A'araf: 27].
Muna imani cewa Shaiɗan - tare da saninsa cewa ba zai iya halakar da bayin Allah masu ikhlasi ba - yana ƙoƙari shi da rundunarsa wajen halakar da su da bata ibadunsu, Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya ce: {Kuma kamar wancan ne Muka sanya wa kowanne Annabi maƙiyi; shaiɗãnun mutãne da aljannu, sãshensu yanã yin ishãra zuwa sãshe da ƙawãtaccen zance bisa ga rũɗi. Kuma dã Ubangijinka Yã so, dã ba su aikatã shi ba, don haka ka bar su da abin da, suke ƙirƙirãwa} [al-An'am: 112]. A cikin Hadisi cewa manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Lallai cewa Ifritu (mai tsaurin kai) daga aljanu ya bijiro min daren jiya - ko wata kalmar kwatankwacinta - dan ya yanke sallata, sai Allah Ya bani iko akansa, sai na yi nufin daure shi a wani ginshiƙi daga ginshiƙan masallaci har ku wayi gari ku kalleshi gaba ɗayanku, sai na tina da faɗin ɗan'uwana (annabi) Sulaiman: Ya Ubangiji ka bani mulkin da ba ya kamata ga wani a bayana", Rauhu ya ce: sai ya sake shi a tabe. (Bukhari ne ya fitar da shi (461) da Muslim (541).) Daga Ibnu Mas'ud - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Babu wani daga cikinku sai an wakilta masa abokinsa daga aljanu" suka ce: Har kai ya manzon Allah? ya ce: " Har ni sai dai cewa Allah Ya taimakeni akansa sai ya musulunta, ba ya umartata sai da alheri". (Muslim ne ya rawaito shi (2814).)
Daga Sabura Dan Abi Fakih - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Na ji manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana cewa: "Lallai Shaiɗan ya zaunawa ɗan Adam ta hanyoyinsa, sai ya zauna masa ta hanyar Musulunci, sai ya ce: Zaka musulunta kabar addininka da addinin iyayenka da iyayen iyayenka, sai ya saba masa sai ya musulunta, sannan ya zauna masa ta hanyar hijira, sai ya ce: Za ka yi hijira ka bar kasarka da samanka, kawai misalin wanda ya yi hijira kamar misalin doki ne a cikin igiya, sai ya saba masa sai ya yi hijira, sannan ya zauna masa ta hanyar Jihadi, sai ya ce: Zaka yi Jihadi, shi wahalar da rai ne da dukiya, zaka yi jihadi akasheka, a aure maka mata, a raba dukiyarka, sai ya saba masa sai ya yi jihadi " Sai manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Wanda ya aikata hakan ya cancanci Allah Ya shigar da shi aljanna, wanda aka kashe ya cancanci Allah - Mai girma da daukaka - Ya shigar da shi aljanna, idan ya nutse ya cancanci Allah Ya shigar da shi aljanna, ko dabbarsa ta taka shi to ya cancanci Allah Ya shigar da shi aljanna". (Nasa'i ne ya fitar da shi (3134), kuma a cikin al-Kubra (4327), da Ahmad (15958), da Ibnu Hibban (4593).)
Idan mummuna ya kasance ba ya yanke ƙauna daga rinjaye akan annabawa - amnici ya tabbata agare su -, to wasunsu yana daga mafi cancanta, daga Abul Ala'i cewa Usman Dan Abil-Aas - Allah Ya yarda da shi - ya zo wurin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai ya ce: Lallai Shaiɗan haƙiƙa ya tsare tsakanina da sallata da karatuna yana rikitar dani, sai manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Wannan Shaiɗan ne ana ce masa Khinzab, idan ka ji shi to ka nemi tsarin Allah daga gare shi, ka yi tofi a hagunka sau uku". Ya ce: Sai na aikata hakan, sai Allah Ya tafiyar da shi daga gare ni. (Muslim ne ya rawaito shi (2203).)
A cikin "Sahihul Bukhari": Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: "Lallai Shaiɗan yana gudana daga ɗan Adam irin gudanar jini". (Buhari ne ya ruwaito shi (2038, 7171).) Ibnu Baɗɗah - Allah ya yi masa rahama - ya yi babi ga wannan ma'anar a cikin littafinsa "al-Ibanah", sai ya ce: "Babin imani cewa Shaiɗan abin halitta ne an dora shi akan ɗan Adam yana gudana daga garesu magudanar jini sai dai wanda Allah Ya tsare shi daga gare shi, wanda ya yi musun hakan to shi yana daga cikin batattun kungiyoyi". (al-Ibanah al-Kubra, na Ibnu Baɗɗah (4/61).)
Kuma muna sanin cewa ɗan Adam mai zuwa yana zo masa daga mala'iku da mai zuwa daga Shaiɗan, kuma Annabinmu - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bayyana mana tayaya zamu kare kanmu daga mai zuwa daga Shaiɗan, daga Abdullahi Dan Mas'ud - Allah ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Lallai Shaiɗan yana da himma ga ɗan Adam, Mala'ika ma yana da himma, amma himmar Shaiɗan ita ce alƙawari da sharri da ƙaryata gaskiya, amma himmar Mala'ika to ita ce alƙawarin alheri da gasgata gaskiya, wanda ya ji haka to ya san cewa hakan daga Allah ne, sai ya godewa Allah, wanda ya ji ɗayan kuma to ya nemi tsarin Allah daga Shaiɗan abin jefewa, sannna ya karanta: {Shaiɗan yana alƙawarta muku talauci kuma yana umartarku da alfasha} aya [al-Baƙara: 268]. (Tirmizi ne ya fitar da shi (2988), da Ibnul Mubarak a cikin Zuhdu (1435), da Ahmad a cikin Zuhdu (854), da Abu Dawud a cikin Zuhdu (164).)
Muna imani cewa Allah Yana kiyaye bayinSa muminai daga makircin Shaiɗanu muddin dai suna neman gafara, a cikin "al-Musnad": "Lallai shaiɗan ya ce: Na rantse da Girmanka ya Ubangiji, ba zan gushe ba ina batar da bayinKa, muddin dai rayukansu suna jikinsu, Ubangiji ya ce: Na rantse da girmaNa da ɗaukaka Ta ba zan gushe ba iNa gafarta musu muddin dai sun nemi gafara Ta". (Ahmad ne ya fitar da shi (11237), da Abdu Dan Humaid (932), da Abu Ya'ala (1273, 1399), da Dabarani cikin al-Ausaɗ (8788), haka a cikin addu'a (1779).)
Kuma muna sanin cewa Shaiɗan yana kamanceceniya da surar ɗan Adam ko da abinda Allah ya yi masa izini a cikinsa na kamanni, A cikin "Sahihul Bukhari" Daga Abu Hurairah - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya wakiltani da tsare zakkar Ramadan sai mai zuwa ya zo min, sai ya fara yana ɗibar abinci sai na kama shi, sai na ce: Lallai saina kaika wurin Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai ya ambaci Hadisin - sai ya ce: Idan ka zo wa shimfiɗarka to ka karanta Ayatul-Kursiyyu, wani mai kiyayewa daga Allah ba zai gushe gareka ba, kuma wani Shaiɗani ba zai kusanceka ba har sai ka wayi gari, sai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Ya yi maka gaskiya amma shi maƙaryaci ne, wannan Shaiɗan ne". Bukhari ya fitar da sh (3275, 5010), Mu'allaƙi daga malaminsa Usman Dan al-Haisum a gurare biyu)
Haƙiƙa mutanen Jahiliyya sun kasance - saboda yawan jahilcinsu - suna neman tsari da shugabannin aljanu, amma hakan ba ya ƙara musu komai sai tsoro da wahala, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya faɗa Yana Mai bada labari game da hakan: {Kuma cewa shi wasu maza daga cikin mutane sun kasance suna neman tsari da wasu maza daga aljanu, sabo da haka suka ƙara musu girman kai} [al-Jin: 6].
Muna imani cewa masu bautar gumaka kawai suna bautawa aljanu ne, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya faɗa Yana Mai bada labari game da haƙiƙanin abin da suke bautawa: {Kuma rãnar da Allah Ya ke tãra su gabã ɗaya, sannan Ya ce wa Malã'iku, "Shin, waɗannan kũ ne suka kasance sunã bauta wa * Suka ce : "Tsarki ya tabbata a gare Ka. Kai ne Majiɓincinmu, bã su ba. Ã'a, sun kasance sunã bauta wa aljannu. Mafi yawansu, da sũ suka yi ĩmani} [Saba'i: 40-41].
Kuma muna sanin cewa Shaiɗan yana ruɗar mutum da kafirci, sannan sai ya barshi a duniya , kamar yadda Allah - Maɗaukakin sarki - Ya faɗa Yana Mai bada labari game da hakan: {Kamar misãlin Shaiɗan a lõkacin da yake cẽ wa mutum, "Ka kãfirta," To, a lõkacin da ya kãfirta ɗin, ya ce (masa): "Lalle bãbu ruwãna da kai. Lalle ni inã tsõron Allah Ubangijin halitta!} [al- Hashr: 16]. Kamar yadda yake ruɗarsa da kafirci to yana ruɗarsa da sihiri, kuma yana koya masa shi, Allah - Ya faɗa yana Mai bada labari game da hakan: {Sai dai cewa Shaiɗanu sun kafirta suna koyawa mutane sihiri} [al-Baƙara: 102].
Kuma muna sanin cewa Shaiɗan yana watsar da masoyansa a lahira, kuma yana zarginsu akan bin da suka yi masa, Allah Ya faɗa Yana Mai bada labari game da Shaiɗan cewa shi zai tsaya yana mai jawabi a cikinsu a cikin wutar Jahannama: {Kuma Shaiɗan ya ce a lõkacin da aka ƙãre al'amarin, "Lalle ne Allah Ya yi muku wa'adi, wa'adin gaskiyã, kuma na yi muku wa'adi, sannan na sãɓã muku. Kuma bãbu wani dalĩli a gare ni a kanku fãce na kirã ku, sannan kun karɓã mini. Sabõda haka kada ku zarge ni, kuma ku zargi kanku. Ban zama mai amfaninku ba, kuma ba ku zama mãsu amfãnĩna ba. Lalle na barranta da abin da kuka haɗã ni da shi gabanin wannan (matsayi). Lalle azzãlumai sunã da azãba mai raɗaɗi} [Ibrahim: 22].
BABIN HALITTAR MUTUM
Muna imani cewa Allah Ya bawa Mala'ikunSa labari cewa Shi zai sanya wani khalifa a ƙasa dan rayata da bauta, Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma a lõkacin da Ubangijinka Ya ce ga malã'iku: "Lalle ne, Ni Mai sanya wani halĩfa ne a cikin ƙasa," suka ce: "Ashe, zã Ka sanya a cikinta, wanda zai yi ɓarna a cikinta, kuma mu, muna yi maka tasbihi tare da gõde maka, kuma muna tsarkakewa gareka" Ya ce: "Lalle ne, Ni Na san abin da ba ku sani ba} [al-Baƙara: 30]. Kuma Allah Ya bayyana cewa Shi ne ya halicci (annabi) Adam daga turbaya, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Lalle ne misãlin Ĩsã a wurin Allah kamar misãlin Ãdam ne, (Allah) Yã halitta shi daga turɓãya, sannan kuma Ya ce masa: "Ka kasance: "Sai yana kasancewa} Kuma Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Lallai Allah - Mai girma da ɗaukaka - Ya halicci (Annabi) Adam daga damƙar da Ya damƙa daga dukkanin ƙasa, sai 'ya'yan Adam suka zo akan gwargwadan ƙasar, daga cikinsu akwai fari da ja da baƙi da tsakanin hakan, da mummuna da mai tsarki, da sassauƙa da mai zafin zuciya, da tsakanin hakan". (Abu Dawuda ya fitar da sh (4693), da Tirmizi (2955), da AbdurRazaƙ a cikin Tafsiri (41), da Ahmad (19582), da Bazzar (3025, 3026).) Wannan turbayar Allah Ya maida ita tabo, sannan Ya halicce shi mataki-mataki, Allah Ya ce: {Kuma lalle ne Mun halicci mutum daga ƙeƙasasshiyar lãka, daga baƙin yumɓu wanda ya canja * {Kuma Aljani Mun haliccẽ shi daga gabãni, daga wutar iskar zafi * Kuma a lõkacin da Ubangijinka ya ce wa malã'iku: "Lalle Nĩ mai halittar wani jiki ne daga ƙẽƙasasshen yumɓu wanda ya canja * "To idan Na daidaitã shi kuma Na hũra daga RũhĩNa a cikinsa, to, ku fãɗi a gare shi, kunã mãsu yin sujada * Sai Mala'iku suka yi sujjada dukkansu baki ɗayansu} [al-Hijr: 26-30]. Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun halitta mutum daga wani tsantsa daga lãka} [al-Mua'Munun: 12]. Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Ka tambaye su: "Shin sũ ne mafi wuya ga halittawa, kõ, kuwa waɗanda Muka halitta?" Lalle Mũ, Mun halitta su daga lãkã mai ɗauri} [al-Saafat: 11].
Imam Ahmad - Allah Ya yi masa rahama - Ya ce - bayan ya koro ayoyin da ambatan halittar (Annabi) Adam - aminci ya tabbata agare shi - yaka zo a cikinsu: "Muna cewa: Wannan ne farkon halittar (Annabi) Adam, Allah Ya halicce shi farkon fara shi daga turɓaya, sannan daga taɓo: Ja da baƙi, da fari, daga taɓon akwai mai daɗi da mai gishiri-gishiri, to wannan ita ce zurriyarsa akwai mai tsarki, da mummuna, baƙi da ja da fari, sannan Ya dan sasa wannan turɓayar ruwa, to wannan shi ne faɗinSa: {daga taɓo} lokacin da sashin taɓon ya manne da sashi, sai ya zama taɓo mai ɗanfarewa - wato mai ɗanfarewa - sannan ya ce: {daga tsatso daga taɓo}, yana cewa: Misalin taɓo, idan an tatso shi sai ya zare tsakanin yatsu, sannan ya yi wari sai ya zama konannan tabo, sai ya yi halitta daga konannen tabon, lokacin da ya bushe sai ya zama bushasshen tabo kamartukunya, yana cewa: Ya zama bushsshen tabo kamar busasshiyar tukunya, yana cewa: Yana da kara kamar karar tukunya. To wannan shi ne bayanin halittar (Annabi) Adam. Amma fadinSa {daga wani asali na ruwa wulakantacce} [al-Sajdah: 8], to wannan shi ne farkon halittar zurriyarsa daga (asali) yana nufin digon maniyyi idan ya zubo daga namiji, to wannan shi ne fadinSa: {daga ruwa}, wato maniyyi, {wulakantacce} wato: mai rauni". (Raddi ga Jahamiyya da zindiƙai (shafi na 179-180 bugun/ Dagsh al-Ajami.)
Kuma muna imani cewa Allah Ya halicci (Annabi) Adam da hannunSa Maɗaukaki, kuma Yasa Mala'ikunSa su yi masa sujjada, Maɗaukakin sarki Ya ce: {To idan Na daidaitã shi kuma Na hũra daga RũhĩNa a cikinsa, to, ku fãɗi a gare shi, kunã mãsu yin sujada * Sai malã'iku suka yi sujada dukkansu gaba ɗaya} [al-Hijr: 29-30]. kuma Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Muminai za su taru ranar Alkiyama, sai su ce: Inama dai zamu nemi ceto gurin Ubangijinmu, sai su zo wa Adam, sai su ce: Kaine baban mutane, Allah Ya halicceka da hannunSa, kuma Yasa Mala'ikunSa su yi maka sujjada". (Bukhari ne ya fitar da shi (4476), da Muslim (193), da Ibnu Majah (4312).)
Muna imani cewa Allah Ya halicci (Annabi) Adam - aminci ya tabbata agare shi - akan surarsa, daga Abu Hurairah - Allah Ya yarda da shi - daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Allah Ya halicci Adam akan surarsa, tsawonsa zira'i sittin ne". (Bukhari ne ya fitar da shi (6227), da Muslim (2841).) Daga gare shi daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Idan ɗayanku zai faɗa da ɗan'uwansa to ya nisanci fuska; domin cewa Allah Ya halicci Adam akan surarsa". (Bukhari ne ya fitar da shi (2559), da Muslim (2612), kuma lafazin nasa ne). Daga Abu huraira - Allah Ya yarda da shi - daga Annabi - tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Idan ɗayanku zai yi duka to ya nisanci fuska, kada ya ce: Allah Ya munana fuskarka da fuskar wanda ya yi kama da kai, domin cewa Allah - Maɗaukakin sarki - Ya halicci Adam akan (annabi) surarsa". (Abdul-Razzaƙ ne ya fitar da shi (17952), da al-Humaidi (1153), da Ahmad (7420), da Bukhari a cikin al-Adabul Mufrad (173), da Ibnu Abi Asim a cikin Sunnah (531).)
Muna imani cewa Allah Ya halittarwa (Annabi) Adam mata daga kansa dan ya nutsu da ita, ita ce Hauwwa'u, Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Shi ne wanda Ya halicceku daga rai ɗaya kuma Ya sanya matarsa daga gareta dan ya nutsu da ita} [al-A'araf: 189]. Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Ya ku Mutane kuji tsoron Ubangijinku wanda ya halicce ku daga rai kwara daya kuma Ya halitta daga gare shi matarsa, kuma Ya yada daga garesu maza masu yawa da mata}. [al-Nisa'a: 1].
Kuma muna imani cewa Allah Ya halicci (Annabi) Adam da Hauwa'u, Ya kuma zaunar da su a aljanna, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Muka ce yakai Adam ka zauna kai da matarka a aljanna kuma ku ci daga gareta a halin wadata duk inda kuke so} [al-Baƙara: 35]. Kuma Ya hanesu daga cin bishiya, sai Shaiɗan ya yi musu waswasi - dan hassada garesu - sai suka ci daga gareta, sai Allah Ya fitar da su daga aljanna, Ya sakko da su zuwa ƙasa, Allah Ya faɗa Yana Mai bada labari game da hakan: {Kuma ya Ãdam! Ka zauna kai da matarka a Aljanna sai ku ci daga inda kuka so; kuma kada ku kusanci wannan itãciya, har ku kasance daga azzãlumai * Sai Shaiɗan ya sanya musu waswãsi dõmin ya bayyana musu abin da aka rufe daga barinsu, daga al'aurarsu, kuma ya ce: "Ubangijinku bai hanã ku daga wannan itãciya ba fãce dõmin kada ku kasance malã'iku biyu ko kuwa ku kasance daga madawwama * Kuma ya yi musu rantsuwa; Lalle ne nĩ, a gare ku, haƙĩƙa, daga mãsu nasĩha ne * Sai ya saukar da su da rũɗi. Sannan a lõkacin da suka ɗanɗani itãciyar, al'aurarsu ta bayyana gare su, kuma suka shiga sunã lĩƙawar ganye a kansu daga ganyen Aljanna. Kuma Ubangjinsu Ya kira su: "Shin, Ban hanã ku ba daga wannan itãciya, kuma Na ce muku lalle ne Shaiɗan, a gare ku, maƙiyi ne bayyananne * Suka ce: "Ya Ubangijinmu! Mun zãlunci kanmu. Kuma idan ba Ka gãfarta mana ba, kuma Ka yi mana rahama, haƙĩƙa, Munã kasancẽwa daga mãsu hasãra * Ya ce: "Ku sauka, sãshenku zuwa ga sãshe yanã maƙiyi, kuma kunã da matabbata a cikin ƙasa, da ɗan jin dãɗi zuwa ga wani lõkaci * Ya ce: "A cikinta kuke rãyuwa, kuma a cikinta kuke mutuwa, kuma daga gare ta ake fitar da ku} [al-A'araf: 19, 25].
Kuma muna imani cewa Allah Ya sanya (Annabi) Adam khalifanSa a ƙasa, Maɗaukakin sarki Ya ce; {Kuma a lõkacin da Ubangijinka Ya ce ga malã'iku: "Lalle ne, Ni Mai sanya wani halĩfa ne a cikin ƙasa," suka ce: "Ashe, zã Ka sanya a cikinta, wanda zai yi ɓarna a cikinta, kuma mu, muna yi maka tasbihi tare da gõde maka, kuma muna tsarkakewa gareka" Ya ce: "Lalle ne, Ni Na san abin da ba ku sani ba} [al-Baƙara: 30].
Haƙiƙa ya jarrebe shi sai ya manta, sannan ya saɓa, sannan UbanugijinSa Ya zaɓe shi Ya shiryar da shi, Allah Ya ce: {Kuma lalle, haƙĩƙa, Mun yi alkawari zuwa ga (Annabi) Ãdamu a gabãnin wannan, sai ya manta, kuma ba Mu sãmi ƙarfin zũciya a gare shiba} [Daha: 115]. Sannan (Annabi) Adam ya karɓi wasu kalmomi daga UbangijinSa, sai suka zama sababi na gafarar Allah gare shi da kuma karɓar tubansa gare shi, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Sai Ãdam ya karɓi wasu kalmõmi daga Ubangjjinsa, sabõda haka ya karɓi tũba a kansa. Lalle ne Shi, Shĩ ne Mai karɓar tũba, Mai jin ƙai * Muka ce: "Ku ku sauka daga gare ta gabã ɗaya. To, imma lalle shiriya ta je muku daga gare Ni, to, wanda ya bi shiriya ta to, bãbu tsõro a kansu, kuma bã su yin baƙin ciki} [al-Baƙara: 37, 38].
Muna imani cewa dukkanin wannan haƙiƙa Allah Ya rubuta shi ga (Annabi) Adam kafin Ya halicce shi da shekara arba'in, ya zo a cikin ingantaccen Hadisi daga Abu Hurairah - Allah - Ya yarda da shi -: Daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "(Annabi) Adam da (Annabi) Musa sun yi jayayya, sai (Annabi) Musa ya ce da shi: Ya Adam kai ne babanmu ka taɓar da mu ka fitar da mu daga aljanna, sai Adam ya ce da shi: Ya Musa Allah Ya zaɓeka da zancenSa, kuma Ya zana maka da hannunSa, zaka zargeni ne akan wani al'amarin da Allah Ya ƙaddara shi akaina kafin Ya halicceni da shekara arba'in? sai (Annabi) Adam ya rinjayi (Annabi) Musa, sai Adam ya rinjayi Musa' sau uku. (Bukhari ne ya fitar da shi (6614), da Muslim (2652), da Abu Dawud (4701), da Tirmizi (2134), da Ibnu Majah (80).)
Muna imani cewa farkon halittar zuriyar (Annabi) Adam shi ne kamar yadda Allah Ya bada labari game da shi da faɗinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: {Ya ku mutãne! Idan kun kasance a cikin shakka a Tãshin kiyãma, to, lalle ne Mũ, Mun halittaku daga turɓaya, sannan kuma daga gudãjin jini, sannan kuma daga tsoka wadda ake halittãwa da wadda ba a halittawa dõmin, Mu bayyana muku. Kuma Munã tabbatar da abin da Muke so a cikin mahaifa zuwa ga wani ajali ambatacce, sannan kuma Munã fitar da ku kunã jãrĩri, sannan kuma dõmin ku kai ga cikar ƙarfinku. Kuma daga cikin ku akwai wanda ke mutuwa, kuma daga gare ku akwai wanda ake mayarwa zuwa ga mafi ƙasƙancin rãyuwa dõmin kada ya san kõme a bãyan ya sani. Kuma kanã ganin ƙasa shiru, sannan idan Muka saukar da ruwa a kanta, sai ta girgiza kuma ta kumbura, kuma ta tsirar da tsirrai daga kõwanne nau'i mai ban sha'awa} [al-Hajj: 5]. Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun halitta mutum daga wani tsantsa daga lãka * Sannan kuma Muka sanya shi, ɗigon maniyyi a cikin matabbata natsattsiya * Sannan kuma Muka halitta shi gudan jini, sannan Muka halitta gudan jinin tsõka, sannan Muka halitta tsõkar ta zama ƙasũsuwa, sannan Muka tufãtar da ƙasũsuwan da wani nãma sannan kuma Muka ƙãga shi wata halitta daban. Sabõda haka albarkun Allah sun bayyana, Shi ne Mafi kyawun mãsu halittawa} [al-Mua'Munun: 12-14]. Daga Abdullahi - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya zantar da mu - alhali shi mai gaskiya ne abin gasgatawa - ya ce: "Lallai ɗayanku ana tara halittarsa a cikin mahaifiyarsa kwana arba'in yana maniyyi, sannan ya zama gudan jini kwatankwacin hakan, sannnan ya zama tsoka kwatankwacin hakan, sannan Allah Ya aiko masa da wani Mala'ika sai a umarce shi da kalmomi huɗu, kuma a ce da shi: Ka rubuta aikinsa, da arziƙinsa, da ajalinsa, ɗan wuta ne ko ɗan aljanna, sannan a busa masa rai". (Bukhari ne ya fitar da shi (3208), da Muslim (2643), da Abu Dawud (4708), da Tirmizi (2137), da Ibnu Majah (76).)
kuma Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya bayyana ta yaya yaro yake kama da mahaifin sa wani lokaci, wani lokci kuma zuwa da mahaifiyarsa, lokacin da Abdullahi Dan Salam ya tambaye shi sai ya ce: Lallai ni mai tambayarka ne game da abu uku babu wanda ya sansu sai annabi, menene farkon alamomin Alkiyama? kuma menene farkon abin cin da 'yan aljanna za su cin shi? kuma me yasa yaro yake kama da babansa ko babarsa? ya ce: "Jibrilu ya bani labarinsa ɗazu-ɗazun nan". Dan Salam ya ce: Wannan maƙiyin Yahudawa ne daga mala'iku, ya ce: "Amma farkon alamomin alKiyama wata wuta ce zata korosu daga gabas zuwa yamma, amma farkon abin cin da 'yan aljanna za su ci to shi ne karin hantar kifi, amma yaro idan ruwan namiji ya riga ruwan mace sai ya yi kama da yaron, idan ruwan mace ya riga ruwan namiji sai ta yi kama da yaron". ya ce: Ina shaida cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma lallai cewa kai manzon Allah ne. (Buhari ne ya fitar da shi (3938).)
Muna imani cewa mutane gaba ɗayansu daga zurriyar Adam ne, kuma (Annabi) Adam daga turɓaya yake, babu fifiko ga wani akan wani sai da tsoron Allah, Allah - sha'aninsa ya ɗaukaka - Ya ce: {Yã kũ mutãne! Lalle ne Mũ, Mun halitta ku daga namiji da mace, kuma Muka sanya ku dangõgi da kabĩlõli, dõmin ku san jũna. Lalle mafĩfĩcinku daraja a wurin Allah, (shĩ ne) wanda yake mafĩfĩcinku a taƙawa. Lalle nẽ Allah Masani ne, Mai ƙididdigẽwa} [al-Hujurat: 13]. Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Lallai Allah - mai girma da ɗaukaka - Ya tafiyar muku da girman kan Jahilyyah, da alfaharinsu da iyaye mumini mai tsoron Allah, da fajiri taɓaɓɓe, ku 'ya'yan Adam ne, kuma Adam daga turɓaya ne...". (Abu dawud ne ya fitar da shi (5116), da Tirmizi (3956), da Ma’afi Ibnu Umar a cikin Zuhdu (147), da Ibnu Wahb a cikin al-Jami'u (30), da Ahmad (8736).)
Kuma muna imani cewa Allah Ya halicci Adam daga turɓaya, kuma Ya halittar masa da mata daga kansa ita ce Hauwa'u - aminci ya tabbata agare su - kuma Ya halicci ragowar mutane daga wulaƙantaccen ruwa, sai dai (Annabi) Isa - aminci ya tabbata agare shi - haƙiƙa Allah Ya halicce shi daga uwa ba tare da uba ba, kamar yadda Allah Ya bada labari game da shi da faɗinSa - Maɗaukakain sarki -: {A lõkacin da Malã'iku suka ce "Yã Maryamu! Lalle ne Allah Yana bã ki bushãra da wata kalma daga gare Shi; sũnansa Masĩhu ĩsa ɗan Maryama, yana mai daraja a dũniya da Lãhira kuma daga Makusanta * "Kuma yana yi wa mutãne magana a cikin shimfiɗar jariri, da kuma lõkacin da yana dattijo, kuma yana daga sãlihai * Ta ce: "Yã Ubangijina! Yãya yãro zai kasance a gare ni, alhãli kuwa wani mutum bai shãfe ni ba?" (Allah) Ya ce: "Kamar wannan ne, Allah yana halittar abin da Yake so. Idan Ya hukunta wani al'amari, sai ya ce masa, "Ka kasance!, Sai yana kasancẽwa} [Aal- Imran: 45-47].
Muna imani cewa (Annabi) Isa - aminci ya tabbata agare shi - duk da halittarsa akwai abin mamaki - to shi bawan Allah ne kuma manzonsa ne, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Shi (Dan Maryama) bai zama ba fãce wani bãwa ne, Mun yi ni'ima a gare shi, kuma Muka sanya shi abin kõyi ga Banĩ Isrã'ĩla} [al-Zukhruf: 59]. To shi mutum ne daga mutane, yana cin abin ci, kuma ba Allah ba ne, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Masĩhu ɗan Maryama bai zama ba fãce Manzo ne kawai, haƙĩƙa, manzanni sun shige dage gabãninsa, kuma uwarsa siddika ce. Sun kasance sunã cin abin ci. Ka duba yadda Muke bayyana musu ãyõyi. Sa'an nan kuma ka duba yadda ake karkatar da su} [al-Ma'ida: 75].
Kuma muna samu a cikin littafin Ubangijinmu cewa Allah Ya yi martani ga wanda ya riya cewa Masihu Allah ne da dalilai masu yawa, daga waɗan nan dalilan: Faɗin Allah - alherinSa ya yawaita Ya ɗaukaka -: {Allah bai riƙi wani abin haihuwa ba, kuma bãbu wani abin bautãwa tãre da Shi. Idan haka ne (akwai abin bautawa tare da Shi), lalle ne dã kõwanne abin bautawar ya tafi da abin da ya halitta, kuma lalle ne, dã waɗansu sun rinjãya a kan waɗansu, tsarki ya tabbata ga Allah, daga abin da suke siffantãwa} [al-Mua'Munun: 91]. Da faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Lalle haƙĩƙa waɗanda suka ce: "Lalle Allah Shĩ ne Masĩhu ɗan Maryama," sun kãfirta. Ka ce: "To, wane ne ke iya mallakar wani abu daga Allah, idan Yã nufi Ya halakar da Masĩhu Dan Maryama da uwarsa da wanda yake a cikin ƙasa gabã ɗaya?" Kuma Allah ne da mallakar sammai da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu, Yanã halitta abin da Yake so. Kuma Allah a kan dukkan kõme, Mai ĩkon yi ne} [al-Ma'ida: 17].
Muna imani cewa Allah Ya halicci mutane akan ɗabi'a, maɗaukakin sarki Ya ce: {Sabõda haka, ka tsayar da fuskarka ga addini, kanã mai karkata zuwa ga gaskiya, halittar Allah da Ya halitta mutãne a kanta. Bãbu musanyãwa ga halittar Allah, wannan shĩ ne addini madaidaici kuma amma mafi yawan mutãne ba su sani ba} [al-Rum: 30]. Ibnu Zaid, da Mujahid, da Ikraima sun ce: Dabi'a: ita ce Musulunci. (Tafsirin Dabari (20/98).)
Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su - ya ce, da Ibrahim al-Nakh'i, da Sa'id ibnu Jubair, da Mujahid, da Ikrimah, da Qatadah, da Dhahhak, da Ibnu Zaid a cikin faɗinSa: {Babu canji ga halittar Allah} " Wato: Ga addinin Allah" kuma Bukhari ya yi babi a cikin "Sahih ɗinsa", sai ya ce: "Babin {Babu canji ga halittar Allah} Ga addinin Allah, {Halittar mutanen farko}: Addinin mutanen farko, Dabi'a kuma: Musulunci".
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Dukkanin wanda aka haifa ana haifarsa ne akan ɗabi'a (ta Musulunci) sai dai iyayensa su maida shi bayahude, ko su maida shi banasare, ko su maida shi bamajushe, kamar dabba ce da ta haifi dabba, shin zakaga mai yankakkiyar jela a cikinsu" Sannan Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi- ya ce: {Halittar Allah da Ya halicci mutane a kanta. Babu musanya ga halittar Allah, wannan shi ne addini madaidaici} [al-Rum: 30]. (Bukhari ne ya fitar da shi (4775), da Muslim (2658), da Abu Dawud (4714), da Tirmizi (2138).)
Daga Iyad ibnu Himar al-Mujasha'i - Allah Ya yarda da shi -: Cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - wata rana ya ce a cikin haɗubarsa: "Ku saurara lalle Ubangiji na Ya umarce ni da in sanar da ku abinda ba ku sani ba, daga cikin abinda Ya sanar da ni a wannan rana tawa, dukkan dukiyar da na bawa wani bawa to halal ce, kuma lallali Ni Na halicci bayi Na gaba ɗaysnsu akan turbar gaskiya, sai dai wasu shaiɗanu sun zo musu sun kautar da su daga kan Addininsu, suka haramta musu abinda Na halatta musu suka umarce su da su yi shirka da Ni abin da ban saukar musu da wani dalili ba" (Muslim ne ya fitar da shi (2865).)
Muna imani cewa Allah Ya kafa hujja ga masu musun tashin Alkiyama da cewa Ya ambace su a farkon halittarsu daga turɓaya, sai Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma ya buga Mana wani misãli, kuma ya manta da halittarsa, ya ce: "Wãne ne ke rãyar da ƙasũsuwa alhãli kuwa sunã rududdugaggu * Ka ce: "Wanda ya ƙãga halittarsu a farkon lõkaci Shĩ ke rãyar da su, kuma Shi, game da kõwacce halitta, Mai ilmi ne} [Y. S̃: 78-79].
Kamar yadda ya tinatar da su cewa Shi Ya haliccesu daga wulaƙantaccen ruwa, to tayaya suke girman kai ga Ubangijinsu, suke nisantar tashinsu da taruwarsu?! Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce; {Wanda Ya kyautata kõme, Wanda Ya halitta shi. Shi ne kuma Ya fãra halittar mutum daga lãka * Sannan Ya sanya ɗiyansa daga wani asali na wani ruwa wulãkantacce * Sannan Ya daidaita shi, kuma Ya hũra a cikinsa, daga ruhinSa kuma Ya sanya muku ji, da ganunuwa da zukãta. Gõdiyarku kaɗan ce ƙwarai * Kuma suka ce: "Shin, idan mun ɓace a cikin ƙasã, shin, lalle mu, tabbas ne munã zama a cikin wata halitta sãbuwa?" Ã'a, su game da gamuwa da Ubangijinsu kãfirai * Ka ce: "Mala’ikan mutuwa ne. wanda aka wakkala a gare ku, shĩ ne ke karɓar rãyukanku. Sannan zuwa ga Ubangijinku ake mayar da ku} [al-Sajda: 7-11].
Muna imani cewa halittar Allah - Maɗaukakin sarki - ga bayi dalili ne akan cewa Shi kaɗai ne wanda Ya cancanci a bautawa, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Yã ku mutãne! Ku bauta wa Ubangjinku, Wanda Ya halicce ku, kũ da waɗanda suke daga gabãninku, tsammãninku ku kãre kanku}! [al-Baƙara: 21].
Kamar yadda Allah Ya bamu labari a cikin alKur'ani cewa (Annabi) Nuhu ya gargaɗi mutanen sa da cewa Allah Ya haliccesu matakai-matakai, to ta yaya ba sa kwadayin nutsuwa?1 Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Me ya sãme ku, bã ku fãtar sãmun natsuwa daga Allah * Alhãli kuwa, lalle ne, Ya halitta. ku, a cikin hãlãye} [Nuhu: 13, 14].
Mutum yana da halaye a cikin Barzahu da cikin gidan lahira, bayaninsu zai zo - in Allah Ya so - a cikin Kundin Imani da ranar lahira.
BABIN HALITTAR RAI
Muna sanin cewa rai daga al'amarin Allah ne, kuma cewa mutane ba sa sanin wani abu daga sha’anin rai sai abin Allah Ya tsinkayar da su akansa, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Sunã tambayar ka ga rũhi. Ka ce: "Rũhi daga al'amarin Ubangijina ne, kuma ba a bã ku (kõme) ba daga ilmi fãce kaɗan} [al-Isa'a: 85]. Daga Abdullahi - Allah Ya yarda da shi - ya ce: "Wata rana ina tare da annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a gona, alhali shi yana dogare a kan dujen dabino, lokacin da Yahudawa suka wuce, sai sashinsu ya ce da sashi: Ku tambaye shi game da rai, sai ya ce: Menene ra'ayinku gare shi? sashinsu ya ce: Kada ya zo muku da wani abinda kuke ƙi fa, sai suka ce: Ku tambaye shi, sai suka tambaye shi game da rai, sai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi shiru bai amsa musu komai ba, sai nasan cewa shi ana yi masa wahayi, sai na tashi daga inda nake, lokacin da wahayi ya sauka, ya ce: {Suna tambayarka game da rai, Ka ce rai yana daga al'amarin Ubangiji na". (Bukhari ya fitar da shi (4721), da Muslim (2794), da Tirmizi (3141).)
Kuma muna imani cewa rayuka ababaen halitta ne, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Allah ne Mai halitta dukan kõme, kuma Shĩ ne Wakĩli a kan kõme} [al-Zumar: 62]. Lokacin da Allah Ya cika halittar (Annabi) Adam - aminci ya tabbata agare shi - sai ya yi busa a cikinsa daga ransa, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce; {To idan Na daidaitã shi kuma Na hũra daga RũhĩNa a cikinsa, to, ku fãɗi a gare shi, kunã mãsu yin sujada} [al-Hijr: 29]. Idan ɗan tayi ya cika wata huɗu a cikin mahaifiyarsa Allah Zai aika masa da mala'ika, sai ya busa masa rai, daga Abdullahi - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bamu labari - alhali shi mai gaskiya ne abin gasgatawa - ya ce: "Lallai cewa ɗayanku ana taro halittarsa a cikin mahaifiyarsa kwana arba'in yana maniyyi, sannan gudan jini kwatankwacin hakan, sannan ya zama tsoka kwatankwacin hakan, sannan Allah Zai aiko masa da mala'ika sai a umarce shi da abubuwa huɗu: Da arziƙinsa da ajalinsa, ɗan wuta ne ko ɗan aljanna ne, sannan a busa masa rai". (Bukhari ne ya fitar da shi (3208), da Muslim (2643), da Abu Dawud (4708), da Tirmizi (2137), da Ibnu Majah (76).) Sai dai Masihu - aminci ya tabbata agare shi - farkon ɗaukar cikins ya kasance ne daga busar mala'ika, Allah Ya ce - kuma zancenSa gaskiya ne: {Wacce ta tsare farjinta sai muka yi busa a cikinta daga ruhin mu. Sai Muka sanya ta ita da ɗanta wata aya ga duniya} [al-Anbiya'a: 91]. Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kaɗai masihu Isa ɗan Maryam Manzon Allah ne kuma kalmarSa ce Ya jefata zuwa maryam kuma rai ne daga gareShi} [al-Nisa'a: 171].
Kuma muna imani cewa rayuka ana karɓarsu a lokacin bacci, sannan a dawo da su zuwa jiki, Allah - Maɗaukaki - Ya ce; {Allah ne ke karɓar rãyuka a lõkacin mutuwarsu, da waɗannan da ba su mutu ba, a cikin barcinsu. Sannan Ya riƙe wanda Ya hukunta mutuwa a kansa kuma Ya saki gudar, har zuwa ga ajali ambatacce. Lalle a cikin wancan, haƙĩƙa, akwai ãyõyi ga mutãne waɗanda ke yin tunãni} [al-Zumar: 42].
Daga Abdullahi Ibnu Abi Katadah daga babansa - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Mun tafi tare da annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi, sai wasu daga mutane suka ce: Da ma ace ka yi dundumi da mu ya Manzon Allah, ya ce: "Ina jin tsoron kada ku yi bacci daga sallah", Bilal ya ce: Ni zan farkar da ku, sai suka kwanta, Bilal ya jingina bayansa ga dabbarsa, sai idanuwansa suka rinjaye shi sai ya yi barci, sai annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya farka, alhali shamakin rana ya ɓullo, sai ya ce: "Ya Bilal, ina abinda ka ce?" ya ce: Ba'a taɓa jefamin wani bacci irinsa ba ko sau ɗaya, ya ce: "Lallai Allah Ya karɓi rayukanku lokacin da ya so, kuma Ya dawo muku da su lokacin da Ya so". (Bukhari ne ya fitar da shi (595), da Abu Dawud (439-440), da Nasa'i (846).)
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Idan ɗayanku ya zo zuwa shinfiɗarsa to ya karakaɗe shinfiɗarsa da cikin mayafinsa, saboda shi ba ya sanin abinda ya maye gurbi akansa, sannan ya ce: Da sunanKa ya Ubangiji na sanya sasannina, kuma da kaine nake ɗauke shi, in ka riƙe raina to kajiƙansa, idan ka sake shi to ka kiyaye shi da abinda kake kiyaye bayinKa salihai da shi. (Bukhari ne ya fitar da shi (6320), da Muslim (2714), da Abu Dawud (5050), da Tirmizi (3401), da Ibnu Majah (3874).)
Muna imani cewa rai yana rabuwa da jiki a lokacin mutuwa, Allah Ya ce: {Kõwanne rai mai ɗanɗanar mutuwa ne, sannan zuwa gare Mu ake mayar da ku} [al-Ankabut: 57]. Shi (rai) yana rabuwa da jiki cikakkiyar rabuwa idan an mutu, kuma ido yana binsa, daga Ummu Salamah ta ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya shigo gurin Abu Salamah, haƙiƙa idansa ya kafe, sai ya rintsar da shi, sannan ya ce: "Lallai rai idan aka karbe shi sai ido ya bi shi..." (Muslim ne ya fitar da shi (920), da Abu Dawud (3118), da Ibnu Majah (1454).) Shi (rai) ba ya mutuwa kamar mutuwar jiki, kawai mutuwarsa (ita ce) rabuwa da jiki.
Kuma muna imani cewa Mala'iku suna fitar da rayuka daga jikkuna a lokacin mutuwa, kuma ni'ima zata afku akansa ko azaba, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma da ka gani, a lokacin da azzalumai suke cikin magagin mutuwa, kuma Mala’iku suna masu shinfiɗa hannuwansu, (suna ce musu) "Ku fitar da kanku: a yau ana saka muku da azabar wulakanci saboda abinda kuka kasance kuna faɗa, wanin gaskiya, ga Allah, kuma kun kasance daga ayoyinSa kuna masu girman kai} [al-An'am: 93].
Mala'ika yana fitar da rai, sannan azaba ko ni'ima su faɗawa ran, kamar yadda yake faɗawa akan jiki, daga Bara'u ɗan Azib - Allah Ya yarda da su - ya ce: Mun fita tare da annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a jana'izar wani mutum daga mutanen Madina, sai muka isa zuwa wani ƙabari, ba'a binne shi ba, sai Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya tsugunna, muka tsugunna a gefansa, kai kace tsuntsaye ne akan kawunan mu, a hannunsa akwai wani icce da yake tona ƙasa da shi, sai ya ɗaga kansa, sai ya ce: Ku nemi tsarin Allah daga azabar ƙabari sau biyu, ko sau uku, sannnan ya ce: "Lallai bawa mumini idan ya kasance a yankewa daga duniya yana fuskantar lahira, sai wasu Mala’iku su sauko gare shi masu fararen fuskoki, kai kace fuskokinsu rana ce, a tare da su akwai likkafani daga likkanin aljanna, da wani tirare daga tiraren aljanna, har sai sun zauna gare shi tsawon ganin ido, sannan Mala'ikan mutuwa - aminci ya tabbata agare shi - ya zo har sai ya zauna a wurin kansa, sai ya ce: Ya ke wannan ran tsarkakakkiya ki fita zuwa gara daga Allah da yarda". Ya ce; sai ta fita tana zuba kamar yadda ɗigon ruwa yake zuba daga salka, sai ya ɗauketa, idan ya karɓeta ba za su barta a hannunsa ba koda kiftawar ido har sai sun karbeta, sai su sanyata a cikin likkafanin, da kuma cikin wannan tiraren, sai ya fita daga gareta kamar mafi dadin tiraren almiski da aka samu akan kasa". Ya ce:"Sai su hau da ita, ba za su wuce - ma'ana da ita ba - ga wasu jama'a na Mala’ika sai sun ce; wannan wane rai ne mai tsarki? sai su ce: wanene dan wane, da mafi kyawun sunayensa wadanda suka kasance suke an batansa da su a duniya har sai sun kai karshe da ita zuwa sama makusanciya, sai su nemi a bude masa, sai a bude musu, sai su raka shi, a kowacce sama manyan Mala’ikunta , har zuwa saman da take binta, Dar zuwa sama ta bakwai, sai Allah - Mai girma da daukak - ya ce ku rubuta littafin bawaNa a Illiyyin ku maida shi kasa, domin Ni daga ita ne Na haliccesu kuma daga gareta zan maida su kuma daga gareta ne zan fitar da su karo na biyu ya ce: "Sai a dawo da ran a cikin jikinsa...". (Abu Dawud ne ya fitar da shi (3212), da Na sa'i (2001), da Ibnu Majah (1548), da Abu Dawud al-Dayalisi (789), da Abul-Razaƙ (6324, 6737), da Ahmad (18534), kuma lafazin nasa ne). A wannan Hadisi sai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ambaci cewa rai yana fita, kuma yana tsiyaya, kuma ana karɓarsa, ana sashi a likkafani, ana hawa da shi, ana dawo da shi, wannnan dukkaninsa sha'anin abin halitta ne.
Kuma muna imani cewa rai bayan rabuwa da jiki, yana tabbata a cikin ni'ima ko azaba har zuwa ranar Alkiyama, daga Ka'abu ɗan Malik - Allah Ya yarda da shi -, daga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Kaɗai ran mumini tsuntsu ne a cikin bishiyar aljanna har sai Allah - mai girma da ɗaukaka - Ya aiko shi zuwa jikinsa a ranar lahira". (Nasa'i ya fitar da shi (2073), da Tirmizi (1641), da Ibnu Majah (4271), da Abdul-Razaƙ a cikin tafsiri (484, 2681), da al-Humaidi (897), da Ahmad (15776, 15777).)
Daga Masruƙ ya ce: Mun tambayi Abdullahi Dan Mas'ud - Allah Ya yarda da shi - game da wannan ayar: {Kada ka yi zaton waɗanda aka kashe a cikin hanyar Allah matattu ne. A'a, rãyayyu ne su, a wurin Ubangijinsu. Ana ciyar da su} [Aal- Imran: 169]. Ya ce: Amma mu haƙiƙa mun yi tambaya game da hakan, sai ya ce: "Rayukansu na cikin cukunan tsuntsaye koraye, suna da wasu fitilu waɗanda ke rataye a Al'arshi, suna yawo a aljanna inda suka so, sannan su dawo zuwa waɗannan fitilun...". (Muslim ya fitar da shi (1887), da Tirmizi (3011), da Ibnu Majah (2801).
KUNDIN ADDINI
Kundin a taƙaice
Muna imani cewa Allah Ya yarda da musulunci a matsayin addini, kuma shi ne addinin dukkanin annabawa da manzanni - aminci ya tabbata agare su - shi ne ɗabi'ar da Allah Ya ɗabi'antar da mutane a kanta, kuma shi ne alƙawarin da Allah Ya karbe shi akan (Annabi) Adam da zuriyarsa.
Kuma muna imani cewa wannan musuluncin shi ne wasiyyar (Annabi) Ibrahim - aminci ya tabbata agare shi - ga 'ya'yan sa, kuma shi ne wasiyyar (Annabi) Ya'aƙubu - aminci ya tabbata agare shi - ga 'ya'yan sa, shi ne mafi kyan addinai kuma mafi cikarsu, kuma Allah ba ya karɓar wani addinin da ba shi ba.
Kuma muna imani cewa wannan addinin shi ne addinin da (Mala’ika) Jibril amintacce ya sauko da shi ga (Annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, kuma yana da matakai su ne: Musulunci, da imani, da kyautatawa, kuma kowanne daga cikinsu yana da rukunai.
Kuma wannan addinin mai tattarowa ne ga kowanne alheri, wanda ya ƙunshi ayyukan zukata da gaɓɓai.
Muna sanin cewa imani faɗa ne da aiki da ƙudircewa, kuma ma'abotansa suna da fifiko a cikin ayyukansu. Muna imani cewa imani yana ƙaruwa yana raguwa, yana ƙaruwa da biyayya kuma yana raguwa da saɓo.
Muna shaidawa cewa masu imani su ne masu rabauta a duniya da lahira, kuma ma'abota wannan addinin na gaskiya makomarsu ita ce aljanna akan saɓanin darajojinsu da matakansu.
Kuma muna sanin cewa haƙiƙa ayoyi masu girma da Hadisai maɗaukaka sun zo akan umarni da lazimtar sunnah da riƙo da ita, da gargadi akan saɓawa hakan kamar yadda suka yi hani daga rarrabuwa da saɓani.
BABIN LALLAI ADDINI AWAJEN ALLAH SHI NE MUSULUNCI
Muna imani cewa Allah Ya yarda da musulunci a matsayin addini, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma na yardar muku da musulunci a matsayin addini} [al-Ma'ida: 3]. Kuma Allah - tsarki ya tabbatar masa ya ɗaukaka - Ya ce: {Lallai kaɗai Addini a wajen Allah shi ne Musulunci} [Aal- Imran: 19]. Shi ne addinin dukkanin annabawa da manzanni - aminci ya tabbata agare su - Maɗaukakin sarki - Ya faɗa yana mai bada labari game da (Annabi) Nuhu - aminci ya tabbata agare shi - cewa shi ya ce: {Kuma an umurce ni da in kasance farkon mãsu miƙa wuya (ga umurnin Allah)} [Yunus: 72]. Allah - Maɗaukakin sarki - Ya faɗa game da (annabi) Ibrahim - aminci ya tabbata agare shi -: {lokacin da Ubangijisa Ya ce da shi ka mika wuya sai ya ce na mika wuya ga Ubangijin talikai}
Kuma muna imani cewa Allah - Maɗaukakin sarki - haƙiƙa Ya cika mana addini, babu wata tawaya a cikinsa ta kowacce fuska daga fuskoki, tsarki ya tabbatar maSa Ya ce: {Kuma yaune Na cika muku Addininku, kuma Na cika muku ni'amarku, kuma Na yarje muku Musulunci a matsayin Addini} [al-Ma'ida: 3]. Shi ne mafi kyan addinai kuma mafi cikarsu, wannan addinin shi ne miƙaƙƙen addini, tafarkin (annabi) Ibrahim - aminci ya tabbata agare shi -, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Kuma wãne ne ya fi kyau ga addini daga wanda ya sallama fuskarsa ga Allah, alhãli kuwa yanã mai kyautatawa kuma ya bi aƙidar (annabi) Ibrãhĩm, Yanã mai karkata zuwa ga gaskiya? Allah Yã riƙi Ibrãhĩm badãɗayi} [al-Nisa'a: 125]. Tsarki ya tabbatar maSa Ya ce: {Kuma wãne ne yake gudu daga aƙĩdar Ibrãhĩm, fãce wanda ya jãhilta ga ransa? Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun zãɓe shi, a cikin dũniya, kuma lalle ne shi, a cikin Lãhira, haƙĩƙa, yana daga sãlihai} [al-Baƙara: 130]. Allah - sha'aninsa ya daukaka kuma sunayenSa sun tsarkaka - Ya ce a sha'anin (annabi) Ibrahim badaɗayi - amincin ya tabbata agare shi -: {Ibrãhĩma bai kasance Bayahũde ba, kuma bai kasance Banasãre ba, amma yã kasance mai karkata zuwa ga gaskiya, mai sallamãwa, kuma bai kasance daga mãsu shirki ba} [Aal- Imran: 67].
Shi ne ɗabi'ar da Allah Ya ɗabi'antar da mutane akanta, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Sabõda haka, ka tsayar da fuskarka ga addini, kanã mai karkata zuwa ga gaskiya, halittar Allah da Ya halitta mutãne a kanta. Bãbu musanyãwa ga halittar Allah, wannan shĩ ne addini madaidaici kuma amma mafi yawan mutãne ba su sani ba} [al-Rum: 30].
Kuma Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Dukkanin wanda aka haifa ana haifarsa ne akan ɗabi'a, sai dai iyayensa su maida shi bayahude, ko su maida shi banasare, ko su maida shi bamajushe, kamar dabba ce da ta haifi dabba, shin zaka ga mai yankakkiyar jela a cikinsu". Sannan Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi- ya ce: {Halittar Allah da Ya halicci mutane a kanta. Babu musanya ga halittar Allah, wannan shi ne addini madaidaici} [al-Rum: 30]. (Bukhari ne ya fitar da shi (1385), da Muslim (2658), da Abu Dawud (4714), da Tirmizi (2138).) Shi ne alƙawarin da Allah Ya karɓe shi ga (annabi) Adam da zuriyarsa, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Kuma a lõkacin da Ubangijinka Ya karɓi (alkawari) daga ɗiyan Ãdam, daga bãyayyakinsu, a zuriyarsu, kuma Ya shaidar da su a kan rãyukansu, (Ya ce): "Shin, bã Nĩ ne Ubangijinku ba?" Suka ce: "Na'am! Mun yi shaida!" (ya ce): "Kada ku ce a Rãnar Kiyãma: Lalle ne mũ, daga wannan, gafalallu ne} [al-A'araf: 172].
Kuma muna imani cewa Allah ba ya karɓar wani addinin da ba shi ba, Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya ce: {Kuma wanda ya nẽmi wanin Musulunci ya zama addini, to, bã zã a karɓa daga gare shi ba. Kuma shi a Lãhira yana daga cikin mãsu hasãra} [Aal- Imran: 85].
BABIN MUSULUNCI
Kuma muna imani cewa wannan addinin shi ne addinin da (Mala’ika) Jibril amintacce ya sauko da shi ga (Annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, kuma yana da matakai su ne: Musulunci, da imani, da kyautatawa, kuma kowanne daga cikinsu yana da rukunai. Daga Umar Dan Khattab, Allah ya yarda da shi ya ce; Wata rana muna zaune a wurin Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - yayin da wani mutum ya ɓullo mana mai tsananin farin tufafi, mai tsananin baƙin gashi, ba a ganin alamar tafiya a gare shi, kuma ba wani daga cikinmu da ya san shi, har ya zauna zuwa ga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, sai ya jingina gwiwoyinsa zuwa gwiwoyinsa, ya ɗora tafukansa a kan cinyoyinsa, sai ya ce: Ya Muhammad, ba ni labari game da musulunci, sai manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Muslulunci: shi ne ka shaida babu wani abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma cewa (Annabi) Muhammad manzon Allah ne, ka tsai da sallah, ka ba da zakka, ka azimci Ramadan, ka ziyarci ɗakin (Allah) idan kana da ikon tafiya zuwa gare shi*" ya ce: ka yi gaskiya, ya ce: Sai muka yi mamakinsa, yana tambayarsa yana gasgatashi, ya ce: Ka ba ni labari game da imani, ya ce: "Ka ba da gaskiya da Allah, da mala'ikunsa, da littattafansa, da manzanninsa, da ranar lahira, ka ba da gaskiya da kaddara alherinta da sharrinta" ya ce: ka yi gaskiya, ya ce: ka ba ni labari game da kyautayi, ya ce: "Ka bautawa Allah kamar kai kana ganinsa, idan ka kasance ba ka ganinsa, to, shi yana ganinka" Ya ce: ka ba ni labari game da alƙiyama, ya ce: Wanda ake tambayar bai fi wanda yake tambayar sani ba". Ya ce: Ka ba ni labarin alamominta, ya ce: "Kuyanga za ta haifi uwargijiyarta, kuma za ka ga marasa takalma talakawa masu kiwon dabbobi suna gasar tsawaita gidaje" Ya ce: Sannan ya tafi, sai na zauna ɗan wani lokaci sannan ya ce da ni: "Ya Umar, shin ka san waye mai tambayar?" Na ce: Allah da Manzonsa ne mafi sani, ya ce: "To, lallai Jibrilu ne ya zo muku don ya sanar da ku addininku". (Muslim ne ya fitar da shi (8), da Abu Dawud (4695), da Tirmizi (2610), da Ibnu Majah (63).)
Haƙiƙa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bayyana rukunan musulunci a cikin wasu Hadisan daban, sai ya ce: "An gina musulunci abisa abubuwa biyar: Shaidawa cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma (annabi) Muhammad manzon Allah ne, da tsaida sallah, da bada zakka, da Hajji, da azumin Ramadan". (Bukhari ya fitar da shi (8), da Muslim (16), da Tirmizi (2609), da Nasa'i (5001).) Daga Dalha ɗan Ubaidullah - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Wani mutum ya zo wurin manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - daga mutanen Najd mai buzuzun kai, ana jin ƙarfin muryarsa, amma ba'a fahimtar abinda yake faɗa, har ya kusanto, sai ga shi yana tambaya game da musulunci, sai manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Salloli biyar ne a yini da dare" sai ya ce: Shin akwai waninta akaina? ya ce: "A'a sai dai ka yi nafila". Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Da azimin Ramadan". Ya ce; Shin akaina akwai waninsa? ya ce: "A'a sai dai inaka yi nafila". ya ce: sai manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ambata masa zakka. Ya ce: Shin akaina akwai waninta ? ya ce: "A'a sai dai ka yi nafila". Ya ce: Sai mutumin ya tafi, alhali yana cewa: Na rantse da Allah ba zan kara ba bazan rage ba. manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Ya rabauta in da gaske yake". (Bukhari ne ya fitar da shi (46), da Muslim (11), da Abu Dawud (391), da Nasa'i (458).)
Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Kuma ba a umarce su da kome ba fãce bauta wa Allah suna mãsu tsarkake addinin gare Shi, mãsu karkata zuwa ga addinin gaskiya, kuma su tsai da sallah kuma su bãyar da zakka, kuma wannan shi ne addinin waɗanda suke a kan hanyar ƙwarai} [al-Bayyinah: 5]. Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Idan suka tuba suka tsaida sallah, suka bada zakka to kubar hanyarsu lallai Allah mai yawan gafara ne Mai yawan jin ai ne} [al-Taubah: 5]. Kuma Allah - tsarki ya tabbatar masa ya ɗaukaka - Ya ce: {Sa’an nan idan sun tuba kuma suka tsayar da Sallah kuma suka bada zakka to ‘yan’uwanku ne a cikin addini} [al-Taubah: 11]. Kuma Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "An umurce ni da in yaki mutane har sai sun shaida cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma (Annabi) Muhammadu Manzon Allah ne, su tsaida sallah, su bayar da zakka, idan suka aikata hakan sun tsare jinanensu da dukiyoyinsu daga gareni sai dai da hakkin Musulunci, kuma hisabinsu yana ga Allah". Bukhari ne ya fitar da shi (25), da Muslim (22).)
Daga Abu Musa - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Sun ce: Ya manzon Allah, wane abu ne a musulunci yafi? ya ce: "Wanda musulmi suka kuɓuta daga harshensa da hannunsa". (Bukhari ya fitar da shi (11), da Muslim (42), da Tirmizi (2504), da Nasa'i (4999).)
Kuma Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Idan bawa ya musulunta sai musuluncinsa ya kyautata, Allah Zai kankare masa dukkanin wani mummuna wanda ya aikatata, sai kuma sakayya bayan haka: Kyakkyawa da tamkarta goma har zuwa ninki ɗari bakwai, mummuna kuma da kwatankwacinta sai dai idan Allah Ya yafe". (Bukhari ne ya fitar da shi - Mu'allaƙi (41), da Nasa'i (4998).)
BABIN IMANI
Muna imani cewa mataki na biyu daga matakan addini shi ne: Imani, Shi kamar yadda ya zo a cikin amsar annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ga (Malaika) Jibrilu lokacin da ya tambaye shi game da imani ya ce: To ka bani labari game da imani, ya ce: "Ka bada gaskiya da Allah, da Mala'ikunSA, da littattafanSa, da manzanninSa, da ranar lahira, kuma ka yi imani da ƙaddara alherinsa da sharrinsa". Ya ce: Ka yi gaskiya... ya ce; Sannan ya tafi sai na zauna wani ɗan lokaci, sannan ya ce da ni: "Ya Umar shin kasan waye mai tambaya?" Na ce; Allah ne da manzonSa mafi sani, ya ce: "To shi Jibrilu ne ya zo muku ya sanar daku addininku". (Muslim ne ya fitar da shi (8), da Abu Dawud (4695), da Tirmizi (2610), da Nasa'i (4990), da Ibnu Majah (63).)
Imani ko da yake annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya fassara shi a cikin Hadisin (Mala’ika) Jibrilu - aminci ya tabbata agare shi - wanda ya gabata da keɓantacciyar ma'ana ita ce faɗinsa: "Ka bada gaskiya da Allah, da mala'ikunSa, da littattafanSa, da manzanninSa, da ranar lahira, ka yi imani da ƙaddara alherinsa da sharrinsa"; saidai yana zuwa kuma da ma'ana mafi gamewa shi ne mai tattaro dukkan alheri, wanda ya ƙunshi ayyukan zukata da gaɓɓai, Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya ce: {Abin sani kawai, nũminai sũ ne waɗanda suke idan an ambaci, Allah, zukãtansu su firgita, kuma idan an karanta ãyõyinSa a kansu, su ƙãrã musu wani ĩmãni, kuma ga Ubangijinsu suke dõgara * Waɗanda suke tsayar da Sallah, kuma daga abin da Muka azũrtã su sunã ciyarwa * Waɗannan sũ ne mũminai da gaskiya. Sunã da darajõji a wurin Ubangijinsu, da wata gãfara da arziki na karimci} [al-Anfal: 2-4].
Kuma annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya fassara shi ga jama'ar Abdul-Kais da alamomi na zahiri, a cikin ingantaccen Hadisi daga Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su - ya ce: Lallai jama'ar AbdulKais lokacin da suka zo wa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "waɗanne mutane ne - ko wadanne jama'a ne?-" suka ce: Rabi'ah. ya ce: "Maraba da mutanen ko da jama'ar ba taɓaɓɓu ba ba kuma masu nadama ba" sai suka ce: Ya manzon Allah mu ba zamu iya zuwa gurinka ba sai a wata mai alfarma, kuma tsakaninmu da kai akwai wannan ƙabilar daga kafiran Mudar, to ka umarce mu da al'amari mai rabewa, wanda zamu bawa waɗanda ke bayanmu labari da shi, kuma mu shiga aljanna da shi. Kuma suka tambaye shi daga abubuwan sha, sai ya umarcesu da abubuwa hudu, kuma ya hanesu daga abubuwa hudu: Ya umarce su da imani da Allah Shi kadai, ya ce: "Kun san menene imani da Allah Shi kadai?" suka ce: Allah da manzonSa ne mafi sani, ya ce: "Shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma cewa (annabi) Muhammadu manzon Allah ne, da tsaida sallah, da bada zakka, da azimtar Ramadan, kuma ku bada khumusi daga ganima". Kuma ya hanesu daga abubuwa haudu: "Daga hantami (wata tukunya ce da ake shafawa mai ana ɗaukar giya a cikinta. al-Nihaya fi garibul-Hadisi, da ƙwaryar da ake tsimin ɓaure a cikinta dan ya bugar kamar giya, da ƙwaryar da ake tsimin dabino da shi ya bugar kamar giya, da kuma man gelo, ya ce: Kukiyayesu kuma ku ba wa na bayan ku labari". (Bukhari ne ya fitar da shi (53), da Muslim (17), da Abu Dawud (3692), da Tirmizi (2611) da Nasa'i (5031).)
Kuma Bukhari - Allah Ya yi masa rahama - ya yi babi a cikin "Sahih" na sa a kan wannan, sai ya ce: "Babin al'amuran imani, da faɗin Allah - Maɗaukakin sarki -: {Bai zama addini ba dõmin kun jũyar da fuskõkinku wajen gabas da yamma, kuma amma addini shi ne ga wanda ya yi ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira da malã'iku da Littattafan (sama) da Annabãwa, kuma ya bãyar da dũkiya, akan yana son ta, ga mai zumunta da marãyu da matalauta da ɗan hanya da mãsu rõƙo, kuma a cikin fansar wuya, kuma ya tsayar da Sallah, kuma ya bãyar da zakka, da mãsu cika alkawari idan sun ƙulla alkawarin da mãsu haƙuri a cikin tsanani da cũta da lõkacin yãƙi. Waɗannan su ne suka yi gaskiya. Kuma waɗannan su ne mãsu taƙawa}. [al-Baƙara: 177].
Muna imani cewa imani faɗa ne da aiki da ƙudircewa, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Imani tsagi saba’in- ko sittin- da wani abu ne, mafi falalarsu faɗin: Babu abin bautawa da cancanta sai Allah, mafi ƙasa kuma kawar da ƙazanta daga hanya*. Kunya wani tsagi ce na imani. (Bukhari ne ya fitar da shi (9), da Muslim (35), kuma lafazin nasa ne, da Abu dawud (4676), da Tirmizi (2614), da Nasa'i (5005), da Ibnu Majah (57).)
Kuma muna imani cewa masu imani suna da fifiko a tsakaninsu a cikin ayyukansu, daga Abu Sa'id al-Kudri - Allah Ya yarda da shi - daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "'Yan aljanna za su shiga aljanna, kuma 'yan wuta za su shiga wuta, sannan Allah - Maɗaukakin sarki - ya ce: Ku fitar da wanda ya kasance a cikin zuciyar sa akwai kwatankwacin ƙwayar zarra na imani daga wuta. Sai su fita daga cikinta haƙiƙa sun yi baƙi, sai ajefasu acikin ƙoramar girgije, ko rayuwa - Malik ya yi kokwanto - sai su tsiro kamar yadda ƙwaya take tsirowa a gefen fadama, shin baka ganin cewa ita tana fita fatsi-fatsi a kanannaɗe?!". Bukhari ne ya fitar da shi (22), da Muslim (184).)
Daga Abu Umama ɗan Sahlu ɗan Hanif cewa shi ya ji Abu sa'id al-Kudri - Allah Ya yarda da shi - yana cewa: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Wata rana ina bacci, naga mutane ana bijirosu gare ni, atare da su akwai riguna, daga cikinsu akwai wanda yakai kirji, daga cikinsu akwai ƙasa da haka, kuma aka bijromin da Umar ɗan al-Khaɗɗab, yana da rigar da yake janta". Suka ce: Me ka fassara hakan ya manzon Allah? ya ce: "addini". (Bukhari ne ya fitar da shi (23), da Muslim (2390), da Tirmizi (2285), daga cikinsa daga sashin sahabban annabi, da kuma Nasa'i (5011).)
Muna imani cewa imani yana ƙaruwa kuma yana raguwa, yana ƙaruwa da ɗa'a kuma yana raguwa da saɓo, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Mu ne ke jẽranta maka lãbãrinsu da gaskiya. Lalle ne sũ, waɗansu samãri ne. Sun yi ĩmãni da Ubangijinsu, kuma Muka ƙãra musu wata shiriya} [al-Kahf: 13]. Kuma Ya ce: {Kuma waɗanda suka yi imani su kara imani} [al-Mudathir: 31].
Kuma tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: " Zai fita daga wuta Wanda ya ce: Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma a cikin zuciyars akwai awon ƙwayar sha'ir na alheri. Zai fita daga wuta Wanda ya ce: Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma a cikin zuciyars akwai awon ƙwayar hatsi na alheri. Zai fita daga wuta Wanda ya ce: Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma a cikin zuciyars akwai awon ƙwayar dawa na alheri (Bukhari ya fitar da shi (44), da Muslim (193), da Tirmizi (2593).)
Umara ɗan Abdul-Aziz ya rubuta zuwa Adi ɗan Adi: "Lallai imani yana da farillai, da shari'u, da iyakoki, da sunnoni, duk wanda ya cika su to ya cika imani, wanda bai cika su ba to bai cika imani ba, idan na rayu zan bayyana muku su har sai kun yi aiki da su, idan na mutu to ni ba mai kwaɗayi bane akan abokantakarku". (Bukhari ne ya fitar da shi - Mu'allaƙi - (1/10), da Ibnu Abi Shaibah a cikin al-Musannaf (31084), a kuma acikin al-Imani (135), da Khallal a cikin Sunnah (1553, 1162), da Ibnu Baɗɗah a cikin al-Ibanah (1166), da al-Lalka'i a cikin Sharhin Usulu I'itiƙadi Ahlussunnah wal jama'ah (1572))
Mu'ammar, da Sufyan al-Sauri, da Malik ɗan Anas, da Ibnu Juraij, da Sufyanu Ibnu Uyainah sun kasance suna cewa: "Imani faɗa ne (da baki) da aikatawa, yana ƙaruwa kuma yana raguwa". (al-Ibanah al-Kubra (2/806), da al-Shari'ah na al-Ajurri (2/606).)
Kuma al-Hafiz Abubakar Abdullahi Ibnu Zubair al-Humaidi ya ce: ".. Lallai cewa imani faɗa ne da aikatawa, yana ƙaruwa kuma yana raguwa, faɗa ba ta amfani sai da aikatawa, kuma aikatawa da faɗa ba sa amfani sai da niyya, kuma faɗa da cikawa da niyya ba sa amfani sai da (bin) sunnah". (Usulus Sunnah na al-Humaidi (shafi na 37).)
Al-Khallal ya ce: "Abdul Malik al-Maimuni ya bani labari ya ce: Ya'ala ɗan Ubaid ya faɗa mini sama da shekara sittin: Imani faɗa ne da aikatawa, cewa wanda yake azimi yake sallah yake aikata ayyuka na gari shi ne mafi yawan imani daga wanda yake sata yake zina". (Assunnah, na Abubakar Ibnu al-Khallal (3/590).)
Ibnu Abi Hatim ya ce: "Na tambayi babana da Abu Zur'ata game mazahabobin Ahlus Sunnah a cikin Usulud Dini, da abinda suka riski mlamai akansa a dukkanin birane, da abinda suke ƙudirewa a hakan, sai suka ce; Mun riski malamai a dukkanin birane - Hijaz da Iraƙ, da Sham, da Yaman - ya kasance daga mazahabinsu: Imani faɗa ne (da baki) da aikatawa, yana ƙaruwa kuma yana raguwa". (Sharhu Usulu I'itiƙadi Ahlussunah wal Jama'ah (1/198), da Aƙidatus Salaf - Muƙaddimatu Ibnu Abi Zaid al-Kirawani ga littafin al-Risalah (shafi na 29).)
Al-Lalka'i ya ce: "Imani faɗa ne (da baki) da aikatawa, da shi ne wasu daga masana fiƙihu suka ce: Malik Ibnu Anas, da Abdul-Aziz Ibnu Abi Salamah al-Majishun, da Laisu Ibnu Sa'ad, da Auza'i, da Sa'id Ibnu Abdul-Aziz, da Ibnu Juraij, da Sufyanu Ibnu Uyainah, da Fudail Ibnu Iyadh, da Nafi'u ibnu Umar al-Jumahi, da Muhammad Ibnu Maslamah al-Da'ifi, da Muhammad Ibnu Abdullah Ibnu Amr Ibnu Usman Ibnu Affan, da Musanna Ibnu al-Sabah, da al-Shafi'i, da Abdullahi ibnu al-Zubair al-Humaidi, da Abu Ibrahim al-Muzani, da Sufyan al-Sauri, da Sharik, da Abubakr Ibnu Ayyash, da Waki'u, da Hammad Ibnu Salamah, da Hammad Ibnu Zaid, da Yahaya Ibnu Sa'id al-kaddan, da Abdullahi Ibnul Mubarak, da Abu Ishak al-Fazari, da al-Nadiru Ibnu Muhammad al-Mirwazi, da al-Nadiru Ibnu Shumail, da Ahmad Ibnu Hanbal, da Ishak Ibnu rahuwaih, da Abu Saur, da Abu Ubaid". (Sharhi Usulul I'itiƙadi Ahlus Sunnah Wal jama'ah na Imam al-Lakal'i (4/913).)
Abu Abdulahi Ibnu Abi Zamanin ya faɗa a cikin littafinsa "Usulus Sunnah": "Babi a cikin cewa imani faɗa ne (da baki) da aikatawa: Daga faɗin Ahlus Sunnah: Lallai cewa imani tsarkake ibada ne ga Allah da zukata, da shaidawa da harsuna, da aiki da gaɓɓai, akan kyakkyawar niyyah, da dacewa da sunnah". (Usulus Sunnah (shafi na 207).)
BABIN KYAUTATAWA
Muna imani cewa mataki na uku daga matakan addini shi ne : Kyautatawa, Shi ne kamar yadda ya zo a cikin amsar Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ga (Malaika) Jibril lokacin da ya tambaye shi game da kyautatawa, ya ce: "Ka bautawa Allah kamar kai kana ganinSa, idan kai ba ka ganinSa to Shi Yana ganinka..." ya ce: Sannan ya tafi sai na zauna wani ɗan lokaci, sannan ya ce da ni: "Ya Umar shin kasan waye mai tambaya?" Na ce: Allah da manzonSa ne mafi sani, ya ce: "To shi ne Jibril ya zo muku ya sanar da ku addininku". (Muslim ne ya fitar da shi (8), da Abu Dawud (4695), da Tirmizi (2610), da Ibnu Majah (63).)
Kuma Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - ya bada labari cewa ma'abota wannan addinin, makomarsu aljanna ce akan banbancin darajojinsu da matakansu - duk ɗaya ne daga cikinsu akwai wanda ya kasance daga ma'abota musulunci, da wanda ya kasance daga ma'abota imani, da wanda ya zama daga ma'abota kyautatawa - sai Allah - sha'aninSa ya buwaya, kuma Ya ɗaukaka - Ya ce: {Kuma abin da Muka yi wahayi zuwa gare ka, daga Littãfi, shi ne gaskiya mai gasgata abunda ya gabace shi lallai Allah mai bada labari ne ga bayinSa kuma Mai gani ne * Sannan Mun gãdar da Littãfin, ga waɗanda Muka zãɓa daga bãyinMu, sannan daga cikinsu, akwai mai zãlunci ga kansa, kuma daga cikinsu akwai mai tsakaitãwa, kuma daga cikinsu akwai mai tsẽrẽwa da ayyukan alhẽri da iznin Allah. Waccan ita ce falalar (Allah) mai girma * Gidãjen Aljannar zamã sunã shigar su. Anã ƙawãce su a cikinsu, da ƙawã ta mundãye daga zĩnãriya da lu'ulu'u, kuma tufãfinsu, a cikinsu alharĩni ne * Kuma suka ce: "Godiya ta tabbata ga Allah Wanda Ya tafiyar da baƙin ciki daga gare mu. Lalle Ubangijinmu, haƙĩƙa Mai gafarane, Mai godiya} [Faɗir: 31-34].
BABIN UMARNI DA LAZIMTAR SUNNAH DA KUMA RIKO DA ITA
Haƙiƙa ayoyi masu girma da Hadisai maɗaukaka sun zo akan umarni da lazimtar sunnah da kuma riƙo da ita, da gargaɗarwa daga saɓanin hakan da hani daga rarrabuwa da saɓani, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Lalle, abin kõyi mai kyau ya kasance gare ku daga Manzon Allah, ga wanda ya kasance yanã fãtan rahamar Allah da Rãnar Lãhira, kuma ya ambaci Allah da yawa} [al-Ahzab: 21]. Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Lallai waɗanda suka rarraba addininsu kuma suka kasance ƙungiya - ƙungiya, kai ba ka zama daga garesu ba a cikin komai} [An'am: 159]. Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Ya sahar'anta muku, game da Addini, abin da ya yi wasiyya da shi ga Nuhu da abin da muka yi wahayi da shi zuwa gare ka, da abin da muka yi wasiyya da shi ga Ibrahim da Musa da Isa cewa ku tsaida addini kada ku rarraba a cikinsa} [al-Shura:13].
Daga Jabir Dan Abdullah - Allah Ya yarda da su - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Bayan haka, to lallai cewa mafificin zance (shi ne) littafin Allah, kuma mafificiyar shiriya (ita ce) shiriyar (annabi) Muhammad, kuma mafi sharrin al'amura abubuwan da aka farar, dukkanin bidi'a ɓata ce". (Muslim ne ya fitar dashi (867), da Nasa'i (1578), da Abu Dawud (2954), da Ibnu Majah (45).)
Daga Abu Hurairah - Allah Ya yarda da shi -: Cewa manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Duk al'ummata za su shiga aljanna sai wanda ya ƙi", suka ce: Ya manzon Allah, waye zai ki? ya ce: "Wanda ya bi ni zai shiga aljanna, wanda ya saɓa mini haƙiƙa ya ki". (Bukhari ne ya fitar da shi (7280).)
Daga Irbad ɗan sariya - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi mana wa'azi wata rana bayan sallar asuba wa’azi mai kaiwa matuka, wanda idanuwa suka zubar da hawaye daga gare shi, kuma zukata suka ji tsoro daga gare shi, sai wani mutum ya ce: Lallai wannan wa'azin mai ban kwana ne, me zaka yi mana alƙawari da shi ya manzon Allah, ya ce: "Ina muku wasicci da tsoron Allah, da ji da bi, koda bawa ne daga Habasha, domin cewa wanda ya rayu daga cikinku zai ga saɓani mai yawa, to na haneku da fararrun al'amura: domin cewa su ɓata ne, duk wanda ya riski hakan daga cikinku to na umarce shi da sunnata da sunnar halifofina shiryayyu masu shiryarwa, ku yi riƙo da su da turamen haƙora". (Abu Dawuda ya fitar da shi (4607), da Tirmizi (2676), da Ibnu Majah (42), da Ahmad (17416), da al-Darimi (96), kuma hadisin Tirmizi ya inganta shi.)
Bukhari ya ce acikin "Sahih ɗin sa", a cikin Kundin Riƙo da AlKur'ani da Sunnah: Babin koyi da sunnonin manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, da faɗin Allah - tsarki ya tabbar maSa ya ɗaukaka -: {Kuma ka sanyamu jagorori ga masu tsoron Allah} [al-Furƙan: 74], ya ce: Jagororin da zamu dinga koyi da waɗanda suka gabace mu, kuma waɗanda ke bayanmu su yi koyi da mu. Ibnu Aunu ya ce: "Abubuwa uku ina son su ga kaina da kuma 'yan uwa na: Wannan sunnar su santa kuma su yi tambaya game da ita, da al-Kur'ani su nemi fahimtar sa su yi tambaya game da shi, kuma su bar mutane sai dai da alheri". (Sahih al-Bukhari (8/139).)
KUNDIN IMANI DA ALLAH
Kundin a taƙaice
Muna imani cewa Allah Shi ne na farko, a gabaninSa babu wani abu, kuma Shi ne na ƙarshe a bayanSa babu wani abu, Ya sanar da mu da kanSa cewa Shi ne wanda Ya halicci sammai da ƙasa, kuma cewa Shi, Shi ne Mamallaki na gaskiya ga sammai da ƙasa, kuma cewa Shi Yana shigar da dare a cikin yini kuma Yana shigar da yini a cikin dare - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -, kuma wannan halittar da muke gani mai shaida ce akan cewa Shi ne mai samarwa Mahalicci Shi kaɗai Yake babu wani Mahalicci tare da Shi.
Kuma Ya ambaci dalilai masu yawa da ba za'a iya sanin yawansu su ba daga ayoyinSa masu shiryarwa cewa Shi ne Mai samarwa Mahalicci ga wannan halittar, kuma Ya tsaida hujja akanmu da abinda muke ganinsa akanmu da kuma abinda muke ganinsa daga gefanmu.
Muna imani da abinda annabawa da manzanni suka yi imani da shi, muna sakankancewa da abinda ya zo da shi na dalilai da hujjoji masu nuni akanSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -,
Muna imani cewa Allah Shi ne Mahalicci, bai halicci halittarSa dan wasa ba; kai ta kasance halitta ce abar kyautatawa dan manufa mai girma.
Da wanin haka na abinda ya zo da yawa a cikin Alkur’ani mai girma - kamar yadda yake a cikin "Suratul An'am" da "al-Nahl" da wasunsu - na dalilai da ba za su ƙirgu ba, da shaidun da ba za su lissafu ba, kuma dukkaninsu masu nuni ne akan samuwarSa da RubibiyyarSa, su dalilai ne na hankali, da hujjoji masu girma, wani mutum bai isa ya zo da kwatankwcinsu ba ko kusa da su, su a nau'i'insu masu dacewa ne ga dukkanin halitta, masu isuwa a cikin tsaida hujja akansu, koda kafirai sun yi musu, kuma mabarnata sun ki, shin kafiri yana da wani dalili ne saidai inkari ko musu?!.
Muna imani cewa Allah Shi ƙaɗai yake a RubibiyyarSa, kuma cewa Shi ne mahalicci Shi kaɗai, Shi ne wanda Ya fara halitta, wani bai yi tarayya da Shi a cikinta ba, kuma cewa Allah Yana halitta da umarninSa - tsarki ya tabbatar masa Ya ɗaukaka -, kuma tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Yana halitta da abinda ya so na sabubba, duk wanda baShi ba to abin halitta ne.
Muna imani cewa Allah Shi ne Ubanngijin kowanne abu ne, kuma Mahaliccinsa Mai jujjuya al'amuransa, Mamallakinsa, Shi ne mai tasarrufi da shi a cikinsa, kuma ba wani abin halitta da ya mallaki jujjuya al'amarin kansa, ko jujjuya al'amarin waninsa sai abinda Allah Ya ba shi iko akansa.
Muna imani cewa Shi ne Mamallaki na Gaskiya, wanda ba Shi ba to abin mallaka ne, duk wani sarki to mulkinsa ɓatacce ne ko mai gushewa ne ɗan wani lokaci.
Muna imani cewa Allah Shi ne Mai rayawa Mai kashewa, Shi kaɗai Yake tsarki ya tabbatar maSa, kuma Shi ne wanda Ya halicci mutuwa da rayuwa, kuma cewa Shi ne wanda Yake kashe rayuka.
Kuma muna imani cewa Shi ne Mai azirtawa Mai ƙarfi, waninSa ba ya azirtawa, kuma babu isasshe inba Shi ba, muna imani cewa Shi - tsarki ya tabbatar maSa - haƙiƙa Ya kewaye kowanne abu da sani, wani ƙaramin abu ko babba ba zai ɓuya daga saninSa ba, kuma cewa Shi - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Masanin gaibu ne da abinda ke bayyane.
Muna imani cewa Shi - Maɗaukakin sarki - haƙiƙa Ya rinjayi kowanne abu a buwaya da hukunci.
Muna imani cewa Ubangiji - sha'aninSa ya ɗaukaka - halitta ta sa ce da umarni, babu wani Ubangiji in ba Shi ba, kuma babu wani Mai shara'antawa in ba Shi ba, Shi ne wanda Ya halicci halitta, kuma Ya shara'anta shari'u, Ya faralanta farillai, Ya bayyana addini, Shi ne mamallakinsu, Shi ne Mai iko Shi kaɗai akan hisabinsu da sakayyarsu.
Muna imani cewa Ubanngiji - sha'aninSa ya ɗaukaka - Mahaliccin bayi ne, kuma Mahaliccin ayyukansu ne.
Muna imani cewa imani da Rubibiyyar Allah kadai, ba ya isar mutum ya zama mumini, wannan imanin ba ya shigar da mai shi aljanna; domin cewa shi bai yi imani cewa Allah Shi ne abin bauta na gaskiya ba, kuma ba'a bautawa kowa sai Allah Shi kaɗai ba.
Muna imani cewa Allah Shi kaɗai Yake a cikin UluhiyyarSa, kuma cewa Shi babu wani abin bautawa da gaskiya sai Allah Shi kaɗai yake ba Shi da abokin tarayya, kuma cewa Shi Shi ne Gaskiya, kuma wanda suke bautawa wani ba Shi ba ƙarya ne, wannnan al'amarin mai girma shi ne wanda saboda shi Allah Ya saukar da littattafai, Ya aiko da manzanni, Ya halicci aljanna da wuta, kuma jumhur ɗin malamun al'umma suka haɗu akansa, kuma ɗabi'a ta yi nuni akansa, kuma kuɓutattun hanukula suka yi shaida a gare shi. Kuma muna sanin sani na yaƙini cewa tushen Da'awar annabawa ga al'ummatansu shi ne: Da'awarsu a yi bautar Allah Shi kaɗai, da barin bautar waninSa.
Ibada ta gaskiya ita ce wacce take kasancewa ga Allah Ubangijin talikai, mai dacewa da shiriyar shugaban manzanni; domin cewa bautar dukkan wani abin bauta wanda ba Shi ba to ɓatacciya ce.
Wannan rukunin tabbatacce da tushe mai ƙarfi na addinin Allah - shi ne tabbatar da Uluhiyya ga Allah Shi kaɗai da kore bautar wani wanda ba Shi ba - shi ne tauraren tushen addini, da madogarar Da'awar manzanni, kuma ma'anarta shi ne: Kaɗaita Mahalicci da ayyukan halitta.
A cikin AlKur’ani da yawa Allah Ya ke kafa hujja ga bayi da ayoyin RubibiyyarSa wacce take lazimtar bautarSa Shi kaɗai - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -.
Muna imani cewa Mahalicci ga waɗannan ayoyin na kasantattu masu girma Shi ne Shi kaɗai - tsarki ya tabbatar maSa -, kamar yadda cewa babu wani mahalicci tare da Shi to ba ya kamata a bautawa waninSa.
Haƙiƙa Allah Ya da dalilan daban-daban da Ya kafasu shaidu akan UluhiyyarSa, fayyacewar wacce hujja za ta tsaya da ita, abin da aka kafa hujja ya bayyana ɓaro-ɓaro da shi; dan kada mutane su zama suna da wata hujja akan Allah.
Tabbatar da Ulihiyya ga Allah, tare da shaida manzanci ga Manzo - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - shi ne wanda Allah Ya sanya shi iyaka tsakanin imanin mutum da Allah da kuma kafirci.
Babu makawa tare da imani da Allah, sai kuma da kafircewa Dagutu, da barranta daga shirka da ma'abotansa.
Wannan imanin ba ya isuwa ya kasance a zuciya, kai babu makawa da harshe sai ya furta shi, kuma imani ba ya tabbata har sai gaɓɓai sun yi aiki da shi, kuma imani yana ban-banta a cikin zuciya a ƙaruwa da raguwa.
Wannan imanin babu makawa bawa ya kasance a cikinsa mai tsarkake ibada ga Allah Ubangijin talikai ne, kuma ya zama mai sakankancewa ba mai kokwanto ba, kuma imaninsa ya zama daga ilimi ne da ikhlasi da karɓuwa, da miƙa wuya da jawuwa da gaskiya a cikin faɗarsa da aikinsa da ƙudircewarsa, tare da so ga wannan addinin, da wanda Ya shar’anta shi , da wanda ya zo da shi, da wanda ya yi addini da shi.
Kamar yadda Allah Ya bayyana haƙiƙanin imani da abinda yake hukuntawa da rukunansa da sharuɗɗansa, to haƙiƙa ya warware shubuhohin mushrikai masu tsaurin kai, kuma ya bayyana cewa ba su da wata hujja a cikin shirkarsu; domin cewa waɗannan kishiyoyin halittarsu aka yi jujjuya al'amuransu ake yi ba sa iya halittar komai, kuma ba sa mallakar kwatankwacin ƙwayar zarra a cikin sammai ko a cikin ƙasa.
Kuma Allah Ya bayyana cewa waɗannan kishiyoyin waɗanda ake bautawa koma bayan Allah ba sa jin kiran wanda ya kirasu, da sun ji kiran ma ba za su iya amsa musu ba, kuma ranar lahira za su kafirce da shirkarsu kuma za su barranta da su.
Kamar yadda Allah Ya bayyana cewa waɗannan kishiyoyin waɗanda ake bautawa koma bayan Allah ba sa anfanarwa kuma ba sa cutarwa, to ta yaya ake bauta musu koma bayan Allah?!
Kuma Allah Ya ɓata bautar da ake wa mala'iku, kuma Ya bayyana cewa su - tare da cewa makusanta ne ga Allah - ba zu su yi ceto ba sai bayan ya yi izini, idan haka halin mala'iku ya ke, to ta yaya ake bauta musu koma bayan Allah.
Annabawa da manzanni - aminci ya tabbata agare su - tare da ɗaukakar matsayinsu a duniya da lahira ba sa mallakar amfani ko cuta ga kawunansu, to ta yaya ga wani koma bayansu?!
Muna imani cewa Allah Shi kaɗai Yake a cikin siffofinSa da siffofin cikarSa da ɗaukakarSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -, kuma cewa Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Yana da sunaye kyawawa da siffofi Maɗaukaka, cikakkun hankula suna maSa shaida da hakan, kuma ɗabi'u managarta suna miƙa wuya gareShi da hakan, kuma malaman al'ummar musulunci sun haɗu akan hakan, kai dukkanin saƙonnin manzanni sunzo da bayanin siffofin Allah da sunayenSa da ayyukanSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -, kuma Allah Ya aibata allolin mushrikai da cewa su ba sa ji ba sa gani.
Muna imani cewa kamar yadda ya siffanta kanSa, kuma kamar yadda manzonSa tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya siffanta Shi da shi, to Shi - tsarki ya tabbatar maSa ya ɗaukaka - babu wani abu tamkarSa Shi Mai ji ne mai gani ne, sai mu tabbatarwa Allah abinda Ya tabbatarwa kanSa da shi ko manzonSa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya tabbatar maSa da shi, mu kore maSa abinda Ya korewa kanSa shi, ko manzonSa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kore maSa shi, ba tare da kore siffar ba ko kamantawa, ko siffantawa ko canjawa ba.
Muna sani, sani na yaƙini cewa Ubangijinmu Mai siffantuwa ne da siffofinSa kafin Ya halicci halitta, kuma cewa Shi ƙololuwar cika ne da ɗaukaka da kyau tun tuntuni har abada; dan Shi ne na farko kuma na ƙarshe, Shi ne na farko babu wani abu kafinSa, kuma na ƙarshe babu wani abu bayanSa, Shi ne na farko da sunayenSa da siffofinSa cika da girma, Shi ne na ƙarshe da sunayenSa da siffofinSa cika da girma.
Muna imani cewa daga siffofin Allah akwai siffofi masu lazimtar zatinSa, kamar rayuwa, da sani, da ji, da gani, da hannu, da yatsu, kuma daga siffofinSa akwai siffofi masu rataye da ganin damarSa, kamar fushi, da yarda, da sauka.
Muna imani cewa Shi ne mai aikata abinda Ya yi nufi, Shi Yana aiki duk lokain da Ya so yadda Ya so, Yana ɗaukaka wanda Ya so, Yana ƙasƙantar da wanda Ya ga dama, ba mai maida umarninSa, kuma ba mai bibiyar hukuncinSa.
Muna imani cewa siffofin Allah daga cikinsu akwai wanda ya zo kai taye, sai mu siffanta Allah da su akan yadda suka zo kai tsaye, kamar ji, da rayuwa, da gani, da wasunsu. Daga cikinsu kuma akwai wanda ya zo aƙayyade, sai ya wanzu akan ƙayyadewarsa, kamar siffanta Shi - tsarki ya tabbatar maSa - da cewa Shi Yana yiwa maƙiyanSa makirci idan suka yi makirci, Yana mantawa da maƙiyanSa idan sun manta da Shi.
Daga siffofinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: Sani, da ji, da gani, da rayuwa, da tabbatuwa, da zance, Shi abin siffantawa ne da zance kafin Ya halicci halitta Ya yi magana da su, kuma zancen Ubangijinmu mai rataya ne da ganin damar Sa, a duk lokacin da Ya so zai yi magana. Haƙiƙa dalili ya zo game da siffar zance ga Allah a cikin al-Kur'ani ta fuskoki da dama, ya zo cewa Shi Yana magana da bayinSa, Yana sirri Yana kiran wanda Ya so daga cikinsu, zai yi magana da halittu ranar lahira, kuma halittu zasu ji zancen Allah ranar lahira.
Muna imani cewa Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - haƙiƙa Ya sa hijabi daga bayinSa na wani haske, ba za su ganShi a duniya ba, duk da wasu daga annabawanSa sun ji zancenSa lokacin da Ya yi magana da su ta bayan shamaki, kamar yadda Ya yi magana da (annabi) Musa - aminci ya tabbata agare shi -.
Zancen Ubangijinmu ana siffanta Shi da cewa sashinsa ya fi dayan zama sabo, kuma sashinsa ya fi sashi.
Daga zancenSa: AlKur'ani, da dukkanin littattafan Allah waɗanda ya saukar ga manzanninSa, kamar litattafan (annabi) Ibrahim da (annabi) Musa - aminci ya tabbata agare su -, da Attaura da Injila, da Zabura dukkaninsu zancen Allah ne, kuma dukkaninsu Allah Ya yi magana da su Jibrilu ya ji su daga gareShi babu wasiɗa (wani a tsakani), kuma Jibrilu ya sauko da su ga annabawan Allah da manzanninSa - aminci ya tabbata agare su -. Attaura ta keɓanta da cewa Allah Ya saukar da ita arubuce a alluna - kuma zancen Allah da kalmominSa ba halittarsu aka yi ba, kuma zancen Allah ba halittarSa ba ce, ba ka ganin cewa Shi Ya banbance tsakanin halitta da umarni, zamu banbance tsakanin kalmomin Allah na kasantuwar duniya, da kalmomin Sa na shari'a.
Daga siffofinSa - tsarki ya tabbatar masa Ya ɗaukaka -: Buwaya, da rinjaye, da jabrut, da malakut, da Ji da isa, da girma, da nufi, da ganin dama, da iko, da rahama, wannna rahamar siffa ce daga siffofinSa, ita raɓawa ce ga Allah raɓawar sifa ga wanda aka siffanta.
Daga siffofinSa: Daukakar rinjaye, da ɗaukakar iko, da ɗaukakar zati, ukun dukkaninsu siffarSa ce masu nuni akan cikarSa, haƙiƙa alKur'ani mai girma da sunnah maɗaukakiya da hankali da kuma ɗabi'a sun yi nuni akan ɗaukaka ta fuskoki masu yawa, kai dalilai masu nuni akan cewa Allah Yana sama nau'o'i ne masu yawa, ƙarƙashin kowane nau'i akwai ɗaiɗaiku masu yawan da ba za su iya iyakantuwa ba.
daga cikin siffofinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: Daidaituwa akan Al'arshi, haƙiƙa Allah Ya ambace shi a gurare bakwai a cikin Alkur’ani.
Daga siffofinSa - tsarki ya tabbatar maSa -: Soyayya. Daga siffofinSa: Yarda. Daga siffofinSa: Kiyayya ga maƙiyanSa; domin cewa su sun ƙi yardarSa, kuma sun ƙi abinda Allah Ya saukarwa manzonSa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -.
Daga siffofinSa: Fushi akan maƙiyanSa da ƙiyayya: Shi ne ƙiyayyarSa ga kafirai.
Daga siffofinSa: Makirci ga maƙiyanSa waɗanda suke yi wa masoyanSa makirci. Daga cikinsu: Takaici, shi ne mafi tsananin fushi. Daga siffofinSa: Yaudarar wanda ya yaudareShi, Allah Yana yaudarar munafukan da suke yaudararSa. Daga cikin siffofinSa - Maɗaukaki - cewa Shi Yana izgili ga wanda Yake yi maSa izgili - tsarki ya tabbatar masa Ya ɗaukaka -.
Daga siffofinSa: Dariya, da mamaki, da zuwa ranar lahira dan yanke hukunci tsakanin mutane.
Muna imani da siffar saukowa, kuma cewa Ubangijinmu Yana sauka zuwa saman duniya sauka ta haƙiƙa da ta dace da ɗaukakarSa da girmanSa. Shi ba kamar saukar halittu ba, kai shi kamar sauran siffofin Sa ne, muna imani da su, kuma muna saninsu, ba ma ɗorawa kanmu sanin yadda suke, ko mu ɗorawa kanmu dawo da su; kai muna imani dasu kamar yadda manzonmu mai gaskiya abin gasgatawa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bada labarin da su.
Muna imani da siffar (Ma'iyya) ga Allah Ubangijin talikai, kuma Allah Yana tare da halittarSa. Wannan Ma'iyyar ɗin nau'i biyu ce: Ma'iyya (Tare) keɓantacciya, wannan tana kasancewa ne ga masoyan Allah da manzanninSa - aminci ya tabbata agare su - kuma abinda take hukuntata wa shi ne nasara da ƙarfafawa. Da kuma (Tare) Ma'iyya gamammiya tare da halitta gaba ɗayansu, muminansu da kafiransu, abinda take hukuntata wa : Sani, da kewayewa, da iko, da sarauta.
Wannan Ma'iyyar ba ta wajabta sauka ko cakuɗuwa, kuma ba ta kore ɗaukakar Allah - Maɗaukakin sarki -; domin cewa ma'anarta da haɗuwar ma'abota ilimi (shi ne): Sani da kewayewa; wato: Cewa Allah - Maɗaukakin sarki - Yana tare da mu da saninSa da kewayewarSa da kuma ikonSa.
Kuma muna tabbatarwa Allah fuskar da ta dace da ɗaukakarSa da girmanSa, da hannun da ya dace da ɗaukakarSa da cikarSa, haƙiƙa labari game da su ya zo a cikin alKur'ani da sunnah ta fuskoki masu yawa, haƙiƙa ambatan hannu ya zo guda biyu, kuma cewa Allah Yana dunƙulesu Yana shinfiɗa su, kuma cewa Ubangiji Yana ninke sammai da su da ƙasa a cikin damƙarSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -, kuma cewa hannu abin siffantawa ne da cewa shi yana da yatsu, dukkanin wannan yana tabbatar da cewa hannun da siffarsa ta zo a cikin alKur'ani da sunnah hannu ne na haƙiƙa wanda ya dace da girmanSa, kada mudorawa kanmu tawilinsu, ko kamantasu, ko canza ayoyin da hadisan da suke nuni akan haka. Daga siffofinSa: Siffar yatsu.
Muna imani da ganin da muminai za su yi wa Ubangijinsu ranar lahira, wannan yana daga abinda Alkur’ani ya tabbatar ne, kuma hadisai daga manzon mu - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - suka jerantu a zuwa a cikin abinda ya yi wa muminai bushara da shi cewa su za su ga Ubangijinsu ido da ido ranar lahira.
Kamar yadda Ya siffanta kanSa da siffofin cika da kyau da girma da buwaya da ji da isa, haƙiƙa Ya korewa kanSa siffofin tawaya, amma korewa a cikin siffofin bai zama shi ne asali ba a cikin Alkur’ani mai girma da sunnah; domin cewa asali shi ne tabbatar da siffofi, alKur'ani da sunnah a cike suke da bayanin siffofin Allah - Mai girma da ɗaukaka - kamar yadda ya kamata da ɗaukakarSa da girmanSa da cikarSa, Ubangiji - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka idan Ya korewa kanSa wata sifa kawai Yana koreta ne; dan bayanin cika a kishiyarta, ko dan cewa mutane sun danganta tawaya zuwa ga ma'abocin buwaya da cika, to Ubangiji Ya kore tawayar da aka danganta maSa.
Muna imani cewa Allah - tsarki ya tabbatar masa Ya ɗaukaka - Yana da kyawawan sunaye, kuma cewa sunayenSa sun kai matuƙa a kyau, babu abinda ya kai su zama mafi kyau, kowanne sunan da aka tsagoshi ga Allah sifa ne gareShi, kuma sunayenSa ba su da adadi.
Kuma Ubangijinmu Ya gargaɗe mu daga ilhadi a cikin sunayenSa, ko musunsu, ko musun ma'anoninsu, ko kore su.
Abin da ya zo a cikin Alkur’ani da Sunnah daga sunayen Allah da siffofinSa sun fi karfin ace wani littafi ya kunshe su, mu muna imani da waɗannan sunayen da siffofin akan nufin Ubangijinmu, da kuma nufin manzonmu - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, kuma muna sanin cewa haƙiƙaninsu mutane ba su san su ba, kuma ba su kewaye da saninsu ba, kuma fahimtarsu ba ta kai garesu ba, kuma bama ɗorawa kanmu tawilinsu.
BABIN IMANI DA SAMUWAR ALLAH
Muna imani cewa Allah Shi ne farko babu wani abu kafinSa, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Shi ne Na farko Na ƙarshe, Bayyane, ɓoyayye} [al-Hadid: 3]. Kuma Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Allah Ya kasance alhali babu wani abu waninSa, Al'arshinSa ya kasance akan ruwa". (Bukhari ne (7418), da Tirmizi (3951).) suka fitar da shi Bukhari ya fitar da shi daga Hadisin Imrana ɗan Hussain a cikin wata riwayar tasa - kuma: "Allah Ya kasance alhali babu wani abu waninSa, Al'arshinSa ya kasance akan ruwa". (Bukhari ne ya fitar da shi (3191)). Kuma Ya sanar damu kanSa cewa Shi ne wanda Ya halicci sammai da ƙasa, kuma cewa Shi ne Mamallakin sammai da ƙasa, kuma cewa Shi Yana shigar da dare a cikin rana, Yana shigar da rana a cikin dare - tsraki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Shĩ ne (Allah) wanda Ya halitta sammai da ƙasa a cikin wasu kwãnuka shida, sannan Ya daidaitu a kan Al'arshi, Yanã sanin abin da ke shiga cikin ƙasa da abin da ke fita daga gare ta, da abin da ke sauka daga sama da abin da ke hawa cikinta, kuma Shĩ yanã tare da ku duk inda kuka kasance. Kuma Allah Mai gani ne ga abin da kuke aikatãwa * Shĩ ne da mulkin sammai da ƙasa, kuma zuwa gare Shĩ (Allah) kawai ake mayar da al'amura * Yanã shigar da dare a cikin yini, kuma Yanã shigar da yini a cikin dare, kuma Shi Masani ne ga abin da yake a cikin ƙirãza} [al-Hadid: 4-6].
Kuma Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya ƙarfafa cewa wannan kasantaccen da ake gani mai shaida ne akan cewa Shi ne Mai samarwa , Mahalicci Shi kaɗai yake, babu wani Mahalicci tare daShi, Allah Ya ce: {Wannan ita ce halittar Allah. To ku nuna mini, mene ne waɗannan da ba shi ba suka halitta?} [Luƙman: 11]?!. Saboda haka ne, haƙiƙa Ya ambaci dalilai masu yawa daga ayoyinSa masu nuni akan cewa Shi, Shi ne Mai samarwa Mahalicci ga wannan kasantacce, Daga cikinsu: Cewa Shi ne Yake fitar da mai rai daga matacce, kuma Yana fitar da matacce daga mai rai. Daga cikinsu: Cewa Shi ne Ya halicci mutane daga turɓaya. Daga cikinsu: Cewa Shi Ya halitta mana mataye daga kawunan mu. Daga cikinsu: Saɓanin harsuna da launuka a cikin halitta. Daga cikinsu: Baccin bayi da daddare da kuma neman arziƙinsu da rana. Daga cikinsu: Cewa Shi yana sanya walƙiya sababi ne dan tsoratarwa da kwaɗaitarwa, kuma cewa Shi Yana saukar da ruwa daga sama. Daga cikinsu: Cewa Shi Ya fari halitta, kamar yadda ya bonSa ya ɗaukaka Ya ce: Yanã fitar da mai rai daga matacce kuma Yanã fitar da matacce daga mai rai, kuma Yanã rãyar da ƙasa a bãyan mutuwarta. Kuma haka ake fitar da ku * Kuma akwai daga ãyõyinSa, Ya halitta ku daga turɓãya, sai gã ku kun zama mutum, kunã wãtsuwa * Kuma akwai daga ãyõyinsa, Ya halitta muku mãtan aure daga kanku, dõmin ku natsu zuwa gare ta, kuma Ya sanya sõyayya da rahama a tsakãninku. Lalle a cikin wancan akwai ãyõyi ga mutãne mãsu yin tunãni * Kuma akwai daga ãyõyinSa halittar sammai da ƙasã da sãɓãwar harsunanku, da launukanku. Lalle a cikin wannan akwai ãyõyi ga mãsu ilmi * Kuma akwai daga cikin ãyõyinSa, barcinku a cikin dare da rãna, da nẽmanku ga falalarsa. Lalle a cikin wannan akwai ãyõyi ga mutãne mãsu saurãrãwa * Kuma akwai daga cikin ãyõyinSa, Ya nũna muku walƙiya a kan tsõro da ɗammãni kuma Ya dinga saukar da ruwa daga sama Sa'an nan Ya rãyar da ƙasã game da shi a bãyan mutuwarta. Lalle a cikin wannan akwai ãyõyi ga mutãne mãsu hankaltawa * Kuma akwai daga ãyõyinsa, tsayuwar sama da asƙã bisa umurninsa, sa'an nan idan Ya kira ku, kira ɗaya, daga ƙasã, sai gã ku kunã fita * Kuma wanda ke cikin sammai da ƙasã Nãsa ne shi kaɗai. Dukansu mãsu tawãli'u ne a gare Shi * Kuma Shi ne wanda Yake fara yin halitta sa’annan Ya dawo da ita, kuma (dawowar) tafi sauki a gare Shi} [al-Rum: 19-27].
Daga hakan - kuma: Cewa Shi Ya tsaida hujja akan halitta da cewa Shi ne Ya haliccesu daga rai ɗaya, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Yã halitta ku daga rai guda, sa'an nan Ya sanya ma'auranta daga gare shi. Kuma ya saukar muku daga dabbõbin gida nau'i takwas, Yanã halitta ku a cikin cikunnan uwayenku, halitta a bãyan wata halitta, a cikin duffai uku. Wannan shĩ ne Allah Ubangijinku. Mulki a gare shi yake. Bãbu abin bautãwa fãce Shi. To, yãya ake karkatar da ku?} [al-Zumar: 6]. Sai Ya ambaci fara halitta, kuma cewa dabbobin ni'ima dukkaninsu ababen halitta ne gareShi - tsarki ya tabbatar maSa -, sannan Ya tsaida hujja akanmu da cewa Shi ne Ya haliccemu a cikin mahaifa a cikin duffai, kuma cewa waninSa ba ya iya halittar maniyyi a matsayin mutum.
A ayoyin da suka gabata sai Ya ambaci dalili daga mafi girman dalilai akan samuwarSa - shi ne halittarSa ga sammai da ƙasa da abinda ke cikinsu da abinda ke samansu.
Daga hakan - kuma: Cewa Shi Ya tsaida hujja akan halitta da dalilin kulawarSa da su da abinda suke samunsa a cikin rayukansu da zuriyarsu, shi ne cewa shi Ya fitar da su daga cikkunan iyayensu ba sa sanin komai, kuma Ya alƙawartan da su har halittarsu da iliminsu suka cika, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma Allah ne Ya fitar da ku daga cikunan iyãyenku, ba da kunã sanin kõme ba, kuma Ya sanya muku ji da gannai da zukãta, tsammãninku zã ku gõde} [al-Nahl: 78]. Kamar yadda Ya samar da kowane abu Ya kuma tanade shi, to haƙiƙa Ya shiryar da dukkanin halittarSa ga abinda ke cikinsa na gyaruwarsu, Maɗaukakin sarki Ya ce Yana Mai bada labari game da Fir'auna cewa shi ya ce: {Ya ce: "To, wãne ne Ubangijinku? Ya Mũsã!} [Daha: 49]. Sai amsar Ubangiji ta zama: {Ya ce: "Ubangijinmu Shi ne wanda Ya bai wa dukan kõme halittarsa, sa'an nan Ya shiryar} [Daha: 50].
Muna imani cewa Shi - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya miƙar da ƙasa, Ya sanya duwatsu tabbatattu a cikinta, Ya tsirar da kowanne abu a abin aunawa a cikinsu da sikeli. To aunawa abin gani a cikinsu akwai mafi alherin mai shaida akan cewa Sh, Shi ne Mai samarwa, kamar yadda cewa saukar da ruwa akan keɓantacciyar siffa mutane ba za su iya saukar da shi ba, ko su taskance abinda ya sauka daga ruwa, to wannan mai shaida ne akan cewa Mai samarwa Shi ne Allah Daya Mai rinjayarwa, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma ƙasa Mun mĩkẽ ta kuma Mun jẽfa duwãtsu tabbatattu a cikinta kuma Mun tsirar a cikinta, daga dukan abu wanda ake aunãwa da sikẽli * Kuma Muka sanyã muku, a cikinta, abũbuwan rãyuwã da wanda ba ku zamã mãsu ciyarwa gare shi ba * Kuma bãbu wani abu fãce a wurinMu, akwai taskõkĩnsa kuma ba Mu saukar da shi ba fãce kan gwargwado sananne * Kuma Muka aika iskõki mãsu barbarar jũna sa'an nan Muka saukar da ruwa daga sama, sa'an nan Muka shãyar da ku shi, kuma ba ku zama mãsu taskacẽwa a gare shi ba} [al-Hijr: 19-22].
Muna imani da abinda annabawa da manzanni suka yi imani da shi, kuma muna sakankancewa da abinda suka zo da shi na dalilai da hujjoji masu nuni akanSa - tsarki ya tabbatar maSa -, kamar yadda Allah Ya bada labarin cewa (annabi) Ibrahim - aminci ya tabbata agare shi - Ya kafawa Namaruzu hujja da cewa Allah Yana zuwa da rana daga gabas waninSa kuwa ba zai iya zuwa da ita daga yamma ba, Maɗaukakin sarki Ya ce: {(Annabi) Ibrahim ya ce Ubangijina Shi ne wanda Yake rayawa kuma Yake kashewa, ya ce to ni ina rayawa ina kashewa, (annabi) Ibrahim ya ce to Allah Ya na zuwa da rana daga gabas to kai ka zo da ita daga yamma} [al-Baƙara: 258].
Haka kuma (Annabi) Ibrahim -amincin Allah ya tabbata a gare shi ya kafawa mutanensa hujja cewa; Allah Shi ne wanda Ya shiryar da shi, kuma Ya ciyar da shi, kuma ya shayar da shi, idan ya yi rashin lafiya Ya warkar da shi, kuma Shi ne wanda Yake kashe shi kuma Yake raya shi, sai ya ce: kamar yadda Allah Ya bada labari game da shi: {Wanda Ya halitta ni, sa'an nan Yanã shiryar da ni * "Kuma Wanda Yake Shĩ ne Yake ciyar da ni, kuma Yanã shãyar da ni * Kuma idan na yi rashin lafiya, to, Shĩ ne Yake warkar da ni * Kuma wanda Yake matar da ni, sa'an nan Ya rãyar da ni} [al-Shu'araa: 78-81]. Kuma Allah - Madaukakin sarki - Ya bada labarin (Annabi) Musa cewa shi ya yi jayayya da Fir'auna yana mai cewa masa: Ubangijinsa Shi ne: [Wanda Ya bawa kowanne abu halittarsa sannan kuma Ya shiryar} [Daha: 50]. Ya zo a cikin Alkur’ani cewa Allah Ya tsarkake kanSa daga dukkanin tawaya, kuma Ya sanar da mu kanSa, sai tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya ce: {Ka tsarkake sũnan Ubangijinka Mafi ɗaukaka * Wanda Yã yi halitta sannan nan Ya daidaita abin halittar * Kuma Wanda Ya ƙaddara (abin da Ya so) sannan Ya shiryar, (da mutum ga hanyar alhẽri da ta sharri)}. [al'Aala: 1-3].
Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya kafa hujja akan cewa Shi ne Mai halittawa Mai samar da wannan kasantaccen kuma babu wani Mahalicci waninSa - da cewa Shi ne wanda Ya tsirar da gonakai masu kyau, kuma mutane ba za su iya tsiro da bishiya ba. Kamar yadda Ya kafa hujja akan cewa Shi Ya sanya ƙasa matabbaciya, kuma Ya sanya ƙoramai da duwatsu matabbata a cikinta, sannan Ya sanya makariya tsakanin koguna biyu; dan kada wannan ya cakuɗa da wannan. Kuma cewa Shi ne kaɗai wanda Yake amsawa mai buƙata idan ya kiraShi - koda ya kasance ba Musulmi ba ne - kuma cewa Shi ne wanda Yake shiryar da mutane a duffan tudu da kogi, kuma cewa Shi ne wanda Yake aiko da iska tana mai bushara kafin saukar ruwa, kuma cewa Shi ne wanda Yake azirta mu, babu wani mai azirtawa waninSa, kuma babu wani Ubangiji wanda baShi ba babu wani Mahalicci waninSa, Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya ce: Kõ wãne ne Ya halitta sammai da ƙasa kuma Ya saukar muku, daga, sama, wani ruwa, Muka tsirar, game da shi, gõnaki mãsu sha'awa, ba ya kasancẽwa gare ku, ku tsirar da itãcensu? Shin, akwai abin bautãwa tãre da Allah? Ã'a, sũ mutãne ne suna daidaitãwa (Allah da wani) * Kõ kuwa wãne ne Ya sanya ƙasa tabbatacciya, kuma Ya sanya kõguna a tsakãninta kuma Ya sanya mata manyan duwãtsu tabatattu, kuma Ya sanya wani shãmaki a tsakãnin tẽkuna biyu? Shin akwai wani abin bautãwa tãre da Allah. Ã'a, mafi yawansu ba su sanĩ ba * Kõ wãne ne yake amsawa mabukaci, kuma yake yaye damuwa, kuma ya sanya ku mamãyan ƙasa? Shin akwai wani abin bautawa tãre da Allah? Kaɗan ƙwarai kuke yin tunãni * Kõ wãne ne yake shiryarwa a cikin duffan ƙasa da tẽku, kuma wãne ne Yake aikõwar iskõki dõmin bãyar da bushãra a gaba ga rahamarSa? Ashe akwai wani abin bautãwa tãre da Allah? tsarki yã tabbata ga Allah daga barin abin da suke shirki da Shi * Kõ wãne ne yake fãra halitta sannan kuma ya mayar da ita, kuma Wãne ne Ya azurta ku daga sama da ƙasa? Ashe, akwai wani abin bautãwa tãre da Allah? Ka ce: "Ku kãwo dalĩlinku idan kun kasance mãsu gaskiya} [al-Naml: 60-64].
Allah - Maɗaukaki kuma sunayenSa sun tsarkaka Ya ce: {Kuma shĩ, ne wanda Ya shimfiɗa kasa, kuma Ya sanya duwãtsu da kõguna a cikinta, kuma daga dukan 'ya'yan itãce Ya sanya ma'aura biyu cikinsu. Yanã sanya dare ya rufe yini. Lalle ne a cikin wancan, haƙĩƙa akwai ãyõyi ga mutãne waɗanda suke yin tunãni * Kuma a cikin ƙasa akwai yankuna mãsu maƙwabtaka, da gõnaki na inabõbi da shũka da dabĩnai iri guda, da waɗanda bã iri guda ba, anã shayar da su da ruwa guda. Kuma Munã fĩfĩta sãshensa a kan sãshe a wajen ci. Lalle ne a cikin wancan akwai ãyõyi ga mutane waɗanda suke hankalta} [al-Ra'ad: 3-4]. Sai Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya tabbatar da cewa Shi ne kaɗai wanda Ya miƙar da ƙasa, kuma Ya halicci daga kowanne bishiyoyi da 'ya'yan itatuwa jinsi bibiyu, kuma cewa Shi ne kaɗai wanda Yake rufe dare da rana. Kuma Ya kafa hujja akan hakan da cewa yanki na ƙasa mai maƙotaka suna fitar da 'ya'yan marmari masu kamanceceniya da juna da waɗanda ba sa kamanceceniya da juna, alhali su ana shayar da su da ruwa ɗaya, tsarki ya tabbatarwa Allah wanda babu wani Ubangiji waninSa, kuma babu wani Mahalicci wanda baShi ba.
Kuma Ya bayyana cewa duwatsu - tare da taurinsu - a cikinsu akwai ƙayatacciyar halitta, a binda yake nuni akan ƙayatarwar Mahalicci, sai Maɗaukakin sarki Ya ce: {Daga duwatsu akwai hanyoyi farare da jajaye mabanbantan launuka da baƙaƙe ƙirin} [Faɗir: 27].
Daga hakan abinda Maɗaukakin sarki Ya bayyana shi garemu na cewa Shi ne wanda Ya halicci waɗannan duniyoyin gaba ɗayansu, kuma Ya sawwake su ga mutum, daga hakan jiragen ruwa suna tafiya a cikin kogi, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Allah ne wanda Ya hõre muku tẽku dõmin jirgi ya gudãna a cikinta da umurninSa, kuma dõmin ku nẽma daga falalarSa, kuma tsammãninku zã ku gõde * Kuma Ya hõre muku abin da ke a cikin sammai da abin da ke a cikin ƙasa, gabã ɗaya daga gare Shi yake. Lalle ne, a cikin wancan, haƙĩƙa, akwai ãyõyi ga mutãne waɗanda ke yin tunãni} [al-Jathiya: 12-13].
Kuma tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya nuna mana samuwarSa da cewa Ya sanya mana abin hawa da tufa da abubuwan ci da abubuwan sha daga waɗannan dabbobin ni'imar, kuma cewa Shi ne Yake riƙe tsuntsaye a sararin samaniya, Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya ce: {Shin ba su ga tsuntsãye ba sunã hõrarru cikin sararin sama bãbu abin da yake riƙe su fãce Allah? Lalle ne a cikin wancan haƙĩƙa, akwai ãyõyi ga mutãne waɗanda suke yin ĩmãni * Kuma Allah ne Ya sanya muku daga gidajenku wurin natsuwa, kuma Ya sanya muku daga fatun dabbõbin ni'ima wasu gidãje kunã ɗaukar su da sauƙi a ranar tafiyarku da rãnar zamanku, kuma daga sũfinsu da gãshinsu da gẽzarsu (Allah) Ya sanya muku kãyan ɗãki da na jin dãɗi zuwa ga wani lõƙaci * Kuma Allah ne Ya sanyã muku inuwa daga abin da Ya halitta, kuma Ya sanyã muku ɗãkuna daga duwãtsu, kuma Ya sanyã muku waɗansu riguna sunã tsare muku zãfi, da waɗansu rĩguna sunã tsare muku makãminku. Kamar wancan ne (Allah) Yake cika ni'imarSa a kanku, tsammãnin ku, kuna sallamawa} [al-Nahl: 79-81]. Dukkanin waɗannan dalilan masu shaida ne akan samuwarSa da RububiyyarSa, waye wanda Ya samar da su sai Shi, tsarki ya tabbatar maSa?! Babu mai samarwa waninSa, kuma babu wani Ubangiji waninSa.
Kuma Ya tsayar mana da wani mai shaida mai girma da yake maimaituwa a kowacce rana, Yana shaida akan samuwarSa da RububiyyarSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -; shi ne: CewaShi Ya tsaga asuba, kuma Ya tsaga ƙwaya da kwalfar gurtsu, tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka ya ce: {Lalle ne, Allah ne Mai tsãgewar ƙwãyar hatsi da kwalfar gurtsu. Yanã fitar da mai rai daga mamaci, kuma (Shi) Mai fitar da mamaci ne daga mai rai, wannan ne Allah. To, yãya ake karkatar da ku * Mai tsãgẽwar sãfiya, kuma Ya sanya dare mai natsuwa, kuma da rãna da watã a bisa lissãfi. wannan ne ƙaddarãwar Mabuwãyi Masani} [al-An'am: 95-96].
Kamar yadda Ya sanya rana da wata ayoyi biyu, Ya sanya dare da rana ayoyi biyu masu nuni akan samuwarSa da RububiyyarSa, Maɗaukakin sarki ya ce: {Mun sanya dare da rana ayoyi biyu sai muka shafe ayar dare kuma muka sanya ayar rana mai gani} [al-Isra'a: 12].
Allah - Maɗaukkain sarki - Ya bayyana cewa yadda ya sanya kogi (ruwa) mai daɗi komai zartsi, kuma nama yana sabo, dakayan ado - dalili ne akan samuwarSa, tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya ce; {Kuma Shĩ ne Ya hõrẽ tẽku dõmin ku ci wani nama sãbõ daga gare shi, kuma kunã fitarwa, daga gare shi, ƙawã wadda kuke yin ado da ita. Kuma kuna ganin jirãge sunã yankan ruwa a cikinsa kuma dõmin ku yi nẽman (fatauci) daga falalarSa. Kuma mai yiwuwa ne kuna gõdẽwa} [al-Nahl: 14]. Allah - Madaukakin sarki - Ya ce: {Kuma shĩ ne Ya gauraya tẽkuna biyu, wannan mai dãdi, mai sauƙin haɗiya, kuma wannan gishiri gurbatacce, kuma Ya sanya wani shãmaki a tsakãninsu da kãriya mai shãmakacẽwa} [al-Furƙan: 53].
Haƙiƙa Allah - Maɗaukakin sarki - Ya bayyana cewa hankula suna riskar cewa ba zai yi wu a sami wannan kasantaccen ba, ba tare da Mai samarwa ba, sai tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya ce: {Shi ne wanda Yake rayawa Yake kashewa, kuma saɓanin dare da rana na gareShi, shin bakwa hankalta ba} [al-Mua'Munun: 80]. Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Ya ce: "Shin to, kunã bautã wa abin da, bã ya, amfãnin ku da Kõme kuma bã ya cũtar da ku baicin Allah * "Tir da ku, kuma da abin da kuke bauta wa, baicin Allah! Shin to, bã ku hankalta} [al-Anbiya: 66-67]. Shin ka ga mafi girma daga waɗannan dalilan masu nunarwa akan samuwarSa da RububiyyarSa - tsarki ya tabbatar masa Ya ɗaukaka -?!
Kuma Allah ya yi inkari akan wanda ya danganta halitta zuwa waninSa, kuma Ya tambayesu tambaya ta ƙure da inkari: Shin an haliccesu ne daga babu? Ko kuma su ne suka halicci kawunansu, kuma suka halicci sammai da ƙasa? Ko kuma akwai taskokin Allah a wurinsu ne? ko kuma su ne masu karfin iko? Allah Ya ce: {Shin, an halitta su ne bã daga kõme ba, kõ kuwa sũ ne mãsu yin halitta * Shin, sun halitta sammai da ƙasa ne? Ã'a ba su dai yi ĩmãnin yaƙĩni ba * Shin, taskõkin Ubangijinka, sunã a wurinsu ne? Kõ kuwa sũ ne mãsu rinjãya?} [al-Dur: 35-37]. Wannan ayar tana daga mafi girman ayoyi masu nuni akan samuwar Mahalicci; saboda haka ya tabbata cewa Jubairu Dan Muɗ'im ya ce: Na ji Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana karanta Dur a magariba, lokacin da yakai wannan ayar: {Shin, an halitta su ne bã daga kõme ba, kõ kuwa sũ ne mãsu yin halitta * Shin, sun halitta sammai da ƙasa ne? Ã'a ba su dai yi ĩmãnin yaƙĩni ba * Shin, taskõkin Ubangijinka, sunã a wurinsu ne? Kõ kuwa sũ ne mãsu rinjãya?} Ya ce: "Zuciyata ta kusa ta tashi". (Bukhari ne ya fitar da shi (4854), da Muslim (463), da Abu Dawud (811), da Nasa'i (987), da Ibnu Majah (832).) Jin Jubairu - Allah Ya yarda da shi - ya kasance ga wannan ayar kafin ya musulunta ne, sai ya bayyana cewa su ababen halitta ne ababen raino ne ababen rinjaye ne, tsarki ya tabbatarwa Allah daga abinda suke siffantawa.
Allah - Madaukakin sarki - Ya ce: {Ban shaida musu halittar sammai da ƙasa ba, kuma ban (shaida musu) halittar rãyukansu ba kuma ban kasance mai riƙon mãsu ɓatarwa (da wani) su zama mataimaka ba} [al-Kahf: 51]. Idan mutum ya jahilci halittar sammai ya jahilci halittar kansa, to tayaya yake inkarin mahaliccinsa kuma wanda ya samar da shi?
Muna imani cewa Allah bai halicci halittarSa dan wasa ba; kai halitta ce da aka kyautatata dan manufa babba, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Kuma ba Mu halitta sama da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu Muna Mãsu wãsã ba * Da Mun yi nufin Mu riƙi wani abin wãsa dã Mun riƙe shi daga gunMu, idan Mun kasance mãsu aikatãwa} [al-Anbiya: 16-17].
Kuma Ya yi wa Nasara martani akan da'awarsu cewa Masihu Allah ne mahalicci, kuma ubangiji ne mai jujjuya wannan halittar. Kuma Ya bayyana cewa Allah wani abu ba ya ɓuya gareShi a ƙasa ko a cikin sama, kuma cewa Shi ne wanda Yake suranta mutum a cikin mahaifu, daga cikin waɗanda Allah Ya halicce shi kuma Ya suranta shi a cikin mahaifa: Masihu - aminci ya tabbata agare shi -, sai Allah - Maɗaukakain sarki - Ya ce; {Lalle ne, Allah bãbu wani abin da ke ɓõyuwa gare Shi a cikin ƙasa, kuma bãbu a cikin sama * Shi ne wanda Yake suranta ku a cikin mahaifu yadda Yake so. Bãbu abin bautãwa fãce Shi Mabuwãyi, Mai hikima} [Aal- Imran: 5-6]. Da ma wanin haka na abinda ya zo da yawa a cikin Alkur’ani mai girma - kamar yadda ya zo a cikin "Suratul An'am" da "al-Nahl" da wasunsu - daga dalilan da ba za su ƙirgu ba, da shaidun da ba za su taƙaitu ba, kuma dukkaninsu masu nuni ne akan samuwarSa da RubibiyyarSa.
BABIN IMANI DA RUBUBIYYAR ALLAH. (Kadaita Allah a ayyukan Sa).
Muna imani cewa Allah Shi kaɗai yake a cikin RububiyyarSa, kuma Shi ne Mahalicci Shi kaɗai, Shi ne wanda Ya fara halitta, babu wani da ya yi tarayya da shi a cikin halittarsa, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce; {Allah ne ke fãra yin halitta, sannan Ya sãke ta sa'an nan zuwa gare Shi ake mayar da ku} [al-Rum: 11]. Tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya ce: {Ka ce: "Shin, daga abũbuwan shirkarku akwai wanda yake fãra halitta, sa'an nan kuma ya mayar da ita?" Ka ce: "Allah ne Yake fãra halitta, sa'an nan kuma Ya mayar da ita. To, yãyã akejũyar da ku?} [Yunus: 34].
Kuma cewa Allah Yana halitta da umarninSa - tsarki ya tabbatar maSa -, Maɗaukakin sarki Ya ce: {UmurninSa idan Yã yi nufin wani abu sai Ya ce masa kawai, "Ka kasance," sai yana kasancewa (kamar yadda Yake nufi)} [Y. S̃: 82]. Tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Yana halittar abinda Ya so na sabubba, Allah - tsarki ya tabbatar masa - Ya ce: {Sai muka fitar da shi biyu-biyu daga tsirrai mabanbanta} [Daha: 53]. Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Daga dukkanin 'ya'yan itatuwa Ya sanya biyu-biyu} [al-Ra'ad: 3]. Allah - Maaaukakin sarki - Ya ce: {Kuma daga kõme Mun halitta nau'ibiyu, watakila zã ku yi tunãni} [al-Zariyat: 49].
Kuma tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya bada labarin cewa Shi ne Ya halicci kowanne abu, dukkanin wanda baShi ba to Shi abin halitta ne, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Allah ne Mai halitta dukan kõme, kuma Shĩ ne Wakĩli a kan kõme} [al-Zumar: 62].
Muna imani cewa Allah Shi ne Ubangijin kowanne abu kuma MahaliccinSa Mai jujjuyaShi, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Yã ku mutãne! Ku bauta wa Ubangjinku, Wanda Ya halicce ku, kũ da waɗanda suke daga gabãninku, tsammãninku ku kãre kanku * Shi ne wanda Ya sanya muku ƙasa shinfiɗa sama kuma gini, kuma Ya saukar da ruwa daga sama sai Ya fitar da shi wani arziƙi gareku daga 'ya'yan itatuwa} [al-Baƙara: 21-22]. Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Lallai Ubangijinku Shi ne Allah wanda Ya halicci sammai da ƙasa a cikin kwana shida sannan Ya daidaita akan Al'arshi} [Yunus: 3]. To Shi - tsarki ya tabbatar masa Ya ɗaukaka - Mahaliccin sammai da ƙasane kuma Mamallakinsu, Shi ne Mai tasarrufi a cikinsu, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Shĩ ke da mabũɗan sammai da ƙasã. Kuma waɗanda suka kãfirta da ãyõyin Allah, waɗannan sũ ne masu hasãra} [al-Zumar: 63]. Wani abin halitta ba ya mallakar jujjuya al'amarin kansa ko jujjuya al'amarin waninSa sai abinda Allah Ya ba shi iko akansa, ba mala'iku ba, ba annabawa ba - aminci ya tabbata garesu, baga waliyyai ba , ba za su iya tasarrufi a cikin kasantacce ba ko jawo amfani ko tunkuɗe cuta, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Ka ce: "Ku kirãyi waɗanda kuka riya (cẽwa abũbuwan bautãwa ne) baicin Allah, bã su Mallakar ma'aunin zarra a cikin sammai, kuma bã su Mallakarsa a cikin ƙasa kuma bã su da wani rabon tãrẽwa a cikinsu (sammai da ƙasa), kuma bã Shi da wani mataimaki daga gare su} [Saba'i: 22].
Muna imani cewa Shi ne Mamallaki na gaskiya, wanda ba Shi ba to mallaka ne, kowanne sarki to mulkinsa na ɗan lokaci ne mai gushewa ne, tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya ce: {Mamallakin Rãnar Sakamako} [al-Fatiha: 4]. Tsarki ya tabbatar maSa Ya ce: {Ka ce: "Yã Allah Mamallakin mulki, Kanã bayar da mulki ga wanda Kake so, Kanã zãre mulki daga wanda Kake so, kuma Kanã buwãyar da wanda Kake so, kuma Kanã ƙasƙantar da wanda Kake so, ga hannunKa alhẽri yake. Lalle ne Kai, a kan kõwanne abu, Mai ĩkon yi ne} [Aal- Imran: 26]. Wanda baShi ba abin reno ne kuma abin rinjaye ne, Allah Ya ce: {Dukkan wanda yake a cikin sammai da ƙasa bai zama ba fãce mai jẽ wa Mai rahama ne yanã bãwã} [Maryam: 93].
Muna imani cewa Allah Shi ne wanda Ya halicci sammai da ƙasa, kuma cewa Shi ne Yake shigar da dare akan rana, kuma yake shigar da rana akan dare, kuma cewa Shi ne Ya hore rana da wata, kowanne yana gudana ga wani ajali abin ambata, Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya ce: {Ya halitta sammai da ƙasã da gaskiya. Yanã shigar da dare a kan rãna, kuma Yanã shigar da rãnã a kan dare kuma Yã hõre rãnã da watã, kõwannensu yanã gudãna zuwa ga ajali ambatacce. To, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai gãfara} [al-Zumar: 5]. Kuma cewaShi - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Shi ne wanda Ya sanya rana haske kuma wata haske, Ya sanya saɓanin dare da rana aya mai nuni akan girman halittarSa da kyakkyawan jujjuyawarSa, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Shĩ ne wanda Ya sanya muku rãnã, babban haske, da watã mai haske, kuma Ya ƙaddara shi ga Manzilõli, dõmin ku san ƙidãyar shẽkaru da lissãfi. Allah bai halitta wannan ba, fãce da gaskiya, Yanã bayyana ãyõyi daki-daki dõmin mutãne waɗanda suke sani * Lalle ne a cikin sãɓãwar dare da yini, da abin da Allah Ya halitta a cikin sammai da ƙasa, haƙĩƙaakwai ãyõyi ga mutãne waɗanda suke yin taƙawa} [Yunus: 5-6]. Kuma cewa Shi ne wanda Ya haliccemu daga rai ɗaya, kuma Ya sanya matarsa daga gareshi, Ya halicci dabbobin ni'ima gaba ɗayansu, Allah - yabonSa ya ɗaukaka kuma sunayenSa sun tsarkaka - Ya ce: {Yã halitta ku daga rai guda, sa'an nan Ya sanya ma'auranta daga gare shi (wannan ran). Kuma ya saukar muku daga dabbõbin gida nau'i takwas Yanã halitta ku a cikin cikunnan uwayenku, halitta a bãyan wata halitta, a cikin duffai uku. Wannan shĩ ne Allah Ubangijinku. Mulki a gare shi yake. Bãbu abin bautãwa fãce Shi. To, yãya ake karkatar da ku?} [al-Zumar: 6].
Muna imani cewa Shi ne Mai azirtawa mai ƙarfi, babu wani mai azirtawa waninSa, babu mai isarwa waninSa, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Lalle Allah, Shĩ ne Mai azurtãwa, Mai ĩkon yi, Mai cikakken ƙarfi} [al-Zariyat: 58]. Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma bãbu wata dabba a cikin ƙasa fãce ga Allah arzikinta yake, kuma Yanã sanin matabbatarta da ma'ajiyarta, duka sunã cikin littãfi bayyananne} [Hud: 6].
Muna imani cewa Shi - tsarki ya tabbatar maSa - Ya kewaye kowanne abu da sani, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Yana sanin abinda ke gabansu da abindake bayansu kuma ba sa kewayewa da wani abu daga saninSa sai abinda Ya so} [al-Baƙara: 255]. Babu wani abu da yake ɓuyawa daga saninSa ƙarami ne ko babba, Allah - sha'aninSa ya buwaya kuma sarautarSa ta ɗaukaka - Ya ce: {Masanin gaibi gwargwadon zarra ba ta nisanta daga gare shi a cikin sammai kuma ba ta nisanta a cikin kasa kuma babu mafi girma face yana a cikin Littafi bayyananne} [Saba'i: 3]. SaninSa mai wanda ya game komai ne da kowanne abu a cikin wannan kasantaccen, Allah - sha;aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Kuma a wurinSa mabũdan gaibi suke, babu wanda yake sanin su fãce Shi, kuma Yanã sanin abin da ke a cikin tudu da ruwa, kuma wani ganye ba ya fãɗuwa, fãce Yã san shi, kuma bãbu wata ƙwãya a cikin duffan ƙasã, kuma babu ɗanye, kuma babu ƙẽƙasasshe, fãce yanã a cikin wani Littãfi mai bayyanãwa} [al-An'am: 59]. Kuma Ya ce - ya na Mai bayyanar da wani ɓangare daga wannan sanin mai kewayewa: {Kuma bãbu wata dabba a cikin ƙasa kuma bãbu wani tsuntsu wanda yake tashi da fukafukansa biyu fãce al'umma ne misãlanku. Ba Mu yi sakacin barin kõme ba a cikin Littãfi, sa'an nan kuma zuwa ga Ubangjinsu ake tãra su} [al-An'am: 38].
Muna imani cewa Shi - tsarki ya tabbatar maSa - Masanin gaibu ne da abin da ke bayyane, Allah - tsarki ya tabbatar maSa - Ya ce: {Shi ne Masanin fake da bayyane, Mai girma, Maɗaukaki} [al-Ra'ad: 9]. Kuma ba ya bayyanar da gaibu ga wani cikin halittarSa sai wanda Ya yarda daga manzo, tsarki ya tabbatar masa Ya ɗaukaka - Ya ce: {Shi kaɗai ne Masanin fake sabõda haka, bã Ya bayyana gaibinSa ga kowa * Fãce ga wanda Yã yarda da shi, wato wani manzo sa'an nan lalle ne, zai sanya gãdi a gaba gare shi da bãya gare shi} [al-Jinn: 26-27]. Dukkanin wanda ya yi da'awar sanin gaibu to shi maƙaryaci ne mai ƙirƙirar ƙarya. Manzanni ba su san gaibu ba, Allah Ya umarci annabinSa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: {Ka ce: Bazance muku ina da taskokin Allah ba kuma ban san gaibu ba} [al-An'am: 50].
Muna imani cewa Allah Shi ne Mai rayawa Mai kashewa Shi kaɗai Ya ke - tsarki ya tabbata maSa -, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Lalle ne Allah Yanã da mulkin sammai da ƙasa, Yanã rãyarwa kuma Yanã matarwa. Kuma bã ku da wani masõyi, kuma bã ku da mataimaki, baicin Allah} [al-Taubah: 116]. Allah - tsarki ya tabbatar maSa - Ya ce: {Kuma shĩ ne wanda Ya rãya ku, sa'an nan kuma Yanã matar da ku, sa'an nan kuma Yanã rãyar da ku. Lalle mutum, haƙĩƙa, mai kãfirci ne} [al-Hajji: 66]. Kuma Shi ne wanda Ya halicci mutuwa da rayuwa, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Shi ne Wanda Ya halicci mutuwa da rãyuwa domin Ya jarraba ku, Ya nũna wãye daga cikinku ya fi kyãwon aiki, Shi ne Mabuwãyi, Mai gafara} [al-Mulk: 2]. Kuma cewa Shi ne wanda Yake kashe rayuka, Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya ce: {Allah ne yake kashe rayuka lokacin mutuwarsu} [al-Zumar: 42].
Muna imani cewa Shi Maɗaukakin sarki Ya rinjayi kowanne abu a buwaya da hukunci, kamar yadda Ubangijinmu - Maɗaukakin sarki - Ya bamu labari da faɗinSa: {Kuma sabõda Allah wanda yake a cikin sammai da ƙasa suke yin sujada, so da ƙi, kuma da inuwõyinsu, a sãfe da maraice} [al-Ra'ad: 15]. Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Rãnar da suke bayyanannu, bãbu wani abu daga gare su wanda yake iya bõyuwa ga Allah. "Mulki ga wa ya ke a yau?" Yana ga Allah, Makaɗaici, Mai tĩlastãwa}. [Ghafir: 16].
Muna imani cewa Shi - Allah Maɗaukakin sarki - Ya halicci sama, Ya dagata ba tare da ginshiƙi ba, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Ya halicci sammai ba tare da ginshiƙai ba kuna kallonsu kuma Ya jefa duwatsu a cikin ƙasa kada ta karkace da ku} [Luƙman: 10]. Ya horewa halitta abin da ke cikin sammai da abinda ke cikin ƙasa baki ɗaya daga gareShi - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka Ya tsarkaka - Ya ce: {Kuma Ya hõre muku abin da ke a cikin sammai da abin da ke a cikin ƙasa, gabã ɗaya daga gare Shi yake. Lalle ne, a cikin wancan, haƙĩƙa, akwai ãyõyi ga mutãne waɗanda ke yin tunãni} [al-Jathiya: 13].
Muna imani cewa Ubangiji - sha'aninSa ya ɗaukaka - halitta da umarni na sa ne, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Ku saurara, halitta da umarni nasa ne Allah - alherinSa ya yawaita - Ubanigijin talikai} [al-A'araf: 54]. Babu wani Ubangiji baShi ba, kuma babu waninSa Mai shara'antawa, kamar yadda Maɗaukakin sarki Ya ce: {Ya shara'anta muku na addini abinda Ya yi wa (annabi) Nuhu wasicci da shi da abinda Muka yi wahayi zuwa gareka} [al-Shura: 13]. Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Ga kowanne (daga kowanne abu) mun sanya muku shari'a da hanya} [al-Ma'ida: 48]. Shi ne wanda Yake shara'anta shari'u, kuma Yake faralanta farillai, Yake bayyana addini. Allah Ya yi inkari akan waɗanda suka riƙi malaman Yahudawansu da masu bautar Nasaransu iyayen giji, kuma suka karɓi abinda suka shra'anta musu na addini. Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Sun riƙi malaman Yahudawansu da masu bautar Nasaransu iyayen giji koma bayan Allah} [al-Taubah: 31]. Kuma Allah - tsarki ya tabbatar masa ya ɗaukaka - Ya ce: {Ko suna da wasu abokan tarayya ne da suke shar'anta musu addini abin da Allah bai musu Izini da shi ba} [al-Shura: 21].
Kamar yadda cewaShi - Maɗaukakin sarki - Shi ne wanda Ya halicci halitta, Shi ne Mamallakinsu, Shi ne wanda Ya shara'anta musu shari'u, Shi ne Mai iko Shi kaɗai akan hisabinsu da sakayyarsu, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Alhãli kuwa Allah ne Ya halicci sammai da ƙasã sabõda gaskiya, Kuma dõmin a sãka wa kowanne rai da abin da ya sanã'anta, kuma su, bã zã a zãlunce su ba} [al-Jathiya: 22]. Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Lalle ne Alkiyama mai zuwa ce, lnã kusa da In ɓõye ta dõmin a sãka wa dukkan rai da abin da take aikatãwa} [Daha: 15].
Muna imani cewa Ubangiji - sha'aninSa ya ɗaukaka - Shi ne Mahaliccin bayi kuma Mahaliccin ayyukansu, Allah - tsarki ya tabbatar maSa - Ya ce: {Alhãli, Allah ne Ya halicce ku da abin da kuke aikatãwa} [al-Saafat: 96].
Muna shaidawa ga Allah shaidawa ta gaskiya cewa Shi - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya sanya Kowacce aya daga ayoyinSa na kasantattu mai shaida ce akan cewa Shi ne Mahalici, kuma Allah Ya ƙarfafa hakan da faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Shin, wanda Yake yin halitta yanã yin kama da wanda ba ya yin halitta? Shin fa, bã ku tunãwa?} [al-Nahl: 17]. Haƙiƙa Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya yi inkari ga wanda Ya sanya masa abokanan tarayya a cikin rububiyyarSa ko UluhiyyarSa; domin cewa Shi ne Mahalicci Shi kaɗai - sha'aninSa ya ɗaukaka - sai Ya ce: {Ko sun sanya masa abokan tarayya ne da suka yi halitta kamar halittarSa, sai halittun suka yi kamanceceniya gare su, ka ce Allah Shi ne Mahaliccin komai kuma Shi ne Makaɗaici Mai rinjaye} [al-Ra'ad: 16].
Mushrikai sun kasance suna imani da Rububiyyar Allah, kuma suna sanin cewa Allah ne Mahalicci Mai azirtawa Mai rayawa Mai kashewa, kuma cewa Shi ne Mai anfanarwa kuma Mai cutarwa, kuma gumakansu da allolinsu ba sa anfanarwa ba sa cutarwa, kuma cewa su sila ne da zasu kusanto da su zuwa ga Allah, tare da hakan Allah bai karɓi hakan daga garesu ba, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Lalle idan ka tambaye su: "Wãne ne ya halitta sammai da ƙasã kuma ya hõre rãnã da watã?" Lalle sunã cẽwa Allah ne. TO, yãya ake karkatar da su? * Alah ne ke shimfiɗa arziki ga wanda Yake so daga cikin bãyinsa kuma Yanã ƙuntãtãwa ga (wanda, Yake so). Lalle Allah, Masani ne ga dukan kõme * Kuma lalle idan ka tambaye su. "Wãne ne ya saukar da ruwa daga sama, har ya rãyar da ƙasã game da shi a bãyan mutuwarta?" Lalle sunã cẽwa, "Allah ne." Ka ce: "Gõdiya tã tabbata ga Allah." Ã'a, mafi yawansu bã su hankalta} [al-Ankabut: 61-63]. Tare da cewa suna neman agajin Allah a lokacin tsanani suna fakewa gareShi idan baƙin ciki ya samesu, hakan ba zai anfanar da su ba; ta inda ba su gushe ba akan shirkarsu da kafircinsu, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {To, a lõkacin da suka shiga cikin jirgin ruwa, sun kirãyi Allah sunã mãsu tsarkake addini a gare shi, to, a lõkacin da Ya tsĩrar da su zuwa ga tudun ƙasã, sai gã su sunã shirki * Dõmin su kãfirce wa abin da Muka bã su kuma dõmin su ji dãɗi sa'an nan kuma zã su sani} [al-Ankabut: 65-66].
BABIN IMANI DA ULUHIYYAR ALLAH (Kadaita Allah da bauta).
Muna imani cewa Allah Shi kaɗai Yake a cikin UluhiyyarSa, kuma cewa Shi babu wani abin bautawa da gaskiya sai Allah, Shi kaɗai yake baShi da abokin tarayya, kuma cewa Shi Shi ne Gaskiya, kuma wanda suke bautawa baShi ba ƙarya ne, wannnan al'amarin mai girma Shi ne wanda saboda shi Allah Ya saukar da littattafai, Ya aiko da manzanni, Ya halicci aljanna da wuta, kuma ɗabi'a ta yi nuni akansa, kuma nagartattun hanukula suka yi shaida gare shi. Kuma muna sanin sani na yaƙini cewa tushen Da'awar annabawa ga al'ummatansu ita ce : Da'awarsu ga bautar Allah Shi kaɗai, da barin bautar waninSa. {Kuma ba Mu aiki wani Manzo ba a gabãninka fãce Munã yin wahayi zuwa gare shi, cẽwa "Lalle ne Shi, bãbu abin bautãwa fãce Nĩ, sai ku bauta Mini} [al-Anbiya: 25]. Tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya ce: {Tabbas mun aiko cikin kowacce al'umma wani manzo da ya isar da sakon ku bautawa Allah kuma ku nesanci dagutu (duk wani abin bauta da ba Allah ba} [al-Nahl: 36]. Allah - tsarki ya tabbatar maSa - Ya ce: {Ka tambayi waɗanda Muka aiko a gabaninka daga manzanninMu shin Mun sanya wasu alloli da za'a bauta musu koma bayan al-Rahman?} [al-zukhruf: 45]. Kowanne annabi ya cewa mutanensa: Ku bautawa Allah baku da wani abin bauta da gaskiya sai Shi, tun daga na farkonsu (annabi) Nuhu zuwa na ƙarshensu (annabi) Muhammad - aminci ya tabbata agare su -, sai Allah Ya ce Yana mai bada labari game da (annabi) Nuhu - aminci ya tabbata agare shi - ya ce: {Ya ku mutanena ! ku bautawa Allah baku da wani Ubangiji waninSa} [al-A'araf: 59]. Kuma Ya bada labari game da na ƙarshensu (annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - Ya ce: {Ka ce: "Nĩ mai gargadi kawai ne, kuma babu wani abin bautawa sai Allah, Makaɗaici, Mai mabuway} [Saad: 65]. Tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya ce: {Wancan ne Allah Ubangijinku. Bãbu wani abin bautãwa fãce Shĩ, Mahaliccin dukan kõme. Sabõda haka ku bauta Masa kuma Shi ne wakĩli a kan dukan, kõme} [al-An'am: 102].
Wannan al'amarin mai girma shi ne wanda saboda shi ne Allah Ya halicci halitta, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma ban halicci aljannu da mutãne ba sai dõmin su bauta Mini} [al-Zariyat: 56]. Ma'anar: "Suna bauta mini", wato: Suna kaɗaitani da ibada, Bukhari - Allah Ya yi masa rahama - ya faɗa a tafsirin wannan ayar: "Ban halicci ma'abota tsira ba daga wannan jama'a biyu sai dan su kadaita ni da bauta" (Haka nan yake acikin Bukhari ba'a danganta shi ba (6/49), Ibnu Hajar ya ambata a cikin "al-Fath" cewa shine faɗin al-Farra'u (8/600).)
Daga Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su - ya ce: Loakcin da annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya aiki Mu'azu Ibnu Jabal zuwa mutanen Yaman ya ce masa: "Lallai kai zaka je wa wasu mutane daga mazowa littafi (Yahudawa da Nasara), to farkon abinda zaka fara kiransu zuwa gareshi shi ne su kaɗaita Allah - Maɗaukakin sarki -". (Bukhari ne ya fitar da shi (1458), da Muslim (19).) Kuma Bukhari - Allah Ya yi masa rahama - ya yi babi akan hakan da faɗinsa: "Babin abinda ya zo a cikin kiran annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - zuwa kaɗaita Allah - alherinSa ya yawaita kuma Ya ɗaukaka -".
Ibada ta gaskiya ita ce wacce ta kasance tsantsa saboda Allah Ubangijin talikai wacce ta dace da shiriyar shugaban manzanni; saboda haka bautar kowanne abin bautar da ba Shi ba to ɓatacciya ce, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Wannan fa dõmin Allah Shĩ ne Gaskiya, kuma abin da suke kira wanda bã Shi ba, shi ne ƙaryã, kuma lalle, Alah shĩ ne Maɗaukaki, Mai girma} [al-Hajj: 62]. Ma'anar: "Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah": Babu wani abin bauta da gaskiya sai Allah; saboda nunin ayar data gabata akan hakan.
Imani da Allah Shi kaɗai, da bauta maSa koma bayan waninSa, shi ne ƙunshin: "Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah", wannan kalmar mai girma ta ƙunshi kore cancantar bauta daga kowanne abin bauta inba Allah ba, da kore Allantaka ta gaskiya daga dukkan wani abin bauta inba Allah ba, da tabbatar da Allantaka ta gaskiya ga Allah Ubangijin talikai, kuma cewa ingantacciyar ibada ba ta kasancewa sai ga Allah Shi kaɗai, wannan kalmar ta zo ne da lafazinta a cikin Alkur’ani da yawa, kuma ayoyi masu yawa sun zo da ma'anarta na korewa da kuma tabbatarwa, kamar yadda yake a cikin faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Tabbas mun aiko cikin kowacce al'umma wani manzo da ya isar da sakon ku bautawa Allah kuma ku nesanci dagutu (duk wani abin bauta da ba Allah ba} [al-Nahl: 36]. Da faɗinSa - sha'aninSa ya buwaya -: {Ku bautawa Allah kada ku yi masa shirka da wani abu} [al-Nisa'a: 36].
Wannan rukunin mai ƙarfi da kuma tushe mai ƙwari na addinin Allah - shi ne tabbatar da Uluhiyya ga Allah Shi kaɗai, da kore bauta daga waninSa - shi ne tauraron tushan addini, da kuma ginshiƙan Da’awar manzanni, ma'anarta: Kaɗaita Mahalicci da ayyukan halitta, ba za ka samu wata Surah daga Surorin AlKur'ani ba ta wofinta daga wannan al'amarin a assasawa ko ƙarfafawa, haƙiƙa Allah Ya tsaida hujja akan halitta da dalilai masu yawa, da shaidu marasa iyaka, ba zai yi wu a taƙaicesu ba ko a lissafe su ba, mafi girman dalili akan wannan al'amarin (shi ne) shaidarSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka; inda Ya ce: {Ka ce: "Wane abu ne mafi girma ga shaida?" Ka ce: "Allah ne shaida a tsakãnina da tsakaninku. Kuma an yi wo min wahayin wannan Alƙur'ãni dõmin in yi muku gargaɗi da shi, da wanda lãbãri ya kai gare shi. Shin lalle ne ku, haƙĩƙa, kunã shaidar cẽwa, lalle ne tãre da Allah akwai wasu abũbuwan bautawa?" Ka ce: "Bã zan yi shaidar (haka) ba." Ka ce: "Abin sani, Shi ne Abin bautãwa Guda kumã lalle ne nĩ barrantacce ne daga abin da kuke yi na shirki} [al-An'am: 19].
Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya shaida, kuma mafi ɗaukakar mai shaida daga halittunSa sun shaida, su ne mala'iku da ma'abota ilimi, akan mafi girman abin shaidawa, shi ne kaɗaitaShi da tabbatar da UluhiyyarSa, sai tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya ce: {Allah Ya shaida cẽwa: Lalle ne bãbu abin bautãwa fãce Shi kuma malãiku da ma'abũta ilmi sun shaida, yana tsaye da ãdalci, bãbu abin bautãwa face Shi, Mabuwãyi, Mai hikima} [Aal- Imran: 18]. Sai mala'iku da ma'abota ilimi suka shaida da abinda Allah Ya yi wa kanSa shaida da shi: {Ya isa Allah Ya zama Mai shaida} [al-Nisa'a: 79].
Ya kafawa halittarSa hujja da cewa Shi - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Shi ne Mahaliccin duk abinda ke cikin wannan duniyar ne, kai Ya sanya kowacce aya ta kasantacce mai shaida ce akan cancantarSa ga Uluhiyya (kadaita Shi) da bauta; saboda haka tambayarsu take yawaita a cikin AlKur'ani game da wannan al'amarin da tabbatarwarsu da cewa Shi ne Mahalicci Mai azirtawa Mai rayawa Mai kashewa, sannan Ya yi musu inkarin rashin bautarSa, ko bautar waninSa tare da Shi, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Lalle idan ka tambaye su: "Wãne ne ya halicci sammai da ƙasã kuma ya hõre rãnã da watã?" Lalle sunã cẽwa Allah ne. To, yãya ake karkatar da su? * Allah ne ke shimfiɗa arziki ga wanda Yake so daga cikin bãyinsa kuma Yanã ƙuntãtãwa ga (wanda, Yaga dama). Lalle Allah, Masani ne ga dukan kõme * Kuma lalle idan ka tambaye su. "Wãne ne ya saukar da ruwa daga sama, har ya rãyar da ƙasã game da shi a bãyan mutuwarta?" Lalle sunã cẽwa, "Allah ne." Ka ce: "Gõdiya tã tabbata ga Allah." Ã'a, mafi yawansu bã su hankalta} [al-Ankabut: 61-63]. Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma lalle ne, idan ka tambaye su, "Wãne ne ya halitta sammai da ƙasa?" Lalle zã su ce, "Mabuwãyi Mai ilmi ne Ya halicce su * Wanda Ya sanya muku ƙasa shimfiɗa kuma Ya sanya muku hanyõyi a cikinta, tsammãninku za ku nẽmi shiryuwa * Kuma Wanda Ya saukar da ruwa daga sama, a kan wani gwargwado, sai Muka rãyar da gari matacce game da shi. Kamar haka nan ake fitar da ku (daga kabari) * Kuma Wanda Ya halitta ma'aura (mace da namiji) dukansu, kuma Ya sanya muku, daga jirgi da dabbõbin ni'ima, abin da kuke hawa} [al-Zukhruf: 9-12].
Allah Ya kafa hujja akan bayinSa da cewa Ya tabbatar da ni'imominSa akansu waɗanda suke wajabta bautar Mai bada ni'imomin kuma Mai samar da su akansu, sai tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya ce: {Ka ce: "Wãne ne Yake azurtã ku daga sama da ƙasa? Shin kõ kuma Wãne ne Yake mallakar jĩ da ganĩ, kuma Wãne ne Yake fitar da mai rai daga matacce, kuma Ya fitar da matacce daga mai rai, Kuma Wãne ne Yake shirya al'amari?" To, zã su ce: "Allah ne." To, ka ce: "Shin fa, bã zã ku yi taƙawa ba? * To, Wancan ne Allah, Ubangijinku Tobbatacce. To, mẽne ne a bãyan gaskiya fãce ɓãta? To, yãya ake karkatar da ku} [Yunus: 31-32].
A cikin Alkur’ani da yawa Allah Ya ke kafawa bayi hujja da ayoyin RububiyyarSa (Kadaita Allah a ayyukan Sa) wacce take wajabta bautarSa Shi kaɗai - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -, kuma cewa Mahalicci ga waɗan nan ayoyin kasantattu masu girma Shi ne Shi kaɗai Ya ke - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -, kuma cewa Shi kamar yadda ba wani mahalicci tare da Shi, to ba ya kamata bautawa waninSa; a saboda haka ne Ya cika waɗannan ayoyin masu zuwa da faɗinSa: {Shin akwai wani Uabngiji tare da Allah}, su ne faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Kõ wãne ne Ya halitta sammai da ƙasa kuma Ya saukar muku, daga, sama, wani ruwa, Muka tsirar, game da shi, gõnaki mãsu sha'awa, ba ya kasancẽwa gare ku, ku tsirar da itãcensu? Shin, akwai abin bautãwa tãre da Allah? Ã'a, sũ mutãne ne suna daidaitãwa (Allah da wani) * Kõ kuwa wãne ne Ya sanya ƙasa tabbatacciya, kuma Ya sanya kõguna a tsakãninta kuma Ya sanya mata manyan duwãtsu tabatattu, kuma Ya sanya wani shãmaki a tsakãnin tẽkuna biyu? Shin akwai wani abin bautãwa tãre da Allah. Ã'a, mafi yawansu ba su sanĩ ba * Kõ wãne ne yake karɓãr (Addu’ar) mabukaci idan ya roke Shi kuma yake yaye damuwa kuma ya sanya ku mamãyan ƙasa? Shin akwai wani abin bautawa tãre da Allah? Kaɗan ƙwarai kuke yin tunãni * Kõ wãne ne yake shiryarwa a cikin duffan ƙasa da tẽku, kuma wãne ne Yake aikõwar iska dõmin bãyar da bushãra a gabanin rahamarSa? Ashe akwai wani abin bautãwa tãre da Allah? tsarki yã tabbata ga Allah daga barin abin da suke shirki da Shi} [al-Naml: 60-63].
A Laokacin da Ya ambaci halittu masu girma masu nuni akan RububiyyarSa wacce take wajabta UluhiyyarSa a cikin surat al-Rum, su ne faɗinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: {Kuma akwai daga ãyõyinSa, Ya halitta ku daga turɓãya, sai gã ku kun zama mutum, kunã wãtsuwa * Kuma akwai daga ãyõyinsa, Ya halitta muku mãtan aure daga kanku, dõmin ku natsu zuwa gare ta, kuma Ya sanya sõyayya da rahama a tsakãninku. Lalle a cikin wancan akwai ãyõyi ga mutãne mãsu yin tunãni * Kuma akwai daga ãyõyinSa halittar sammai da ƙasã da sãɓãwar harsunanku, da launukanku. Lalle a cikin wannan akwai ãyõyi ga mãsu ilmi * Kuma akwai daga cikin ãyõyinSa, barcinku a cikin dare da rãna, da nẽmanku ga falalarsa. Lalle a cikin wannan akwai ãyõyi ga mutãne mãsu saurãrãwa * Kuma akwai daga cikin ãyõyinSa, Ya nũna muku walƙiya a kan tsõro da ɗammãni kuma Ya dinga saukar da ruwa daga sama Sa'an nan Ya rãyar da ƙasã game da shi a bãyan mutuwarta. Lalle a cikin wannan akwai ãyõyi ga mutãne mãsu hankaltawa * Kuma akwai daga ãyõyinsa, tsayuwar sama da kasa bisa umurninsa, sa'an nan idan Ya kira ku, kira ɗaya, daga ƙasã, sai gã ku kunã fita * Kuma wanda ke cikin sammai da ƙasa Nasa ne, Shi kaɗai, dukkansu masu tawali’u ne gareShi * Shi ne Wanda Ya fara halitta, sannan ya saketa, kuma (sakewarta) tafi sauƙi a gareShi, Kuma Yana da misali mafi ɗaukaka a cikin sammai da ƙasa, kuma Shi ne Mabuwayi Gwani * Ya bũga muku wani misãli daga kanku. Kõ kunã da abõkan tarayya, daga cikin bãyin da hannãyenku na dãma suka mallaka, a cikin arzikinku, watau ku zama daidai a ciki kunã tsõron su kamar tsoron ku ga kanku? Haka dai Muke bayyana ãyõyi, daki-daki, ga mutãne mãsu hankaltawa * Ã'aha! waɗanda suka yi zalinci sun bi son zũciyõyinsu, bã tãre da wani ilmi ba. To wãne ne zai shiryar da wanda Allah Ya ɓatar, kuma bã su da waɗansu mataimaka?} [al-Rum: 20-29]. Ya ɓuɗe kowacce aya daga cikinsu da faɗinSa: {Daga ayoyinSa}; wato: Daga dalilai kasantattu masu nuni akan RububiyyarSa mai tabbatar da UluhiyyarSa abin da ka ambata, sannan ya biye bayansu da ambatan wannan misalin wanda Allah Ya buga shi ga wanda ya bauɗe da wani abu daga halittarSa, Yana cewa: "Shin ɗayanku ya kasance mai tarayya da bawansa a cikin shinfiɗarsa da matarsa?! Haka nan Allanku baYa yarda a daidaita wani da Shi daga halittarSa"; Katada ne ya faɗa. (Tafsirin Dabari (20/95).) Sannan ya rifesu da bayanin cewa lafiyayyar ɗabi'a tana hukanta bautarSa Shi kaɗai - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka, saboda haka Ya ce: {Sabõda haka, ka tsayar da fuskarka ga addini, kanã mai karkata zuwa ga gaskiya, halittar Allah da Ya halitta mutãne a kanta. Bãbu musanyãwa ga halittar Allah, wannan shĩ ne addini madaidaici kuma amma mafi yawan mutãne ba su sani ba} [al-Rum: 30].
Haƙiƙa Allah Ya yi bayani daki-daki a cikin dalilan ya kafa da shaidu akan UluhiyyarSa bayani filla-filla da hujja take tsayuwa da shi, kuma abin da aka kafawa hujja yake bayyana da shi; dan kada ya zama hujja ga mutane akan Allah, kuma kamar yadda Allah Ya kafa hujja akan mutane da dalilai na yanke, da hujjoji masu haske, kuma Ya tsaida masu shaida masu rinjaye masu nuni akan kaɗaituwarSa; to haƙiƙa Ya buga misalai kuma Ya zo da gaskiya, tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka, Allah sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Kuma Allah Ya buga wani misãli, mutane biyu, ɗayansu bẽbe ne, ba ya iya sãmun ikon yin kõme, kuma shi nauyi ne a kan mai mallakarsa, inda duk ya fuskantar da shi, bã ya zuwa da wani alhẽri. Shin, yanã daidaita, shi da (da na biyun) wanda yake umurni da a yi ãdalci kuma yanã a kan tafarki madaidaici?} [al-Nahl: 76]. Ibnu Jarir a tafsirin wannan ayar ya ce: "Wannan misali ne Allah - Maɗaukakin sarki - Ya buga shi ga kanSa da allolin da ake bautawa koma bayanSa, sai ambatanSa Ya ɗaukaka Ya ce: {Allah Ya buga misalin mutum biyu, ɗayansu bebene ba shi da iko akan wani abu} yana nufi da hakan gunkin da ba ya jin komai; domin cewa shi kodai katakon da sassaƙa ne, ko tagullar da aka kera, ba shi da iko akan anfanar da wanda ya yi masa hidima, ko tunkuɗe wata cuta daga gare shi, shi mai dogara ne akan majiɓincin al'amuransa, yana cewa: Shi abin dogar ne ga ɗan uwansa da masoyansa da iyalan gidansa, to haka gunki ya dogara ga wanda yake bauta masa, yana bukatar ya dauke shi, ya ajiye shi ya yi masa hidima, kamar bebe a cikin mutane wanda ba shi da iko akan komai, to shi ya dogara ga masoyansa daga 'ya'yan uwansa da wasunsu {Duk inda ya fuskantar da shi ba ya zuwa da alheri} yana cewa: Duk inda ya fuskantar da shi ba ya zuwa da alheri; domin cewa shi ba ya fahimtar abinda ake fada masa, kum ba shi da iko ya bayyanarwa kansa abinda yake nufi, shi ba ya fahimta kuma ba'a fahimtar sa, haka nan gunki, ba ya fahimtar abinda ake fada masa, ballantana ya yi shawara a wani al'amarinsa, kuma ba ya furuci ballanta ya yi umarni ya kuma yi hani, Allah - Madaukakin sarki - Yana cewa: {Shin shi zai yi dadai da wanda yake umarni da adalci} yana nufin: Shin zai yi dadai wannan beban wanda ya dogara ga mai gidansa wanda ba ya zuwa da wani alheri duk inda ya fuskanta, da wanda shi mai magana ne mai zance ne yana umarni da gaskiya, kuma yana kira zuwa gare ta, Shi ne Allah Shi kadai marinjayi, wanda Yake kiran bayinSa zuwa kadaita shi da biyayyarSa? yana cewa: Shi Madaukakin sarki ba zai yi daidai da gunkin da siffarsa abinda aka siffanta ba”. {Tafsirin Dabari (17/262).)
Kuma Allah Ya buga misali ga Allan ƙarya da Allan gaskiya, kamar yadda Mujahid ya ce. (Tafsirin Dabari (21/282).) Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya ce: {Allah Yã buga misãli; wani mutum (bãwa) a cikinsa akwai mãsu tarayya, mãsu mũgun hãlin jãyayya, da wani mutum (bãwa) dukkansa na wani mutum ne, Shin, zã su daidaita ga misãli? Gõdiya ta tabbata ga Allah (a kan bayãni). Ã'a, mafi yawan mutãne ba su sani ba} [al-Zumar: 29].
Wannan al'amarin - wanda shi ne tabbatar da kaɗaitaka ga Allah, tare da shaidar manzanci ga Manzo (annabi Muhammad) - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - shi ne wanda Allah Ya sanya shi iyaka tsakanin imanin mutum da Allah da kuma kafirci, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma idan watanni, mãsu alfarma suka shige, to, ku yãki mushirikai inda kuka sãmẽ su, kuma ku kãmã su, kuma ku tsare su, kuma ku zaune musu dukkan madãkata. To, idan sun tũba, kuma suka tsayar da Sallah, kuma suka bãyar da zakka, to ku sakar musu hanyarsu. Lalle Allah ne Mai gãfara, Mai jin ƙai} [al-Taubah: 5]. Tsarki ya tabbatar maSa Ya ce: {Sa’an nan idan sun tuba kuma suka tsayar da Sallah kuma suka bada zakka to ‘yan’uwanku ne a cikin addini} [al-Taubah: 11]. Daga Dan Umar - Allah Ya yarda da su - cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "An umurce ni da in yaki mutane har sai sun shaida cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma (Annabi) Muhammadu Manzon Allah ne, su tsaida sallah, su bayar da zakka, idan suka aikata hakan sun tsare jinanensu da dukiyoyinsu daga gareni sai dai da hakkin Musulunci, kuma hisabinsu yana ga Allah". (Bukhari ne ya fitar da shi (1399, 7284), da Muslim (20), da Abu Dawud (1556), da Tirmizi (2607) da Nasa'i (2443).)
Wannan imanin ba ya isuwa ya zama a zuciya, kai babu makawa harshe sai ya furta shi; saboda haka tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "An umarceni in yaƙi mutane har sai sunce: Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah". Bukhari ne ya fitar da shi (25), da Muslim (22).) Imani ba ya tabbata har sai gaɓɓai sun yi aiki da shi, Allah Ya ce - kuma maganarSa gaskiya ce: {Abin sani kawai, nũminai sũ ne waɗanda suke idan an ambaci, Allah, zukãtansu su firgita, kuma idan an karanta ãyõyinSa a kansu, su ƙãrã musu wani ĩmãni, kuma ga Ubangijinsu suke dõgara * Waɗanda suke tsayar da Sallah, kuma daga abin da Muka azũrtã su sunã ciyarwa * Waɗan nan su ne muminai na haƙiƙa} [al-Anfal: 2-4]. Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Bai zama addini ba dõmin kun jũyar da fuskõkinku wajen gabas da yamma, kuma amma addini shi ne ga wanda ya yi ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira da malã'iku da Littattafan (sama) da Annabãwa, kuma ya bãyar da dũkiya, akan yana son ta, ga mai zumunta da marãyu da matalauta da ɗan hanya da mãsu rõƙo, kuma a cikin fansar wuya, kuma ya tsayar da Sallah, kuma ya bãyar da zakka, da mãsu cika alkawari idan sun ƙulla alkawarin da mãsu haƙuri a cikin tsanani da cũta da lõkacin yãƙi. Waɗannan su ne suka yi gaskiya. Kuma waɗannan su ne mãsu taƙawa}. [al-Baƙara: 177].
kuma Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Wanda ya ga wani mummunan abu daga cikinku, to ya canza shi da hannunsa, idan ba zai iya ba to (ya canza shi) da harshe, idan ba zai iya ba to (ya canza shi) da zuciyarsa, wannan shi ne mafi raunin imani". (Muslim ne ya fitar da shi (49), da Abu Dawud (1140), da Tirmizi (2172), da Nasa'i (5008), da Ibnu Majah (1275).) Sai wannan hadisin ya yi nuni akan cewa imani yana ban banta da juna a zuciya.
babu makawa tare da imani da Allah sai an kafircewa dagutu, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Duk wanda ya kafurce wa ɗagutu ya kuma yi imani da Allah to tabbas ya yi riƙo da ƙwaƙƙwarar igiyar da ba ta tsinkewa} [al-Baƙara: 256]. Barranta daga shirka da ma'abotanta, ba zai zama mai tauhidi ba har sai ya barranata daga shirka da ma'abotanta, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Kuma (ka ambaci) lõkacin da (annabi) Ibrãhĩm ya ce wa babansa da mutãnensa, "Lalle nĩ mai barranta ne daga abin da kuke bautãwa} [al-Zukhruf: 26].
Wannan imanin babu makawa bawa ya zama mai tsarkake ibada da Allah Ubangijin talkai, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Shĩ ne Rayayye, bãbu abin bautãwa fãce Shi. Sabõda haka ku kira Shi, kunã mãsu tsarkake addini a gare Shi. Gõdiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu} [Ghafir: 65]. Tsarki ya tabbatar maSa Ya ce: {Kuma ba'a Umarce su ba sai su bautawa Allah suna masu tsarkake Addini a gare shi suna masu kaucewa ɓata} [al-Bayyinah: 5]. Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Aka ce ya Manzon Allah waye mafi azirtar mutane da cetanka a ranar AlKiyama? Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Haƙiƙa ya Abu Huraira na yi zatan babu wanda zai tambayeni game da wannan Hadisin na farko daga kai; saboda abinda na gani na kwaɗayinka akan Hadisi, mafi arziƙin mutane da cetona a ranar AlKiyama, wanda ya ce: Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, yana mai tsarkakewa daga zuciyarsa ko ransa". (Buhari ne ya fitar da shi (99, 6570).)
Kuma Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Lalle Allah Ya haramta wuta ga wanda ya ce: Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, yana mai neman yardar Allah da hakan". (Bukhari ne ya fitar da shi (425), da Muslim (33), da Nasa'i (788), da Ibnu Majah (754).)
Kuma ya zama mai sakankancewa ba mai kokwanto ba, Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya ce: {Cewa kaɗai muminai su ne waɗanda suka yi imani da Allah da ManzonSa sannan kuma ba su yi kwakwanto ba} [al-Hujurat: 15]. Allah Ya faɗa Yana mai bada labari game da kafirin nan ma'abocin gona cewa shi ya ce: {Kuma bã ni zaton sa’a (Alkiyama) mai tsayuwa ce, kuma lalle ne, idan an mayar da ni zuwa ga Ubangijiĩna, to, lalle ne, zan sãmi abin da yake mafi alhẽri daga gare ta ya zama makõma} [al-Kahf: 36].
Kuma imaninsa ya zama daga ilimi ne, sai ya san haƙiƙanin imani da abinda yake hukunta shi da abinda yake kishiyantakarsa, (Allah) Maɗaukakin sarki Ya ce: {To ka sani, cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah} [Muhammad: 19].
Kuma babu makawa tare da ilimi da ikhlasi sai an sami yarda da abinda manzo - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya zo da shi, da kuma abinda imani ya ƙunsa, kuma kalmar: {Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah} ta yi nuni akan bauta wa Allah Shi kaɗai, da barin bautar abinda baShi ba, wanda ya faɗeta, kuma bai yarda da bautar Allah Shi kaɗai ba, to ya zama daga waɗanda Allah Ya faɗa a ciknsu: {Lalle sũ, sun kasance idan an ce musu: "Bãbu abin bautãwa, fãce Allah," sai su dõra girman kai * Kuma suna cewa shin mu zamu bar allolinmu dan wani mawaƙi mahaukaci} [al-Saafat: 35-36].
Kuma ya miƙa wuya ya jawu, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma wanda ya miƙa fuskarsa zuwa ga Allah, alhali kuma yana mai kyautatawa to lalle ya yi riƙo ga igiya amintacciya} [Luƙman: 22].
Kuma ya zama mai gaskiya a cikin maganarsa da aikinsa da ƙudircewarsa har ya samu abinda annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi bushara da shi a cikin faɗinsa: "Babu wani bawa da zai shaida babu abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma cewa (annabi) Muhammad Manzon Allah ne a halin kasancewarsa mai gaskiya daga zuciyarsa face Allah ya haramta masa shiga wuta". (Bukhari ne ya fitar da shi (128), da Muslim (32).)
Kuma ya zama yana son wannan addinin, da wanda ya shar’anta shi , da wanda ya zo da shi, da wanda ya yi addini da shi, Allah Maɗaukkain sarki Ya ce: {Kuma daga mutane akwai wanda yake riƙon kinaye baicin Allah suna son su kamar son Allah, kuma waɗanda suka yi imani ne mafiya tsananin so ga Allah} [al-Baƙara: 165]. Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Imanin ɗayanku ba zai cika ba har sai na kasance mafi soyuwa a gare shi daga ɗansa da mahafinsa da mutane baki ɗaya" (Bukhari ne ya fitar da shi (15), da Muslim (44), da Nasa'i (5013), da Ibnu Majah (67).) Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Abu uku wanda suka kasance a tare da shi ya samu zaƙin imani: Allah da Manzansa su kasance mafi soyuwa a gare shi daga waninsu, kuma ya so mutum ba yana sonsa ba ne sai dan Allah, kuma ya ki komawa cikin kafirci bayan Allah Ya tserar da shi daga cikinsa kamar yadda yake ƙin a jefa shi cikin wuta". (Bukhari ne ya fitar da shi (16), da Muslim (43), da Tirmizi (2624), da nasa'i (4987), da Ibnu Majah (4033).)
Kamar yadda Allah Ya bayyana haƙiƙanin imani, da abinda yake hukuntawa da rukunansa da sharuɗɗansa, to haƙiƙa Ya warware shubuhohin mushrikai masu tsaurin kai, kuma ya bayyana cewa ba su da wata hujja a cikin shirkarsu; domin cewa waɗannan kishiyoyin halittarsu aka yi jujjuya al'amuransu ake yi ba sa iya halittar komai, kuma ba sa mallakar kwatankwacin ƙwayar zarra a cikin sammai ko a cikin ƙasa, Allah maɗaukakin sarki Ya ce: {Shin, sunã shirki da abin da bã ya halittar kõme, kuma sũne ake halittãwa? * Kuma ba su iya bãyar da taimako gare su, kuma kansu ma, bã su iya taimaka! * Kuma idan kun kirãye su zuwa ga shiriya, bã zã su bĩ ku ba, daidai ne a gare ku, shin, kun kirãye su, kõ kuwa kũ mãsu kawaici ne! * Lalle ne waɗannan da kuke kira, baicin Allah, bãyĩ ne misãlanku: to, ku kirãye su, sa'an nan su karɓa muku, idan kun kasance mãsu gaskiya! * Shin sunã da ƙafãfu da suke yin tafia da su? Kõ sunã da hannãye da suke damƙa da su? Kõ sunã da idãnu da suke gani da su? Ko sunã da kunnuwa da suke saurãre da su? Ka ce: "Ku kirãwo abũbuwan shirkinku sa'an nan kuma ku yi mini kaidi, sa'an nan kada ku saurãra mini * Lalle ne, Majiɓincĩna Allah ne Wanda Ya saukar da Littãfi kuma Shĩ ne Yake jiɓintar sãlihai * Kuma waɗanda kuke kira, baicinSa, bã su iya taimakõn ku, kuma kansu ma, bã su iya taimaka * Kuma idan ka kirãye su zuwa ga shiriya, bã zã su ji ba, kuma kanã ganin su, sunã dũbi zuwa gare ka, alhãli kuwa sũ, bã su gani} [al-A'araf: 198-191]. Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Ka ce: "Ku kirãyi waɗanda kuka riya (cẽwa abũbuwan bautãwa ne) baicin Allah, bã su Mallakar ma'aunin zarra a cikin sammai, kuma bã su Mallakarsa a cikin ƙasa kuma bã su da wani rabon tãrẽwa a cikinsu (sammai da ƙasa), kuma bã Shi da wani mataimaki daga gare su * Kuma ceto ba ya amfani a wurinSa face fa ga wanda (Allah) Ya yi izni gare shi} [Saba'i: 22,23], wannan ta yanke jijiyoyin shirka gaba ɗayanta.
Kuma Allah Ya bayyana cewa waɗannan kishiyoyin waɗanda ake bautawa koma bayan Allah ba sa jin kiran wanda ya kirasu, da sun ji kiran ma ba za su iya amsa musu ba, kuma ranar lahira za su kafirce da shirkarsu kuma zasu barranta da su, Allah sha'aninSa ya ɗaukaka kuma sarautarSa ta ɗaukaka - ya ce: {Idan kun kira su, bã zã su ji kiranku ba, kuma kõ sun jiya, bã zã su karɓa muku ba, kuma a Rãnar Alkiyama zã su kãfirce wa shirkinku, kuma bãbu mai bã ka lãbãri, kamar wanda ya sani} [Faɗir: 14].
Kamar yadda Allah Ya bayyana cewa waɗannan kishiyoyin waɗanda ake bautawa koma bayan Allah ba sa anfanarwa kuma ba sa cutarwa, to ta yaya ake bauta musu koma bayan Allah?! Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma suka riƙi abũbuwan bautawa, baicin Shi, bã su yin halittar kõme alhãli sũ ne ake halittãwa kuma bã su mallakar wa kansu wata cũta ko wani amfãni, kuma bã su mallakar mutuwa kuma bã su mallakar rãyarwa, kuma bã su mallakar tãyarwa} [al-Furƙan: 3].
Kuma Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya bayyanar da cewa kishiyoyin ba sa mallakar wani arziƙi ga mabiyansu, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma sunã bautã wa, baicin Allah, abin da yake bã ya mallakar wani arziki dõminsu, daga sammai da ƙasa game da kõme, kuma bã su iyawa (ga aikata kõme)} [al-Nahl: 73]. To ta yaya suke bautawa wanda ba ya mallakar komai, kuma ba ya iya azirtawa, baya iya anfanarwa, ko ya cutar?!
Ya kafa musu hujja da cewa su idan wata cuta ta samesu, ko suka afka cikin baƙin ciki; sai su fake ga Allah Shi kaɗai suna masu tsarkake addini gareShi, idan Ya tsiratar da su sai su koma zuwa shirkarsu, Allah - Maɗaukkain sarki - Ya ce: {To, a lõkacin da suka shiga cikin jirgin ruwa, sun kirãyi Allah sunã mãsu tsarkake addini a gare shi, to, a lõkacin da Ya tsĩrar da su zuwa ga tudun ƙasã, sai gã su sunã shirki} [al-Ankabut: 65].
Kamar yadda Allah Ya ɓata da'awar mushrikai a cikin riƙon kishiyoyi, to haƙiƙa Ya ɓata kowace da'awa da cewa Allah Ya riƙi ɗa, sai tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya ce: {Allah bai riƙi wani abin haihuwa ba, kuma bãbu wani abin bautãwa tãre da Shi. Idan haka ne (akwai abin bautawa tare da Shi), lalle ne dã kõwane abin bautawar ya tafi da abin da ya halitta, kuma lalle ne, dã waɗansu sun rinjãya a kan waɗansu, tsarki ya tabbata ga Allah, daga abin da suke siffantãwa} [al-Mu’uminun: 91]. Tsarki ya tabbatar maSa Ya ce: {Dã waɗansu abũbuwan bautawa sun kasance a cikinsu (sama da ƙasa) fãce Allah, haƙĩƙa dã su biyun sun ɓãci. Sabõda haka tsarki ya tabbata ga Allah Ubangijin Al'arshi daga abin da suke siffantãwa} [al-Anbiya: 22]. Kuma Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya bayyana cewa Yahudawa da Nasara sun riya cewa Allah Ya riƙi ɗa, sai Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya ce: {Kuma Yahũdãwa suka ce: "Uzairu ɗan Allah ne."Kuma Nasãra suka ce: "Masĩhu ɗan Allah ne." Wancan zancensu ne da bãkunansu. Sunã kamã da maganar waɗanda suka kãfirta daga gabãni. Allah Yã la'ance su! Yãya aka karkatar da su?} [al-Taubah: 30]. Allah Ya warware akidarsu tun daga asalinsa; to ta yaya mutumin da yake cin abinci zai zama Allah?! Allah ba Ya ci, ba Ya sha, baYa buƙatuwa ga abinda mutum yake buƙatuwa gare shi , Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Masĩhu ɗan Maryama bai zama ba fãce Manzo ne kawai, haƙĩƙa, manzanni sun shige dake gabãninsa, kuma babarsa siddika ce. Sun kasance sunã cin abinci. Ka duba yadda Muke bayyana musu ãyõyi. Sa'an nan kuma ka duba yadda ake karkatar da su * Ka ce: "Ashe kunã bauta wa, baicin Allah, abin da ba ya mallakar wata cuta sabõda ku , kuma haka wani amfani alhãli kuwa Allah Shi ne Mai ji, Masani? * [al-Ma'ida: 75-76].
Allah Ya ɓata bautar (da ake wa) mala'iku, kuma Ya bayyana cewa su - tare da kasancewarsu makusanta ga Allah - ba sa mallakar ceto sai bayan izninSa, sai Ubangijinmu - ambatanSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Akwai malã'iku da yawa a cikin sammai cẽtonsu bã ya wadãtar da kõme fãce bãyan Allah Yã yi izni (da shi) ga wanda Yake so, kuma Yake yarda} [al-Najm: 26]. Kuma suna jin tsoron Ubangijinsu daga birbishinsu, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma ga Allah, abin da yake a cikin sammai da ƙasa na dabba da mala'iku, suke yin sujada, kuma bã su kangara * Suna tsõron Ubangijinsu daga bisansu, kuma suna aikata abin da ake umuruin su} [al-Nahl: 49-50]. Allah - tsarki ya tabbatar maSa - Ya ce: {Masĩhu bã ya ƙyãmar ya kasance bãwa ga Allah, kuma haka malã'ikun nan makusanta. Kuma wanda ya yi ƙyãmar bautarSa kuma yi yi girman kai, to, zai tãra su zuwa gare shi gabã ɗaya} [al-Nisa'a: 172]. Idan haka halin mala'iku yake, to ta yaya za'a dinga bauta musu koma bayan Allah?
Haka annabawa da manzanni - aminci ya tabbata agare su - tare da ɗaukakar matsayinsu a duniya da lahira ba sa mallakar amfani ko cuta ga kawunansu, to ta yaya ga koma bayansu?! Tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya faɗa Yana Mai bada labari game da annabawa cewa su suna bautawa Ubangijinsu ta hanyar kwaɗayi da tsoro: {Lalle ne su sun kasance suna gudun tsere zuwa ga ayyukan alheri, kuma suna kiranMu dan kwadayi da fargaba. Kuma sun kasance masu kankar da kai gare Mu} [al-Anbiya'a: 90]. Kuma Ya umarci annabinSa muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya faɗI kamar yadda Allah Ya bada labari game da shi da faɗinSa: {Ka ce: "Bã ni mallaka wa raina wani amfãni, kuma haka ban tunkuɗe wata cũta, face abinda da Allah Ya so. Kuma dã na kasance inã sanin gaibi, dã lalle ne, nã yawaita daga alhẽri kuma cũta bã zã ta shãfe ni ba, nĩ ban zama ba fĩce mai gargaɗi, kuma mai bãyar da bishãra ga mutãne waɗanda suke yin ĩmãni} [al-A'araf: 188]. Lokacin da tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya yi mummunar addu'a akan waɗanda suka cruce shi daga mushrikai a yaƙin Uhud sai Allah - Maɗaukakin sarki - Ya saukar maSa da faɗinSa: {Bãbu kõme a gare ka game da al'amarin (shiryar da su banda isar da manzanci). Ko Allah Ya karɓi tũbarsu, kõ kuwa Ya yimusu azãba, to lalle ne sũ, mãsu zãlunci ne} [Aal- Imran: 128]. Daga Zuhri ya ce: Salim ya zantar da ni daga babansa - Allah Ya yarda da shi -, cewa shi ya ji manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - idan ya ɗago kansa daga ruku'u a raka'a ta ƙarshe ta asuba yana cewa: "Ya Allah Ka la'anci wane da wane da wane", bayan ya ce: "Allah Ya ji wanda ya gode maSa, ya Ubangijinmu godiya ta tabbata gareKa", sai Allah Ya saukar da: {Babu wani abu na al'amari gareka} zuwa faɗinSa: {Lallai su azzalimai ne}. (Bukhari ne ya fitar da shi (4559), da Nasa'i (1078).)
BABIN IMANI DA SUNAYEN ALLAH DA SIFFOFINSA
Muna imani da cewa Allah Shi kaɗai yake a cikin siffofinSa da siffofin cikarSa da girmanSa tsarki ya tabbatar maSa, kuma cewa Allah - tsarki ya tabbbatar maSa Ya ɗaukaka - Yana da sunaye kyawawa da siffofi maɗaukaka, Nassoshin AlKur'ani da Hadisi sun jerantu akan hakan, kuma cikakkun hankula sun yi shaida gareShi da hakan, nagartattun ɗabi'u sun miƙa wuya ga hakan, maluman al'ummar musulunci sun haɗu akan hakan, kai dukkanin saƙonnin Allah sun zo da bayanin siffofin Allah da sunayenSa da ayyukanSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -. Allah Ya aibata mushrikai akan bautarsu ga gumaka; domin cewa su ababen halitta ne irinsu, kai su ne ma mafi gazaa kuma mafi tawaya daga gare su, su ba sa gani ba sa ji, kai basu da kafafuwan da zasu dinga tafiya da su, ko hannun da zasu dinga damka da su, Allah - tsarki ya tabbatar maSa - Ya ce: {Lalle ne waɗannan da kuke kira, baicin Allah, bãyĩ ne misãlanku: to, ku kirãye su, sa'an nan su karɓa muku, idan kun kasance mãsu gaskiya! * Shin sunã da ƙafãfu da suke yin tafia da su? Kõ sunã da hannãye da suke damƙa da su? Kõ sunã da idãnu da suke gani da su? Ko sunã da kunnuwa da suke saurãre da su? Ka ce: "Ku kirãwo abũbuwan shirkinku sa'an nan kuma ku yi mini kaidi, sa'an nan kada ku saurãra mini} [al-A'araf: 194-195]. Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma mutãnen (Annabi) Mũsã suka riƙa bayan tafiyarsa (ganawa da Allah) daga kayan su, maraƙi, jiki yanã rũri. Shin, ba su ganĩ ba, cẽwa lalle ne shi, bã ya yi musu magana, kuma bã ya shiryar da su ga hanya, sun riƙa shi, kuma sun kasance mãsu zãlunci} [al-A'araf: 148].
Kuma muna imani cewa kamar yadda Ya siffanta kanSa, kuma kamar yadda manzonSa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - Ya siffantashi, to Shi - tsarki ya tabbatar maSa - babu wani abu tamkarSa, Shi ne Mai ji Mai gani, Maɗaukakin sarki Ya ce: [Babu abinda ya yi kama da Shi kuma Shi ne Mai ji kuma Mai gani}. [al-Shura:11]. Sai mu tabbatarwa Allah abinda Ya tabbatarwa kanSa shi, ko manzonSa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya tabbatar maSa, kuma mu kore abinda Ya korewa kanSa Shi, ko manzonSa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kore maSa ba tare da musu ba, ko kamantawa ba, ba kuma tare da siffantawa ko canjawa ba, kuma muna sani sani na sakankancewa cewa Ubangijinmu Mai siffantuwa ne da siffofinSa kafin Ya halicci halitta, kuma cewa Shi Yana ƙololuwar cika da girma da kyau tuntuni har abada; Domin Shi ne Na farko kuma Na ƙarshe, Shi ne Na farko babu wani abu kafinSa, kuma na karshe babu wani abu bayanSa, Shi ne na farko da sunayenSa da siffofinSa cika da girma, Shi ne na karshe da sunayenSa da siffofinSa a cika da girma.
Kuma muna imani cewa Shi - tsarki ya tabbatar maSa - kamar yadda halitta ba su kewaye sani daShi ba, to haka nan gannai ba sa riskarSa, Maɗaukakain sarki Ya ce: {Yanã sanin abin da ke a gaba gare su da abin da ke bãyansu, kuma bã su kẽwayẽwa da shi ga sani} [Daha: 110]. Kuma Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Gannai bã su iya riskuwarSa, kuma Shĩ Yanã riskuwar gannai, kuma Shĩ ne Mai tausasãwa, Masani} [al-An'am: 103]. Imam Ibnu Kutaibah - Allah Ya yi masa rahama - ya ce: "Wajibi akanmu mu tiƙe a siffofin Allah inda Ya tiƙe a cikin siffofinSa, ko inda manzonSa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - Ya tiƙe, kada mu gusar da lafazin akan yadda larabawa suka san shi, kuma suka ajiyeshi akansa, mu kame daga koma bayan haka". (al-Ikhtilaf fil lafzi wal-raddi alal Jahamiyya, na Ibnu Kutaibah (shafi na 44).)
Muna imani cewa daga siffofin Allah akwai siffofi masu lazimtar zatinSa, kamar rayuwa, da ilimi, da ji, da gani, da hannu, da yatsu, daga cikinsu akwai siffofi masu rataye da mashi'arSa, kamar fushi, da yarda, da sauka. Kuma muna imani cewa Shi ne Mai aikata abinda Yake nufi, Shi Yana aikata abinda Ya so duk lokacin da Ya so yadd da Ya so, Yana ɗaukaka wanda Ya so, Yana ƙasƙantar da wanda Ya so, ba mai juyar da umarninSa, kuma babu mai bibiyar hukuncinSa.
Muna imani cewa siffofin Allah daga cikinsu akwai wanda ya zo kai tsaye, sai mu siffanta Allah da shi kai tsaye, kamar ji, da rayuwa, da gani, da wasunsu, daga cikinsu akwai wanda ya zo aƙayyade, sai ya wanzu akan ƙayyadewarsa, kamar siffantaShi - tsarki ya tabbatar maSa - da cewa Shi Yana yi wa maƙiyanSa makirci idan sun yi makirci, Yana mantawa da maƙiyanSa idan sun manta daShi.
Muna imani cewa wasu daga siffofinSa siffar Allah ta zo da su ta fuska ɗaya, kamar siffar rayuwa, da tsayuwa da kai, da girma, suna zuwa a cikin AlKur’ani ko sunna ta fuska ɗaya. Kuma muna samun wasu siffofin labari ya zo game da su a cikin AlKur’ani ko Hadisi ta fuskoki da yawa, kamar siffar zance, da ɗaukaka, da hannu, da ganin muminai ga Ubangijinsu a farfajiyar alƙiyama ranar lahira da kuma aljanna.
Dada siffofinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: Sani da ji, Maɗaukkain sarki ya ce: {Ya ce: "Ubangijina Yanã sanin magana a cikin sama da ƙasa kuma Shi ne Mai ji, Masani} [al-Anbiya: 4].
Daga siffofinSa: Gani, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Lallai Allah Shi ne Mai ji Mai gani} [Ghafir: 20]. Daga Abu Yunus Sulaim ɗan Jubair bara na Abu Hurairah - Allah Ya yarda da shi - ya ce: "Na ji Abu Hurairah - Allah Ya yarda da shi - yana karanta wannan ayar: {Allah Ya na umartarku ku mayar da amanoni zuwa ga masu su} [al-Nisa'i: 58] zuwa faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Mai ji ne kuma Mai gani ne} ya ce: Na ga manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana sanya babban yatsansa akan kunnansa, wanda ke biye da shi kuma akan idansa, Abu Hurairah - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Na ga manzon Allah - tsira daamincin Allah su tabbata agare shi - yana karanta ta, kuma yana sanya yatsunsa biyu, Ibnu Yunus ya ce: al-Muƙri ya ce: Yana nufin: {Lallai Allah mai ji ne kuma mai gani ne}, Yana nufin cewa lallai Allah Yana da ji da gani". (Abu Dawud ya fitar da shi (4728), da Hafsu ɗan Umar a wani yanki na ƙira'o'in annabi (33), da Ibnu Khuzaimah a cikin al-Tauhid (49), da Ibnu Hatam a cikin al-Tafsir (5524).)
Daga siffofinSa - tsarki ya tabbabatar masa Ya ɗaukaka -: Ido, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma domin a rike ka da kyau a kan idoNa} [Daha: 39]. Kuma Ya ce: {Ka yi haƙuri da hukuncin Ubangijinka, lallai fa kai kana kan idanunMu} [al-Dur: 48]. Kuma yabonSa ya ɗaukaka ya ce: {Ka ƙera jirgin ruwa bisa idanuwan Mu} [Hud: 37]. Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Suna gudana a idanuwan Mu} [al-Kamar: 14]. Naga Nafi'u daga Abdullahi - Allah Ya yarda da shi - ya ce: An ambaci Dujal a wajen annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai ya ce: "Lallai Allah ba Ya buyuwa a gareku, lallai Allah ba mai ido daya ba ne - sai ya yi nuni da hannunsa zuwa idansa - kuma Masihu Jujal mai ido ɗaya ne na dama, kai ka ce idansa =inabine a bayyane". (Bukhari ne ya fitar da shi (7407), da Muslim (169), da Abu Dawud (4757), da Tirmizi (2241).)
Daga siffofinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: Rayuwa da tsayuwa da kai, Allah Maɗaukakain sarki Ya ce: {Allah, bãbu wani abin bautawa fãce Shi, Rãyayye wanda komai ya tsayu da shi. [Aal- Imran: 2].
Daga siffofinSa - tsarki ya tabbatar masa Ya ɗaukaka -: Zance, Shi abin siffantawa ne da zance kafin Ya halicci halitta, kuma Yana yi musu magana, zancen Ubangijinmu ya kasance ne da ganin damar Sa, duk lokacin da Ya so zai yi magana, haƙiƙa Hadisi ya zo game da siffar zance ga Allah a cikin AlKur'ani ta fuskoki da yawa, dukkan abinda Allah Ya bada labari da shi game da kansa da cewa Shi Yana umarni ko Yana hani to shi Mai nuni ne akan zance, kamar faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Lalle Allah nã yin umurni da ãdalci da kyautatãwa, da bai wa ma'abũcin zumunta, kuma yanã hani ga alfãsha da abin da aka ƙi da zalinci. Yanã yi muku gargaɗi, ɗammãnin ku, kunã tunãwa} [al-Nahl: 90]. Kuma dukkanin abinda Allah Ya bada labarin sa game da kanSa cewa Shi Ya ce, ko Yana cewa, to shi mai nuni ne akan zance, kamar faɗinSa - sha'aninSa ya ɗaukaka -: {Lokacin da Allah Ya ce ya Isa lallai Ni Mai kasheka ne kuma Mai daukeka ne zuwa gare Ni} [Aal- Imran: 55]. Dukkan abinda Hadisi ya zo a cikinsa game da labarurruka da aka jingina ga Allah to shi mai nuni ne akan tabbatar da siffar zance ga Allah Ubangijin talikai, Allah Ya ce: {Ta ce waye ya baka wannan labarin ?, ya ce: Masani Mai bada labari Shi ne Ya bani labari} [al-Tahrim: 3].
Dukkan abinda ya zo na kira ko ganawa wanda aka jingina ga Allah to shi mai nuni ne akan siffar zance ga Allah Ubangijin talikai, kamar yadda yake a cikin faɗinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Kuma Muka kira shi daga gẽfen dũtse na dãma kuma Muka kusanta shi yanã wanda muka gana da shi}. [Maryam: 52]. Dukkan abinda ya zo na zance da aka jingina ga Allah, ko magana da ta zo a cikin AlKur’ani abin siffantawa da Allah, to shi dalili ne akan siffar zance. Wannan ya fi karfin a lissafe shi, daga hakan cewa Shi - Maɗaukakin sarki - Ya yi wa mala'iku magana, Maɗaukkain sarki ya ce: {Ka tuna lokacin da Ubangijinka ya ce da Mala'iku lallai Ni zan sanya halifa a bayan kasa} [al-Baƙara: 30]. Kuma Ya yi wa (annabi) Adam magana: {Muka ce Ya kai Adam ! Ka zauna kai da matarka a aljanna kuma ku ci daga gareta a halin wadata duk inda kuke so} [al-Baƙara: 35]. Kuma ya yi wa (annabi) Musa - aminci ya tabbata agareshi - magana: {Ya ce ya Musa lallai Ni na zaɓeka akan mutane da saƙo Na da kuma zance Na} [al-A'araf: 144].
Zancen Ubangijinmu daga gare shi akwai kira, kamar yadda Ya kira (annabi) Ibrahim badaɗayi - aminci ya tabbata agare shi -, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma Muka kira shi cẽwa "Ya Ibrahĩm!} [al-Saafat: 104]. Daga cikinsa akwai wanda yake zama ganawa, kamar yadda Ubangijinmu Ya gana da (annabi) Musa - aminci ya tabbata agare shi -: {Kuma Muka kira shi daga gẽfen dũtse na dãma kuma Muka kusanta shi yanã wanda muka gana da shi}. [Maryam: 52]. Ibnu Abbas - Allah Ya yarda dasu - ya faɗa a kan wannan ayar: "Har ya ji ƙarar alƙalami". (Ibnu Abu Shaibah ya fitar da shi (32506), da Hannad a cikin Zuhdu (149), da Abdullahi ɗan Ahmad a cikin al-Sunnah (1231), da Dabari a cikin Tafsiri (15/559), da Hakim (3472).) Suddi ya ce: {Muka kusanto shi dan ganawa} Ya ce: "An shigar da shi sama sai aka yi masa magana". (Tafisr Ibnu Kathir (5/238), da al-Durr al-Mansur fa al-Tafsir bil Ma'asur (5/515).) Kuma zancen Ubngijinmu mala'iku suna jinsa kamar yadda yake a cikin faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Har a lokacin da aka kuranye tsoro daga zukatansu suka ce me Ubangijinku Ya ce? suka ce: Gaskiya kuma Shi ne Maɗaukaki Mai girma} (Saba'i: 23). Daga Masruƙ daga Abdullahi - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Idan Allah Zai yi magana da wahayi, sai ma'abota sama su ji wata ƙara ga sama kamar ƙarar sarƙa akanfar dutse, sai su suma, ba za su gushe ba har sai (mala'ika) Jibrilu ya zo musu, har idan Jibrilu ya zo musu sai a yaye musu tsoron daga zukatansu. Ya ce: Sai suce: Ya Jibrilu, mai Ubangijinka Ya ce? sai ya ce: Ya faɗi gaskiya, sai su ce: Gaskiya ne, gaskiya ne". (Abu Dawud ne ya fitar da shi (4738), da Usman ɗan al-Darimi a cikin raddi ga Jahamiyya (158), da Abdullahi ɗan Ahmad a cikin al-Sunnah (536), da Muhammad ɗan Nasr a cikin Ta'azimu ƙadris Salah (217).)
Kuma Zai yi magana da halittu a ranar lahira, kamar yadda manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bada labari da hakan: "Babu wani ɗaya daga cikinku sai Ubangijinsa ya yi magana da shi, babu wani mai tafinta tsakaninSa da Shi, kuma babu wani shamakin da zai shamakance shi". (Bukhari ne ya fitar da shi (7443), da Muslim (1016), da Tirmizi (2415), da Ibnu Majah (185).)
Kuma halittu zasu ji zancen Allah ranar lahira, kamar yadda yake a cikin Hadisi daga Abdullahi ɗan Unais - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Naji annabi - tsira da amincin Allah su tabbata aagre shi - yana cewa: "Allah Zai tara bayi, sai Ya kirasu da wani sautin da wanda ke nesa zai ji kamar yadda wanda ke kusa zai ji: Ni ne Sarki, ni ne Mai sakamako". (Bukhari ne ya fitar da shi Mu'allaƙi (9/141), a cikin al-Adabul Mufrad (970), da a cikin Kalƙu af'alil ibad (90), da Ahmad (16042).)
Muna imani cewa Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - haƙiƙa Ya shamakance daga halittarSa, ba zasu gan shi a duniya ba, kuma Yana magana da wanda Ya so daga mala'ikunSa da manzanninSa - aminci ya tabbata agare su - ta bayan shamaki, Allah maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma bã ya kasancẽwa ga wani mutum Allah Ya yi masa magana fãce da wahayi, kõ daga bãYan wani shãmaki, kõ Ya aika wani Manzo, sa'an nan Ya yi wahayi, da izninsa ga abin da Yake so. Lalle Shĩ, Maɗaukaki ne Mai hikima} [Al-shura: 51].
Daga Abu Musa - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya miƙe (da wata huɗuba) a cikinmu da kalmomi biyar, sai ya ce: Lallai Allah - Mai girma da ɗaukaka - ba Ya bacci, kuma ba Ya kamata gareShi Ya yi bacci, Yana ƙuntata arziƙi kuma Yana yalwata shi, ana kai aikin dare zuwa gareShi kafin aikin rana, da aikin rana kafin aikin dare, shamakinsa haske ne da Ya yaye shi da hasken fuskarSa sun ƙone inda ganinSa ya tiƙe daga halittarSa". (Muslim ne ya fitar da shi (179), da Ibnu Majah (195).
Zancen Ubangijinmu ana siffanta shi da cewa sashinsa mafi sabunta ne daga sashi, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Wani ambatõ daga Ubangijinsu sãbo, bã ya zuwa gare su fãce sun saurãre shi, alhãli kuwa sunã mãsu yin wãsa} [al-Anbiya: 2]. Sahinsa kuma ya fifici sashi, Daga Abu sa'id al-Kudri - Allah Ya yarda da shi -: Cewa wani mutum ya ji wani mutum yana karanta: {Ka ce Shi ne Allah Shi kadai}, yana maimaita ta, lokacin da ya wayi gari sai ya zo wurin manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai ya ambata masa hakan, kai kace mutumin yana ganin ƙanƙantarta, sai manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Na rantse da wanda raina yake hannunSa, lallai cewa ita ta yi daidai da ɗaya bisa uku na AlKur'ani". (Bukhari ne ya fitar da shi (5013), da Abu Dawud (1461), da Nasa'i (995).)
Daga Abdullahi bn Abbas - Allah ya yarda da shi - ya ce: (Yayin da Jibrilu - amincin Allah ya tabbata a gare shi - zaune tare da Annabi -tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ji wata ƙara daga sama, sai ya ɗaga kansa sama, ya ce: Wannan wata ƙofa ce daga sama da aka buɗe a yau kuma ba a taɓa buɗe ta ba har zuwa yau, sai wani Mala'ika ya sakko daga ciki, don haka ya ce: Wannan wani Mala'ika ne da ya sakko duniya, kuma bai taɓa zuwa ƙasa ba sai yau, sai ya yi sallama ya ce: Ina yi maka albishir da haske guda biyu da aka ba ka wanda ba a bawa wani Annabi a gabaninka ba: Fatiha, da ƙarshen suratul Baƙarah, ba za ku karanta wani Harafi daga cikinta ba ku roki wani abu fa ce sai an baku shi). (Muslim ne ya fitar da shi (806), da Nasa'i (912).)
AlKur'ani da dukkan littattafan Allah waɗanda aka saukar ga manzannin Allah - aminci ya tabbata agare su -, kamar Suhufi Ibrahim da Musa - aminci ya tabbata agare su -, da Attaura da Linjila, da Zabura - dukkaninsu zancen Allah ne, kuma dukkaninsu Allah Ya yi magana da su, kuma Jibrilu - aminci ya tabbata agare shi - ya ji su daga gareShi ba tare da sila ba, kuma Allah Ya saukar da Attaura arubuce akan alluna, Jibrilu ya sauka da wahayi ga annabawan Allah da manzanninSa - aminci ya tabbata agare su -, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Rũhi amintacce ne ya saukar da shi * A zũciyarka, dõmin ka kasance daga mãsu gargaɗi} [al-Shu'araa: 193-194]. Kuma Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Ku yi imani da Allah da manzanSa annabi ummiyyi wanda yake imani da Allah da kalmominSa da litattafanSa ku bi shi kwa shiriya} [al-A'araf: 158]. Zancen Allah da kalmominSa ba halittarsu aka yi ba; saboda haka ne manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya nemi tsari da kalmomin Allah, sai tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Duk wanda ya sauka wani masauki, sai ya ce: Ina neman tsari da kalmomin Allah cikakku daga sharrin abin da Ya halitta, to, babu abin da zai cutar da shi har ya bar wannan masaukin". (Muslim ne ya fitar da shi (2708), da Tirmizi (3437), da Ibnu Majah (3547). Da, kalmomin Allah halittarsu aka yi da annabinmu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - bai nemi tsari da su ba, zancen Allah ba halittarSa ba ne, ba ka ganin "Allah Ya raba tsakanin maganarSa da halittarSa, bai ambace shi magana ba, sai Ya ce: "Ku saurara halitta ta Shi ce haka kuma umarni nasa ne} [al-Aaraf: 54], lokacin da ya ce: {Ku saurara halitta tasa ce } babu wani halitta face ya kasance ya shiga a cikin hakan. Sannan ya ambaci abin da ba halitta ba sai Ya ce: {da umarni} Umarninsa shi ne faɗinSa, Allah - alherinSa ya yawaita - Ubanigijijn talikai da maganarSa ta zama abar halitta". (Aduba: Raddi ga Jahamiyya na Imam Ahmad (shafi na 224).
Muna banbancewa tsakanin kalmomin Allah na kasantattu waɗanda aka ambata, a misalin faɗinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Kuma lalle ne, haƙĩƙa, an ƙaryata manzanni daga gabãninka, sai suka yi haƙuri a kan abin da aka ƙaryata su, kuma aka cũtar da su, har taimakonMu ya je musu, kuma babu mai musanyãwa ga kalmõmin Allah. Kuma lalle ne (abin da yake natsar da kai) ya zo maka daga lãbãrin (annabãwan) farko} [al-An'am: 34]. Da faɗinSa - Maɗaukakin sarki: {Ka ce: "Dã tẽku ta kasance tawada ga (rubũtun) kalmõmin Ubangijina, lalle ne dã tẽkun ta ƙãre a gabãnin kalmõmin Ubangijĩna su ƙãre, kuma kõda mun jẽ da misãlinsa dõmin ƙari} [al-Kahf: 109]. ZancenSa na shari'a wanda ya zo a misalin faɗinSa - Ya girmama Ya buwaya -: {Kuma kalmar Ubangijinka tã cika, tanã gaskiya da ãdalci. Babu mai musanyãwa ga kalmõminSa, kuma Shi ne Mai ji, Masani} [al-An'am: 115]. Da faɗinSa - ambatanSa ya ɗaukaka -: {Lokacin da Ya jarrabi (annabi) Ibrahim da wasu kalmomi sai ya cika su} [al-Baƙara: 124].
Imam al-Darimi ya ce: "Ba mai musun zancen Allah - Mai girma da ɗaukaka - sai wanda yake son ɓata abinda Allah - Mai girma da ɗaukaka - Ya saukar, ta yaya wanda Ya sanar da bayi magana, kuma Ya sa su furuci a ce Zai kasa magana?!". (Raddi ga Jahamiyya na al-darimi ( shafi na 155).)
Daga siffofinSa - tsarki ya tabbatar masa Ya ɗaukaka -: Buwaya, Allah Ya ce: {Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin rinjãye, daga barin abin da suke siffantãwa} [al-Saafat: 180]. Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Wanda yake neman buwaya to buwaya gabaɗaya ta Allah ce} [Faɗir: 10].
Daga siffofinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: Rinjaya, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Babu wani abin bautawa da gaskiya sai Allah Daya Mai rinjaye} [Saad: 65].
Daga siffofinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: Jabarut, da Karfin mulki, da ji-da-isa, da girma, haƙiƙa annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance yana faɗa a cikin ruku'unsa: "Tsarki ya tabbatarwa ma’abocin Jabarut da Karfin mulki, da ji-da-isa da girma". (Abu Dawud ya fitar da shi (873), da Nasa'i (1049), da Ahmad (23980), da Tirmizi a cikin Shama'il (314), da al-Bazzar (2750).) Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Allah - Mai girma da ɗaukaka - Ya ce: Ji-da-isa mayafina ne, girma kuma gwafsona ne, duk wanda ya yi jayayya da Ni da ɗaya daga cikinsu, zan jefa shi a cikin wata". (Abu Dawud ya fitar da shi (4090), da Ibnu Majah (4174), da al-Humaidi (1183), da Ibnu Abi Shaibah (27111), da Ahmad (7382).)
Daga siffofinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: Nufi da Mashi'ah (ganin dama), Allah - Maɗaukakain sarki - Ya ce: {Allah Yana nufin sauƙi gare ku, kuma ba Ya nufin tsanani gare ku} [al-Baƙara: 185]. Da faɗinSa: {Kuma Allah Yana nufin Ya tabbatar da gaskiya da kalmominSa, kuma Ya katse ƙarshen kafirai} [al-Anfal: 7]. Da faɗinsa: {Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda} [al-Takweer: 29].
Daga siffofinSa - tsarki ya tabbabatar masa Ya ɗaukaka -: Iko, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma akwai daga ãyõyinSa, halittar sammai da ƙasa da abin da Ya wãtsa a cikinsu na dabba, alhãli kuwa Shĩ Mai ĩko ne ga tãra su, a lõkacin da Yake so} [al-Shura: 29]. Da faɗinSa: {Lallai Allah Mai ikone akan dukkan komai} [al-Baƙara: 20].
Daga siffofinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: Rahama, Mai yawan rahama Mai yawan jin ƙai - tsarki ya tabbatar maSa - Ya ce: {Rahamata ta yalwaci kowanne abu} [al-A'araf: 156]. Tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya ce: {Ubangijinku Ya rubutawa kanSa rahama} [al-An'am: 54]. Wannan rahamr siffa ce daga siffofinSa, ita abar jinginawa ce ga Allah, jingina siffa ga wanda aka siffanta. Rahama ta kan zo a cikin AlKur'ani da Sunnah abar jinginawa ga Allah, jingina abin halitta ga mahaliccinSa, kamar yadda yake a cikin faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Kuma Shi ne Ya aika iskõkin bushãra gaba ga rahamarSa, kuma Muka saukar da ruwa mai tsarkakẽwa daga sama} [al-Furƙan: 48]. Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Na ji Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana cewa: "Lallai Allah Ya halicci rahama, ranar da Ya halicce ta rahama ɗari". (Bukhari ne ya fitar da shi (6469), da Muslim (2752), da Tirmizi (3541), da Ibnu Majah (4293).) To wannan rahamar halittarta aka yi an jinginata ga Allah daga jingina abin halitta ga mahaliccin Sa.
Daga siffofinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: Daukaka, ita ce ɗaukakar rinjaye, da ɗaukakar daraja, da ɗaukakar zati. Ukun duka siffofinSa ne, kuma su masu nuni ne akan cikarSa, haƙiƙa Alkur’ani mai girma da Sunnar annabi maɗaukakiya da hankali da ɗabi'a sun yi nuni akan ɗaukaka ta fuskoki da yawa, dukkanin abinda Allah Ya bada labari da shi ko manzonSa ya bada labarin sa cewa Shi maɗaukaki ne ko mafi ɗaukaka ne, ko aka yi nuni gare shi cewa Shi Yana cikin ɗaukaka, to shi mai nuni ne akan ɗaukakarSa, kuma kowanne labarin da a cikinsa cewa Maɗaukakin sarki Ya sakko a cikinsa kamar saukar wahayi, da saukar umarni, kuma cewa shi Yana zuwa kuma zai zo ranar AlKiyama dan yin hukunci, ko cewa Shi Yana sakkowa a kowanne dare da kuma yammacin Arfa, da saukar mala'iku, to duka suna nuni ne akan ɗaukakarSa, haka nan kowanne labarin da a cikinsa akwai cewa Shi Yana sama, ko cewa Shi Yana birbishin sama, ko cewa Shi Yana birbishin Al’Arshi, ko cewa Shi Ya daidaita akan Al'arshi - to shi mai nuni ne akan ɗaukakarSa, haka nan dukkan abinda a cikinsa akwai hawa zuwa gareShi - tsarki ya tabbatar maSa - da makamancinsa to shi ma yana nuni ne akan daukakarSa.
Daga hakan: Cewa mala'iku suna jin tsoron Ubangijinsu daga birbishinsu, kuma cewa su suna hawa zuwa gareShi, kuma ayyuka ana ɗaga su zuwa gareShi, kuma ana hawa zuwa gareShi, kuma cewa Allah Ya ɗaga (annabi) Isa - aminci ya tabbata agare shi - zuwa gareShi, kuma ya yi Isra'i da annabinmu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, kuma an yi Mi'iraji da shi zuwa sama. Dukkanin wannan nuni ne akan ɗaukakarSa, kai dalilai masu nuni akan cewa Allah Yana ya ɗaukaka nau'o'i ne masu yawa, kuma ƙarƙashin kowanne nau'i akwai ɗaiɗaiku masu yawan da ba za su ƙirgu ba sai da wahala.
Daga waɗannan dalilan akwai: FaɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {(Allah) Shi ne da abin da ke cikin sammai da abin da ke cikin ƙasa, kuma Shi ne Maɗaukaki, Mai girma} [al-Shura: 4]. Da faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Wancan! sabõda lalle ne Allah, shĩ ne Gaskiya, kuma lalle ne, abin da suke kira waninSa shi ne ƙarya. Kuma lalle ne Allah, Shĩ ne Maɗaukaki, Mai girma} [al-Hajj: 62]. Da faɗinsa: {Zuwa gare shi magana mai daɗi ke hawa, kuma aiki na ƙwarai yana ɗaukarta} [Faɗir: 10]. Da faɗinSa - tsarki ya tabbatar maSa -: {Kuma wannan Littãfi ne, Mun saukar da shi, mai albarka ne, sai ku bĩ shi kuma ku yi taƙawa, tsammãninku, anã jin ƙanku} [al-An'am: 155]. Da faɗinSa: {Lalle ne Mũ, Mun saukar da shi, yanã abin karantãwa na Lãrabci; tsammãninkũ, kunã hankalta} [Yusuf: 2]. Da faɗinSa - tsarki ya tabbatar maSa -: {Suna tsõron Ubangijinsu daga bisansu, kuma suna aikata abin da ake umurninsu} [al-Nahl: 50]. Da faɗinSa: {Lallai Ni Mai kasheka (bacci) ne kuma Mai ɗagoka ne} [Aal- Imran: 55]. Da faɗinSa: {Malã'iku da Ruhi (Jibrila) sunã tãkãwa zuwa gare Shi, a cikin yini wanda gwargwadonsa, shẽkara dubu hamsin ne} [al-Ma'arij: 4]. Da faɗinSa - yabonSa ya ɗaukaka -: {Allah, wanda Ya halicci sammai bakwai ɗin kuma daga ƙasã kwatankwacinsu, umuruinSa yanã ta sauka a tsakaninsu dõmin ku san lalle Allah Mai ĩkon yi ne akan dukan kõme, kuma lalle Allah, haƙĩƙa Ya kẽwaye ga dukan kõme da sani} [al-Dalak: 12]. Da faɗin Allah - tsarki ya tabbatar maSa -: {Ã'a, Allah Ya ɗauke shi zuwa garẽ Shi, kuma Allah Yã kasance Mabuwãyi, Mai hikima} [al-Nisa'a: 158]. Da faɗin Ubangijnmu - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: {Tsarki ya tabbata ga wanda Ya yi tafiyar dare da bãwanSa da daddare daga Masallaci mai alfarma zuwa ga Masallaci mafi nĩsa wanda Muka sanya albarka a gefensa dõmin Mu nũna masa daga ãyõyinMu. Lalle ne Shi shĩ ne Mai ji, Mai gani} [al-Isa'a: 1].
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Lokacin da Allah Ya gama halitta, Ya rubuta wani littafi a warinSa: Ta rinjaya, ko Ya ce: Rahamata ta rigayi fishi Na, shi (Littafin) yana wajenSa a birbishin Al'arshi". (Bukhari ne ya fitar da shi (7553), da Muslim (2751), da Tirmizi (3543), da Ibnu Majah (189).) Daga Mu'awiyah Bin Hakam AsSulami - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Wata rana ina sallah tare da manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, sai wani mutum daga cikin mutane ya yi atishawa, sai na ce: Allah Ya yi maka rahama, sai mutane suka kalleni da idanuwansu, sai na ce: Ya yi wabin mahaifiyarsa, me ya sameku ne kuke kallona?! sai suka buga hannayensu akan cinyoyinsu, lokacin da na ga suna ƙoƙarin sani in yi shiru sai na yi shirun, lokacin da tsira da amincin Allh su tabbata agare shi ya yi sallah, fansarsa babana da babata, ban taɓa ganin malami ba kafinsa ko abayansa mafi iya koyarwa sama da shi, na rantse da Allah, bai yi min tsawa ba bai dake ni ba, bai zageni ba. Ya ce: "Lalle wannan sallar babu wani abu da yake inganta a cikinta daga zancen mutane, kadai shi ne tasbihi da kabbara da karatun AlKur'ani". Ko kamar yadda manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce. Na ce: Ya manzon Allh, ni ban dade da barin jahiliyya ba, hakika Allah Ya zo da musulunci, lallai daga cikinmu akwai wasu mutane sun zowa bokaye, ya ce: "kar ka je wurinsu". ya ce: daga cikinmu akwai wasu mutane suna camfi, ya ce: "Wannan wani abu ne da suke jinsa a kirajensu kada ya toshesu". Ya ce daga cikinmu akwai masu zane a kasa - har zuwa inda ya ce - sai ya ce mata : Ina Allah yake ? Sai ta ce: Yana sama. Sai ya ce; Ni kuma wanene ? Sai ta ce: Kai Manzan Allah ne. Sai ya ce: Ka ‘yanta ta, domin ita mumina ce. (Muslim ya fitar da shi (537), da Abu Dawud (930), da Nasa'i (1218).)
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Mala'iku da daddare da mala'iku da rana suna bibiyar juna a cikinku, suna taruwa a sallar Asuba da sallar la'asar, sannan waɗamda suka kwana a cikinku su hau sama, sai Ya tambayesu, alhali Shi ne mafi sani da su: Yaya kuka bar bayiNa? sai su ce: Mun barsu suna sallah, kuma mun same su suna sallah". (Bukhari ne ya fitar da shi (555), da Muslim (632), da Nasa'i (485).) Kuma a cikn Hadisin Abu Razin Al’uƙaili - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Na ce: Ya manzon Allah, ina Ubangijinmu Ya ke kafin Ya halicci halittarSa? ya ce: "Ya kasance a cikin girgije babu iska a ƙarƙashinSa kuma babu iska a birbishinSa, Ya halicci Al'arshinSa akan ruwa". (Tirmizi ya fitar da shi (3109), da Ibnu Majah (182), da Dayalisi (1189), da Ahmad (16188), da Ibnu abi Asim a cikin Sunnah (625).) Waɗannan da wasunsu daga ayoyi da Hadisai masu yawa masu nuni akan ɗaukakar Allah.
Dalilai masu nuni akan ɗaukaka ba za su iya lissafuwa ba, haƙiƙa malaman musulunci sun haɗu akan tabbatar da shi, kamar yadda hankali da ɗabi'a nagartacciya suka yi nuni akansa, Imamu Ibnu Baɗɗah - Allah ya yi masa rahama - ya ce: "Musulmai daga sahabbai da tabi'ai da dukkan masu ilimi daga muminai sun haɗu akan cewa Allah - alherinSa ya yawaita Ya ɗaukaka - Yana kan Al'arshinSa, a birbishin sammanSa, Yana mai nisantar halittarSa, kuma iliminSa mai kewayewane ga dukkan halittarSa". (al-Ibanah al-Kubra, na Ibnu Baɗɗah (7/136).)
ADDarimi - Allah Ya yi masa rahama - ya cirato: Faɗin Ibnul Mubarak lokacin da aka tambaye shi: "Dame zamu san Ubangijinmu? ya ce: Da cewa Shi Yana kan Al'rshi, a birbishin sama ta bakwai akan Al'arshi, Ya nisanci halittarSa". (Raddi ga Jahamiyya na al-Darimi ( shafi na 98).)
Daga cikin siffofinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: Daidaituwa akan Al'arshi, haƙiƙa Allah Ya ambace shi a gurare bakwai daga littafinSa, daga cikinsu akwai faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Lalle ne Ubangijinku Allah ne, wanda Ya halitta sammai da ƙasa a cikin kwãnaki shida, sannan kuma Ya daidaita a kan Al'arshi, Yanã sanya dare ya rufe yini, yanã nẽman sa da gaggawa, kuma rãnã da watã da taurãri hõrarru ne da umurninSa. To, Shĩ ne da halittar kuma da umurnin. Albarkar Allah Ubangijin halittu tã bayyana!} [al-A'araf: 54]. Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Lokacin da Allah Ya gama halitta, Ya rubuta wani littafi a warinSa: Ta rinjaya, ko Ya ce: Rahamata ta rigayi fishi Na, shi yana wajenSa a birbishin Al'arshi". (Bukhari ne ya fitar da shi (7553), da Muslim (2751), da Tirmizi (3543), da Ibnu Majah (189).) Kuma LalaKal'i ya fitar daga Ibnu Uyaynah ya ce: An tambayi Rabi'a game da faɗinSa: {Ubngiji al-Rahman Ya didaita a kan Al'arshi}: Yaya Ya daidaita? ya ce: "Daidaituwa ba abin jahilta ba ce, amma tayaya ba abin hankalta ba ce, saƙo na Allah ne, isarwa kuma ta manzo ce, kuma gasgatawace ta wajaba akanmu". (Sharhu usulu I'itiƙad Ahlus Sunnah Wal jama'ah (3/442), da kuma Al'arsh na al-Zahbi (2/213).) Kuma an cirato kwatankwacin wannan maganar daga jagoran gidan Hijira Malik - Allah Ya yi masa rahama -. (Abu Nu'aim ya fitar da shi a cikin al-Hilya (325-326), da al-Baihaƙi a cikin al-Asma'u wal-Sifat (2/304), da Ibnu Abdul-Barr a cikin al-Tamhid (7/138), kuma al-Zahbi - Allah Ya yi masa rahama - ya ce: "Haƙiƙa malamai sun yi riƙo da faɗin imamu Malik: "Daidaituwa sananniya ce, kuma tayaya take ba’a sani ba, kuma imani da shi wajibi ne, tambaya game da shi bidi'a ce". Ka'idah da suka tafi akanta a cikin wannan babin" A duba: Al-Uluwwu na al-Zahabi (1/117).)
Daga siffofinSa - tsarki ya tabbabatar masa Ya ɗaukaka -: So, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Da sannu Allah Zai zo da wasu mutanen da Yake son su suma suke son Sa} [al-Ma'ida: 54]. Imam Darimi - Allah Ya yi masa rahama - ya ce: "Sai Ya haɗa tsakanin soyayya biyu: Soyayyar Mahalicci , da soyayyar abin halitta a gwame, sannan Ya raba tsakanin a binda ake so da abinda ba'a so; dan halittarSa su san cewa kishiyoyi ne ba'a haɗe suke ba, sai Ya ce: {Allah baYa son bayyanar da mummunan magana} [al-Nisa'i: 148]. da kuma {Lallai cewa Shi baYa son masu ɓarna} [al-An'am: 141]". (Naƙdhu al-Darimi (2/865).)
Kuma Ya ce: {Lallai Allah Yana son masu yawan tuba kuma Yana son masu yawan son tsarkaka} [al-Baƙara: 222]. Daga Sahlu ɗan Sa'ad - Allah Ya yarda da shi -, ya ce: Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya faɗa ranar Khaibara: "Gobe zan bada tuta ga wani mutumin da za’a yi nasara ta hannunsa, yana son Allah da manzonSa, kuma Allah da manzonSa suna sonsa". (Bukhari ne ya fitar da shi (3009), da Muslim (2406), da Abu Dawud (3661).) Annabi- tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Imanin ɗayanku ba ya cika har sai na kasance mafi soyuwa a gare shi sama da babansa da ɗansa da mutane bakiɗaya" (Bukhari ne ya fitar dashi (15), da Muslim (44), da Nasa'i (5013), da Ibnu Majah (67).)
Daga siffofin Sa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: Yarda, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Marigaya na farko daga waɗanda suka yi hijira da mutanen Madina da waɗanda suka bi su da kyautatawa Allah Ya yarda da su suma sun yarda da Shi} [al-Taubah: 100]. Daga A'isha - Allah Ya yarda da ita - ta ce: Wani dare na rasa manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabata agare shi - a shinfiɗa, sai na laluba shi, sai hannuna ya faɗa akan cikin diga-digansa, alhali shi yana cikin masallaci, su suna kafe, shi yana cewa: "Ya Allah ina neman tsari da yardarKa daga fushinKa, da kuma afuwarKa daga uƙubarKa, kuma ina neman tsarinKa daga gareKa, ba zan iya iyakance yabo a gareKa ba kamar yadda Ka yabi kanKa da kanKa". (Muslim ne ya fitar da shi (486), da Abu Dawud (879), da Tirmizi (3493), da Nasa'i (169), da Ibnu Majah (3841).)
Daga siffofinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: KiyayyarSa ga maƙiyanSa; hakan domin cewa su sun ki yardarSa, kuma sun ki abinda Allah Ya saukar ga manzonSa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Wannan, dõmin lalle sũ sun bi abin da ya fusãtar da Allah kuma sun ƙi yardarSa, sabõda haka Ya ɓãta ayyukansu} [Muhammad: 28], Da faɗinSa: {Sai dai Allah Ya ki fitar su, sai Ya nauyayasu kuma a ka ce; ku zauna tare da mazauna gida} [al-Taubah: 46]. Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Allah Ya ce: Idan bawaNa ya so haɗuwa da Ni sai in so haɗuwa da shi, idan kuma ya ki haɗuwa daNi sai in ki haɗuwa da shi". (Bukhari ne ya fitar da shi (7504), da Nasa'i (1835).)
Daga siffofinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: Fushi akan maƙiyanSa, Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya ce: {Allah Ya yi fushi akansu kuma Ya la'ancesu} [al-Fath: 6]. Daga ɗan Abbas - Allah Ya yarda da su - ya ce: "Fushin Allah Ya tsananta akan wanda Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kashe shi a tafarkin Allah, fushin Allah ya tsananta akan mutanen da suka sa fuskar annabin Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ta yi jini". (Bukhari ne ya fitar da shi (4074).)
Daga siffofinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: Kiyayya, ita ce kiyayyarSa ga kafirai, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Lallai waɗanda suka kafirta ana kiransu lallai ƙiyayyar Allah ita ce mafi girma daga ƙiyayyarku ga kawunanku} [Ghafir: 10].
Daga siffofinSa - tsarki ya tabbata masa Ya ɗukaka -: MakircinSa ga maƙiyanSa waɗanda suke makirci ga masoyanSa, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: Kuma sun yi makirci kuma muma mun kulla makirci alhalin su ba su sani ba * Ka duba yadda karshan makirsu ya kasance, lalle mu mun mutsike su, su da mutanan su baki daya. [al-Naml: 50-51].
Daga siffofinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: Fusatawa, shi ne mafi tsananin fushi, Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Sabõda haka a lõkacin da suka husãtar da Mu, Muka yi musu azãbar rãmuwa sai Muka nutsar da su gabã ɗaya} [al-Zukhruf: 55]. Katada da Siddi sun ce: "{Yayin da suka fusatar daMu} wato: Suka sa muka yi fushi". (Tafsirin Dabari (21/622).)
Daga siffofinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: Yaudarar wanda yake yaudararSa, Allah Yana yaudarar munafukan da suke yaudararSa, Allah - sha'aninSa ya buwaya kuma girmanSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Suna yaudarar Allah da waɗanda suka yi ĩmãni, alhãli bã su yaudarar kõwa fãce kansu, kuma bã su sani ba!} [al-Baƙara: 9]. Kuma Ya ce: {Lallai munafukai suna yaudarar Allah alhli Shi ne Mai yaudararsu} [al-Nisa'a: 142].
Kuma Allah Ya bayyana cewa Yana mantawa da maƙiyanSa kamar yadda suka mance haɗuwa da Shi, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Waɗanda suka riƙi addininsu abin shagala da wãsa, kuma rãyuwar dũniya ta rũɗe su." To, a yau Munã mantãwa da su, kamar yadda suka manta da haɗuwa da yininsu wannan, da kuma abin da suka kasance da ãyoyinMu sunã musu}. [al-A'araf: 51].
Daga siffofinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: Cewa Shi Yana izgili ga wanda Ya yi maSa izgili - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Allah Yana yin izgili gare su kuma Yana kara su a cikin ɓatarsu, suna ɗimuwa} [al-Baƙara: 15]. Ibn Abbas - Allah Ya yarda da su - ya ce: "Yana yi musu izgili dan yi musu azaba". (Tafsirul Dabari (1/304), da Ibnu Abi Hatim a cikin al-Tafsir (143).)
Daga siffofinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: Dariya, daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi -: Cewa manzon Allah - tsaira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Allah Yana dariya ga wasu mutum biyu waɗanda ɗayansu ya kashe ɗayan kuma za su shiga aljanna". (Bukhari ne ya fitar da shi (2826), da Muslim (1890), da Nasa'i (3166), da Ibnu Majah (191).) A cikin Hadisin Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - mai tsawo a ganin Allah - Maɗaukakin sarki - ranar Alkiyama , kuma ya ambata a cikinsa ƙissar na ƙarshen wanda zai shiga aljanna. "....sai Allah Ya ce: Kaicanka ya kai ɗan Adam, ya mamakin yaudararka, shin yanzu ba ka ɗauki alƙawarurrka ba, cewa ba zaka tambayi wanin abinda aka baka ba? sai ya ce: Ya Ubangiji kada Kasanyani mafi taɓewar halittarKa, sai Allah - Mai girma da ɗaukaka - Ya yi masa dariya, sannan Ya yi masa izinin shiga aljanna...". (Bukhari ne ya fitar da shi (806).)
Waki'u ya ce: "Idan an tambayeku: Shin Ubangijinmu Yana dariya? To ku ce: Haka muka ji". (Sharhi Usulul I'itiƙadi Ahlus Sunnah Wal jama'ah (3/477).)
Kuma alHafiz Ibnu Baɗɗah - Allah Ya yi masa rahama - ya yi babi a cikin littafinsa "al-Ibanah"; "Babin imani da cewa Allah - mai girma da ɗaukaka - Yana dariya" Kum a cikinsa ya ce: "Ku sani - Allah Ya yi muku rahama - cewa daga siffofin muminai masu gaskiya gasgata inganatattun Hadisai, da kuma karɓarsu, da barin bijire musu da ƙiyasi, da ajiye magana da ra'ayiyyuka da soye-soyen rayuka; domin cewa imani shi ne gasgatawa, mumini kuma shi ne mai gasgatawa, Allah - Mai girma da ɗaukaka - Ya ce: {To, a'aha! Ina rantsuwa da Ubangijinka, ba za su yi ĩmãni ba, sai sun yarda da hukuncinka ga abin da ya sãɓa a tsakãninsu, sa'an nan kuma ba su sãmi wani ƙunci a cikin zukãtansu ba, daga abin da ka hukunta, kuma su sallama sallamãwa} [al-Nisa'a: 65]. Daga alamomin muminai: Su siffanta Allah da abinda Ya siffanta kanSa da shi, da kuma abinda manzonSa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya siffantaShi da shi daga abinda malamai suka cirato, kuma amintattu daga masu ciratowa waɗanda su ne hujja a cikin abinda suka ruwaito shi na halal da haram da sunnoni da bayanai, ba'a cewa acikin abinda ya inganta daga manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: Ta yaya? kuma: Dan me? kawai su bi kada su ƙirƙira, kuma su miƙa wuya kada suyi jayayya, su yi yaƙini kada su yi kokwanto, daga abinda ya inganta daga annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ma'abota adalci suka ruwaito shi, wanda ya lazimtarwa muminai karbar riwayarsa da barin saba masa: Cewa Allah Yana dariya, ba'a inkarin hakan, kuma babu mai yin musunsa sai dan bidi'a abin zargin hali a wurin malamai". (al-Ibanah al-Kubra na Ibnu Baɗɗah (7/91).)
Daga siffofinSa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: Zuwa a ranar lahira dan rabe hukunci tsakanin mutane, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Ba wani abu suke sauraro ba sai mala'iku su zo musu ko Ubangijinka Ya zo} [al-an'am: 158]. Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma Ubangijinka Ya zo, alhãli malã'iku na jẽre, sahu- sahu} [al-Fajr: 22]. Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Shin suna jira, fãce dai Allah Ya je musu a cikin wasu inuwõyi na girgije, da malã'iku, kuma an hukunta al'amarin? Kuma zuwa ga Allah al'amurra ake mayar da su} [al-Baƙara: 210]. Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Allah Zai tara mutane ranar Alkiyama, sai Ya ce: Wanda ya kasance yana bautawa wani abu to ya bi shi..." Kuma ya koro Hadisn zuwa faɗinSa: "Kuma wannan al'ummar za su wanzu, sai su ce: Wannan ne wurinmu har Ubangijinmu ya zo, idan Ubangijinmu ya zo zamu san shi , sai Allah - Mai girma da ɗaukaka - ya zo musu sai Ya ce: Ni ne Ubangijinku, sai su ce: Kai ne Ubangijnmu sai su bi Shi". (Bukhari ne ya fitar da shi (806), da Muslim (182), da Abu Dawud (4730), da Tirmizi (2554), da Ibnu Majah (178).)
Daga Abul Aliya a cikin faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Ba wani abu suke sauraro ba sai Allah Ya zo musu a cikin wata inuwa daga girgije alhali mala'iku} [al-Baƙara: 210] yana cewa: "Mala'iku za su zo a cikin wata inuwa daga girgije, Allah kuma - mai girma da ɗaukaka - Zai zo a abinda Ya so". (al-Asma'u Wassifat na Baihaƙi (2/370).)
Daga siffarSa - tsarki cewa Ubangij tsarki ya tabbatar masa Ya ɗaukaka - cewa Yana sauka zuwa saman duniya, sauka ta haƙiƙa da ta dace da ɗaukakarSa da girmanSa. Shi ba kamar saukar halittu ba ne, kai shi kamar sauran siffofinSa ne muna imani da su, kuma muna saninsu, bama ɗorawa kanmu sanin yaya hakikanin su yake, ko mu ɗorawa kanmu kin imani da su; kai muna imani da su kamar yadda manzonmu mai gaskiya abin gasgatawa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bamu labari da su, sai ya ce: "Idan rabin dare ya shuɗe, ko biyu bisa ukunsa, Allah - alherinSa ya yawaita kuma Ya ɗaukaka - Yana sauka zuwa saman duniya, sai Ya ce: Shin akwai mai roko a ba shi? shin akwai mai addu'a a amsa masa? Shin akwai mai neman gafara a gafarta msa? har asuba ta yi". (Muslim ne ya fitar da shi (758).)
Kuma babban malami Muhammad Ibnu Khuzaimah - Allah Ya yi masa rahama - ya yi babi acikin littafinsa "al-Tauhid" da faɗinsa: "Babin Hadisai masu tabbatattun Isnadi (madogara) ingantattu waɗanda malaman Hijaz da Iraƙ suka ruwaito su daga annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a cikin sakkowar Ubangiji - Maɗaukaki - zuwa saman duniya kowanne dare, muna shaidawa shaidar mai tabbatarwa da harshensa, mai gasgatawa da zuciyarsa, mai sakankancewa da abinda ke cikin waɗannan Hadisan na saukar Ubangiji, ba ta re da mun siffanta yadda saukar take ba; domin annabinmu Musɗafa bai siffanta mana kaifiyyar sakkowar Mahaliccinmu zuwa saman duniya ba, kuma ya sanar da mu cewa Shi Yana saukowa, Allah - Maɗaukaki - Shi ko annabinsa babu wanda ya bar bayanin abinda muslmai suke da bukata gare shi na al'amarin addininsu, mu masu fada ne masu gasgatawa da abinda ke cikin wadannan Hadisan na ambatan saukowar ba tare da an dora mana fadin siffrSa ko siffar sakkowar take ba; dan annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - bai siffanta mana hakan ba". (al-Tauhid na Ibnu Khuzaimah (1/289).)
Kuma al-Hafiz Ibnu Baɗɗah - Allah Ya yi masa rahama - ya yi babi a cikin littafinsa "al-Ibanah" da faɗinsa: "Babin imani da gasgatawa cewa Allah - Maɗaukakin sarki - Yana saukowa a cikin kowanne dare zuwa saman duniya ba tare da gushewa ba ko kuma kaifiyya ba, sannan Allah Ya yi masa rahama ya ce: "Ku sani - Allah Ya yi muku rahama - cewa Allah Ya wajabtawa bayinSa muminai biyayyar manzonSa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, da karɓar abinda ya faɗe shi, da imani da dukkan abinda Hadisai suka inganta da shi, da miƙa wuya ga hakan ta hanyar barin bijirewa a cikinsa da buga misalai da ƙiyasai zuwa faɗin: saboda me? kuma tayaya?... haƙiƙa ya inganta daga annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - cewa shi ya ce: "Ubangijinmu alhairinSa ya yawaita kuma Ya ɗaukaka -Yana saukowa kowanne dare lokacin da ɗaya bisa ukun dare na ƙarshe ya rage, Yana cewa: Waye zai roƙeNi in amsa masa, waye zai tambayeNi in ba shi, waye zai nemi gafaraTa in gafarta masa". A cikin wani hadisi mai tsawo zamu ambace shi - in Allah Ya so - cikakkensa, manyan masana Hadisi amintattu kuma masu tabbatarwa da masana fiƙihu masu tsantseni ne suka ruwaito shi, waɗanda suka dakko mana shari'ar musulunci zuwa garemu da kuma ginshiƙensa, kamar sallah, da zakka, da azumi, da hajji, da jihadi, da abinda yake bin hakan daga sauran hukunce-hukunce na aure, da saki, da saya da siyarwa, da halal da haram". (al-Ibanah al-Kubra na Ibnu Baɗɗah (7/201). (Kuma Bukhari ne ya fitar da shi (1145), da Muslim (758), da Abu Dawud (1315), da Tirmizi (446), da Ibnu Majah (1366).)
Kuma muna imani da siffar ma'iyyah (cewa Allah Yana Tare da halittar sa), Allah Ubangijin talikai, kuma Allah Yana tare da halittarSa da saninSa da kiyayewarSa, da Mashi'arSa, haƙiƙa Alkur’ani da Sunnah sun yi nuni akan tabbatarwarsu ga Allah - Maɗaukakin sarki -, Allah Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Ashe, ba ka ga cẽwa lalle Allah Yanã sane da abin da yake a cikin sammai da abin da ke cikin ƙasa ba? Wata gãnãwa ta mutum uku bã zã ta kasance ba fãce Allah Shĩ ne na huɗu ɗinta, kuma bãbu ta mutum biyar fãce Shĩ ne na shida ɗinta, kuma babu abin da ya kãsa wannan kuma babu abin da yake mafi yawa fãce Shĩ Yanã tãre da su duk inda suka kasance, sa'an nan Ya bã su lãbãri game da abin da suka aikata a Rãnar kiyãma. Lalle Allah Masani ne ga dukkan kõme} [al-Mujadalah: 7].
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Ku sassauta wa kanku, lallai ku ba kwa kiran kurma ko wanda ba ya nan, lallai cewa ku kuna kiran Mai yawan ji ne kuma Makusanci, Shi Yana tare da ku". (Bukhari ne ya fitar da shi (4205), da Muslim (2704), da Abu Dawud (1526), da Tirmizi (3461).)
Wannan Ma'iyyar (kasancewar) nau'i biyu ce:
Keɓantacciyar Ma'iyyah: Wannan tana kasancewa ne ga manzannin Allah - aminci ya tabbata agare su - da masoyanSa, kuma abinda take hukuntawa: Nasara (taimakonsa) da ƙarfafawa, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Ya ce: "Kada ku ji tsõro. Lalle Nĩ, Inã tãre da ku, Ina ji, kuma Inã gani} [Daha: 46].
Da kuma Ma'iyya gamammiya: Wato: Cewa Allah Yana tare da halittarSa gaba ɗayansu, muminansu da kafiransu, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma Shi Yana tare da ku aduk inda kuke} [al-Hadid: 4]. Ma'anar wannan Ma'iyyar shi ne: Sani da kewayewa, da iko, da sarauta.
Wannan Ma'iyyar ba ta kore ɗaukakar Allah (Allah na sama)?- Maɗaukakin sarki -; domin ma'anarta - kamar yadda ya gabata da haɗuwar malamai shi ne: Sani da wanda yake na kwakwaf ; wato: Allah - Maɗaukakin sarki Yana tare da halittarSa da saninSa da kuma kewayewarSa.
Daga siffofinSa - Maɗaukakin sarki -: Mamaki, daga Abu Hurairah - Allah Ya yarda da shi - daga annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Allah Ya yi mamaki daga mutanen da za su shiga aljanna a cikin sarƙoƙi". (Bukhari ne ya fitar da shi (3010), da Abu Dawud (2677).) Daga Uƙubah ɗan Amir - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Na ji manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana cewa: "Ubangijinku Yana mamaki ga mai kiwon dabbabi a ƙololuwar wani yanki na dutse, yana kiran sallah kuma ya yi sallah, sai Allah - Mai girma da ɗaukaka - Ya ce: "Ku yi duba ga bawaNa wannan yana kiran sallah, kuma yana yin sallah, yana tsoroNa, haƙiƙa Na gafartawa bawaNa, kuma na shigar da shi aljanna". (Abu Dawud ne ya ruwaito shi (1203), da Nasa'i (666), da Ahmad (17312), da Ibnu Abi Asim a cikin al-Sunna (584), da Rauyani (232).)
Kuma muna imani da ganin muminai ga Ubnguijinsu ranar lahira, kamar yadda Alkur’ani ya yi nuni akan hakan, kuma Hadisai masu yawa sun zo daga mnzonmu - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a cikin abin da ya yi wa muminai albishir da shi cewa za su ga Uabngijinsu ganin ido ranar Alkiyama - wannan Allah ne mafi sani - ita ce mafi girman ni'imar 'yan aljanna - Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Wasu fuskõki, a rãnar nan, mãsu annuri ne * Zuwa ga Ubangijinsu mãsu kallo ne} [al-Kiyama: 22-23]. Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Waɗanda suka kyautata, suna da kyakkyawa da kuma ƙari} [Yunus: 26]. Da faɗinSa - sha'aninSa ya ɗaukaka -: {A'aha! Haƙĩƙa, lalle ne sũ daga Ubangijinsu, rãnar nan, waɗanda ake shãmakancẽwa ne} [al-Muɗaffifin: 15]. Haƙiƙa an tambayi Imam Malik sai aka ce da shi: Ya Abu Abdullahi: Shin muminai za su ga Ubangijinsu ranar Alkiyama ? sai ya ce: Da muminai ba za su ga Ubangijinsu ranar lahira ba da Allah bai aibata kafirai da shamakancewa ba sai Ya ce: {A'aha! Haƙĩƙa, lalle ne sũ daga Ubangijinsu, rãnar nan, waɗanda ake shãmakancẽwa ne} (Sharhi Usulul I'itiƙadi Ahlus Sunnah Wal jama'ah (2/468).)
Daga Abu Sa'id alKudri - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Mun ce: Ya manzon Allah, shin zamu ga Ubanugijinmu ranar lahira? ya ce: "Shin kuna cunkoso a ganin wata da rana idan ta kasance a fili fatau?" muka ce:: A'a, ya ce: "Lallai ku ba ku yi turmutsitsi ba a ganin Ubangijinku a wannan ranar, sai dai kamar yadda kuke turmutsitsi a ganinsu", sannan ya ce: '"Mai kira zai yi kira: Ko waɗanne mutane su tafi ga abinda suka kasance suna bautawa, sai ma'abota gicciyayye (kuros) su tafi ga kros ɗinsu, ma'abota gumaka tare da gumakansu, ma'abota kowadanne alloli tare da allolinsu, har wanda yake bautawa Allah ne kawai zai saura, mutumin kirki da fajiri, da wasu kura daga mazowa litafi, sannan a zo da Jahannama za'a bijiro da ita kai ka ce kawalwalniya ce, sai a ce wa Yahudawa: Mekuke bautawa? sai su ce: Mun kasance muna bautawa Uazairu dan Allah, sai ace: Karya kuke yi Allah baShi da mata ko da, to me kuke nufi? sai su ce: muna so kashayar damu, sai ace: Ku sha , sai su fada cikin Jahannama, sannan acewa Nasara: Me kuka kasance kuna bautawa: sai su ce: Mun kasance muna bautawa Masihu dan Allah, sai a ce: Karya kuke yi, karya ne Allah baShi da mata ko da, to me kuke nufi? sai su ce: Muna son kashayar damu, sai ace: Ku sha sai su fada cikin Jahannama, har wanda yake bautawa Allah, mutumin kirki da fajiri ne zasu saura, sai a ce da su: Meya ya tsareku alhali mutane sun tafi? sai su ce: Mun rabu da su, kuma mu a yau mune nafi bukatuwa gare shi a yau, mu din nan mun ji mai kira yana kira: Kowadanne mutane su riski abinda suka kasance suna bautawa, mu kawai muna jiran Ubangijinmu ne, ya ce: sai AlJabbaru Ya zo musu a cikin wata sura ba'a surar da suka ganShi a cikinta ba tun a karon farko, sai Ya ce: Ni ne Ubangijinku, sai su ce: kai ne Ubangijinmu, ba mai yi maSa magana sai annabawa, sai ya ce: Shin a tsakaninku da Shi akwai wata alamar da zaku san shi ? sai su ce: kwauri, sai Ya yaye kwaurinSa, sai kowanne mumini ya yi maSa sujjada". (Bukhari ne ya fitar da shi (7439), da Muslim (183).)
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Lallai ku zaku ga Ubangijin ku kamar yadda kuke ganin wannan watan, ba za ku yi cunkoso a cikin ganainSa ba" (Bukhari ne ya fitar da shi (554), da Muslim (633), da Abu Dawud (4729), da Tirmizi (2551), da Ibnu Majah (177).)
Daga Abu Hurairah - Allah Ya yarda da shi -: Cewa wasu mutane su ce : Ya manzon Allah, shin zamu ga Ubangjinmu ranar lahira? ya ce: "Shin kuna turmutsitsi a wata daren goma sha huɗu wanda babu girgije kusa da shi?" suka ce: A'a ya manzon Allah, ya ce: "Shin kuna cunkoso a ranar da babu wani shamaki kusa da ita" suka ce: A'a, ya ce: " Lallai ku za ku ga Ubangijinku kamar hakan, za'a tashi mutane ranar al-Kiyama, sai ya ce: Wanda ya kasance yana bautawa wani abu to ya bi shi, daga cikinsu akwai mai bin rana, daga cikinsu akwai mai bin wata, daga cikinsu akwai mai bin ɗagutai, sai wannan al'ummar ta tsaya a cikinsu akwai munafikanta, sai Allah Ya zo musu, sai Ya ce: Ni ne Ubangijinku, sai su ce: Kai ne Ubangijinmu, sai Ya kirasu, sai a shinfida siradi a bayan Jahannama, sai in zama farkon wanda zai ketare siradi daga manzanni da al'ummarsa, babu wanda zai yi magana awannan lokacin sai manzanni, kuma zancen manzanni a wannan lokacin: Ya Allah Ka kubutar , Ya Allah Ka kuɓutar". (Bukhari ne ya fitar da shi (806), da Muslim (182), da Abu Dawud (4730), da Tirmizi (2554), da Ibnu Majah (178).)
Hadisan ganin Allah - Alhamdulillah - mutawatirai ne daga manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, faɗin Allah - maɗaukakin sarki - {Ya ce Ya Ubangiji Ka nuna min in yi duba zuwa gareKa. Ya ce ba za ka ganni ba sai dai ka yi duba zuwa dutse idan ya tabbata a gurinsa to zaka ganni} [al-Aaraf: 143]. babu kore ganin Allah; domin wannan a duniya ne. Shi mai kamanceceniya ne da faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a amsar da ya bai wa Abu Zarr - Allah Ya yarda da shi - lokacin da ya tambayi manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: Shin kaga Ubangijinka? ya ce: "Wani haskene ta yaya zan gan shi". (Muslim ne ya fitar da shi (178), da Tirmizi (3282).) Annabin mu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - bai ga UbangijinSa a daren da aka yi Isra'i da shi ba; haƙiƙi Allah Maɗaukakin sarki Ya bamu labari game da abinda UbangijinSa Ya girmamshi da shi na ayoyi a daren da aka yi Isra'i da shi, sai Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Tsarki ya tabbata ga wanda Ya yi tafiyar dare da bãwanSa da dare daga Masallaci mai alfarma zuwa Masallaci mafi nĩsa, wanda Muka sanya albarka a gefensa dõmin Mu nũna masa daga ãyõyinMu. Lalle ne Shi shĩ ne Mai ji, Mai gani} [al-Isa'a: 1]. Allah Maɗaukakin sarki Bai ambaci cewa annabi - tsira da amincin Allah su tabbata aagre shi - ya ga Ubangijinsa ba, da ya ga Ubangijinsa da Allah Ya ambaci hakan ta babin yin baiwa gare shi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -.
Haka nan faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Gannai bã su iya riskuwarSa, kuma Shĩ Yanã riskuwar gannai, kuma Shĩ ne Mai tausasãwa, Masani} [al-An'am: 103]. Ba ya nuni akan kore ganin Allah ba ne; domin riska Ma’anace ƙari akan gani. Kuma: Domin cewa ayoyin da suka gabata akan wannan ayar sun zo ne a siyaƙin ƙarfafa tauhidi da kore ɗa, ba su zama a cikin bayanan Alkiyama ba har su zama masu alaka da ganin Allah.
Al-Darimi - Allah Ya yi masa rahama - ya ce: "Waɗannan Hadisan gaba ɗayansu - kuma mafi yawa daga cikinsu - haƙiƙa an ruwaitosu akan gasgatasu da imani da su, mun riski ma'abota fiƙihu da zurfin ilimi daga malummanmu, musulmai ba su gushe ba ada da yanzu suna ganinsu kuma suna imani da su, ba sa neman yin inkarinsu kuma ba sa inkarinsu, wanda ya yi inkarinsu daga karkatattu sai suka danganta shi zuwa ɓata, kai ya kasance daga mafi girman kwaɗayinsu da mafi gwggwaɓan ladan Allah akan kansu shi ne duba zuwa fuskar Mahaliccinsu har ba za su daidaita komai da shi ba daga ni'imar aljanna". (Raddi ga Jahamiyya na al-Darimi ( shafi na 122).)
Shugaban masu tafsiri Ibnu Jarir Dabari - Allah Ya yi masa rahama - Ya ce: "Amma magana ta daidai akan ganin muminai ga Ubangijinsu - mai girma da ɗaukaka - ranar lahira - shi ne addininmu wanda muke addini da shi, kuma mun riski Ahlus Sunnah Wal jama'ah - shi ne: Cewa 'yan aljanna zasu ganShi akan abinda Hadisai suka inganta da shi daga manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -". (Saril Sunnah, na al-Dabari (shafi na 20).)
Ibnu Baɗɗah - Allah Ya yi masa rahama - ya ce: "Kawai sun so ɓata RububiyyarSa ne ta hanyar musanta ganinSa; domin cewa duk lokacin da suka tabbatar da ganinSa sun tabbatar da RububiyyarSa; domin Allah - Maɗaukakin sarki - Ya sanya ladan wanda ya gasgata shi da gaibu yana mai imani cewa zai ganShi ɓaro-ɓaro". (al-Ibanah al-Kubra, na Ibnu Baɗɗah (2/7).)
Walidu ɗan Muslim ya ce: Na tambayi Auza'i, da Malik ɗan Anas, da Sufyan al-Sauri, da Laisu ɗan Sa'ad, game da waɗannan Hadisan da a cikinsu akwai ganin Allah da wanin wannan, sai suka ce: "Ka zartar da su batare da kaifiyya ba". (al-Sifat na al-Daru al-Kuɗni (Shafi na 75).)
Kuma muna tabbatar wa Allah fuska da ta dace da ɗaukakarSa da girmanSa, kamar yadda Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kowanne abu mai mutuwa ne sai fuskarSa, hukunci ya tabbata gareShi kuma gareShi ne za'a maidaku} [al-Kasas: 88], Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Kuma fuskarar Ubangijinka, Ma’abocin girma da karimci, ita ce zata wanzu} [al-Rahman: 27], Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Waɗanda suka yi haƙuri dan neman fuskar Ubangijinsu} [al-Ra'ad: 22], Kuma Ya ce: {Fãce dan nẽman fuskar Ubangijinsa Mafi ɗaukaka} [al-Lail: 20], Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Suna nufin fuskarSa}. [al-An'am: 52]. Daga annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - cewa shi ya ce: "Aljannatai guda biyu ƙwarransu na azurfa ne, da abinda yake cikinsu, da kuma aljannatai guda biyu ƙwarransu na zinariya ne da abinda ke cikinsu, kuma abinda yake tsakanin mutane da abinda yake tsakanin su ga Ubangijinsu, babu komai sai wani mayafi na girma akan fuskarSa a cikin aljannar dawwama". (Bukhari ne ya fitar da shi (4878), da Muslim (180), da Tirmizi (2528), da Ibnu Majah (186).)
Kuma Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Lallai Allah - Mai girma da ɗaukaka - ba Ya bacci, kuma ba ya kamata gareShi Ya yi bacci, Yana ƙasƙantar da ma'auni kuma Yana ɗaukaka shi, ana ɗaga aikin dare kafin aikin rana zuwa gare Shi, da aikin rana kafin aikin dare, shamakinSa shi ne haske, da ace zai yaye shi da giza-gizan fuskarSa sun ƙona inda ganinsa ya tiƙe daga halittarSa". (Muslim ne ya fitar dashi (179), da Ibnu Majah (195 - 196).)
Abu Usman al-Sabuni - Allah Yayi masa rahama - ya ce: "Haka nan suke cewa a dukkanin siffofin da Alkur’ani ya sauka da ambatansu, kuma Hadisai ingantattu suka zo da su: na ji, da gani, da ido, da fuska, da sani, da ƙarfi, da iko, da buwaya, da girma, da nufi, da Mashi'ah, da magana, da zance, da yarda, da fushi, da rayuwa, da farkawa, da farin ciki, da dariya, da wasunsu ba tare da kamantawa ga wani abu daga hakan ba da siffofin ababen halitta, kai suna tiƙewa acikinsu zuwa abinda Allah - Maɗaukakin sarki - Ya faɗe shi da abinda manzonSa - tsira da a mincin Allah su tabbata agare shi - ya faɗe shi - ba tare da ƙari akaiba, ba kuma tare da jinginawa gare shi ba, ba kum tare da tayaya ba, ba kamantawa ba, ba canjawa ba, ba kuma tare da gusar da wani lafazin labari daga abinda larabawa suka sani ba, kuma suka dora su akansa na wani mummunan tawili ba, kuma suna gudanar da shi akan zahiri zuwa ga Allah - madaukakin sarki - da cewa tawilinsa babu wanda ya san shi sai Allah, kamar yadda Allah Ya bada labari game da shi dangane da matabbata a cikin ilimi cewa su suna cewa a cikin fadinSa - Madaukain sarki -: {Matabbata a cikin ilimi suna cewa mun yi imani da shi dukkansa daga Ubangijinmu ne kuma ba mai wa'azantuwa sai dai ma'abota hankula} [Aal- Imran: 7]. (Aƙidatus Salaf ashabul Hadis, na Abu Usman al-Sabuni (shafi na 16-17).)
Daga siffofinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: Siffar hannu, haƙiƙa bayani ya zo da ita a cikin Alkur’ani da Sunnah ta fuskoki da yawa, wani lokaci a ambacesu biyu, wani lokaci kuma Maɗaukakin sarki Yana bada labarin cewa Yana damƙesu kuma Yana shinfiɗasu, kuma cewa Shi - Maɗaukakin sarki - Zai damƙi ƙasa da hannunSa, kuma Zai ninke sammai da damanSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -. Wani lokaci kuma abin siffantawa da cewa suna da yatsu, dukkanin wannan yana tabbatar da cewa hannun da bayaninsa ya zo a cikin AlKur'ani da Hadisi hannu ne na haƙiƙa wanda ya dace da ɗaukakarSa, ba zamu dorawa kanmu tawilinsu ba ko kamantasu ko canja ayoyin da Hadisan masu nuni akan su ba, Allah - Madaukakin sarki Ya ce: {(Allah) Ya ce, "Yã Ibilis! Mẽ ya hana ka, ka yi sujada ga abin da Nã halitta da HannayeNa biyu? Shin, kã yi girman kai ne, kõ kuwa kã kasance daga maɗaukaka ne?} [Saad: 75]. Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Lallai waɗanda suke maka caffa kaɗai suna yi wa Allah caffa ne hannun Allah birbishin hannunsu} [al-Fath: 10], Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya ce: {Kuma ba su girmama Allah a kan haƙĩƙanin girmansa ba, kasa duka damƙarSa ce, a Rãnar kiyãma, kuma sammai abũbuwan naɗewa ne ga dãmanSa. Tsarki ya tabbata a gare Shi, kuma Ya ɗaukaka daga barin abin da suke shirki da shi} [al-Zumar: 67].
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "(Annabi) Adam da (Annabi) Musa - aminci ya tabbata agare su - sun yi jayayya a wurin Ubangijinsu, sai (annabi) Adam ya kafa wa (annabi) Musa hujja, (Annabi) Musa ya ce: Kai ne Adam wanda Allah Ya halicceka da hannunSa, kuma Ya busa daga ransa a acikinka". (Bukhari ne ya fitar da shi (6614), da Muslim (2652), da Abu Dawud (4701), da Tirmizi (2134), da Ibnu Majah (80).) A cikin wata riwayar: "(Annabi) Adam da (Annabi) Musa sun yi jayayya, sai (Annabi) Musa ya ce da shi: Ya Adam, Kai ne babanmu ka taɓar da mu ka fitar da mu daga aljanna, sai Adam ya ce da shi: Ya Musa Allah Ya zaɓeka da zancenSa, kuma Ya zana maka da hannunSa". (Bukhari ne ya fitar da shi (6614), da Muslim (2652), da Abu Dawud (4701), da Tirmizi (2134), da Ibnu Majah (80).)
A cikin ingantaccen Hadisi manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Lallai masu adalci a wurin Allah suna kan munbarirrika na haske, a daman Ubangiji Mai rahama - Mai girma da ɗaukaka - su duka hannayensa biyun dama ne, waɗanda suke adalci a hukuncinsu da iyalansu da abin da suka jiɓinta". (Muslim ne ya fitar da shi (1827), da Nasa'i (5379).)
Daga Abu Musa - Allah Ya yarda da shi - daga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Lalle ne Allah - Maɗaukakin sarki - Yana shimfiɗa hannunSa da dare domin masu laifi da rana su tuba, kuma yana shimfiɗa hannunSa da rana domin masu laifi da dare su tuba, har sai rana ta ɓullo daga yammacinta". (Muslim ne ya fitar da shi (2759).)
A cikin ingantaccen Hadisi daga manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Shin kuna ganin abinda Ya ciyar tun lokacin da Ya halicci sama da ƙasa? domin abinda ke hannunSa bai ragu ba, kuma Al'arshinSa ya kasance akan ruwa, kuma a hannunSa akwai ma'auni Yana ƙasƙantar wa Yana kuma ɗaukakawa". (Bukhari ne ya fitar da shi (4684), da Muslim (993), da Tirmizi (3045), da Ibnu Majah (197).)
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Lokacin da Allah Ya halicci Adam, Ya busa rai a cikinsa, sai ya yi atishawa, sai ya ce: Godiya ta tabbata ga Allah, sai ya godewa Allah da izininSa..." har zuwa inda ya ce: "Sai Allah Ya ce masa alhali hannayensa biyu a dunƙule suke: Ka zaɓi wanda kake so, ya ce: Na zaɓi daman Ubangijina, kuma hannayen Ubangijina su biyun dama ne mai albarka, sannan Ya shinfiɗasu, sai ga Adam da zuriyarsa a cikinsu". (Tirmizi ne ya fitar da shi (3368), da Abu Asim a cikin al-Sunnah (596), da al-Bazzar (8194), da Nasa'i a cikin al-Kubra (9977).)
Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Lallai zukatan 'yan Adam baki ɗayansu suna tsakanin yatsu biyu daga cikin yatsun (Allah) Rahman, kamar zuciya ɗaya Yana sarrafa ta yadda Ya so". (Muslim ne ya fitar da shi (2654).)
Abdullahi ɗan Imam Ahmad ya fitar a cikin littafinsa "Sunnah", da sanadinsa daga Waki'u ya ce: 'Mu Muna miƙa wuya ga waɗannan Hadisan kamar yadda suka zo, kada mu ce: Ta yaya haka? kuma kada: Dan me yasa haka? yana nufin misalin Hadisin Ibnu Mas'ud - Allah Ya yarda da shi -: "Lallai Allah - Mai girma da ɗaukaka - Zai ɗauki sammai akan yatsa, duwatsu ma akan yatsa". Da Hadisin annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Lallai zukatan 'ya'yan Adam gaba ɗayansu suna tsakanin yatsu biyu daga yatsun ArRahman". (Muslim ne ya fitar da shi (2654).) Da makamantan wadannan Hadisai. (Sunnah, na Abdullahi ɗan Ahmad (1/267).)
Sharik - Allah Ya yi masa rahama - ya ce yana mai bada amsa ga wanda ya tambaye shi daga wanda yake inkarin wasu daga Hadisan siffofi: "Lallai waɗanda suka zo da waɗannan Hadisan su ne waɗanda suka zo da Alkur’ani, kuma cewa salloli biyar ne, da Hajjin ɗaki, da azimin Ramadan, ba mu san Allah ba sai ta waɗannan hadisan". (Sunnah, na Abdullahi ɗan Ahmad (1/273).)
AlHafiz Ibnu Baɗɗah - Allah Yayi masa rahama - Ya ce - bayan ya koro Hadisan da suke nuni akan siffar hannu ga Allah Ubangijin talikai: "Waɗannan Hadisan da ire-irensu, da abinda ya zo a ma'anarsu a cikin cikar addini, da cikar Sunna: Shi ne yin imani da su, da karɓarsu ta hanyar barin bijirewa akan su, da bin sawun magabata na gari wajan ruwaito su ba tare da kaifiyya ba, ko ta yaya ba". (al-Ibanah al-Kubra, na Ibnu Baɗɗah (3/313).)
Kamar yadda Ya siffanta kanSa da siffofin cika da kyau da girma da buwaya da ji-da-isa, haƙiƙa Ya korewa kanSa siffofin tawaya, amma korewa a cikin siffofin bai zama shi ne asali ba a cikin Alkur’ani mai girma da Sunnah; domin cewa asali shi ne tabbatar da siffofi, AlKur'ani da Sunnah a cike suke da bayanin siffofin Allah - Mai girma da ɗaukaka - kamar yadda ya kamata da ɗaukakarSa da girmanSa da cikarSa, Ubangiji - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka, idan Ya korewa kanSa wata sifa kawai Yana koreta ne; dan bayanin cika a kishiyarta, ko dan cewa mutane sun danganta tawaya zuwa ga ma'abocin buwaya da cika, to Ubangiji Ya kore tawayar da aka danganta maSa.
Daga abinda Ubangiji Ya korewa kansa: Gyangyaɗi da bacci, kamar yadda yake a cikin faɗinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Allah babu abin bautawa da gaskiya sai Shi Rayayye Tsayayye da kanSa gyanagyaɗi ba ya ɗaukarSa ballantana bacci} [al-Baƙara: 255]. Kuma Ya kore mantuwa, sai Allah Ya ce: {Kuma Ubangijinka bai kasance Mai mantuwa ba} [Mryam: 64]. Kuma Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya korewa kanSa gajiya; domin cewa Yahudawa - tsinuwar Allah ta tabbata akan su - sun dangantawa Allah gajiya lokacin da Ya halicci halitta, kuma Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya korewa kanSa cewa Shi Ya huta bayan kammala halitta, sai Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun halitta sammai da ƙasã da abin da ke a tsakãninsu, a cikin kwãnaki shida, alhãli wata'yar wahala ba ta shãfe Mu ba} [Q: 38].
Kuma Ubangijinmu Ya tabbatar cewa Shi Ya halicci halitta dan wasu hikimomi masu girma, kuma Bai halicci halittarSa dan wasa ba, sai Ubangijinmu Ya korewa kanSa wasa, sai Maɗaukakin sarki Ya ce: {Shin, to, kun yi zaton cẽwa Mun halitta ku ne da wãsa kuma lalle ku, zuwa gare Mu, bã zã ku kõmo ba} [al-Mua'Munun: 115]. Kuma Allah Ya bayyana cewa hukuncinSa shi ne adalci, kuma maganarSa ita ce rabewa, kuma cewa Shi baYa zalintar wani; dan cikar adalcinSa - tsarki ya tabbatar masa Ya ɗaukaka -, sai Ubangijinmu - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma suka samu abin da suka aikata a halarce kuma Ubangijinka baYa zalintar wani ɗaya} [al-Kahf: 49]. Kuma Ya ce: {Kuma Ubangijinka bamai zalintar bayi ba ne} [Fussilat: 46].
Kuma Yahudawa da Nasara sun danganta wa Allah ɗa, dan kamanceceniya da waɗanda suka kafirta dake gabaninsu, sai Allah Ya korewa kanSa ɗa, sai Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Allah bai riki wani abin haihuwa ba kuma babu wani abin bauta tare da Shi} [al-Mu’uminun: 91]. Kuma tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya bayyana cewa wanda yake da ɗa to babu makawa ya kasance yana da mata, Allah wanda ya tsarkaka ne daga mata da kuma ɗa, sai tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya ce: {Mafarin halittar sammai da ƙasa. Yãya ɗã zai zama a gare Shi alhãli kuwa mãta ba ta kasance ba, a gare Shi, kuma Ya halitta dukkan, kõme, kuma Shĩ, game da dukan kõme, Masani ne?} [al-An'am: 101]. Kuma Ya ce: {Kuma lalle ne shĩ girman Ubangijinmu, Ya ɗaukaka, bai riƙi mãta ba, kuma bai riƙi ɗã ba} [al-Jinn: 3].
Kuma muna imani Allah - tsarki ya tabbatar masa Ya ɗaukaka - Yana da sunaye kyawawa, kuma sunayenSa haƙiƙa sun kai matuƙa a kyau, babu wani abu da ya kai su kyau, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Allah bãbu abin bautãwa fãce Shi. Yanã da sunãye mafiya kyau} [Daha: 8]. Daga cikinsu abinda ya zo a cikin faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Godiya ta tabbata ga Allah, Ubangijin talikai * Mai rahama, Mai jin ƙai * {Mamallakin ranar sakamako} [Fatiha: 2-4]. Haka a cikin faɗinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: (Wanda Ya saukar da Alƙur'ani) Shi ne Allah, wanda bãbu wani abin bautãwa fãce Shi Masanin fake da bayyane, Shĩ ne Mai rahama, Mai jin ƙai * Shĩ ne Allah, wanda bãbu abin bautãwa fãce shi, Mai mulki, Mai tsarki, Aminci, Mai amintarwa, Mai Tsarẽwa, Mabuwãyi, Mai Aljabbar, Mai nuna isa, tsarki ya tabbata a gare Shi daga abin da suke yi na shirki da Shi * Shĩ ne Allah, Mai halitta, Mahalicci, Mai sũrantãwa. Yanã da sũnãye mãsu kyau, abin da ke a cikin sammai da ƙasa sunã tsarkake Shi, kuma Shĩ ne Mabuwãyi, Mai hikima} [Suratul Hashr: 22-24].
Sunayen Allah tsagosu aka yi ba a sandare suke ba, kuma kowanne suna ana tsago sifa daga cikin shi, sai aka tsago siffar rahama daga ArRahim, buwaya kuma daga alAziz, hikima kuma daga alHakim, rayuwa kuma daga alHayyu, haka nan.
Kuma sunayenSa ba su da iyaka, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Ina roƙonKa da dukkanin sunan da Ka ambaci kanKa da shi, ko Ka saukar da shi a cikin littafinKa, ko Ka sanar da wani daga halittarKa, ko Ka barwa kanka saninsa a cikin iliminka na gaibu a wajenka" (al-Dabbi ne ya fitar da shi a cikin al-Du'a (6), da Ibnu Abi Shaibah a cikin al-Musannaf (29930), haka a cikin Musnad (329), da Ahmad (3712), da al-Haris ɗan Abi Usamah a cikin al-Musnad kamar yanda yake a cikin Bugyatul Bahis (1057).) Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Lalle Allah Yana da sunaye casa’in da tara: dari ba ɗaya, wanda ya kiyaye su zai shiga aljanna". (Bukhari ne ya fitar da shi (2736), da Muslim (2677), da Tirmizi (3506), da Ibnu Majah (3860).)
Kuma Ubangijin mu Ya gargaɗar da mu daga Ilhadi (karkatarwa) a cikin sunayenSa, sai Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma Allah Yanã da sũnãye mãsu kyau. Sai ku rõƙe shi da su, kuma ku bar waɗanda suke yin ilhãdi a cikin sũnãyenSa: zã a sãka musu abin da suka kasance sunã aikatãwa} [Suratul A'araf: 180].
Ilhadi a cikin sunayenSa nau'o'i ne: Daga cikinsu: Ambaton wani da sunayenSa waɗanda ba ya halatta a ambaci mutane da su, kamar Mahalicci, da Mai yawan rahama, da wasunsu. Daga cikinsu: Ambaton gumaka da wasu sunayen da aka tsago daga sunayen Allah, kamar Lata daga sunan Allah, da Uzza daga Al’Aziz. Daga cikinsu: Yin musunsu, ko musun ma'anoninsu, ko kore su.
Abinda ya zo a cikin Alkur’ani da Hadisi na sunayen Allah da siffofinSa sun fi karfin wani littafi ya kunshe su, sai dai ya ishemu ɗaukaka cewa mu mun yi nuni zuwa wasu jumloli a wannan babin.
Kuma muna imani cewa musulmi yana wajaba akansa kada ya siffanta Allah, ko ya ambaceShi sai da abinda (Shi Allah din) Ya siffanta kanSa da shi ko Ya ambaci kanSa da shi, ko manzonSa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya siffanta Shi ko ya ambaceShi da shi, kuma ya kore maSa abinda Ya korewa kanSa da shi ko manzonSa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kore maSa, kuma ya yi shiru daga koma bayan hakan.
Kuma mu muna imani da waɗannan sunayen da siffofin akan manufar Ubangijinmu, da kuma manufar manzonmu - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, kuma muna sanin cewa haƙiƙaninsu babu wani mutum da ya sansu, kuma ba su kewaye da saninsu ba, kuma fahimtarsu ba ta isu zuwa garesu ba, kuma ba ma ɗorawa kanmu tawilinsu; domin Allah - Ya umarci annabinSa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: {Kuma ni bana daga cikin masu ƙalƙalen faɗarsa} [Saad: 86]. Kamar yadda a cikin aljanna akwai nau'o'in ni'ima wadda ambatansu ya zo a cikin Alkur’ani da Sunah ba sa tarayya, tare da kamanceceniyar su a suna da ni'imar duniya, sai dai a tsakaninsu akwai nisa da banbancin da sanin mutum bai isa ya kewaye shi ba, idan mun kasance muna imani da ni'imar aljanna, alhali mu bamu ganta ba, kuma bama sanin haƙiƙaninta da kaifiyyarta - to Allah Shi ne mafi girma da ɗan Adam ya yi tarayya daShi dan kawai tarayya a (sunan) siffofi da sunaye, kuma hakan ba ya lazimtar kore sunaye da siffofi ga Allah dan kawai tarayya a lafazi.
Haƙiƙa bayanan shugabannin shiriya da ilimi sun zo akan tabbatar da hakan, Ibnu Abi Zamanin ya ce: "To waɗannan siffofin Ubangijinmu ne waɗanda Ya siffanta kanSa da su a cikin littafinSa, kuma annabinSa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya siffantaShi da su, kuma babu wani abu na iyakancewa ko kamantawa ko ƙaddarawa a cikinsu, tsarki ya tabbatarwa wanda babu wani abu kwatankwacinSa, Shi ne Mai yawan ji Mai yawan gani, idanuwa ba su gan shi ba ballatana su iyakance Shi tayaya yake, sai dai zukata sun ganShi a cikin haƙiƙani imani da Shi". (Usul al-Sitta na Ibnu Abi zamanin (shafi na 74).)
Abdul-Rahman ɗan Kasim ya ce: "Ba ya kamata ga wani ya siffanta Allah sai da abinda Ya siffanta kanSa da shi a cikin Alkur’ani, kuma kada ya siffanta hannayenSa da wani abu, ko fuskarSa da wani abu, sai dai ya ce; Yana da hannaye biyu, kamar yadda Ya siffanta kanSa da shi a cikin AlKur'ani, kuma Yana da fuska kamar yadda Ya siffanta kanSa, ya tsaya a inda Ya siffanta kanSa da shi a cikin AlKur'ani; domin cewa Shi - alherinSa ya yawaita kuma Ya ɗaukaka - ba Shi da tamka kuma baShi da kama, sai dai Shi ne Allah babu wani abin bauta da gaskiya sai Shi kamar yadda Ya siffanta kanSa, kuma hannayenSa a shinfiɗe suke kamar yadda Ya siffanta su: {Kuma ƙasa duka damƙarSa ce a ranar AlKiyama, kuma sammai abubuwan naɗewa ne da damanSa} [Zumar: 67]. Kamar yadda Ya siffanta kanSa". (Usul al-Sitta na Ibnu Abi zamanin (shafi na 75).)
Imaml Humaidi - Allah Ya yi masa rahama - ya ce: "Abinda Alkur’ani da Hadisi suka yi furuci da shi, misalin: {Kuma Yahudawa suka ce hannun Allah a ƙuƙumi yake, an ƙuƙunce hannuwansu). [Ma'ida: 64]. Da misalin: {Kuma sammai an ninkesu a damanSa} [Zumar: 67]. Da abinda ke kama da wannan na Alkur’ani da Hadisi, ba zamu yi ƙari a cikinsa ba, kuma ba za mu fassara shi ba, muna tsayawa akan abinda AlKur'ani da Sunnah suka tsaya akansa". (al-Uluwwu lil Aliyyil-Azim na al-Zahabi (shafi na 168).)
Imam Ahmad ya ce: "Muna bautawa Allah da siffofinSa kamar yadda Ya siffanta kanSa da su, haƙiƙa Ya kyautata siffa ga kanSa, kuma kada mu ƙetare Alkur’ani da Hadisi, sai mu faɗi yadda Ya faɗa, kuma mu siffantaShi kamar yadda Ya siffanta kanSa, kada mu ƙetare hakan, muna imani da Alkur’ani dukkanin sa, muhkam ɗinsa da masu rikitarwarsa, ba za mu kore maSa - Maɗaukakin sarki - ambatanSa ga wata sifa daga siffofinSa dan wani munin da aka munanana , kuma ba za mu gusar da abinda ya siffanta kansa da shi ba na zance, da sauka da kaɗaitakarSa da bawanSa a ranar Kiyama, da ɗora kanafinsa a gare shi, wadannan dukkaninsu suna nuni ne akan cewa Allah za'a ganShi a lahira, kuma iyakancewa a wannan bidi'a ce, mika wuya ga Allah da umarninSa, Allah Bai gusheba mai magana ne, masani mai yawan gafara ne, Masanin gaibu da abinda ke bayyane masanin gaibu, wadannan siffofin Allah ne Ya siffanta kanSa da su, ba za’a turesu ba kuma ba za’a ki karbar su ba, kuma ya ce: {Allah, bãbu wani abin bautawa fãce Shi, Rãyayye Mai tsayuwa da kõme} [al-Baƙara: 255]. {Babu abin bautawa da gaskiya sai Shi, Mai mulki, Mai tsarki, Aminci, Mai amintarwa, Mai tsarewa, Mabuwayi, Mai tilastawa, Mai nuna isa} [Hashr: 23]. Waɗannan siffofin Allah ne da sunayenSa". (Al’Ibanah al-Kubra, na Ibnu Baɗɗah (7/326).)
Imam Abul-Kasim ya ce - alhali an tambaye shi game da siffofin Ubangiji - Allah Maɗaukakin sarki - sai ya ce: "Mazahabar Malik, da Sauri, da Auza'i, da Shafi'i, da Hammad ɗan Salamah, da Hammad ɗan Zaid, da Ahmad ɗan Hanbali, da Yahaya ɗan Sa'id, da Abdul-Rahman ɗan Mahdi, da Ishaƙ ɗan Rahuwaih: Cewa siffofin Allah waɗanda Ya siffanta kanSa da su, ko manzonSa ya siffanta Shi da su, na ji, da gani, da fuska, da hannaye, da sauran siffofi, kawai su akan zahirinsu ne sananne yadda suka shahara, ba tare da tayaya ba?, ya za'a yi babu wani wahami a cikinsu, babu kamantawa kuma babu tawili". (al-Uluwwu lil Aliyyil-Azim na al-Zahabi (2/459).)
Kuma ya ce: "Ni, anan zan anbaci jama'a - da yardar Allah - Maɗaukakin sarki - daga shugabanninmu magabata da suka yi bayani a kan waɗannan ma'anonin, daga cikin su akwai: Abu Abdullahi Sufyan ɗan sa'id ɗan masruƙ Sauri; domin shi ya bayyanar da ƙudirinsa, da mazahabarsa a Sunnah a sama da guri ɗaya, haƙiƙa ya yi shiftar (Akidar sa) ga Shua'b ɗan Harb, kuma daga cikinsu akwai: Abu Muhammad Sufyan ɗan Uyayynah al-Hilali; cewa shi ya amsa a ƙudirinsa lokacin da aka tambaye shi, kamar yadda Muhammad ɗan Ishaƙ al-saƙafi ya ruwaito, daga cikinsu akwai Abu Amr Abdurrahman ɗan Amr al-Auza'i jagoran mutanen Sham; cewa shi ya bayyanar da kudirinsa a zamaninsa. Kuma Ibnu Ishak ya ruwaitoshi Alfuzazi, daga cikinsu akwai: Abu AbdrRahman dan Abdullahi dan Mubarak jagoran Khurasan, da Fudail dan Iyad, da Waki'u dan al-Jarrah, da Yusuf dan Asbad sun bayyanar da kudirin su, shi ne kuma mazahabarsu, daga cikinsu akwai: Sharik dan Abdullahi al-Nakha'i, da Yahaya dan sa'id Kaddan, da Abu Ishak al-Fuzari, daga cikinsu akwai: Abu Abdullah, da su Malik da Shafi’u da Ahmad bin Hanbal, Abu Ahmad Alharawi ya kasance cikin manyan malaman Khurasan, ya ce: Ya kamata ga wanda Allah ya yi mishi baiwa da ilimi na shiriya da Karama da Sunna cikin wadanda suka saura ababan koyi, ya ce: Mu ce Allah tsarki ya tabbata a gare shi, Shi kadai yake ba shi da abokin tarayya, ba shi da kishiya, babu irinsa, babu kamarsa, Shi ne kadai abin bauta shi kadai, wanda kowa yake nufatarsa da bukatu, ba shi da mata kuma ba shi da da, kuma ba shi da kowanne abokin tarayya a hukuncin da. (al-Hujja fi bayanil Manhajja (2/508).)
Kuma ya ce - Allah Ya yi masa rahama -: "Hanyar Hadisai da suke bayanin siffofiin Ubangiji: Shi ne mu yi imani da su, kuma kada a gitta musu, (da maganar wani) a zartar dasu kamar yadda magabata suka zartar da su, ba tare da kamantawa ba, ko tawili". (al-Targib Wal Tarhib, na madaidaicin Sunnah (1/253).)
Ibnu Kutaibah - Allah Ya yi masa rahama - ya ce: "Magana madaidaiciya a waɗannan nassosin - wato nassosin siffofi - shi ne mu yi imani da abinda ya inganta daga gare su ta hanyar riwayar amintattu, sai mu yi imani da ganin Allah da kuma tajalli, kuma cewa Shi Yana yin mamaki, Yana sauka zuwa saman duniya, kuma cewaShi Ya daidaitu akan Al'arshi, da kuma rai, da hannaye, ba tare da mun faɗi wata kaifiyya ba a hakan, ko mu iyakance, ko mu ƙiyasta akan abin da ya zo muddin dai ba shi ya zo da shi ba, sai mu yi kwaɗayin mu kasance a wannan maganar da kuma ƙudirewa ta hanyar tsira gobe in Allah - Maɗaukakin sarki - Ya so". (al-Ikhtilaf fil lafzi wal-raddi alal Jahamiyya, na Ibnu Kutaibah (shafi na 53).)
Al-Zuhri ya ce: "Bayani yana ga Allah, kuma isarwa tana ga manzo, mu kuma wajibinmu shi ne miƙa wuya". (al-Hujja fi bayanil Manhajja (2/512), da Sharhus Sunnah na al-Bagawi (1/171).)
KUNDIN IMANI DA MALA'IKU
Kundin a taƙaice
Muna imani da mala'iku, kuma muna sani, sani na sakankancewa cewa imani da mala'iku shi ne rukuni na biyu daga cikin rukunan Imani.
Imani da mala'iku yana kunshe da wasu ma'anoni:
Na dayansu: Gasgatawa da samuwarsu
Na biyu: Saukar da su matsayinsu, da tabbatar da cewa su bayin Allah ne kuma halittarsa ce, kamar mutum da aljani, ababen umarta ne kuma an ɗora musu aiki, basu da wani iko sai abinda Allah - Maɗaukakin sarki - Ya basu iko akansa, kuma mutuwa halas ce garesu, sai dai Allah - Maɗaukakin sarki - Ya sanya musu wani lokaci mai nisa, ba zai dauki ran su ba har sai sun kai shi, kuma ba'a siffantasu da wani abinda zai kai ga siffanta su ga yi musu shirka ga Allah - Maɗaukakin sarki -, kuma ba'a kiransu alloli, kamar yadda mushrikai suka yi da'awa.
Na uku: Tabbatar da cewa a cikinsu akwai manzannin Allah, Yana aikosu ga wanda Ya so cikin mutane, zai iya yi wu wa Ya aiko sashinsu ga sashi, tabbatar da hakan yana bin cewa daga cikinsu akwai masu ɗauke da Al'arshi, daga cikinsu akwai waɗanda suka yi sawu-sawu, daga cikinsu akwai masu gadin aljanna, daga cikinsu akwai masu gadin wuta, daga cikinsu akwai masu rubuta ayyuka, daga cikinsu akwai masu koro girgije, haƙiƙa Alkur’ani ya zo da hakan gaba ɗayansa ko mafi yawansa. (Shu'abul Iman (1/296).)
Na Huɗu: Imani da mala'iku a dunƙule da kuma a rarrabe, sai mu yi imani da samuwar mala'iku a dunƙule, kuma mu yi imani da wanda muka sani na sunayensu da siffofinsu da ayyukansu, kamar yadda ya zo a cikin Alkur’ani da Sunnah imani a fayyace.
Muna imani da wanda muka sani daga cikinsu da wanda ba mu sani ba, kuma muna imani da ayyukansu da siffofinsu, kuma muna sanin cewa abinda ya boyu garemu na adadinsu da ayyukansu da siffofinsu shi ne mafi yawa daga abinda muka sani, sai dai cewa muna imani da dukkanin hakan, kamar yadda Allah da manzonSa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - suka bamu labari, ba zamu nemi wata kaifiyya ba, kuma ba zamu ki yarda da shi ba, da hankulanmu ba, kuma ba zamu yi ɗimuwa da ra'ayukanmu ba, kuma ba zamu yi tawili da (wani) ijtihadinmu ba, kai mu ce : Mun yi imani, mun gasgata, kuma mun miƙa wuya.
Kuma muna imani cewa Allah Ya halicci mala'iku daga haske, su halitta ce daga halittar Allah, Ya haliccesu kan wata kebantacciyar siffa babu wanda ya san haƙiƙaninsu sai Allah, su bayi ne ababen halitta, Ya halicce su dan su bauta maSa, da tsayuwa da umarninSa, su suna bauta maSa, kuma ba sa kin bauta masa.
Daga nau’ukan bautar da suke yi: Tasbihi, da sujjada, da tsoro, da firgita, su - tare da girman bautar da suke - suna tsoron Ubanugijinsu mafi tsananin tsoro, kuma daga bautarsu: cewa su suna jibinta saboda Allah, kuma suna soyayya saboda Allah.
Muna imani cewa Allah Ya haliccesu akan wata siffar da babu wanda ya san hakikaninta sai wanda Ya halicce su.
Muna imani cewa Allah Ya sanya musu fuka-fukai, kuma haƙiƙa ya yi musu izinin zuwa ga annabawa da manzanni - aminci ya tabbata agare su - akan siffar mutane, wanda ya riya daga mushrikai cewa mala'iku 'ya'yan Allah mata ne to haƙiƙa Allah Ya ƙaryata shi.
Muna imani cewa mala'iku ba sa ci, ba sa sha; domin ba su da sha'awa. Kuma daga ɗabi'unsu akwai kunya, kuma su suna cutuwa daga abinda 'ya'yan Adam suke cutuwa da shi.
Muna imani cewa Allah Ya sanya ƙarfi a cikinsu da tsanani abinda ba za’a iya sanin hakikanin hakan ba, kuma mala'iku halittu ne masu yawa babu mai iya sanin adadinsu sai wanda Ya halicce su.
Muna imani cewa Allah Ya ɗaukaka su, kuma Ya ɗora musu wasu (su Mala’iku) ayyuka masu girma da yawa daban-daban, mafi girma shi ne su zama manzanni tsakanin Allah da bayinSa, suna kai musu wahayi, mala'ikan da aka wakilta da saukar da wahayi zuwa annabawan Allah da manzanninSa - aminci ya tabbata agare su - shi ne (Mala’ika) Jibrilu - aminci ya tabbata agare shi -. Allah Zai iya aiko su zuwa wanin annabawa dan jarrabawa.
Daga ayyukansu akwai: Daukar Al'arshi, da rubuta ƙaddara, da tsayuwa akan sha'anin mahaifa da abinda ke cikinsu - halitta da surantawa da busa rai - da kashe bayi, da busa rayuka a cikin jikkuna a duniya da lahira, da yaƙi tare da muminai, da addu'a ga muminai da nema musu gafara, da zuwa wuraren ibadun muminai, da daga kalmominsu masu tsarki, da labartawa Ubangiji game da ayyukansu - Shi ne mai bada labari Masani wanda ba Ya buƙatuwa zuwa ga wanda zai ba Shi labari.
Daga ayyukansu akwai: Sakkowa ƙasa a lokutan imani, kamar ranar Juma'a da ranar Arfa, da Lailatul ƙadri.
Daga ayyukansu akwai: Isarwa annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - salatin al'ummarsa gare shi.
Daga ayyukansu akwai: Kiyaye 'ya'yan Adam, da rubuta kyawawan ayyuka da munana, da gadin Madinar annabi daga Dujal, da tambayar mamaci a cikin ƙabarinsa, da yi wa muminai albishir da rabo mai girma a lokacin mutuwa, da tarbarsu a gidan lahira, da zuwa gurinsu ta ƙofofin aljanna, kuma cewa za su sakko tare da Allah suna masu sawu-sawu a ranar AlKiyama.
Daga ayyukansu: Daga cikinsu akwai masu gadin aljanna, da masu gadin wuta.
Kuma muna imani cewa Allah Ya sanya wasu muƙamai da matakai ga mala'iku, mafi girman mala'iku a matsayi shi ne (Mala’ika) Jibril da Mika'il da Israfil, kuma daga mafi ɗaukakarsu akwai: Masu dauke da Al'arshi, haka nan waɗanda suka halarci yaƙin Badr daga mala'iku, kuma a kowacce sama akwai mala'ikun da ba mai iya iyakance adadinsu sai Allah, waɗannan mala'ikun kowanne daga cikinsu yana da wani matsayi sananne, a cikinsu akwai makusanta.
BABIN WAJABCIN IMANI DA MALA'IKU
Muna imani da mala'iku, kuma muna sane sani na sakankancewa cewa imani da mala'iku shi ne rukuni na biyu daga cikin rukunan imani, Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Manzo ya yi imani da abin da aka saukar daga Ubangijinsa zuwa gare shi, hakanan muminai ma, kowa ya yi imani da Allah da mala'ikunSa da littattafanSa da manzanninSa} [al-Baƙara: 285]. Kuma Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya ce: {Ba wai juya fuskoki bangaren gabas ko yamma shi ne biyayayya da ɗa'a ba, amma aikin ɗa'a shi ne wanda ya yi imani da Allah da ranar lahira da mala'iku da littafi da annabawa} [Baƙara: 177]. Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance wata rana ya fito wajen mutane, sai wani mutum ya zo masa, sai ya ce: Ya manzon Allah, menene imani? ya ce: "Kayi imani da Allah, da mala'ikunSa, da littafinSa, da haɗuwa da Shi, da manzanninSa, kuma ka yi imani da tashin ƙarshe". (Bukhari ne ya fitar da shi (4777), da Muslim (9), da Ibnu Majah (64).)
AlBaihaƙi - Allah Ya yi masa rahama - Ya ce: "Imani da mala'iku yana kunshe da wasu ma'anoni: Na ɗayansu: Gasgata samuwarsu. Na ƙarshen: Saukar da su matsayinsu, da tabbatar da cewa su bayin Allah ne kuma halittarSa ce, kamar mutum da aljani, ababen umarta ne kuma an ɗora musu aiki, basu da wani iko sai abinda Allah - Maɗaukakin sarki - Ya basu iko akansa, kuma mutuwa halas ce garesu, sai dai Allah - Maɗaukakin sarki - Ya sanya musu wani lokaci mai nisa, ba zai kashe su ba har sai sun kai shi, kuma ba'a siffantasu da wani abinda zai kai ga siffanta su ga yi musu shirka ga Allah - Maɗaukakin sarki -, kuma ba'a kiransu alloli, kamar yadda (mutanan) farko suka yi da'awa. (Ana faɗin na farko, ana nufin su ne malaman falsafah). Na uku: Tabbatar da cewa daga cikinsu akwai manzannin Allah , Yana aiko su ga wanda Ya so zuwa ga mutane, zai iya yi wuwa Ya aiko sashin su ga sashi, tabbatar hakan yana bin cewa daga cikinsu akwai masu ɗaukar Al'arshi, daga cikinsu akwai waɗanda suka yi sawu-sawu, daga cikinsu akwai masu gadin aljanna, daga cikinsu akwai masu gadin wuta, daga cikinsu akwai masu rubuta ayyuka, daga cikinsu akwai masu koro girgije, haƙiƙa AlKur'ani ya zo da hakan gaba ɗayansa ko mafi yawansa. (Shu'abul Iman (1/296).)
Sai Baihaƙi ya ambaci abubuwa uku daga ma'anonin imani da mala'iku.
Na huɗu: Imani da mala'iku a dunƙule da kuma a rarrabe, sai mu yi imani da samuwar mala'iku a dunƙule, kuma mu yi imani da abinda muka sani na sunayensu da siffofinsu da ayyukansu kamar yadda ya zo a cikin Alkur’ani da sunnah imani a rarrabe.
Kuma muna sanin cewa abinda ya boyu garemu na adadinsu da ayyukansu da siffofinsu shi ne mafi yawa daga abinda muka sani, sai dai cewa mu muna imani da dukkanin hakan kamar yadda Allah da manzonSa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - suka bamu labari, ba za mu nemi wata kaifiyya gare shi ba, kuma ba zamu juyar da shi da hankulanmu ba, kuma ba za mu dimauce da ra'ayukanmu ba, kuma ba zamu yi tawilinsa da ijtihadinmu ba, kai sai dai mu ce : Mun yi imani, kuma mun gasgata, mun miƙa wuya.
BABIN HALITTAR MALA'IKU DA YAWAN ADADINSU DA SIFFOFINSU
Kuma muna imani cewa Allah Ya halicci mala'iku daga haske, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "An halicci mala'iku daga haske". (Muslim ne ya fitar da shi (2996).) Su haliatta ce daga halittar Allah, Allah Ya haliccesu akan wata kebantacciyar sifa, sai dai cewa su ba rayuka ba ne kawai, ba kuma ƙarfi ba ne kawai, kai su wata duniya ce ta boye, kuma bayi ne da ya halitta, Ya halicce su ne dan bautar Sa, da tsayuwa da umarninSa, su suna bauta maSa, kuma ba sa hanuwa daga bautarSa.
Daga bautarsu akwai: Tasbihi, da sujjada, da tsoro, da razana, da wanin hakan, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Ba sa sabawa Allah ga abin da Ya umarce su kuma suna aikata abin da ake umartarsu} [al-Tahrim: 6]. Ya ce kuma: {Kuma ga Allah, abin da yake a cikin sammai da ƙasa na dabba da mala'iku, suke yin sujada, kuma bã su kangara} [Nahl: 49]. Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Kuma kana ganin mala'iku suna masu tsayawa da haƙƙoƙin da aka ɗora musu daga kewayen Al'arshi suna tasbihi gami da godewa Ubangijinsu} [Zumar: 75]. Su - tare da girman bautar da suke yi - suna jin tsoron Ubangijinsu mafi tsananin tsoro, Allah - sha'aninSa Ya ɗaukaka - Ya ce: {Suna tsõron Ubangijinsu daga bisansu, kuma suna aikata abin da ake umurnin su} [al-Nahl: 50].
Daga bautarsu: Cewa su suna jibinta saboda Allah, kuma suna so saboda Allah, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Idan Allah Ya so bawa sai Ya kira (Mala'ika) Jibril: Lallai Allah Yana son wane to kaima ka so shi, sai Jibril ya so shi, sannan ya yi yekuwa ga 'yan sama: Cewa Allah Yana son wane to kuma ku so shi, sai 'yan sama su so shi, sannan a sanya masa karbuwa a ƙasa". (Bukhari ya fitar da shi (3209), da Muslim (2637), da Tirmizi (3161).) Kuma suna gaba, suna ƙiyayya saboda Allah, kuma suna kishi ga abinda Allah Ya haramta, suna tsinewa wanda Allah Ya tsine masa, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Lalle ne, waɗanda suka kãfirta kuma suka mutu alhãli kuwa suna kãfirai, waɗannan akwai, a kansu, la'anar Allah da Malã'iku da mutãne gabã ɗaya} [Baƙara: 161]. Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Mala'iku ba sa shiga gidan da a cikinsa akwai mutum mutumi ko hotuna". (Muslim ne ya fitar da shi (2112).)
Muna imani cewa Allah Ya halicce su akan wata siffar da ba wanda ya san hakikaninta sai wanda Ya halicce su akanta. Daga Jabir ɗan Abdullahi - Allah Ya yarda da su - daga annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "An bani izini in yi magana game da wani mala'ika daga mala'ikun Allah cikin masu ɗauke da Al'arshi, lallai tsakanin fatar kunnensa zuwa wuyansa tafiyar shekara ɗari bakwai ce"." (Abu Dawud ne ya fitar da shi (4727), da Ibnu Dahman a cikin Mashyikarsa (21), da Dabarani a cikin al-Ausaɗ (1709), da Abu al-Sheikh a cikin al-Azamah (313).)
Kuma muna imani cewa Allah Ya sanya musu fuka-fukai, Allah Ya ce: {Wanda Ya sanya mala'iku manzanni masu fuka-fukai, bibiyu, da uku-uku, da hurhuɗu, Yana ƙarawa a abinda Yake so a cikin halitta} [Faɗir: 1]. Daga Abdullahi ɗan Mas'ud - Allah Ya yarda da shi -: "Cewa (Annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ga (Mala’ika) Jibrilu yana da fuka-fukai ɗari shida". (Bukhari ya fitar da shi (4857), da Muslim (174), da Tirmizi (3277).) Kuma suna da zukata, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Har a lokacin da aka kuranye tsoro daga zukatansu, sai suka ce: Menene Ubangijinku Ya ce? suka ce: Gaskiya, kuma Shi ne Maɗaukaki, Mai girma} [Saba'i: 23].
Kuma Allah Ya yi musu izini cewa su zo wa annabawa da manzanni - aminci ya tabbata agare su - a siffar ɗan Adam, sai suka je wurin (Annabi) Ibrahim, da (Annabi) Luɗ - aminci ya tabbata agare su - a siffar baƙin da ba su sansu ba, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya faɗa yana mai bada labari game da hakan: {Shin, lãbãrin Bãƙin Ibrãhĩm, waɗanda aka girmama, ya zo maka? * A lõkacin da suka shiga gare shi, sai suka yi sallama; ya ce "Aminci ya tabbata a gare ku, mutãne bãƙi!} [Zariyat: 24-25]. Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma a lõkacin da manzanninMu suka je wa Lũɗu aka ɓãta masa rai game da su, ya, ƙuntata rai sabõda su. Ya ce: "Wannan yini ne mai tsananin masĩfa} [Hud: 77]. (Mala'ika) Jibrilu - aminci ya tabbata agare shi - ya zo wajen (nana) Maryam - aminci ya tabbata agare ta - a surar da ba ta san shi ba a farkon lokaci, kamar yadda Allah Ya bamu labari da faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Sai muka aika mata da ruhinmu sai ya kamanta mata wani mutum madaidaici gareta * Sai ta ce lallai ni ina neman tsarin (Allah) Mai Rahman daga gareka in ka kasnce mai tsoron Allah ne * Ya ce kaɗai ni manzon Ubangijinki ne} [Maryam: 17-19]. Daga Dan Umar - Allah ya yarda da su - ya ce: "Jibril - aminci ya tabbata agare shi - ya kasance yana zo wa annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a surar Dihyah". (Ahmad ne ya ruwaito shi (5857), da Muhammad ɗan Nasr al-Mirwazi a cikin Ta'azimu ƙadris Salah (372), da Ibnu Baɗɗah a cikin al-Ibanah (831).)
Muna imani cewa mala'iku ba sa ci, ba sa sha; domin ba su da sha'awa; saboda haka ne lokacin da suka shiga wurin (Annabi) Ibrahim - aminci ya tabbata agare shi - ya gabatar musu da abinci ba su ci ba, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce Yana Mai bada labari game da hakan: {Sai ya jũya zuwa ga iyãlinsa, sannan ya zo da maraƙi tutturna * Sai ya kusantar da shi zuwa gare su, ya ce: "Bã zã ku ci ba? * Sai ya ji tsõro daga gare su. Suka ce: "Kada ka ji tsõro." Kuma suka yi masa bushãra da (haihuwar) wani yaro mai ilmi} [Zariyat: 26-28]. Kuma daga halittar su akwai kunya, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Shin ba na ji kunyar mutumin da mala'iku suke jin kunyarsa ba". (Muslim ya fitar da shi (2401).)
Kuma cewa su suna cutuwa da abinda 'ya'yan Adam suke cutuwa da shi, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Wanda ya ci daga wannan bakala, tafarnuwa - a wani karon ya ce: Wanda ya ci albasa da tafarnuwa da algarif - to kada ya kusanci masallacinmu; domin mala'iku suna cutuwa daga abinda 'ya'yan Adam suke cutuwa da shi". (Bukhari ne ya fitar da shi (854), da Muslim (564), kuma lafazin nasa ne, da Abu dawud (3822), da Tirmizi (1806), da Nasa'i (707), da Ibnu Majah (3365).)
Kuma muna imani cewa Allah Ya sanya musu ƙarfi da tsananin da ba wanda ya iya sanin hakikaninsa (sai shi Allah), Maɗaukakin sarki Ya ce: {Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi} [al-Takweer: 20]. Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Akanta akwai wasu mala'iku masu kauri, masu ƙarfi, ba sa saɓawa Allah ga abin da Ya umarce su, kuma suna aikata abin da ake umartar su} [al-Tahrim: 6]. Kuma Allah Ya aiko da wani mala'ika zuwa alƙaryun (Annabi) Luɗ, garu ruwa bakwai ne, sai ya juyar da su akansu, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Sannan a lõkacin da umurninMu ya je, Muka sanya na samanta ya zama na ƙasanta, kuma Muka yi ruwan duwãtsu a kanta (ƙasar Lũɗu) daga taɓo cũrarre} [Hud: 82].
Muna imani cewa mala'iku halitta ne masu yawa, ba mai iya sanin adadinsu sai wanda Ya halicce su, daga annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Sai aka ɗago min Baitil Ma'amur, sai na tambayi (mala'ika) Jibril, sai ya ce: Wannan Baitul ma'amur ne kowacce rana mala'iku dubu saba'in ne suke sallah a cikinsa, idan suka fita ba za su dawo gare shi ba har ƙarshen wanda ke kansu...". (Bukharin ya fitar da shi (3207), da Muslim (164), da Tirmizi (3346), da Nasa'i (448).)
Daga Abu Zarr - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Ni ina ganin abinda ba kwa gani, kuma ina jin abinda ba kwa ji, sama ta yi kuka kuma ya dace da ta yi kukan, babu wani bugeren da zai ishi yatsu huɗu a cikinta sai akawai mala'ika ya sanya goshinsa yana sujjada ga Allah". (Tirmizi ya fitar da shi (2312), da Ibnu Majah (4190), da Ibnu Abi Shaibah (27044), da Ahmad (21516), da al-Bazzar (3924, 3925).)
Daga annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - cewa shi - ya ce: "Za'a zo da Jahannama a wannan ranar tana da linzami dubu saba'in, tare da kowanne linzami akwai mala'iku dubu saba'in suna janta". (Muslim ne ya fitar da shi (2842), da Tirmizi (2573).)
Mushrikai sun yi da'awar cewa mala'iku 'ya'yan Allah ne mata, sai Allah Ya ƙaryata su da faɗinSa: {Kõ kuma Mun halitta malã'iku mãtã ne, alhãli kuwa sũ suna halarce ?} [al-Saafat: 150]. Kuma Ya mayar musu da maganarsu da faɗinSa - Maɗaukaki: {Shin fa Ubangijnku Ya zaɓeku da ɗiya maza ne, kuma Ya riƙi 'ya'ya mata daga mala'iku? Lallai ne ku haƙiƙa kuna faɗar magana mai girma!} [al-Isra'i: 40].
BABIN AYYUKAN MALA'IKU
Muna imani cewa Allah Ya ɗaukaka su, kuma Ya ɗora musu wasu ayyuka masu girma masu yawa daban-daban, mafi ɗaukakarsu; Shi ne su zama manzanni tsakanin Allah da bayinSa suna isar musu da wahayi, mala'ikan da aka wakilta da saukar da wahayi zuwa annabawan Allah da manzanninSa - aminci ya tabbata agare su - shi ne (Mala'ika) Jibril - aminci ya tabbata agare shi - kamar yadda Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya ce: {Ka ce, Ruhi Mai tsarki ne ya sassaukar da shi, daga Ubangijinka da gaskiya} [al-Nahl: 102]. Kuma Maɗaukkain sarki Ya ce: [Lallai cewa shi saukarwar Ubangijin talikai ne} Rũhi amintacce ne ya sauka da shi * A zũciyarka, dõmin ka kasance daga mãsu gargaɗi * Da harshe na Larabci mai bayãni} [al-Shu'araa:192-195].
Kuma Allah Yakan aiko su zuwa ga da ba annabawa ba dan jarrabawa, kamar yadda yake a cikin ƙissar mutum ukun nan daga Bani isra'il, daga AbdurRahman ɗan Abi Amrah cewa Abu Hurairah - Allah Ya yarda da shi - ya zantar da shi cewa shi ya ji manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana cewa: "Lallai wasu mutum uku daga Banu Isra'il: Kuturu, da mai sanƙo, da makaho, Allah Ya nufin cewa Zai jarrabe su, sai ya aiko musu da wani mala'ika, sai ya zo wa kuturu, sai ya ce: wanne abu ne mafi soyuwa gareka? ya ce: Kyakkyawan launi, da kyakkyawar fata, haƙiƙa mutane sun ƙyamaceni, ya ce: Sai ya shafe shi sai ya tafiyar da shi, sai aka ba shi kyakkyawan launi, da kyakkyawar fata, sai ya ce: wacce dukiya ce mafi soyuwa gareka? ya ce: Raƙuma - ko ya ce: Shanu, shi ya yi kokwanto a hakan: Lallai cewa kuturu, da mai sanƙo, ɗayansu ya ce: Raƙuma, ɗayan kuma ya ce: Shanu - sai aka ba shi taguwa mai ciki, sai ya ce: Allah Ya yi maka albarka a cikinta. Kuma ya zo wa mai sanko, sai ya ce: Wanne abu ne mafi soyuwa gareka? ya ce: Kyakkyawan gashi, wannan abin da mutane suke kyanmatata ya tafi, ya ce: sai ya shafe shi sai ya tafi, kuma aka ba shi kyakkyawan gashi, ya ce: Wacce dukiya ce mafi soyuwa gareka? Ya ce: Shanu, ya ce: sai aka ba shi saniya mai ciki, ya ce: Allah ya yi maka albarka a abinda ya baka. Kuma ya zo wa makaho, sai ya ce: Wanne abu ne mafi soyuwa gareka? Ya ce: Allah Ya dawo min da ganina, in dinga ganin mutane da shi, sai ya shafe shi sai Allah Ya dawo masa da ganinsa, ya ce: Wacce dukiya ce mafi soyuwa gareka? ya ce: Tumakai, sai aka ba shi akuya mai haihuwa, sai wadancan biyun suka haihu, wannan ma ta haihu, sai wannan ya zama yana da fili fal na rakuma, wannan ma fili fal na shanu, wancan ma fili fal na tumakai. Sai ya zo wa kuturu a surarsa da yanayinsa, sai ya ce: Wani mutum ne miskini, guzuri ya yanke min ina kan tafiyata, ba ni da wani guziri a yau sai ga Allah, sannan kai, ina roƙonka dan wanda ya ba ka kyakkyawan launi, da kyakkyawar fata, da dukiya, ka ba ni rakumi in yi guziri da shi a wannan tafiyata, sai ya ce masa: Hakkoki da yawa, sai ya ce masa: Kamar ni na sanka da, ba kai ne kuturu ba mutane suna kinka, kuma talaka, sai Allah Ya baka? sai ya ce: Hakika na gada ne daga iyaye da kakanni, sai ya ce: In ka kasance karya kake yi to Allah Ya maida kai kan abinda kake. Sannan ya zo wa mai kora, ya fada masa kamar yadda ya fadawa kuturu, shi kuma ya mayar masa kamar (yadda) kuturun ya mayar masa, sai ya ce: In ka kasance karya kake yi to Allah Ya maida kai kan abinda kake. Sannan ya zo wa makahon a surarsa, sai ya ce: wani mutum ne miskini kuma matafiyi guzuri ya yanke mini a tafiyata, a yau ba ni da wani guziri sai Allah sannan kai, ina rokonka da wanda Ya dawo maka da ganinka ka ba ni wata akuya in yi guziri da ita a tafiyata, sai ya ce: Da na kasance makaho, sai Allah Ya dawo mini da ganina, kuma talaka haƙiƙa Allah Ya wadatani, ka ɗauki abin da kake so, na rantse da Allah ba zan takura maka da wani abin da ka ɗauka ba saboda Allah a yau, sai ya ce: Ka riƙe dukiyarka, kawai an jarrabaku ne, haƙiƙa Allah Ya yarda da kai, kuma Ya yi fushi ga 'yan uwanka biyu". (Bukhari ne ya fitar da shi (3464), da muslim (2964).)
Daga cikinsu akwai maɗauka Al'arshi, Ubangiji - sha'aninSa ya ɗaukaka kuma sarautarSa ta ɗaukaka - Ya ce: {Kuma malã'iku (su bayyana) a kan sãsanninta, kuma wasu (malã'iku) takwas na ɗauke da Al'arshin Ubangijinka, a sama da su, a wannan rãnar} [al-Haaƙah: 17].
Daga ayyukansu: Rubuta ƙaddara, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Lallai ɗayanku ana tara halittarsa a cikin mahaifiyarsa kwana arba'in yana maniyyi, sannan ya zama gudan jini kwatankwacin hakan, sannnan ya zama tsoka kwatankwacin hakan, sannan Allah Ya aiko masa da wani Mala'ika sai a umarce shi da kalmomi huɗu, kuma a ce da shi: Ka rubuta aikinsa, da arziƙinsa, da ajalinsa, ɗan wuta ne ko ɗan aljanna". (Bukhari ne ya fitar da shi (3208), da Muslim (2643), da Abu Dawud (4708), da Tirmizi (2137), da Ibnu Majah (76).)
Daga ayyukansu akwai: Tsayuwa akan sa'anin mahaifa da waɗanda ke cikinsu - a halitta da surantawa da busa rai- haƙiƙa manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Idan darare arba'in da biyu suka shuɗewa maniyyi, sai Allah Ya aiko masa da wani mla'ika, sai ya suranta shi kuma Ya halicci jinsa da ganinsa da fatarsa da namansa da ƙashinsa, sannan ya ce: Ya Ubangiji, namiji ne ko mace? sai Ubangijin ka Ya hukunta abina Ya so, kuma mala'ikan ya rubuta, sannan ya ce: Ya Ubangiji ajalinsa, sai Ubanigijinka Ya faɗi abinda ya so, kuma mala'ikan ya rubuta". (Muslim ne ya fitar da shi (2645).)
Kuma daga Anas - Allah Ya yarda da shi - daga annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Allah Ya wakilta wani mala'ika a mahaifa, sai ya ce: Ya Ubangiji maniyyi, ya Ubangiji gudan jini, ya Ubangiji gudan tsoka, idan Allah Ya yi nufin Ya hukunta halittarta, sai ya ce: Ya Ubangiji, namiji ne ko mace? ɗan wuta ne ko ɗan aljanna ne? menene arziƙin? menen ajalin? sai a rubuta hakan a cikin mahaifiyarsa". (Bukhari ne ya fitar da shi (6595), da Muslim (2646).)
Daga ayyukansu: Daukar rayukan bayi, Allah Ya ce - kuma zancensa gaskiya ne: {Har sai da mutuwa ta zo wa ɗayanku sai mazanninmu su kashe shi kuma su ba sa sakaci} [al-An'am: 61]. Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {To, yãya hãlinsu yake a lõkacin da malã'iku ke karɓar rãyukansu, sunã dũkan fuskõkinsu da ɗuwaiwansu?} [Muhammad: 27].
Daga ayyukansu: Busa rayuka a cikin jikkuna a duniya da lahira, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Lallai ɗayanku ana tara halittarsa a cikin mahaifiyarsa kwana arba'in yana maniyyi, sannan ya zama gudan jini kwatankwacin hakan, sannnan ya zama tsoka kwatankwacin hakan, sannan Allah Ya aiko masa da wani Mala'ika sai a umarce shi da kalmomi huɗu, kuma a ce da shi: Ka rubuta aikinsa, da arziƙinsa, da ajalinsa, ɗan wuta ne ko ɗan aljanna, sannan a busa masa rai". (Bukhari ne ya fitar da shi (3208), da Muslim (2643), da Abu Dawud (4708), da Tirmizi (2137), da Ibnu Majah (76).) Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Sannan sai a yi wata busar daban a cikin ƙaho sai gasu a tsaitsaye suna sauraare} [al-Zumar: 68].
Daga ayyukansu: Jihadi tare da muminai, da tabbatar da muminai a fagen yaƙi, da kuma guraren wahala na rayuwa, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka kuma sarautarSa ta ɗaukaka - Ya ce: {A lõkacin da Ubangijinka Yake yin wahayi zuwa ga Malã'iku cẽwa: "Lalle ne Ni, Inã tãre da ku, sai ku tabbatar da waɗanda suka yi ĩmãni: Zã Ni jẽfa tsõro a cikin zukãtan waɗanda suka kãfirta, sai ku yi dũka bisa ga wuyõyi kuma ku yi dũka daga gare su ga dukkan yãtsu} [al-Anfal: 12]. Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Lallai Shaiɗan yana da himma ga ɗan Adam, mala'ika ma yana da himma. Amma himmar Shaiɗan ita ce alƙawari da sharri da ƙaryata gaskiya, amma himmar mala'ika to ita ce alƙawarin alheri da gasgata gaskiya, wanda ya ji haka to ya san cewa shi daga Allah ne, sai ya godewa Allah, wanda ya ji ɗayan to ya nemi tsarin Allah daga Shaiɗan abin jefewa, sannna ya karanta: {Shaiɗan yana alƙawarta muku talauci kuma yana umartarku da alfasha} aya [al-Baƙara: 268]. (Tirmizi ne ya fitar da shi (2988), da Ibnul Mubarak a cikin Zuhdu (1435), da Ahmad a cikin Zuhdu (854), da Abu Dawud a cikin Zuhdu (164).)
Daga ayyukansu: Addu'a ga muminai da nema musu gafara, Allah - Maɗaukakai - ya ce: {Waɗanda ke ɗaukar Al'arshi da waɗanda ke kẽwayensa, sunã tasbĩhi gami da gõde wa Ubangijinsu, kuma sunã yin ĩmãni da Shi, kuma sunã yin istigfãri dõmin waɗanda suka yi ĩmãni, (sunã cẽwa), "Yã Ubangijinmu! Kã yalwaci dukkan kõme da rahama da ilmi to Ka yi gãfara ga waɗanda suka tũba kuma suka bi hanyarKa, kuma Ka tsare su daga azãbar Jahĩm} [Gafir: 7].
Daga cikin ayyukansu akwai: Halartar ibadun muminai a lokutan imani da alheri, da kuma mafifitan lokuta, kamar ranar Juma'a, da ranar Arfa, da Lailatul ƙadr, da sallolin Asuba da la'asar, da ɗaga kalmominsu masu tsarki, da bai wa Ubangiji labari game da ayyukansu - alhali Shi ne Masani wanda baYa buƙatuwa ga wanda zai ba Shi labari - Allah - ambatanSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Da lokacin alfijir, lallai ne karatun alfijir ya kasance wanda ake halarta ne} [al-Isra'a: 78]. Kuma Allah - tsarki ya tabbatar maSa - Ya ce: {Mala'iku da Rũhi suna sauka a cikinsa da iznin Ubangijinsu sabõda kowane umurni} [al-Kadr: 4].
Kuma tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Mala'iku da daddare da mala'iku da rana suna bibiyar juna a cikinku, suna taruwa a sallar Asuba da sallar la'asar, sannan waɗanda suka kwana a cikinku su hau sama, sai Ya tambayesu, alhali Shi ne mafi sani da su: Yaya kukabar bayiNa? sai su ce: Mun barsu alhali su suna sallah, kuma mun je musu alhali su suna sallah". (Bukhari ne ya fitar da shi (555), da Muslim (632), da Nasa'i (485).)
Kuma tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Lallai Allah Yana da wasu mala'iku suna kewayawa a hanyoyi suna neman ma'abota zikiri, idan suka samu wasu mutane suna ambatan Allah sai su yi kira: Ku zo wa buƙatunku. Ya ce: Sai su lilliɓesu da fukafukansu zuwa saman duniya". (Bukhari ne ya fitar da shi (6408), da Muslim (2689).)
Kuma mala'iku suna halartar guraren imani, kamar ranar Juma'a da ranar Arfa, da Lailatul ƙadr, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Idan liman ya fito sai mala'iku su halarto suna sauraron zikiri". (Bukhari ne ya fitar da shi (881), da Muslim (850), da Abu Dawud (351), da Tirmizi (499) da Nasa'i (1388).)
Daga ayyukansu akwai: Isar wa annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - salatin al'ummarsa gare shi - manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Ku yi salati gareni; domin salatinku yana isa gareni a duk inda kuke". (Abu Dawud ne ya ruwaito shi (204), da Ahmad (8804), da Dabarani a cikin al-Ausaɗ (8030), da Baihaƙi acikin al-Shuab (3865).)
Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Allah Yana da wasu mala'iku waɗanda suke yawo a ƙasa, suna isar min da sallamar al'ummata". (Nasa'i ne ya fitar da shi (1282), da Abdur Razaɗƙ (3116), da Ibnu Abi Shaibah a cikin al-Musannaf (8797), da kuma a cikin al-Musnad (269), da Ahmad (3666).)
Daga ayyukansu akwai: Kiyaye 'ya'yan Adam, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kowannenku; yana da waɗansu mala'iku masu maye juna a gaba gare shi da baya gare shi, suna tsare shi da umarnin Allah} [al-Ra'ad: 11]. Ali ɗan Abi Dalha ya ce, daga Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su -: Masu biyewa juna: "Su ne daga umarnin Allah, su ne mala'iku". (Dabarani ne ya fitar da shi a cikin al-Tafsir (13/463), da Ibnu Abi Hatim a cikin al-Tafsir (12198).)
Daga ayyukansu akwai: Rubuta kyawawan ayyuka da munana, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Masu girma marubuta} [al-Infiɗar: 11]. Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {A lõkacin da mãsu haɗuwa biyu suke haɗuwa daga dãma, kuma daga hagu akwai wani (malã'ika) zaunanne * Bã ya lafazi da wata magana fãce a lĩƙe da shi akwai mai tsaro halartacce} [Suratu Q: 17, 18]. Kuma Ya ce: {Kuma Yana aiko muku da masu kiyayewa} [al-An'am: 61]. Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - ya faɗa a cikin sha'aninsu: {Ko sunã zaton lalle Mũ, bã Mu jin asĩrinsu da gãnãwarsu? Na'am! Kuma manzannin Mu na tãre da su sunã rubũtãwa} [al-Zukhruf: 80]. Kuma tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Allah Yana cewa: Kada ku rubuta masa shi har sai ya aikata shi, idan ya aikata shi to ku rubuta masa kwatankwacinsa, idan kuma ya bar shi saboda Ni to ku rubuta masa kyakkyawa, idan ya yi nufin ya aikata kyakkyawa bai aikata shi ba to ku rubuta masa kyakkyawa, idan ya aikata shi to ku rubuta masa kwatankwacinsa goma har zuwa ninki ɗari bakwai". (Bukhari ya fitar d da shi (7501), da Muslim (128), da Tirmizi (3073).) Kuma tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Mala'iku su ce: Ya Ubangiji, wancan bawanKa ne yana son ya aikata mummunan aiki - alhali Ya fi su ganin shi - sai Ya ce: Ku lura da shi, idan ya aikata shi to ku rubutata masa kwatankwacin shi, idan ya bar shi to ku rubuta masa shi kyakkywa, kawai ya bar shi ne saboda Ni". (Muslim ne ya fitar da shi (129).)
Daga ayyukansu akwai: Gadin Madinar annabi daga Jujal, manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "A kwai mala'iku a iyakokin Madina annoba da Jujal ba za su shige ta ba". (Bukhri ne ya fitar da shi (1880), da Muslim (1379).)
Daga cikin ayyukan su akwai: Tambayar mamaci a cikin ƙabarin sa, Daga Barra'u ɗan Azib - Allah Ya yarda da shi - ya ce: manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya faɗa yana mai bada labari game da halin mutum idan an sashi a cikin ƙabarinsa: "Sai mala'iku biyu su zo masa sai su zaunar da shi, sai su ce da shi: Waye Uabangijinka? sai ya ce: Ubangijina (shi ne) Allah, sai su ce: Menene addininka? sai ya ce: Addinina musulunci, sai su ce masa: Wanne mutum ne wanda aka aiko shi a cikinku? ya ce: Sai ya ce: Shi ne manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -". (Abu Dawud ne ya fitar da shi (4753), da Nasa'i (2001), da Ibnu Majah (1548), da Dayalisi (789), da Abdur razaƙ (6737), da Ibnu Abi Shaibah (12185).)
Daga ayyukansu: Cewa daga cikinsu akwai masu tsaron aljanna, daga Anas ɗan Malik - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Zan zo ƙofar aljanna ranar Alkiyama, sai in nemi a buɗe sai mai gadin ya ce: Waye kai? sai in ce: Muhammad ne, sai ya ce: Da kai ne aka umarce ni ba zan buɗewa wani kafinka ba". (Muslim ne ya ruwaito shi (197).) Da mai gadin wuta, Allah - Maɗaukaikn sarki - Ya ce: {Kuma suka yi kira, "Ya Mãliku! Ubangijinka Ya kashe mu mana " ya ce: "Lalle kũ mazauna ne} [al-Zukhruf: 77]. Kuma Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya ce: {A gare ta akwai (matsara) gõma shã tara * Kuma baMu sanya ma'abota wuta ba (masu gadi) sai mala'iku} [al-Mudathir: 30-31]. Haƙiƙa ya tabbata a cikin inagantaccen hadisi daga Abdullahi ɗan Mas'ud - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Za'a zo da Jahannama a wannan ranar tana da linazami dubu saba'in, tare da kowanne linzami akwai mala'iku dubu saba'in suna janta". (Muslim ne ya fitar da shi (2842), da Tirmizi (2573).) (Tafsir al-Kurɗubi (19/80).)
BABIN MATAKAN MALA'IKU
Muna imani cewa Allah Ya sanya darajoji da matakai ga mala'iku, Allah - tsarki ya tabbatar maSa - Ya ce Yana mai bada labari game da su: {Kuma bãbu kõwa daga cikinmu, fãce yanã da matsayi sananne * Kuma lalle mu, haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin sahu-sahu (dõmin ibãda} [al-Saafat: 164-166].
Mafi girman mala'iku a daraja (shi ne) Jibril da Mika'il da Israfil; saboda haka ne annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi kamun ƙafa da Rububiyyar Allah ga na ukun farko daga cikinsu, daga Abu Salama ɗan AbdulRahman ɗan Auf ya ce: Na tambayi A'isha uwar muminai - Allah Ya yarda da ita -: Da wanne abu ne annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agre shi - ya kasance yana buɗe sallarsa idan ya tashi da daddare? ta ce: Ya kasance idan ya tashi da daddare yana buɗe sallarsa. "Ya Allah Ubangijin jibrila da Mika'ila, da Israfilu, Mahaliccin sammai da ƙasa, Masanin gaibu da fili, Kai ne wanda Kake yin hukunci a tsakanin bayinKa cikin abinda suka kasance sun saɓa cikinsa, Ka shiryar da ni cikin abinda suke saɓani a cikinsa na gaskiya da izininKa, lallai Kai ne Mai shiryar da wanda Kake so zuwa tafarki madaidaici". (Muslim ne ya fitar da shi (770), da Abu Dawud (767), da Nasa'i (1625), da Ibnu Majah (1357).)
Daga mafi ɗaukakarsu akwai masu dauke da Al'arshi, haka nan waɗanda suka halarci yaƙin Badr daga mala'iku, Daga Mu'az ɗan Rufa'ah ɗan Rafi'in AzZuraƙi daga babansa - Allah Ya yarda da shi - babansa ya kasance daga waɗanda suka halarci yaƙin Badar - ya ce: (Mala'ika) Jibril ya zo wajen annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai ya ce: "Me kuke ɗaukar waɗanda suka yi yaƙin Badar a cikinku? ya ce: Daga mafifitan musulmai - ko wata kalma kwatankwaciyarta - ya ce: Haka nan wanda ya halarci Badar a cikin mala'iku". (Bukhari ne ya fitar da shi (3992).)
A kowacce sama akwai mala'ikun da babu wanda zai iya iyakance adadinsu sai Allah, waɗannan mala'ikun kowanne daga cikinsu yana da wani sanannen matsayi, daga cikinsu akwai makusanta; saboda haka manzo - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya faɗa game da hawan ran mumini da kuma hawansa bayan mutuwarsa: "Sai su hau da shi (ran) ba za su wuce ba - yana nufin da shi - ga wasu jama'a daga mala'iku sai su ce: Wannan wane rai ne mai tsarki? sai su ce: Wane ne ɗan wane, da mafi kyan sunayensa waɗanda suka kasance ake kiransa da su a duniya, har sai sun tiƙe da shi zuwa saman duniya, sai su nemi a buɗe masa, sai a buɗe musu, sai makusanta a kowacce sama su raka shi zuwa saman da take biye da ita (wannan saman)". (Abu Dawud ne ya fitar da shi (3212), da Nasa'i (2001), da Ibnu Majah (1548), da Abu Dawud al-Dayalisi (789), da Abdur Razaƙ (6737, 6324), da Ahmad (18534), kuma lafazin nasa ne).)
KUNDIN IMANI DA LITTATTAFAI
Kundin a taƙaice
Muna imani da littattafai, su ne: Littattafan Allah waɗanda aka saukar ga manzanninSa da annabawanSa - aminci ya tabbata agare su - wadanda muka sani daga cikinsu su ne: Suhufi Ibrahim da Suhufi Musa, da Attaura, da Zabura, da Linjila, da Alkur’ani, kuma muna imani da waɗanda muka sani daga cikinsu da waɗanda ba mu sani ba.
Muna imani cewa dukkan waɗannan littattafan sune zancen Allah kuma wahayinSa, Attaura Allah Ya rubutata da hannunSa. Waɗannan littattafan Ya saukar da su ga manzanninSa - aminci ya tabbata agare su - (Mala'ika) Jibrilu amintacce ne ya sauko da su, kuma sun ƙunshi shari'un Allah, da labarai da wa'azuzzuka da umarni da hani, kuma kowanne littafi ya kasance a zamaninsa shi ne wahayin da yake wajaba a yi aiki da shi, da neman hukunci a gare shi ga al'ummar da aka saukar da shi gare ta .
Kuma muna imani cewa sashinsu sun fi sashi, Attaura Allah Ya rubutata da hannunSa.
Muna sani, sani na yaƙini cewa imani da liattattfai shi ne rukuni na uku daga rukunan imani, muna imani da su gaba ɗayansu, ba ma kasancewa kamar waɗanda suka yi imani da sashi, kuma suka kafircewa sashi.
Muna imani cewa dukkanin litattafan da suka rigayi Alkur’ani Allah bai laminci kiyayesu ba; kai Ya wakilta kiyayesu ga mutanen da Allah Ya saukar musu da su; saboda haka canje-canje ya shiga cikinsu, kuma waɗannan littattafan na Allah sun fuskanci bacewa da mantuwa, kuma masu ƙirƙirar ƙarya suka rubuta su, suka danganta su ga Allah akan ƙarya da ƙage, su suna rubuta su kuma suna karanta su da harsunan su dan zurfafawa a cikin rikitar da mutane; dan su yi zaton su daga Allah ne.
Muna imani cewa Alkur’ani mai girma shi ne mafi girman littattafan Allah kuma mafi cikarsu mafi ɗaukakarsu, kuma shi ne na ƙareshen su, (Mala’ika) Jibrilu - aminci ya tabbata agare shi - ne ya saukar da shi a zuciyar Manzon mu (annabi) Muhammad - tsira da aminci su tabbata agare shi - da harshen Larabci mabayyani, kuma Allah Ya zaɓa masa mafi ɗaukakar Harsuna; hakan domin harshen Larabci shi ne mafi fasahar harsuna kuma mafi bayyanarsu mafi yalwarsu, kuma mafi yawaitar su wurin bada ma'anoni; saboda haka ne ya saukar da mafi ɗaukakar littattafai da mafi ɗaukakar harshe ga mafi ɗaukakar manzanni, da jakadancin mafi daukakkar mala'iku, kuma hakan ya kasance a cikin mafi daukakar gurare a bayan kasa, kuma an fara saukar da shi a cikin mafi daukakar watannin shekara, shi ne Ramadan, sai ya cika ta kowacce fuska, kuma farkon abinda Allah ya saukar daga gare shi shi ne fadinsa - Maɗaukakin sarki : {Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, wanda Ya yi halitta} [Alaƙ: 1]. Daga na ƙarshen abinda aka saukar daga gare shi shi ne faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Kuma yaune Na cika muku Addininku, kuma Na cika muku ni'amarku, kuma Na yarje muku Musulunci a matsayin Addini} [Ma'ida: 3]. Ya sauka kaɗan - kaɗan ga manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a cikin shekarun annabta,, daga cikinsa akwai wanda ya sauka kafin hijira da bayan hijira, adadin surorinsa sura ɗari da goma sha huɗu ne, mafi girman sura ita ce "Suratul Fatiha", "Suratul Ikhlas" ta yi daidai da ɗaya bisa uku na Alkur’ani, kuma mafi girman ayoyinsa ayatul Kursiyyi.
Allah Ya yi yabo ga wannan littafin mai girma, kuma Ya sanya shi haske da shiriya da rahama ga muminai, kuma wa'azi da waraka daga cututtukan zukata da jikkuna.
Kuma muna imani cewa wannan littafin mai girma shi ne mafi cikar littattafan Allah kuma mafi tattarowarsu, ya ƙunshi hujjoji da dalilai, da buga misalai abinda zai tsaya da hujja ga talikai har zuwa tashin Alkiyama - haƙiƙa ya tattaro dukkanin abinda ke cikin litatttafan Allah da suka gabata ya kumayi ƙari akan su, kuma ya ƙunshi dukkan abinda ake buƙatuwa gare shi na tushen addini da shari'u da hujjoji da hikimomi da wa'azuzzuka da labarai, shi ya kai koli a fasaha da bayani. Daga mafi girman dalilai akan cewa wannan Alkur’ani zancen Ubangijin talikai ne, cewa manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ummiyyi ne ba ya karatu kuma ba ya rubutu, kuma Allah ya saukar masa da mafi girman littattafai kuma mafi cikarsu a fasaha da bayani.
Muna imani cewa Alkur’ani aya ce mai karfi a lafazinsa da ma'anarsa, kuma Allah Ya kalubalanci aljan da mutum baki ɗaya cewa su zo da kwatankwacinsa, ko surori goma, ko sura ɗaya daga kwatankwacinsa.
Kuma muna imani cewa wannan Alkur’ani shi zancen Allah ne abin saukarwa, ba halittarsa aka yi ba, kuma shi abin haddacewa ne a cikin zukata, abin rubutawa a cikin takardu, abin karantawa a cikin mihirabai da masallatai, hakan ba ya fitar da shi ya zama zancen Allah. Kuma zancen Allah siffa ce daga siffofinSa, abin da ya kasance daga siffofin Allah to ba zai zama halitta ba; dan da ya zama abin halitta da abinda yake gudana akan sauran fararru na ƙarewa da gushewa da canji ya gudana a akansa.
Kuma muna imani cewa wannan Alkur’ani haƙiƙa Allah Ya lamince kiyaye shi, bai sanya hakan ga halittatrSa ba, kuma Ya sanya shi abin kyautatawa matuƙar kyautatawa kamar yadda Ya sanya shi mai ma’anoni a nesa, kuma Ya bayyana cewa karkatattu suna bin masu ma’anoni na nesa daga gare shi, muminai kuma suna imani da shi gaba ɗayansa mai ma’anoni a kusa da mai ma’anoni a nesa.
Kuma Ya sanya shi mai hukunci akan dukkanin littattafan da suka gabata, kuma mai rinjaye akan su, kuma cewa wannan littafin yana bamu labaran al'ummun da suka gabata, kuma yana rabewa tsakanin ma'abota littafi (Yahudawa da Nasara) cikin abinda suka yi saɓani a akansa.
Muna imani cewa wannan Alkur’anin mai girma shi ne zancen Ubangijin talikai, Ruhi (Mala’ika Jibrilu) amintacce ne ya saukar da shi, wannan wani sanannen al'amari ne da larura a addinin musulunci, da dukkanin musulmai malamai daga cikinsu da gamagari sun haɗu akan hakan, wani bai yi saɓani daga cikinsu akan hakan ba, haƙiƙa Allah Ya yi shaida ga wannan Alkur’anin da cewa shi daga gurinSa yake, kuma mala'iku sun shaida cewa wannan Alkur’anin saukakke ne daga Gwani Abin yabo. Kuma Yahudawa da Nasara na zamanin sun yi shaida ga manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, kuma Allah Ya ambaci wannan shaidar a cikin abin babban littafinSa da ya saukar. Kuma mai shaida daga aljanu ya yi shaida cewa wannan Alkur’anin saukakke ne daga Allah kuma cewa shi mai dacewa ne da abinda (annabi) Musa - aminci ya tabbata agare shi - ya zo da shi ne, kuma kafiran Kuraishawa sun shaida cewa wannan Alkur’anin ba zancen mutum ba ne, kuma shi wanda ya sabawa zancensu ne.
Kuma muna imani cewa abin da Alkur’anin ya ƙunsa na ilimin sanin Allah, da hukunce-hukuncen shari'a, da ladubba ababen kiyayewa - cewa hakan abin tabbatarwa ne a ɗabi'u, kuma mai dacewa ne ga abinda annabawa - aminci ya tabbata agare su - suka zo da shi, dukkanin tushen da ƙarfafawa ya zo a cikin Alkur’ani su ne waɗanda manzanni suka yi kira zuwa gare su, kuma suka ƙarfafa akansu.
Alkur’anin mai girma mai dacewa ne da abinda Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - yake nufinsa ne ga halittu, kuma mai dacewa ne da abinda halitta suke nufi ga Mahalicci; hakan domin cewa Allah Shi ne Mahalicci, Yana sanin abinda bayi suke buƙatuwa gare shi, kuma Yana sanin abinda zai gyara addini su da jikin su da dukiyoyinsu da gidajensu, bai yi umarni da wani abu ba sai a cikin umarninSa akwai matuƙar maslaha, kuma bai yi hani ga wani al'amari ba sai acikin hanin akwai matuƙar sani da kuma kiyayewa.
Alkur’anin mai girma ya dace ne da abinda hankula suke hukunta shi, saboda haka ne Allah Ya ambaci tushen abubuwan da Ya haramta a cikin "Suratul An'am" Ya rufe su da faɗinSa: {Ko kwa hankalta}.
Dalilain da Alkur’anin mai girma ya zo da su dalilai ne a cikin matuƙar bayani da fasaha da ƙarfi da kusanci da sauƙi, kowanne mutum zai iya fahimtarsu, kuma wani ba zai iya warwaresu ba ko ya kawar da su, wannan ba'a saninsa daga zancen mutane, kuma dlilansa ba zai yiwu - ta kowanne hali daga halaye ba - su shiryar akan ɓata.
Alkur’anin mai girma shi ne zancen Ubangijin talikai, tare da hakan shi abin sauƙaƙewa ne ga kowane mutum, bai kasance sananne ga mutane ba a ce wani daga cikinsu ya rubuta wani littafi, kuma ya zama mai sauƙi ga kowanne mutum, kuma abin yin magana da shi ga kowanne mutum, wannan ba ya kasancewa sai ga wannan littafin mai girma.
Alkur’anin mai girma abin kiyayewa ne daga canzawa da jirkitawa, kuma Allah Ya rubuta masa wanzuwa da dawwama har zuwa tashin Alkiyama, wannan wanzuwar da dawwamar da rashin canjin suna nuni akan cewa shi saukakke ne daga Gwani Abin yabo, tare da wanzuwarsa da dawwamarsa da kiyayewarsa, kuma tare da yadda a kullum ake samun sabon ilimi da fannoni da abubuwan da ake bincikowa, bamu taɓa samun cewa akwai wani ilimin da ya ƙunshi saɓanin abinda Alkur’anin ya zo da shi ba, kai ilimummuka suna dacewa da Alkur’anin a cikin abinda ambatansa ya zo a cikin Alkur’anin, kamar halittar sammai, da halittar mutum, da wanin hakan.
Alkur’anin mai girma mai shiryarwa ne ga abinda shi ne mafi tabbata, mai tattaro kowanne alheri, shi mai tattaro labari ne game da Mahalicci da abin halitta, da duniya da lahira, da aljanu da mutane, da umarni da hani, da ladubba da wajibai, da aljanna da wuta, shi mai tattaro imani ne da aiki da sakamako.
Alkur’ani mai girma waraka ne ga cututtuka, kuma ba'a taɓa samu wani zance daga zantukan mutane ba zancen da a cikinsa akwai waraka daga cutukan zukata da jiki, kamar yadda yake a cikin AlKur’ani mai girma wanda shi ne zancen Ubangijin talikai.
Alkur’ani yana bamu labaran al’ummun da suka gabata kamar yadda suka faru, kuma labarukansu ba su yaɗu ba tsakanin mutanen Makka ba, sai Allah Ya bamu labarinsu kamar yadda suke, wannan mai shaida ne akan cewa wannan saukakke ne daga Gwani Abin yabo.
Alkur’ani mai girma wanda ya ƙunshi matuƙar bayani da fasaha da labaran gaibu da shari'un Ubangiji, wani manzo ummiyyi ne wanda ba ya karatu ba ya rubutu ne ya zo da shi, wannan mai nuni ne akan cewa shi saukakke ne daga Gwani Abin yabo. Sura ɗaya daga AlKur'ani mai girma saukakkiya ce a cikin lokuta mabanbanta, da kuma gurare mabanbanta, tare da hakan ana karanta surar kamar yadda aka saukar da ita a karo ɗaya, kuma al'ada ta gudana cewa mutane kwarewarsu tana ban-banta da juna, kuma tsarinsu yana saɓawa idan sun wallafa littattafai a lokuta maban-banta.
Manzo - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - haƙiƙa Allah Ya ba shi sunnah kamar yadda Ya ba shi Alkur’ani: Wanda ya yi duba a cikin Alkur’ani da sunnah zai ga cewa a tsakaninsu akwai banbance-banbancen da ba ya ɓoyuwa.
Kuma cewa Alkur’ani ya ƙunshi nusarwa ga annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - zuwa abinda yake kamata ya kasance, ko abinda yake wajaba ya aikata shi.
BABIN WAJABCIN IMANI DA LITTATTAFAI
Muna imani da littattafai, su ne littatttafan Allah saukakku ga manzanninSa da annbawanSa - aminci ya tabbata agare su -.
Waɗanda muka sani daga cikinsu su ne: Suhufi Ibrahim, da Suhufi Musa, da Attaura, da Zabura, da Linjila, da AlKur'ani.
Kuma muna imani da waɗanda muka sani daga cikinsu da waɗanda ba mu sani ba.
Muna imani cewa dukkan waɗannan littattafan su ne zancen Allah kuma wahayinSa ne, Ya saukar da su ga manzanninSa - aminci ya tabbata agare su - (Mala'ika) Jibrilu amintacce ne ya saukar da su, kuma sun ƙunshi shari'un Allah, da labarai da wa'azuzzuka da umarni da hani, kuma kowanne littafi ya kasance a zamaninsa shi ne wahayin da yake wajaba a yi aiki da shi, da neman hukunci gare shi.
Kuma muna imani cewa sashinsu sun fi sashi, Attaura Allah Ya rubutata ne da hannunSa, Allah Maɗaukaki - Ya ce: {Kuma Muka rubũta masa a cikin alluna daga kõwanne abu, wa'azi da rarrabewa ga dukkan kowanne abu} [al-A'araf: 145]. Kum (annabi) Tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya faɗa yana mai bada labari game da (Annabi) Adam ya cewa (annabi) Musa - aminci ya tabbata agare shi -: "Ya Musa Allah Ya zaɓeka da zancenSa, kuma Ya rubuta maka (Attaura) da hannunSa". (Bukhari ne ya fitar da shi (6614), da Muslim (2652), da Abu Dawud (4701), da Tirmizi (2134), da Ibnu Majah (80).) Kuma Allah Ya faɗa dangane da sha'anin Attaura: {Lallai Mu Mun saukar da Attaura wacce a ciknta akwai shiriya da haske wacce annabawan da suka miƙa wuya suna yin hukunci da ita} [al-Ma'ida: 44]. Kuma Allah Ya faɗa a sha'anin Injila: {Kuma Mun ba shi Injila wacce a cikinta akwai shiriya da haske kuma mai gasgatawa ce ga binda ke gabanta na Attaura, kuma shiriya ce kuma wa'azi ce ga masu tsoron Allah}. [al-Ma'ida: 46].
Imani da littattafai shi ne rukuni na uku daga rukunan imani da Allah, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Manzon Allah yã yi ĩmãni da abin da aka saukar zuwa gare shi daga Ubangijinsa, da mũminai. Kõwanensu yã yi ĩmãni da Allah, da mala'ikunSa, da littattafanSa, da manzanninSa. Bã mu rarrabẽwa a tsakãnin daya daga manzanninSa. Kuma (mũminai) suka ce: "Mun ji kuma mun yi dã'a; (Muna nẽman) gãfararKa, yã Ubangijinmu, kuma zuwa a gare Ka makõma take } [al-Baƙara: 285]. Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance wata rana ya fito wajen mutane, sai wani mutum ya zo masa, sai ya ce: Ya manzon Allah, menene imani? ya ce: "Ka yi imani da Allah, da mala'ikunSa, da littafinSa, da haɗuwa daShi, da manzanninSa, kuma ka yi imani da tashi na ƙarshe". (Bukhari ne ya fitar da shi (4777), da Muslim (9), da Ibnu Majah (64).) Kada mu zama kamar waɗanda suka yi imani da sashinsu, suka kafirta wa wani sashi, kamar yadda Allah Ya bada labari game da su da faɗinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: {Lalle ne, waɗanda suke kãfirta da Allah da ManzonSa kuma sunã nufin su rarrabe a tsakãnin Allah da manzanninSa, kuma sunã cẽwa: "Munã ĩmãni da sãshe, kuma munã kãfirta da sãshe." Kuma sunã nufin su riƙi hanya a tsakãnin wannan} [al-Nisa'a: 150]. Ko kuma kamar waɗanda suka kafirce da littattafan da Allah Ya saukar da su ga manzanninSa, inda Allah Ya faɗa Yana Mai bada labari game da su da faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Waɗanda suka ƙaryata, game da Littãfin, kuma da abin da Muka aika Manzanninmu da shi. To, za su sani} [Ghafir: 70].
Kuma muna imani cewa dukkan littattafan da suka rigayi Alkur’ani Allah bai laminci kiyayesu ba; kai Ya wakilta kiyayesu ne ga mutanen da Allah Ya saukarwa su, sai Maɗaukakin sarki Ya ce: {Lalle ne Mu, Mun saukar da Attaura a cikinta akwai shiriya da haske, annabawa waɗan da suke sun sallama suna yin hukunci da ita ga waɗanda suke tuba (Yahudu) da Malamai na Allah, da manyan malamai ga abin da ake nema da su tsare daga litattafin Allah, kuma sun kasance a kansa masu ba da shaida} [al-Ma'ida: 44]. Sabo da haka ne canje-canje suka shiga ciki, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Sabo da warware alƙawarinsu ne muka la'ancesu kuma Muka sanya zukatansu busassu, suna karkatar da magana daga gurarenta sun manta wani kaso daga abinda aka tunasar da su shi} [al-Ma'ida: 13].
Kuma waɗannan littattafan na Allah sun fiskanci bacewa da mantawa, kuma maƙaryata sun rubuta abin da suka rubuta suka jingina su ga Allah dan ƙarya da ƙage, Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {To, bone ya tabbata ga waɗanda suke rubũta littãfi da hannuwansu sa'an nan kuma su ce wannan daga wurin Allah yake, dõmin su sayi kuɗi kaɗan da shi, sannan bone ya tabbata a gare su daga abin da hannayensu ke rubũtãwa, kuma bone ya tabbata a gare su daga abin da suke sanã'antãwa} [al-Baƙara: 79]. Suna karanta su da harsunansu dan zirfafawa a rikitar da al’umma; dan su yi zatan cewa su daga Allah ne. Allah Ya faɗa Yana Mai bada labari game da hakan da faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Kuma lalle ne, daga cikinsu akwai wata tawaga suna karkatar da harsunansu da Littãfi dõmin ku yi zaton sa (abinda suka fada) daga Littãfin, alhãli kuwa bã daga Littãfin (yake ba). Kuma suna cẽwa: "Shi daga wurinAllah yake." Alhãli kuwa shi, bã daga wurin Allah yake ba. Sunã faɗar ƙarya ga Allah, alhãli kuwa sunã sane} [Aal- Imran: 78].
BABIN IMANI DA ALKUR'ANI MAI GIRMA
Muna imani cewa Alkur’ani mai girma shi ne mafi girman littattafan Allah kuma mafi cikarsu mafi ɗaukakarsu, shi ne na ƙarshensu, (Mala'ika) Jibrilu ne - aminci ya tabbata agare shi - ya saukar da shi a zuciyar manzonmu (annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma lalle shi (Alƙur'ãni), haƙĩƙa, saukarwar Ubangijinhalittu ne * Rũhi amintacce ne ya sauka da shi * A zũciyarka, dõmin ka kasance daga mãsu gargaɗi} [al-Shu'araa: 192-194]. Allah Ya zaɓa masa mafi ɗaukakar harsuna, sai Ya saukar da shi da harshen Larabci mabayyani, (Allah) Maɗaukakin sarki Ya ce: {Lalle ne Mũ, Mun saukar da shi, yanã abin karantãwa na Lãrabci; tsammãninkũ, kunã hankalta} [Yusuf: 2]. Ibn Kutaibah ya ce: "Wanda nazarinsa ya yawaita kuma iliminsa ya yalwata, kuma ya fahimci mazahabobin Larabawa da fannoninsu a cikin tsarin azanci shi ne kaɗai yake sanin falalar Alkur’ani, abinda Allah Ya keɓanci harshensu da shi banda sauran dukkanin harsuna; cewa shi babu wata al'umma a cikin dukkanin al'ummatai da aka ba ta bayani, da yalwar fage, (irin) abinda aka bai wa Larabawa keɓantaccen abu daga Allah; sabo da abinda ya kimsa shi ga manzo - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, kuma Ya yi nufinsa na tabbatar da dalilai akan annabtarsa da littafin, sai Ya sanya shi alamarsa, kamar yadda Ya sanya alamar kowanne annabi daga manzanni, ga mafi shaharar al'amura na abinda ke cikin zamaninsa wanda aka aikoshi a lokacin". (Tawil Mushkil al-Kur'an (Shafi na 17).)
Farkon abinda Allah Ya saukar daga gareshi (Alkur’ani): FaɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, wanda Ya yi halitta} [Alaƙ: 1]. Daga Uwar muminai A'isha - Allah Ya yarda da ita - cewa ita ta ce a farkon abinda aka farawa manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - da shi: Har gaskiya ta zo masa alhali shi yana kogon Hira, sai mala'ika ya zo masa, sai ya ce: "Ka ranta, ya ce:: Ni ba mai karatu ba ne, ya ce: sai ya ɗaukeni, sai ya lulluɓeni har sai da ya kai ni ga matuka, sannan ya sake ni, sai ya ce: Ka karanta, na ce: Ni ba mai karatu ba ne, sai ya ɗaukeni, sai ya lulluɓeni karo na biyu har yakai wahala gareni, sannan ya sakeni, sai ya ce: Ka karanta, sai na ce: Ni ba mai karatu ba ne, sai ya ɗaukeni, sai ya lulluɓeni karo na uku, sannan ya sakeni, sai ya ce: {Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, wanda Ya yi halitta * Ya halicci mutum daga gudan jini * Ka yi karatu, kuma Ubangijinka Shi ne Mafi karamci} [al-Alaƙ: 1-3]. Sai manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya dawo zuciyarsa tana karkarwa. (Bukhari ya fitar da shi (3), da Muslim (160), da Tirmizi (3632).) Daga na karshe ƙarshen abinda ya sauka daga Alkur’ani shi ne faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Kuma yaune Na cika muku Addininku, kuma Na cika muku ni'amarku, kuma Na yarje muku Musulunci a matsayin Addini} [Ma'ida: 3]".
Haƙiƙa Alkur’ani ya sauka da kaɗan-kaɗan ga manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - cikin shekarun annabtarsa, daga cikinsu akwai waɗanda suke Almakki, (wanda aka saukar kafin hijira), da kuma Almadani (wanda aka saukar bayan hijira), kuma adadin surorinsa sura ɗari ce da goma sha huɗu, kuma mafi girman sura "Suratul Fatiha". Daga dan Abbas - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Yayin da Jibrilu - amincin Allah ya tabbata a gare shi - yana zaune a wajen annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai ya ji wata ƙara daga samansa, sai ya ɗaga kansa sama, ya ce: "Wannan wata ƙofa ce daga sama da aka buɗe a yau kuma ba a taɓa buɗe ta ba har zuwa yau, sai wani Mala'ika ya sauko daga ciki, don haka ya ce: Wannan wani Mala'ika ne da ya sauko duniya, kuma bai taɓa zuwa ƙasa ba sai yau sai yayi sallama ya ce: Ina yi maka albishir da haske guda biyu da aka ba ka wanda ba a bawa wani Annabi a gabanka ba: Fatiha, da ƙarshen suratul Baƙarah, ba za ku karanta wani Harafi daga cikinta ba ku roqi wani abu fa ce sai dai in an baku shi). (Muslim ne ya fitar da shi (806), da Nasa'i (912).) Kuma "Suratul Ikhlas" ta yi daidai da ɗaya bisa uku na Alkur’ani, Daga Abu Hurairah - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya fito zuwa gurinmu sai ya ce: "Zan karanta muku ɗaya bisa uku na Alkur’ani". sai ya karanta: Ka ce Shi ne Allah Shi kadai * Allah Abin nufi da buƙata} har yakai ƙarshenta. (Muslim ne ya fitar da shi (812).)
Kuma mafi girman ayoyinsa Ayatul Kursiyyi, Daga Ubayyu ɗan Ka'ab - Allah Ya yarda da shi - ya ce: manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Ya kai baban Munzir, shin ka san wacce aya ce daga littafin Allah mafi girma a tare da kai?" ya ce: Na ce: Allah da ManzonSa ne mafi sani. Ya ce: "Ya Kai baban al-Munzir, shin ka san wacce aya ce daga littafin Allah mafi girma a tare dakai?" ya ce: Na ce; {Allah wanda babu wani abin bautawa da gaskiya sai Shi, Rayayye Tsayayye da kanSa} [Baƙara: 255]. Ya ce: Sai ya daki ƙirjina, ya ce: "Wallahi ilimi ya faranta maka kai baban Munzir". (Muslim ya fitar da shi (810), da Abu Dawud (1460).)
Kuma Allah Ya yabi kanSa da saukar da wannan littafin, sai Maɗaukakin sarki Ya ce: {Gõdiya ta tabbata ga Allah wanda Ya saukar da Littafi a kan bãwansa kuma bai sanya karkata ba a gare shi} [Kahf: 1]. Kamar yadda - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - ya yi yabo ga wannan littafin mai girma, sai Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka kuma sarautarSa ta ɗaukaka - Ya ce: {Dã Mun saukar da wannan Alƙur'ani a kan dũtse, dã lalle kã ga dũtsen yanã mai tawãli'u, mai tsattsãgẽwa sabõda tsõron Allah, kuma waɗancan misãlai Munã bayyana su ne ga mutãne, da fatan za su yi tunãni} [al'Hashr: 21]. Kuma tsarki ya tabbatar maSa Ya ce: {Da lalle a ce an saukar da wani littafi abin karatu wanda ake tafiyar da duwatsu game da shi, ko kuma aka yanyanke ƙasa da shi, ko kuwa aka yi magana da matattu da shi} [Ra'ad: 31]. Kuma Ya sanya shi shiriya da rahama ga muminai, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {wannan (Alkur'ãni) hukunce-hukuncen natsuwa ne ga mutãne, da shiriya, da rahama, ga mutãne waɗanda ke da yaƙĩni} [al-Jathiya: 20]. Kuma wa'azi ne da waraka daga cutukan zukata da jikkuna, sai Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Ya ku mutãne! Lalle wa'azi yã jẽ muku daga Ubangijinku, da waraka ga abin da yake a cikin ƙirãza, da shiriya da rahama ga muminai} [Yunus: 57]. Tsarki ya tabbatar maSa Ya ce: {Kuma Munã sassaukarwa daga Alƙur'ãni, abin da yake waraka ne da rahama ga mũminai. Kuma bã ya ƙãra wa azzãlumai (kõme) fãce hasãra} [al-Isra'a: 82].
Kuma muna imani wannan littafin mai girma shi ne mafi cikar littattafan Allah mafi tattarowarsu, kuma ya ƙunshi hujjoji da dalilai, da buga misalai a binda hujja take tsayuwa da shi akan halitta zuwa tashin Alkiyama, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Yã kũ mutãne! Haƙĩƙa wani dalĩli daga Ubangijinku yã je muku kuma Mun saukar da wani haske, bayyananne zuwa gare ku} [al-Nisa'a: 174], Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma bã zã su zo maka da wani misãli ba, fãce Mun je maka da gaskiya da mafi kyau ga fassara} [al-Furƙan: 33], Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun jujjuya (bayanai) dõmin mutãne, a cikin wannan Alƙur'ãni, daga kõwane misãli sai mafi yawan mutãne suka ƙi (kõme) fãce kãfirci} [al-Isra'a: 89], Tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya ce: {Kuma lalle ne haƙĩƙa, Mun sarrafa bayãni a cikin wannan Alƙur'ãni dõmin su yi tunãni, kuma bã ya ƙãra musu kõme fãce gudu} [al-Isra'a: 41], Ibnu Jarir ya ce: "Ambatansa ya ɗaukaka Ya ce: {Haƙiƙi mun jujjuya} ga waɗannan mushrikan masu ƙirƙirar ƙarya ga Allah (Abcikin wannan Alkur’ani ) izina da ayoyi da hujjoji, kuma mun buga musu misalai a cikinsa, mun gargaɗar da su a cikinsa, kuma mun gargaɗar da su {dan su wa'azantu} yana cewa; Dan su wa'azantu ga waɗancan hujjojin akansu, sai su hankalci kuskuren da su suke akansa suna tabbata, suyi izina da izinoni, sai su wa'azantu da su, su maye gurbi daga jahilcinsu, amma ba su yi izina da su ba, kuma ba su wa'azantu da abinda yake zo musu na ayoyi da gargaɗi ba". (Tafsir al-Dabari (17/453).)
Haƙiƙa wannan Alkur’ani mai girma ya ƙunshi dukkan abinda ke cikin littattafan Allah da suka gabata, kuma ya yi ƙari akansu, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma kalmar Ubangijinka tã cika, tanã gaskiya da ãdalci. Babu mai musanyãwa ga kalmõminSa, kuma Shi ne Maiji, Masani} [An'am: 115]. Kuma ya ƙunshi dukkan abinda halitta suke buƙatuwa gare shi na tushen imani da shari'u da hujjoji da hikimomi da wa'azuzzuka da labarai, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Lallai wannan Alkur’anin yana shiryarwa ga (halaye) waɗanda suke mafi daidaituwa} [Isra'a: 9], Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Mu Muna bayar da labari a gareka mafi kyawun labari ga abinda Muka yi wahayin wannan Alkur’ani gareka} [Yusuf: 3], Shi yana cikin kololuwar fasaha da bayani, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Allah ne Ya sassaukar da mafi kyawun labari, Littafi mai kama da juna wanda ake kokkomawa karatunsa} [Zumar: 23]. Kuma (Annabi) tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "An aikoni da dunkulallun kalmomi, kuma an bani nasara da tsoro". (Bukhari ya fitar da shi (2977), da Muslim (523), da Tirmizi (1553), da Nasa'i (3087).)
Daga mafi girman dalilai akan cewa wannan Alkur’ani zancen Allah ne Ubangijin talikai: Cewa manzo - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - Ummiyyi ne ba ya karatu ba ya rubutu, kuma an saukar masa da mafi girman littattafai kuma mafi cikarsu a fasaha da bayani, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma ba ka kasance kana karãtun wani littãfi ba a gabãninsa, kuma bã ka rubũtunsa da dãmanka dã haka yã auku, dã mãsu ɓarnã sun yi shakka} [Ankabut: 48], kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Ku yi imani da Allah da manzanSa annabi ba uwa (ummiyyi) wanda yake imani da Allah da kalmominSa da litattafanSa ku bi shi kwa shiriya} [al-A'araf: 155].
Kuma muna imani cewa Alkur’ani aya ce mai rinjayarwa a lafazinsa da ma'anarsa, kuma Allah Ya yi wa aljanu da mutane gabaɗayansu kalubale cewa su zo da kwatankwacinsa, ko surori goma daga kwatankwacinsa, ko sura ɗaya, Allah Ubangijin talikai alherinSa ya yawaita, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Ka ce: "Lalle ne idan mutãne da aljannu sun tãru a kan su zo da misãlin wannan Alƙur'ãni bã zã su zo da misãlinsa ba, kuma kõ dã sãshinsu yã kasance, mataimaki ga sãshi} [al-Isra'a: 88], kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kõ sunã cẽwa, "Yã ƙirƙire shi?" Ka ce: "Ku zo da sũra guda misãlinsa, kuma ku kirãyi wanda kuka iya duka, baicin Allah, idan kun kasance mãsu gaskiya} [Hud: 13]. Kuma Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {To idan kun kasance a cikin kokwanto daga abinda muka saukar ga bawanMu to ku zo da sura daga kwatankwacinsa kuma ku kira masu shaidarku koma bayan Allah in kun kasance masu gaskiya ne}. [Baƙara: 23].
Kuma muna imani cewa wannan Alkur’ani haƙiƙa Allah Ya lamunce kiyaye shi, kuma bai sanya hakan ga halittarSa ba, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Lalle Mũ ne, Muka saukar da Ambato (Alƙur'ãni), kuma lale Mũ, haƙĩƙa, Mãsu kiyayẽwane gare shi} [Hijr: 9]. kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {ɓarna bã zã ta je masa ba daga gaba gare shi. kuma bã zã ta zo ba daga bãya gare shi. Saukarwa ce daga Mai hikima, Gõdadde} [Fussilat: 42], Kuma Ya sanya shi abin kyautatawa ta ɓangaren gamammiyar kyautatawa, Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {A. L̃.R. Littãfi ne an kyautata ãyõyinsa, sa'an nan an bayyanã su daki-daki, daga wurin Mai hikima, Mai ƙididdigewa} [Hud: 1], kamar yadda Ya sanya shi mai kama da juna gaba ɗayansa, sai Allah - tsarki ya tabbatar maSa - Ya ce: {Allah ne Yasaukar da mafi kyawun labari, Littafi mai kama da juna wanda ake kokkomawa karatunsa} [Zumar: 23], kuma Ya sanya daga gare shi abin kyutatawa da mai kama da juna, sai Maɗaukakin sarki Ya ce: {Shi ne wanda ya saukar da Littãfi a gare ka, daga cikinsa akwai ãyõyi bayyanannu, su ne mafi yawan Littãfin, da wasu mãsu kamã da jũna. To, amma waɗanda yake a cikin zukãtansu akwai karkata sai suna bin abin da yake da kamã da jũna daga gare shi, dõmin nẽman yin fitina da tãwĩlinsa. Kuma bãbu wanda ya san tãwĩlinsafãce Allah. Kuma matabbata a cikin ilmi sunã cẽwa: "Mun yi ĩmãni da Shi; dukkansa daga wurin Ubangijinmu yake." Kuma bãbu mai tunãni fãce ma'abũta hankula} [Aal- Imran: 7], Kuma Ya bayyana cewa ma'abota karkata suna bin abinda ya yi kama da juna daga gare shi , muminai kuma suna imani da shi gaba ɗayansa abin kyautatawarsa da kuma mai kama da junansa.
Kuma Ya sanya shi mai hukunci akan dukkan litattafan da suka gabata, kuma mai rinjaye akansu, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Kuma Mun saukar da Littafi zuwa gareka da gaskiya, yana mai gasgatawa ga abinda ya gabace shi na littafi (Attaura da Linjila), kuma mai rinjayarwa akansa} [Ma'ida: 48]. Kuma Allah Ya bayyana cewa wannan littafin yana karanto mana labaran al'ummun da suka gabata, kamar yadda ya ke a cikin faɗin Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka -: {Wannan daga lãbarun gaibi ne, Munã yin wahayinsa zuwa gare ka, kuma ba ka kasance a wurinsu ba a lõkacin da suke yin niyyar zartar da al'amarinsu, alhãli sunã yin mãkirci} [Yusuf: 102], Misalansu suna da yawa, Alkur’ani yana rabewa tsakanin ma'abota littafi (Yahudu da Nasara) a cikin abinda suka yi saɓani a cikinsa, Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya ce: {Lalle ne wannan Alƙur'ãni yanã gaya wa Banĩ Isrãĩla mafi yawan abin da sũ suke sãɓa wa jũnansu a ciki} [Naml: 76].
Umar ɗan al-Kaɗɗab - Allah Ya yarda da shi - ya faɗa akan minbarinsa: Lallai wannan Alkur’ani zancen Allah ne - Mai girma da ɗaukaka -, to ku sanya shi a bigirensa, kada ku bi soye-soyen zukatanku a akansa. (Ahmad ya fitar da shi acikin Zuhdu (191), da al-Darimi (3398), da Abdullahi ɗan Ahmad a cikin al-Sunnah (117), da al-Ajurri a cikin al-Shari'ah (155) kuma lafazin nasa ne, da Ibnu Baɗɗah a cikin al-Ibanah (23).)
Kuma Umar ɗan Khaɗɗab - Allah a yarda da shi - ya ce: "AlKur'ani zancen Allah ne, kada ku juyar da shi akan ra’ayoyinku". (Al-ajurri ne ya fitar da shi a cikin al-Shari'ah (156).)
Daga Farwah ɗan Naufal al-Ashja'i ya ce: "Khabbab ɗan Arat - Allah Ya yarda da shi - ya kasance maƙocina ne, sai wata rana ya ce da ni: Ya wane, ka nemi kusanci zuwa ga Allah - Maɗaukakin sarki - gwargwadan ikonka, ka sani cewa kai ba zaka nemi kusanci zuwa gare shi ba da wani abu shi ne mafi soyuwa gare shi kamar zancenSa". (Abu Ubaid ya fitar da shi a cikin Fada'ilul AlKur'ani (shafi na 77), da Ibnu Abi Shaibah (30722), da Ahmad a cikin Zuhdu (192), da Usman ɗan Sa'id al-Darimi a cikin Raddi ga Jahamiyya (160), da Abdullahi ɗan Ahmad a cikin al-Sunnah (111).)
Kuma muna imani cewa wannan AlKur'anin shi ne zancen Allah, saukakke ba halittarsa aka yi ba , kuma cewa shi abin haddacewane a cikin zukata, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Ã'a, shĩ ãyõyi ne bayyanannu a cikin ƙirãzan waɗanda aka bai wa ilmi. Kuma bãbu mai musun ãyõyinMu fãce azzãlumai} [Ankabut: 49]. Duk ɗaya ne ya kasance abin rubutawa a cikin takardu ne, ko abin karantawa a cikin mihirabai da masallatai, hakan ba ya fitar da shi daga kasancewarsa zancen Allah ne, Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Lalle waɗanda ke karãtun Littãfin Allah kuma suka tsayar da salla, kuma suka ciyar daga abin da Muka azurta su da shi, a asirce da bayyane, sunã fãtan (sãmun) wani fatauci ne wanda bã ya yin tasgaro} [Faɗir: 29], Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Lalle shi (wannan littãfi), haƙĩƙa, abin karantãwa ne mai daraja * A cikin wani littafi tsararre * Bãbu mai shãfa shi fãce waɗanda aka tsarkake * Abin saukarwã ne daga Ubangijin halitta duka} [al-Waƙi'ah: 77-80].
AlKur'ani mai girma zancen Allah ne, kuma zancenSa siffa ce daga siffofinSa, abinda ya kasance daga siffofin Allah to ba ya zama abin halitta; dan da ya zama abin halitta da abinda yake gudana akan sauran fararru na ƙarewa da gushewa da canji da ya gudana akansa, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Shin, bã su kula da Alƙur'ãni, kuma dã yã kasance daga wurin wanin Allah haƙĩƙa, dã sun sãmu, a cikinsa, sãɓã wa jũnamai yawa?} [al-Nisa'a: 82], Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Idan wani daga mushirikai ya nemi maƙwabtakarka to, ka ba shi maƙwabtakar har ya ji, maganar Allah, sa'an nan ka isar da shi ga wurin amincewarsa. Wancan fa domin lalle ne su, mutãne ne waɗanda ba su sani ba} [al-Taubah: 6].
Daga Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su - ya ce: Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -ya kasance yana nemawa Hassan da Hussain tsari, yana cewa: "Lallai babanku ya kasance yana nemawa Isma'il da Ishaƙ tsari da su: Ina neman tsari da kalmomin Allah cikakku daga sharrin kowanne Shaiɗani da abinda ke da dafi, da kuma kowanne ido mai zargi". (Bukhari ne ya fitar da shi (3371), da Abu Dawud (4737), kuma ya ce: Wannan dalili ne akan cewa Alkur’ani ba halittarsa aka yi ba, da kuma Tirmizi (2060), da Ibnu Majah (3525).)
Isma'il ɗan Abi Uwais ya hakaito ijma'in mutanen Madina akan cewa Alkur’ani ba halittarsa aka yi ba , sai ya ce: "Malik ya kasance da maluman mutanen garin mu suna cewa: Alkur’ani daga Allah ne, kuma babu wani abin halitta daga Allah, maluman mutanen Madina a lokacin Malik ɗan Anas (su ne): Muhammad ɗan Abdurrahman ɗan Abu Zi'ib, da Abdul Aziz ɗan Abu Salamah al-Majishun, da Abu Bakar ɗan Abu Sabusarah, da Ibrahim ɗan Sa'ad al-Zuhri, da Sa'id ɗan Abdur Rahman al-Jumahi, da Hatim ɗan Isma'il, da Abdullahi ɗan Abdul Aziz al-Umari al-Zahid, da Abu Damirah Anasa ɗan Iyad, da Muhammad ɗan Abu Fudaik". (Sharhi Usulul I'itiƙadi Ahlus Sunnah Wal jama'ah (2/300).)
Shu'aib ɗan Harb ya ce: Na cewa Abu Abdullahi Sufyan ɗan Sa'id al-Sauri: "Ka zantar da ni da wani zance daga sunnah wanda Allah - Mai girma da ɗaukaka - Zai amfanar da ni shi, idan na tsaya a gaban Allah - alherinSa ya yawaita kuma Ya ɗaukaka - Ya tambayeni game da shi ya ce da ni; Daga ina ka karɓi wannan? Na ce: Ya Ubangiji Sufyanu al-Sauri ne ya zantar da ni wannan hadisin, kuma na karɓa daga gare shi, ni sai in tsira, kai kuma a kamaka. sai ya ce: Ya Shu’aib Wannan ƙarfafawa ce, wacce take makurar ƙarfafawa, ka rubuta: Da sunan Alah Mai rahama Mai jin ƙai: Alkur’ani zancen Allah ne ba halittarsa aka yi ba, daga shi ne ya fara kuma daga gareShi ne zai koma". (Sharhi Usulul I'itiƙadi Ahlus Sunnah Wal jama'ah (1/170).)
Imam Ibnu Jarir al-Dabari ya ce: "Ibnu Uyaynah ya zantar da mu ya ce: Na ji Amr ɗan Dinar yana cewa: Na riski malummanmu tun tsawon shekaru saba'in suna cewa: AlKur'ani zancen Allah ne, daga gare Shi ya fara kuma zuwa gareShi ne zai koma". (Sarihus Sunnah, na al-Dabari (shafi na 19).)
Kuma daga Hassan ɗan Ayyuba ya ce: "Na ji Ahmad ɗan Hanbali yana faɗa game da Furyani ya ce: Na ji al-Sauri - yana nufin Sufyan - yana cewa: Wanda ya ce: AlKur'ani halittarsa aka yi to shi zindiƙi ne". Kuma daga Abdullahi ɗan Ahmad ɗan Hanbali ya ce: Na ji babana yana cewa: Labari ya isar mini daga Ibrahim ɗan Sa'ad, da Sa'id ɗan AbdurRahman al-Jumahi, da Wahbu ɗan Jarir, da Abu al-Nasr Hashim ɗan Kasim, da Sulaiman ɗan Harb sun ce: AlKur'ani ba halittarsa aka yi ba". (Sharhi Usulul I'itiƙadi Ahlus Sunnah Wal jama'ah (2/277).)
Kuma shugaban shugabanni Muhammad ɗan Khuzaimah - Allah Ya yi masa rahama - ya yi babi akan wannan mas'alar, sai ya ce: "Babi daga dalilan da suke nuni akan cewa Alkur’ani zancen Allah ne Mahalicci, kuma maganarSa ba halittarta aka yi ba". (AtTauhid na Ibnu Khuzaimah (1/404).)
Abu Sa'id al-Darimi ya ce: "A cikin waɗannan hadisan akwai bayanin cewa AlKur'ani ba halittarsa aka yi ba; domin cewa babu wani abu ga halittu na banbanci a falalar dake tsakaninsu kamar tsakanin Allah da halittarSa a falala; domin falalar abinda ke tsakanin halittu ana iya riskarsa, amma ba za’a iya riskar fifikon Allah akan halittarSa ba, kuma wani ba zai iya kiyaye shi ba, haka nan fifikon zancenSa akan zancen ababen halitta, da ya kasance zance abin halitta da fifikon dake tsakanin sa da tsakanin sauran zantuka kamar fifikon Allah ne akan halittarSa, kai bai kai yanki ɗaya bisa goma daga yanki miliyan ba kai ko kusa da haakn ma bai kai ba, to ku fahimce shi; domin cewa shi babu wani abu tamkarsa, kuma zancenSa bai zama kamar wani zance ba, kuma ba za’a taba zuwa da kwatankwacinsa ba har a bada". (Raddi ga Jahamiyya na al-darimi ( shafi na 188).)
Daga Abu Yusuf - Allah Ya yi masa rahama - cewa shi ya ce: "Amma AlKur'ani to shi zancen Allah ne - Maɗaukakin sarki -, kuma wahayinSa ne kuma saukarwarSa ne, akan haka ne na samu Abu Hanifa da shugabanni, kuma su agurinsu ba halittarSa aka yi ba, kuma ba Mahalicci ba ne". (Al-I'itiƙad na Naisaburi (shafi na 135).)
BABIN ALKUR'ANI MAI GIRMA SAUKAKKENE DAGA UBANGIJIN TALIKAI
Muna imani cewa wannan AlKur'anin mai girma shi ne zancen Ubangijin talikai, Ruhi amintacce ne ya saukar da shi, wannan wani al'amari ne sananne da lalura daga addinin musulmai, kuma musulmai sun haɗu akan hakan, wani bai yi saɓani a hakan ba, kuma wannan al'amarin - shi ne kasancewarsa daga Ubangijin talikai - dalilai da yawa waɗanda ba zai yi wu a taƙaicesu ba ko kuma kididdige su ba suna nuni haka, daga cikinsu:
Shaidar Allah ga wannan AlKur'anin cewa shi daga Allah ne, Allah Ya faɗa - kuma zancenSa gaskiya ne: {Ka ce wane abu ne mafi girman shaida ? ka ce: Allah Shaida ne tsakanina da ku, kuma an yi min wahayin wannan AlKur'anin dan in gargaɗar da ku da shi da wanda labari ya kai gare shi} [al-An'am: 19]. kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Sai dai Allah Yana shaida da abinda Ya saukar gareka Ya saukar da shi da saninSa}. [al-Nisa'a: 166].
Daga ciki kuma: Shaidar mala'iku cewa wannan AlKur'anin saukakkene daga Gwani kuma Abin yabo, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Amma Allah Yanã shaida da abin da Ya saukar zuwa gare ka. Yã saukar da shi da saninSa. Kuma malã'iku sunã shaida. Kuma Allah Yã isa Ya zama shaida} [al-Nisa'a: 166].
Daga ciki: Cewa shi mai dacewa ne ga abinda annabawa - aminci ya tabbata agare su - suka zo da shi, kamar yadda yake a cikin faɗarSa - Maɗaukakin sarki -: {Kuma Ubangijinka Ya hukunta kada ku bauta wa kõwa fãce Shi, kuma game da mahaifa biyu ku kyautata kyautatawa, ko dai ɗayansu ya kai ga tsũfa a wurinka ko dukansu biyu, to, kada ka ce musu 'tir' kuma kada ka tsãwace su kuma ka faɗa musu magana mai karimci} [al-Isra'a: 23]. Zuwa faɗinsa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: {Wancan yãnã daga abin da Ubangijinka Ya yi wahayi zuwa gare ka na hikima. Kuma kada ka sanya wani abin bautãwa na daban tãre da Allah har a jẽfa ka a cikin Jahannama kanã wanda ake zargi, wanda ake tunkuɗẽwa} [al-Isra'a: 39].
Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Yã saukar da Littãfi a gare ka da gaskiya, yana mai gaskatãwa ga abin da ke gaba gare shi, kuma Allah Yã saukar da Attaura da Linjĩlã} [Aal- Imran: 3]. Dukkan waɗannan su ne asalin bayanan da ƙarfafawa ta zo akan su, su ne waɗanda manzanni suka yi kira garesu kuma suka ƙarfafa akansu.
Daga cikinsu: Shaidar mazuwa littafi (Yahudawa da Nasara) na zamani ga manzo - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - kuma Allah Ya ambaci wannan shaidar a cikin kyakkyawan saukakken (littafinSa), sai Maɗaukakin sarki Ya ce: {Ka ce: "Shin, kun gani, idan (Alƙur'ãni) ya kasance daga wurin Allah yake, kuma kuka kãfirta da shi, kuma wani mai shaida daga Banĩ Isrã'ĩla ya bãyar da shaida a kan kwatankwacinsa, sa'an nan ya yi ĩmãni, kuma kuka kangare? Lalle Allah bã Ya shiryar da mutãne azzãlumai} [al-Ahƙaf: 10]. A cikin "Bukhari da Muslim" daga labarin Warƙah bayan manzo - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ba shi lbarin abinda ya gani "Sai Warƙah ya ce masa: Wannan mala'ikan da Allah Ya saukarwa (Annabi) Musa ne". (Bukhari ne ya fitar da shi (3392), da Muslim (160).)
A cikin Kissar Ja'afar - Allah Ya yarda da shi - lokacin da Najjashi ya tambaye shi : Shin a tare da kai akwai wani abu daga abinda manzo - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya zo da shi? sai ya karanta masa, sannan Najjashi ya ce: "Na rantse da Allah, lallai wannan zancen da zancen da (Annabi) Musa ya zo da shi suna fita ta alkuki ɗaya ne”. (Ishaƙ ɗan Rahuwaih ne ya fitar da shi (1835), da Ahmad (22498), da Ibnu Khuzaimah (2260), da al-Dahawi a cikin Sharhu Mushkilil Aasar (5598), da Abu Nu'aim a cikin al-Hilyah (1/115), da kuma cikin Dala'il al-Nubuwwah (194).)
Daga ciki kuma: Shaidar aljanu cewa wannan AlKur'anin saukakkene daga Allah, kuma shi mai dacewa ne da abinda (Annabi) Musa - aminci ya tabbata agare shi - ya zo da shi: Kuma a lõkcin da Muka jũya waɗansu jama'a na aljamiu zuwa gare ka sunã saurãren Alƙur'ãni. To, alõkacin da suka halarce shi suka ce: "Ku yi shiru." Sa'an nan da aka ƙãre, suka jũya zuwa ga jama'arsu sunã mãsu gargaɗi * Suka ce: "Ya mutãnenmu! Lalle mũ, mun ji wani littãfi an saukar da shi a bãyãn Mũsã, mai gaskatãwa ga abin da ke a gaba da shi, yanã shiryarwa ga gaskiya da kuma zuwa ga hanya madaidaiciya} [al-Ahƙaf: 29-30]. kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Ka ce: "An yi wahayi zuwa gare ni cewa wasu jama'a na aljannu sun saurũri (karatuna), sai suka ce: Lalle ne mũ mun ji wani abin karantãwa (Alƙui'ãni), mai ban mãmãki * Yana nũni zuwa ga hanyar ƙwarai, sabõda haka mun yi ĩmãni da shi bã zã mu kõma bautã wa Ubangijinmu tãre da kõwa ba} [al-Jinn: 1-2].
Daga kuma: Shaidar kafiran Kuraishawa cewa wannan AlKur'anin ba zancen mutum bane, kuma shi ya saɓa da zancensu, daga Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su -: "Cewa Walidu ɗan Mugira ya zo wurin annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, sai ya karanta masa AlKur'ani, kai kace shi ya raurawar da zuciyarsa, sai hakan ya kai ga Abu Jahl, sai ya zo masa, sai ya ce: Ya baffa, lallai mutanenka suna ganin su tara maka dukiya. Ya ce: Dan me? ya ce: Dan su baka ita domin kai ka zo wa Muhammad dan ka yi watsi da abin da ya zo kafin shi (gargajiya), ya ce: Haƙiƙa Kuraish ta san cewa ni ina daga mafi yawancinsu a dukiya. Ya ce: To ka faɗi maganar da za ta kai ga mutanen ka dangane da Alkur’ani cewa kai mai inkarinsa ne, ko cewa kai mai ƙinsa ne ya ce: To me zan ce?! na rantse da Allah babu wani mutum a cikinku wanda ya fi ni sanin wakoki, ko kuma ya fini sanin rubutun zube, ko ya fini sanin kasida ko ya fi ni sanin wakokin aljanu, wallahi abinda yake fada bai yi kama da wani abu daga wannan ba, kuma na rantse da Allah akwai dadi a abinda yake fada, kuma a tare da shi akwai kyau, kuma cewa shi samansa mai bada 'ya'yan itatuwa ne kuma kasansa mai bayarwa ne da yawa, kuma shi yana daukaka kuma ba'a daukaka akansa, kuma shi yana karya abinda ke kasansa". (Hakim ya fitar da shi (3872), da Baihaƙi a cikin Shu'ab (133), da kuma cikin Dala'ilul al-Nubuwwah (2/198).)
Daga cikin su : Cewa AlKur'ani mai girma mai dacewa ne da abinda Allah - tsraki ya tabbatar amSa Ya ɗaukaka - yake nufinSa ga halitta, Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya ce: {Kuma lalle wannan ne tafarkĩNa, yana madaidaici: Sai ku bĩ shi, kuma kada ku bi wasu hanyõyi, su rarrabu da ku daga barin hanyãTa. Wannan ne Allah Ya yi muku wasiyya da shi tsammãninku, kunã yin taƙawa} [al-An'am: 153].
Daga ciki kuma: Cewa abinda AlKur'ani ya ƙunsa na ilimummukan Allah, da hukunce-huknce na shari'a da ladubba ababen kiyayewa dukkaninsa yana daga abinda ya tabbata a cikin ɗabi'a, Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Sabõda haka, ka tsayar da fuskarka ga addini, kanã mai karkata zuwa ga gaskiya, halittar Allah da Ya halitta mutãne a kanta. Bãbu musanyãwa ga halittar Allah, wannan shĩ ne addini madaidaici kuma amma mafi yawan mutãne ba su sani ba} [al-Rum: 30].
Daga cikinsu: AlKur'ani mai girma mai dacewa ne da abinda acikinsa akwai gyara halitta; hakan domin cewa Allah Shi ne Mahalicci, to Yana sanin abinda bayi suke buƙatuwa gare shi, kuma Yana sanin abinda yake gyara addinansu da jikkunasu da dukiyoyinsu da gidajensu, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Ashe, wanda Ya yi halitta bã zai iya saninta ba, alhãli kuwa shi Mai tausasãwa ne, kuma Mai labartawa?} [al-Mulk: 14]. Bai yi umarni ba sai a cikin umarninSa akwai matuƙar maslaha, kuma bai yi hani ba sai ahanin na Sa akwai matuƙar gamamman sani da kuma bada kariya.
Daga cikinsu cewa AlKur'ani mai dacewa ne da abinda hankula suke hukunta shi; sabo da haka ne lokacin da Allah Ya ambaci tushen abubuwan da aka haramta a cikin "Suratul An'am" sai Ya rufesu da faɗinSa: {Kwa ji tsoron Allah}, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Ka ce: "Ku zo, in karanta abin da Ubangijinku Ya haramta." wãjibi ne a kanku kada ku yi shirkin kõme da Shi, kuma ga mahaifa biyu (ku kyautata) kyautatãwa, kuma kada ku kashe ɗiyanku sabõda talauci, Mũ ne Muke azurta ku, kũ da su, kuma kada ku kusanci abũbuwa alfãsha, abin da ya bayyana daga gare ta da abin da ya ɓõyu, kada ku kashe rai wanda Allah Ya haramta, fãce da hakki. Wannan ne (Allah) Ya yi muku wasiyya da Shi: Tsammãninku, kunã hankalta} [al-An'am: 151].
Maganar AlKur'ani ga ma'bota hankula shi ne mafi yawa daga taƙaitawa, kamar yadda da yawa ake neman tunani da dubawa da izina ga bayi cikin abinda Yake umarni da shi, ko Yake hani daga gare shi.
Daga cikinsu: Cewa dalilan da AlKur'ani mai girma ya zo da su dalilai ne da suka kai aƙololuwa a bayani, da fasaha, da ƙarfi, da kusanci da sauƙi, kowane mutum zai iya fahimtar su, wannan ba'a sanin sa acikin zancen wani daga cikin mutane, kamar yadda yake a cikin faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Wannan shĩ ne halittar Allah. To ku nũna mini, "Mẽne ne waɗanan da ba Shi ba suka halitta? Ã'a, azzalumai sunã a cikin ɓata bayyananna} [Luƙman: 11]. Haka a cikin faɗinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: {Dã waɗansu abũbuwan bautawa sun kasance a cikinsu (sama da ƙasa) fãce Allah, haƙĩƙa dã su biyun sun ɓãci. Sabõda haka tsarki ya tabbata ga Allah Ubangijin Al'arshi daga abin da suke siffantãwa} [al-Anbiyaa: 22]. Kamar yadda dalilansa ba sa taba yi wu wa - ta kowane hali - su yi nuni zuwa ƙarya, daga ƙarfin dalilansa ba zai yi wu a warwaresu ko juyar da su ba, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma ka ce: "Gaskiya tã zo, kuma ƙarya ta lãlãce. Lalle ne ƙarya ta kasance lãlãtacciya} [al-Isra'a: 81].
Daga cikinsu: AlKur'ani mai girma - alhali shi ne zancen Ubangijin talikai - abin sauƙaƙewa ne ga kowa, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur, ani dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?} [al-Kamar: 17]. Kuma bai kasance a al'adar mutane wani daga cikinsu ya rubuta wani littafi ba kuma ya zama mai sauƙi ga kowa, kuma ya yi magana da shi ga kowa, wannan ba ya kasancewa sai ga wannan littafin mai girma.
Daga cikinsu: AlKur'ani mai girma abin kiyayewa ne daga canji da jirkitawa, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Lalle Mũ ne, Muka saukar da Ambato (Alƙur'ãni), kuma lale Mũ, haƙĩƙa, Mãsu kiyayẽwane gare shi} [al-Hijr: 9]. Kuma Allah Ya rubuta masa wanzuwa da dawwama har zuwa tashin Alkiyama, wannan wanzuwar da dawwamar da rashin canjin suna nuni akan cewa shi saukakke ne daga Gwani Abin yabo, Allah Ya ce: {Shin, bã su kula da Alƙur'ãni, kuma dã yã kasance daga wurin wanin Allah haƙĩƙa, dã sun sãmu, a cikinsa, sãɓã wa jũnamai yawa?} [al-Nisa'a: 82].
Tare da wanzuwarsa da dawwamarsa da kiyayewarsa tare kuma da sabuntuwar ilimummuka da fannoni da ilmummukan da ake ganowa, bamu taɓa samun cewa akwai wani ilimin da ya ƙunshi saɓanin abinda AlKur'ani ya zo da shi ba, kai ilimummuka suna dacewa da AlKur'ani cikin abinda ambatansa ya zo a cikin AlKur'ani, kamar halittar sammai, da halittar mutum da wanin hakan.
Daga cikinsu: AlKur'ani mai girma mai shiryarwa ne ga ɗabi'u mafi tabbata, mai tattaro kowane alheri, shi mai tattaro labari ne game da Mahalicci da abin halitta, da duniya da lahira, da aljanu da mutane, da umarni da hani, da ladubba da wajibai, da aljanna da wuta, shi mai tattaro imani ne da aiki da sakamako, maɗaukakin sarki Ya ce: {Ba mu yi sakacin barin komai a cikin littafi (Alkur’ani) ba} [al-An'am: 38], kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Lallai wannan al-Kur'anin yana shiryarwa ga (halaye) waɗanda suke mafi daidaituwa} [al-Isra'a: 9].
Daga cikinsu: Cewa AlKur'ani mai girma waraka ne daga cutuka, Allah Maɗaukain sarki Ya ce: {Ya ku mutãne! Lalle wa'azi yã jẽ muku daga Ubangijinku, da waraka ga abin da yake a cikin ƙirãza, da shiriya da rahama ga muminai} [Yunus: 57]. Kuma ba'a taɓa samun wani zance ba daga zantukan mutane zancen da a cikinsa akwai waraka daga cutukan zukata da jikkuna, kamar yadda yake a cikin AlKur'ani mai girma wanda shi ne zancen Ubangijin talikai ba.
Daga cikinsu: Cewa Allah Ya kalubalanci mutum da aljani kan su zo da kwatankwacinsa, ko da kwatankwacin sura daga gare shi ne, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kõ sunã cewa: "Yã ƙirƙira shi ne."Ka ce: "Sai ku zo da sũrõri gõma misãlinsa ƙirƙirarru, kuma ku kirãyi wanda kuke iyãwa, baicin Allah, idan kun kasance mãsu gaskiya} [Yunus: 38], kuma Ya bayyana cewa shi babu kokwanto a cikinsa, sai Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya ce: {Kuma wannan Alƙur'ãni bai kasance ga a ƙirƙira shi ba daga wanin Allah, kuma amma shi gaskatawar wannan ne da yake a gabãninsa da bayãnin hukuncin littãffan Allah, Bãbu shakka a cikinsa, daga Ubangijin halittu yake} [Yunus: 37].
Daga cikinsu: Cewa wannan AlKur'anin yana bamu labarin al'ummun da suka shuɗe kamar yadda suka faru, kuma labarunsu ba su zama masu yaɗuwa a tsakanin mutanen Makka ba, sai Allah Ya bamu labarinsu, kamar yadda yake a cikin faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Mũ, Munã bãyar da lãbãri a gare ka, mafi kyãwon lãbãri ga abin da Muka yi wahayin wannan Alƙur'ãni zuwa gare ka. Kuma lalle ne kã kasance a gabãninsa, haƙĩƙa, daga gafalallu} [Yusuf: 3]. Wannan mai shaida ne akan cewa wannan saukakke ne daga Gwani Abin yabo.
Daga dalila: Wannan AlKur'anin mai girma wanda ya ƙunshi matuƙar bayani da fasaha da labaran ɓoye da shari'un Ubangiji wanda wani manzo ba uwa (ummiyyi) ya zo da shi ba ya karatu ba ya rubutu, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Kuma ba ka kasance kana karãtun wani littãfi ba a gabãninsa, kuma bã ka rubũtunsa da dãmanka dã haka yã auku, dã mãsu ɓarnã sun yi shakka} [al-Ankabut: 48], kuma Maɗaukakin sarki Ya ce: {Sune waɗanda suke bin manzo annabi ba uwa wanda suke samunsa a rubuce a gurinsu a cikin AtTaura da Linjila} [al-A'araf: 157].
Daga cikinsu: Cewa sura ɗaya daga AlKur'ani mai girma ta sauka a lokuta manisanta kuma acikin wurare mabanbanta, tare da hakan ana karanta sura kamar an saukar da ita sau ɗaya, kuma al'ada ta gudana cewa mutune malakarsu tana saɓawa, kuma uslubansu suna saɓawa idan sun wallafa littattafai a lokuta manisanta.
Daga cikinsu: Cewa manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - haƙiƙa Allah Ya ba shi sunnah kamar yanda Ya bashi AlKur'ani, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: ‘’Ku saurara ni an bani Littafi da kwatankwacin sa tare da shi". (Abu Dawud ya fitar da shi (4604), da Tirmizi (2664), da Ibnu Abi Shaibah a cikin al-Musannaf (24816), da kuma a cikin al-Musnad (927), da Ahmad (17174).)
Daga cikinsu: Cewa AlKur'ani ya ƙunshi fuskantarwar annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - zuwa abinda yake kamata ya kasance, ko abinda yake wajaba a aikata shi, kamar yadda yake a cikin faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Bã dõmin wani Littãfi daga Allah ba, wanda ya gabãta, dã azãba mai girma daga Allah tã shãfe ku a cikin abin da kuka kãma} [al-Anfal: 68], da faɗinSa - Maɗaukain sarki -: {Yã kai Annabi! Don me kake haramta abin da Allah Ya halatta maka, kanã nẽman yardar mãtanka, alhãli kuwa Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai} [al-Tahrim: 1], da kuma fadinSa - Maɗaukakin sarki -: {Yã game huska kuma ya jũya bãya * Sabõda makãho yã je masa * To, me ya sanar da kai cẽwa watakila shi ne zai tsarkaka * Ko ya tuna, dõmin tunãwar ta amfane shi? * Amma wanda ya wadãtu da dũkiya * Sa'an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi! * To, me zai cũce ka idan bai tsarkaka ba?} [Abasa: 1-7], da faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Kuma bã dõmin Mun tabbatar da kai ba, lalle ne, haƙĩƙa, dã kã yi kusa ka karkata zuwa gare su ta wani abu kaɗan * A lõkacin, lalle ne, dã Mun ɗanɗana maka ninkin azãbar rãyuwa da ninkin azãbar mutuwa, sa'an nan kuma bã zã ka sãmi mataimaki ba a kanMu} [al-israa: 74-75]. Da a ce AlKur'ani daga wajen manzo - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ne da bai naɗi wannan akan kansa ba; lokacin da irin wannan fadakarwar mai girma ta zo a cikinsa ga annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -; sai ya yi nuni a yanke akan cewa shi ba daga wajensa yake ba, kawai (Alkur’ani) daga wajen Masani ne kuma Gwani.
KUNDIN MANZANNI DA ANNABAWA - AMINCI YA TABBATA AGARESU -
Kundin a taƙaice
Muna imani cewa imani da manzanni - aminci ya tabbata agare su - shi ne rukuni na huɗu daga rukunan imani da Allah - Maɗaukakin sarki -.
Muna imani cewa tushen Da’awar manzanni - aminci ya tabbata agare su - shi ne sanin Allah - Maɗaukakin sarki - da sunayenSa da siffofinSa da ayyukanSa, kuma cewa su gaba ɗayansu an aiko su ne da tauhidi, kuma sun yi kira zuwa bautar Allah Shi kaɗai da barin bautar abinda ba Shi ba, annabawa da manzanni sune mafi cikar mutane a tauhidi da imani, kuma su ne mafi sanin halitta da Mahalicci - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - da abinda yake wajaba gareShi, da abinda yake hanuwa akanSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka.
Kowane annabi ya kira mutanensa zuwa asali biyu masu girma, sune: Bautar Allah Shi kaɗai, da imani da ranar lahira, da abinda Allah Ya tanadar na ni'ima ga masoyanSa, da azaba ga maƙiyanSa.
Kuma muna imani cewa annabawa - aminci ya tabbata agare su - sun haɗu a manyan tushe (asali) da suka yi kira zuwa gare su, dukkaninsu sun yi kira zuwa ga imani da Allah da mala'ikunSa da littattafanSa da manzanninSa da ranar lahira, da imani da ƙaddara alherinta da sharrinta, kuma dukkaninsu sun yi kira zuwa tushen ibadu, kamar sallah, da zakka, da azimi, da hajji, da tushen ɗabi'u ababen yabo, kuma sun yi hani daga tushen ɗabi'u ababan zargi, annabawa - aminci ya tabbata agare su - sun haɗu a kan tushen, amma shari'un da suka yi kira zuwa garesu to sun banbanta a hukunce-hukuncensu da rabe-rabensu.
Kuma muna imani cewa imani yana wajaba da dukkanin annabawa - aminci ya tabbata agare su - da gasgatasu a dukkan abinda suka bada labari da shi na gaibu, da yi musu biyayya a cikin abinda suka yi umarni da shi, da hanuwa daga dukkan abinda suka yi hani daga gare shi, da son su da girmama su da koyi da su, da yi musu shaida cewa sun isar da saƙo kuma sun bada amana, sun yi nasiha ga Allah da kuma bayinSa, kuma sun yi jihadi sabo da Allah hakikanin jihadi. Kuma aiki da shari'ar manzo yana wajaba akan dukkanin al'ummar da aka aiko mata manzon, kuma yana wajaba akan wannan al'ummar - al'ummar (Annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - daga aljanu da mutane yin aiki da shari'ar cikamakin annabawa da manzanni (annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ; domin cewa shi an aiko shi ne zuwa ga dukkanin aljanu da mutane.
Dukkanin annabawa da manzanni - aminci ya tabbata agare su - sun zo dan fitar da mutane daga duffan kafirci da shirka da jahilci, koda sun kasance a cikin ɗaukaka ta duniya da sarauta da ƙarfi da tsanani da noma da kamfanoni.
Kuma muna imani cewa Allah Ya aiko su suna masu albishir da aljanna kuma masu gargaɗi da wuta; dan kada mutane su zama suna da wata hujja akan Allah bayan (ya aiko da) manzanni.
Kuma muna imani cewa Allah Ya aiko wa kowacce al'umma wani manzo, wanda muka san sunansa daga cikinsu to imani da shi ya zama dole, wanda bamu san sunansa daga cikinsu ba to muna imani da shi a dunƙule. Imani da dukkanin annabawa da manzanni - aminci ya tabbata agare su - wajibi ne akan kowanne musulmi namiji da musulma mace, wanda ya kafircewa wani annabi ɗaya to haƙiƙa ya kafircewa dukkan annabawa - aminci ya tabbata agare su -.
Kuma muna imani cewa Allah Ya aiko manzanninSa zuwa wanda Ya so daga bayinSa daidai da abinda hikimarSa take hukunta shi, sabo da haka babu mai bibiya ga hukuncinSa, Yana aikata abinda Ya so kuma Yana zaɓa.
Kuma muna imani cewa annabta baiwa ce ta Allah, kuma rahama ce ta Ubangiji Yana bada ita ga wanda Ya so daga cikin bayinSa, Allah Ya na zaɓa daga mala'iku haka daga mutane.
Annabawa da manzanni - aminci ya tabbata agare su - wasu sun fi wasu a tsakanisu, kuma mafifitansu sune Ulul Azmi, kuma mafifitan Ulul Azmi sune baɗayi biyu: (annabi) Ibrahim, da (annabi) Muhammad - aminci ya tabbata agare su -, kuma annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi hani kan fifita tsakanin annabawa idan ta fuskar ƙabilancine da ta'assubanci ko tauye daraja, kuma kamar yadda Allah Ya zaɓi (annabi) Ibrahim da (annabi) Muhammad - aminci ya tabbata agare su - badaɗayi biyu, to haƙiƙa Ya zaɓi (annabi) Musa - aminci ya tabbata aagre shi - kuma Ya zaɓoshi akan mutane da saƙonninSa da kuma magana da shi, annabinmu - Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance hakika ya samu daukaka ta badadayantaka, da kuma daukakar cewa Ubangijinsa Ya yi magana da shi ta bayan shamaki a daren da aka yi Isara'i da shi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, sai annabinmu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance tabbas ya samu daukakar badadayantka, da kuma daukakar magana da shi.
Kuma muna imani cewa annabawa sune mafifitan mutane, babu wani da ya isa ya kai matsayin annabi, ba waliyyi ba ko waninsa, kuma fifita wani daga mutane akan wani daga annabawa ba ya halatta, kuma annabta ba a samunta daga kokarin aiki, kuma bawa ba ya samunta da wani ƙoƙarin ɗa'a, ko tsarkake rai da yin aiki tukuru da tsarkake zuciya da tsafeta da kuma tsarkake suluki.
Kuma muna imani cewa Allah bai aiko wani manzo ba sai wanda yake namiji, kuma muna sanin cewa manzanni da annabawa - aminci ya tabbata agare su - mutanene kamar sauran mutane, kuma su ne mafi cikar mutane a addinansu da hankulansu da ɗabi'unsu, saidai su ana yi musu wahayi ne, kuma su ma'asumaine a cikin abinda suke isar da shi daga Allah, idan annabi ya yi ijtihadi a cikin abinda ba'a yi masa wahayin wani abu ba a cikinsa ba kuma bai dace ba, to Allah baYa tabbatar da shi akan ijtihadinsa, kai a saukar da wahayi gareshi dan daidaita shi.
Manzanni da annabawa - aminci ya tabbata agare su - ba sa mallakar wani amfani ko cutarwa ga kansu, tare da cewa suna da matsayi mai girma, da daraja maɗaukakiya, da matsayi abin yabo a duniya da lahira, idan sun kasance ba sa mallakar amfani ga kansu ko cutarwa to ba sa mallaka ga wasunsu shi ne mafi cancanta, idan sun kasance ba sa mallaka ga kawunasu ko ga wasunsu - halin rayuwarsu - wani amfani ko cutarwa to su a wannan karon yana daga mafi cancanta cewa ba sa mallakar amfani ko cutarwa ga wasun su, bayan mutuwarsu.
Kuma ba su sanin gaibu sai gwargwadan abinda Allah Ya tsinkayar da su akansa, kuma Ya yi musu izini a kansa.
Kuma annabawa da manzanni - aminci ya tabbata agare su - suna bautar Allah dan tsoro da kuma kwaɗayi, kuma suna neman wasila (tsani) zuwa gareShi, kuma suna neman kusanci gareShi - tsarki ya tabbatar maSa Ya kuma ɗaukaka -.
Kuma muna imani cewa annabawa da manzanni - aminci ya tabbata agare su - suna samun abinda mutane suke samu na bala'i da rashin lafiya, kuma baƙin ciki da mutuwa suna samun su, kuma su suna da mata da zurriya, kuma suna cin abinci suna shiga kasuwanni, kuma muna sanin cewa Masihu - aminci ya tabbata agare shi - Allah Ya dauke shi a raye lokacin da mutanensa suka so kashe shi.
Muna shaidawa cewa haƙiƙa sun yi wa halitta nasiha, sun sauke amana, sun isar da saƙonnin Ubangijinsu, dan mabiya ba su amsa ba hakan ba ya cutar da su, ko kuma manya sun yi musu girman kai.
Kuma muna imani cewa Allah Ya ba kowane annabi ayoyi da hujjoji waɗanda irinsu zasu sa mutane su yi imani.
Kuma muna imani cewa Allah bai aiko wani annabi ba, sai a tare da shi akwai ayar da take nuni akan gaskiyarsa, daidai ne mun santa ko bamu santa ba, haƙiƙa Allah Ya ambata mana wani kaso daga cikinsu , akwai waɗanda ke cikin Alkur’ani mai girma. Kuma muna sanin cewa akwai wasu ayoyin masu yawa Allah Ya ƙarfafa manzannin da suka gabata da su, amma Allah bai ambta mana su ba, wani lokaci kuma Allah Yana ambatan ayoyi bayyananu, wani lokaci kuma Yana ambatan hujja, kuma muna sanin cewa ayoyi da hujjojin da Allah Ya ƙarfafa manzanninSa da annabawanSa - aminci ya tabbata agare shi - da su suna da yawa sosai.
Mafi girman dalilan da suke nuni akan gaskiyarsu shi ne abinda suke kira zuwa gare shi na tauhidin da ya tabbata a cikin ɗabi'u da hankulan da suke shaidawa akan kyawunnansu, da abin da suka zo da shi na ilimi mai amfani da aiki na gari da shiriya da addinin gaskiya da adalci. Da kuma shaidar da Allah Ya yi wa manzanninSa cewa su suna kan gaskiya, kuma abinda suka zo da shi shi ne gaskiya. Daga cikin mafi girman ayoyinsu wahayin da yake sauka gare su daga Allah, kuma mafi girman wahayi shi ne Alkur’ani mai girma ayar annabinmu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, wannan wahayin ba zai yi wu wani mutum ya zo da irinsa ba; domin cewa shi zancen Allah ne kuma wahayinSa ne, dan kuma abinda ke cikinsa na bada labarukan gaibu, dan kuma abinda ke cikinsa na shiriya da haske da rahama da hikima.
Daga abinda Allah Ya ƙarfafi manzanni - aminci ya tabbata agare su - da shi hujjoji na hankali waɗanda Allah Yake ƙara musu su, sai aka ƙure kafiri kuma ƙaryarsa ta ɓaci.
Daga mafi girman ayoyinsu bada labaran da suke na gaibun da Allah Ya yi musu izinin bada labarinsa. Daga cikinsu: Tsirar da annabawan da suka gabata - aminci ya tabbata agare su - da tsirar da mabiyansu daga makircin maƙiyansu, da halakar da masu ɗagawa masu girman kai, da kuma gargaɗin da Allah ya yi ga waɗanda ake kira da abinda aka yi wa waɗanda suka gabata, kuma sunnar Allah mai shuɗewa ce akan hakan: Daga cikinsu: Cikar ɗabi'unsu, da kyakkyawan ɗabi'unsu da ayyukansu da tarihinsu, da gaskiyar zantukansu daga abinda yake hanawa a yi musu ƙarya. Daga cikinsu: Gamamman bayani mai girma a cikin kawo ayoyin annabawa, da abinda suka zo da shi na ilimi da shiriya da addinin gaskiya, abinda yake ba zai yi wu tare da shi su haɗu akan kawo ƙarya. Daga cikinsu: su ba sa neman wani lada akan saƙonninsu, kuma basa neman wani mulki. Daga cikinsu: ba'a taɓa samun wanda ya soki annabcin annabawa ba sai jahili wanda bai yi duba ba a kan abinda suka zo da shi ba na addini da ilimi da shiriya ba, ko mai tsaurin kai mai girman kai.
Daga mafi girman ayoyinsu abinda yake kasancewa dalili a bayyane wanda idanu suke ganinsa, kuma hankula suke sallama masa, kamar dilmiyar da mutanen (annabi) Nuhu, da taguwar (annabi) Salihu, da tahaddin da (annabi) Hudu ya yi wa mutanensa na su kulla masa kaidi baki ɗayansu, da tsiratar da (annabi) Ibrahim daga wuta, da ayoyin (annabi) Musa, daga cikinsu akwai: Sanda, da fari, da kwarkwata, da kwaɗi, da jini, da Dufana, da dilmiyar da Fir'auna da mutanensa, da ayoyin (annabi) Dawud - aminci ya tabbata agare shi -, kamar tasbihin duwatsu da lauya ƙarfe, da ayoyin (annabi) Sulaiman - aminci ya tabbata agare shi -, da hore iska da aljanu gare shi , da yadda ya san maganar tsuntsaye, da ayoyin Masihu - aminci ya tabbata agare shi - kamar warkar da kutare da bebaye da makaho, da raya matattu, kuma cewa shi ya kasance yana kwaba tabo kamar yanayin tsuntsu sai ya yi busa acikinsa da izinin Allah sai ya zama tsuntsu, da ayoyin annabinmu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, su suna da yawa ba su iyakantu ba sai da wahala, kamar tsagewar wata, da Isra'i da Mi'iraji da yawaitar da zancen dabbobi, da tasbihin tsakawankwani, da shisshiken kututturen dabino, da taimakon Allah gare shi akan makiyansa.
Daga ayoyin annabawa: Halin annabi mai kira zuwa gaskiya; domin mutane suna banbantawa tsakanin mai kira zuwa tsantsar gaskiya a maganarsa, da mai da'awa maƙarya a cikin maganarsa...zuwa wanin haka daga ayoyi.
Ayoyin (Mu’ujizozin) annabawa gaba ɗayansu sun ba ce banda Alkur’ani mai girma, da sunnar annabinmu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - su biyun wanzajju ne; domin cewa su wahayi ne Allah Ya laminci kiyayesu, kuma a cikinsu akwai mafi girman dalilai da hujjoji akan gaskiyar manzanci, da gaskiyar manzo - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -.
Kuma muna imani cewa Allah Ya ƙarfafi Manzanninsa - aminci ya tabbata agare su - da abinda hikimarSa take hukunta shi na ayoyi da hujjojin kasantattu da na shari'a, sai Allah Ya shiryar da wanda Ya so da falalarSa, kuma Ya ɓatar da wanda Ya so da adalcinSa, sai dai mai tsaurin kai ayoyin ba sa ƙara masa komai sai tsaurin kai da girman kai.
Kuma muna imani cewa Allah da Ya ga dama da muatne gaba ɗaya sun shiriya.
Kuma muna imani cewa dalilan annabawa da ayoyin (Mu’ujizozin ) da suka zo da su da hujjojin da Allah Ya ƙare su da su ya koru ga wani mai da'awar annabta ya zo da su, ko wani matsafi, ko wani maƙaryaci; domin Allah Ya hukunta cewa baZai taimaki mai ɓatarwa ba, da wani ingantaccen dalili, kuma ba Zai gasgata maƙaryaci da wani dalili na gaskiya ba; domin shi Mai hikima ne a cikin shari'arSa da umarninSa, kuma hikimar Allah da sunnarSa masu gudana sun hana hakan.
Kuma muna imani cewa annabinmu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - shi ne manzon Ubangijin talikai, kuma shi ne cikamakin annabawa da manzanni, shi ne shugaban 'ya'yan Adam , kuma shi ne badaɗin Ubangijin talikai.
Kuma muna sanin cewa an ba shi ayoyi (Mu’ujizozin)?irinsa wanda da ba'a baiwa wani daga manzanni - aminci ya tabbata agare su - ba, mafi girman ayoyinsa shi ne Alkur’ani mai girma, kuma farkon abinda aka fara da shi na wahayi shi ne mafarki mai kyau a cikin bacci, ya kasance ba ya ganin wani mafarki sai ya zo tamkar ɓullowar asuba, kuma farkon abinda aka saukar masa shi ne farkon "Surar Alaƙ" kuma a bayanta an saukar da "Muddasir", sannan wahayi ya yi ta sauka ya kuma jerantu, kuma cewa shi ya zauna a Makka shekara goma sha uku yana kiran mutane zuwa tauhidi, kuma ya zauna a Madina shekara goma yana bayyanar da shari'un Allah, kuma yana kira zuwa addininsa, yana jihadi a tafarkinSa, har Allah Ya dauki ransa yana dan shekara sittin da uku - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi, fansarsa babana da babata.
Kuma muna sanin cewa daga mafi girman ayoyinsa (Mu’ujizozin )?bayan Alkur’ani mai girma (shi ne) Isra'i da Mi'iraji. Daga ayoyinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - tsagewar wata, kuma Allah Ya keɓance shi da wasu keɓantattun abubuwa masu yawa, waɗannan keɓantattun abubuwan malamai sun ambacesu a cikin litattafansu wani lokaci, wani lokaci kuma suna ware wasu littattafan su kaɗai sabo da su.
Kuma muna imani cewa imani da shi yana wajaba akan kowane ɗaya daga aljanu da mutane, da gasgata shi a cikin abinda ya bada labari, da binsa a cikin abinda ya yi umarni.
Kuma muna imani cewa yana wajaba kada a bautawa Allah sai da abinda Ya shara'anta, haƙiƙa Allah Ya yi gargaɗi daga saɓawa al'amarinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, kuma Ya yi umarni da girmama shi da kuma sonsa, kuma cewa shi yana wajaba manzo - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya zama mafi soyuwar mutane daga kansu da mahaifinsu da ɗansa da mutane gaba ɗaya.
Kuma muna imani cewa Allah Ya haɗa ambatan annabinmu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - da ambatanSa a cikin (Kalmar) shahada biyu da kiran sallah, haƙiƙa ambatansa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yawaita a cikin littattafan Allah waɗanda suka gabata, da kuma cikin AlKur'ani mai girma, kuma shugabannin musulunci sun wallafa littattafai mabanbanta a cikin bayanin sunnarsa, da tarihinsa, da ɗabi'unsa, da yaƙe-yaƙensa.
Kuma muna imani cewa Allah Ya aiko manzonSa zuwa ga halitta baki ɗaya, shi ne manzon Allah zuwa nauyaya biyu: Aljani da mutum, kuma Allah Ya juyar da wasu jama'a cikin aljanu zuwa gareshi suna sauraransa; dan su zama masu gargaɗi ga na bayansu cikin mutanensu, kuma dan hujja ta tsayu akansu, kuma Allah Ya ɗauki alƙawari ga kowane annabi daga annabawa da manzanni - aminci ya tabbata agare su -: Lallai idan an aiko (annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - alhali shi yana raye zai yi imani da shi.
Kuma muna imani cewa annabawa sun yi wa mutanensu albishir da shi, kuma siffofinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - da siffofin sahabbansa - Allah Ya yarda da su - sun zo a cikin Attaura da Linjila, kuma (Isa) Masihu - aminci ya tabbata agare shi - ya yiwa Banu isra'ila albishir da shi ta keɓantacciyar fuska, Banu Israila sun kasance suna saninsa kamar yadda suke sanin 'ya'yayensu. Daga alamomin annbacinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi waɗanda sun kasance a gurin mazowa laittafi tambarin annabci akan kafaɗarsa maɗaukakiya.
Kuma muna imani da gamewar manzancinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - saboda haka ne ya aika wasiku zuwa ga sarakuna da shugabanni yana kiransu zuwa bautar Allah Shi kaɗai, da imani da saƙonsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - da kuma gasgata shi .
Kuma muna imani cewa Allah Ya tattarowa annabinmu - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ƙasa, sai ya ga inda mulkin al'ummarsa zai kai, a cikin kasar.
Daga dalilan gamewar saƙonsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - cewa Nasaran Najran sun ƙi yin Mubahala (tsineneniya) da shi, kuma sun yarda su ba shi jizya alhali su suna ƙasƙantattu; dan saninsu cewa shi annabi ne.
Daga dalilan gamewar saƙonsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - musuluntar mafi yawa daga maluman Yahudawa da masu bauta cikin Nasara, kai dubunnan waɗanda aka karkato da zukatansu zuwa musulunci daga mazowa littafi ne (Yahudawa ne da Nasara). Daga dalilan gamewar saƙon sa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - cewa shi ya yaƙi Rumawa, kuma ya umarci sahabbansa da yaƙar Farisa da Rumawa a bayansa.
Daga dalilan gamewar saƙonsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - shi ya yi wa Suraƙatu alƙawarin cewa shi zai ɗaura mundayen Kisra, sai ya ɗaurasu a khalifancin Umar - Allah Ya yarda da shi -.
Kuma muna sani na sakankancewa cewa Allah hikimarSa ta hukunta cewa Yana shiryar da wanda ya so da falalarSa, kuma Ya na ɓatar da wanda ya ga dama da adalcinsa, kamar yadda hikimarsa ta hukunta ya zama kowane annabi yana da maƙiyi, kuma ya zama akwai taimakekeniya akan ƙarya da haduwar maganganunsu tsakani waɗannan maƙiyan, maganganun shugabanni akowace al'umma mai kama da juna ne: wani lokaci suna cewa: Lallai shi matsafi ne ko boka ko maƙaryaci. Wani lokaci kuma suna musun a ce ya zo musu da wata aya, wani lokaci kuma suna da'awar cewa yana ƙirƙirar ƙarya ga Allah, wani lokaci kuma suna siffanta shi da hauka, ya nesanta ga manzannin Allah - aminci ya tabbata agare su - alhali su sun fi mutane cikar hankula kuma sunfisu tsarkin zukata. Wani lokaci kuma suna neman girmama abinda suke kiransu zuwa gare shi na kira zuwa bautar Allah Shi kaɗai, wani lokaci kuma suna kin karbar da'awarsa; domin cewa shi mutum ne, wani lokaci kuma suna neman su da al'amuran da ba sa cikin ikon halitta - dan girman kai da tsaurin kai - hakika sun nemi annabi muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bubbugo da ruwa daga kasa, ko ya kasance yana da aljani ko ya fado musu da sama fadowa, ko ya zo musu da Allah da mala'iku, ko ya hau sama, kuma ya sauko musu da wani littafin, kuma suna cewa mabiyansu: kada su saurari wannan AlKur'anin ku watsar da shi, wani lokaci kuma suna fuskantar manzo da karya da cewa mutum ne yake koyar da shi, abinda yake zo masa ba wahayi ne daga Allah ba.
Sukan juyawa manzo baya; domin waɗanda ke binsa su ne raunana, wani lokaci suna yi wa manzanni izgili, wani lokaci kuma suna yaudarar manzo, suna kwaɗayi a jawosu ko karkata garesu, wani lokaci kuma da aibatawa da abinda mai tsaurin kai ya sani cewa shi maƙaryaci ne a cikin maganarsa, kamar aibatawar Fir'auna ga (Annabi) Musa da kafirci.
Wani lokaci kuma shugabannin suna barazana ga annabi da cewa za’a fitar da shi daga garin, kafiran Kuraishawa sun yi wa annabinmu Muhammad da wanda ke tare da shi da Banu Hashim takunkumi a kwarin (Makkah) shekara uku, suka fitar da shi daga garinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, mutanen (Annabi) Ibrahim - aminci ya tabbata agare shi - sun yi ƙoƙarin ƙona shi da wuta, sai Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya tsiratar da shi, Banu isra'ila sunyi ƙoƙarin kashe annabawa, kai sun kashe waɗanda suka kashe...
Wannan ita ce ɗabi'ar masu girman kai ga manzanni, kuma wannan ita ce sunna mai gudana wacce manyan (gari) suke bin ta a cikin kowace al'umma tare da masu gyara.
BABIN IMANI DA MANZANNI - TSIRA DA AMINCI YA TABBATA AGARE SU -
Imani da manzanni - aminci ya tabbata agare su - shi ne rukuni na huɗu daga rukunan imani, Allah -sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Manzo ya yi imani da abin da aka saukar daga Ubangijinsa zuwa gare shi hakanan muminai ma kowa ya yi imani da Allah da mala'ikunSa da littattafanSa da manzanninSa ba mu bambanta tsakanin kowa daga manazanninSa} [al-Baƙara: 285], Kuma Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya ce: {Ba wai juya fuskoki bangaren gabas ko yamma shi ne biyayayya da ɗa'a ba, amma aikin ɗa'a shi ne wanda ya yi imani da Allah da ranar lahira da mala'iku da littafi da annabawa} [al-Baƙara: 177], Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance wata rana ya fito wajen mutane, sai wani mutum ya zo masa, sai ya ce: Ya manzon Allah, menene imani? ya ce: "Ka yi imani da Allah, da mala'ikunSa, da littafinSa, da haɗuwa daShi, da manzanninSa, kuma ka yi imani da tashin ƙarshe". (Bukhari ne ya fitar da shi (4777), da Muslim (9), da Ibnu Majah (64).)
Muna imani cewa tushen Da'awar manzanni - aminci ya tabbata agare su - shi ne sanin Allah - Maɗaukakin sarki - da sunayenSa da siffofinSa da ayyukanSa, kuma cewa su an aikosu da tauhidi, kuma sun yi kira zuwa butar Allah Shi kaɗai da barin bautar wanda baShi ba, Allah Maɗaukakin sarki ya ce: {Kuma ba Mu aiki wani Manzo ba a gabãninka fãce Munã yin wahayi zuwa gare shi, cẽwa "Lalle ne Shi, bãbu abin bautãwa fãce Nĩ, sai ku bauta Mini} [al-Anbiya'a: 25], kuma kowane annabi ya cewa mutanensa: {Ku bautawa Allah ba ku da wani abin bauta da gaskiya wanda ba shi ba shin bakwaji tsoronSa ba} [al-A'araf: 65]. Annabawa da manzanni su ne mafi cikar mutane a tauhidi da imani, kuma su ne suka fi kowa sanin Mahalicci - tsarki ya tabbatar amSa Ya ɗaukaka -
Kowane annabi ya kira mutanensa zuwa asali biyu masu girma, sune: Bautar Allah Shi kaɗai, da imani da ranar lahira, da abinda Allah Ya tanadar na ni'ima ga masoyanSa, da azaba ga maƙiyanSa, (Allah) Maɗaukakin sarki Ya ce: {Lalle ne, haƙĩƙa Mun aika Nũhu zuwa ga mutãnẽnsa, sai ya ce: "Yã mutãnẽna! Ku bauta waAllah! Bã ku da wani abin bautãwa waninSa. Lalle ne nĩ, inã yimuku tsõron azãbar wani Yini mai girma} [al-A'araf: 59], kuma sha'aninSa ya ɗaukaka Ya ce: {Kuma zuwa ga Madyana (Mun aika) ɗan'uwansu Shu'aibu. Ya ce: "Ya Mutãnena! Ku bauta wa Allah. Ba ku da wani abin bautãwa fãce shi kuma kada ku rage mũdu da sikẽli. Lalle nĩ, inã ganin ku da wadãta. Kuma lalle inã ji muku tsõron azãbar yini mai kẽwayẽwa} [Hud: 84], Kuma Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya ce: {Kuma ka ambaci ɗan'uwan Ãdãwa a lõkacin da ya yi gargaɗi ga mutãnensa, a Tuddan Rairayi, alhãli kuwa waɗansu mãsu gargaɗi sun shũɗe agaba gare shi da bãya gare shi (da cẽwa) "Kada ku bauta wa kõwa fãce Allah. Lalle nĩ inã tsõrata muku azãbar yini mai girma} [al-Ahƙaf: 21].
Kuma muna imani cewa annabawa - aminci ya tabbata agare su - sun haɗu a babban tushen da suka yi kira zuwa gare shi, dukkaninsu sun yi kira zuwa ga imani da Allah da mala'ikunSa da littattafanSa da manzanninSa da ranar lahira, da imani da ƙaddara alherinta da sharrinta, kuma dukkaninsu sun yi kira zuwa tushen ibadu, kamar sallah, da zakka, da azimi, da hajji, da tushen kyawawan ɗabi'u, kuma sun yi hani game da tushen ɗabi'u ababen zargi, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Ya sahar'anta muku, game da Addini, abin da ya yi wasiyya da shi ga (annabi) Nuhu da abin da muka yi wahayi da shi zuwa gare Ka, da abin da muka yi wasiyya da shi ga (annabi) Ibrahim da (annabi) Musa da (annabi) Isa cewa ku tsaida addini kada ku rarraba a cikinsa} [al-Shura:13]. Annabawa - aminci ya tabbata agare su - sun haɗu a tushe, amma shari'ar da suka yi kira zuwa garesu to sun banbanta a cikin hukunce-hukuncen su da rarrabe-rarrabensu, Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Kuma mun saukar maka da littafi da agskiya mai gasgatawa ne ga abinda ke gabansa na littafi (AtTaura da Linjila) da mai rinjaye ne akansa, to sai ka yi hukunci a tsakaninsu da abinda Allah Ya saukar kada ka bi soye-soyen zukatan su daga abinda ya zo maka na gaskiya kowanne mun sanya daga gareku shari'a da hanya (ta binta)} [al-Ma'ida: 48].
Kuma muna imani cewa imani yana wajaba da dukkanin annabawa - aminci ya tabbata agare su - da gasgatasu a dukkan abinda suka bada labari da shi na gaibu, da yi musu biyayya a cikin abinda suka yi umarni da shi, da hanuwa daga dukkan abinda suka yi hani daga gare shi, da son su da girmama su da koyi da su, da yi musu shaida cewa sun isar da saƙo kuma sun bada amana, sun yi nasiha ga Allah da kuma bayinSa, kuma sun yi Jihadi sabo da Allah makurar Jihadinsa. Kuma aiki da shari'ar manzo yana wajaba akan dukkanin al'ummar da aka aiko mata manzon, kuma yana wajaba akan wannan al'ummar - al'ummar (Annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - daga aljanu da mutane yin aiki da shari'ar cikamakin annabawa da manzanni (annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ; domin shi an aiko shi ne zuwa ga dukkanin aljanu da mutane.
Dukkan annabawa da manzanni - aminci ya tabbata agare su - sun zo ne dan fitar da mutane daga duffan kafirci da shirka da jahilci, koda sun kasance a cikin ɗaukaka ta duniya da sarauta da ƙarfi da tsanani da noma da kanfanoni, Allah Maɗaukakin sarki Ya faɗa a cikin sha'anin (annabi) Musa - aminci ya tabbata agare shi: {Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun aika Mũsã game, da ãyõin Mu cẽwa, "Ka fitar da mutãnenkadaga duhu zuwa ga haske. Kuma ka tunar musu da kwãnukan (masĩfun) Allah." Lalle ne a cikin wancan akwai ãyõyi dõmin dukan mai yawan haƙuri, mai gõdiya} [Ibrahim: 5], kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Shin, kunã yin ginin sitadiyo a kõwane tsauni ne, kunã yin wãsa? * Kuma kunã riƙon matsãrar ruwa, tsammãninku, ku dawwama? * Kuma idan kun yi damƙa, sai ku yi damƙar kunã mãsu tanƙwasãwa} [al-Shu'araa:128-130], kuma Maɗaukakin sarki Ya ce: {Shin, kuma ba su yi tafiya ba, a cikin ƙasã dõmin su gani yadda aƙibar waɗanda ke a gabãninsu ta kasance? Sun kasance mafiya ƙarfi daga gare su kuma suka nõmi ƙasa suka rãya ta fiye da yadda suka raya ta, kuma manzanninsu suka je musu da hujjoji bayyanannu. Sabo da haka Allah ba Ya yiwuwa Ya zãlunce su, amma kansu suka kasance sunã zãlunta} [Rum: 9].
Kuma muna imani cewa Allah Ya aikosu suna masu albishir da aljanna kuma masu gargaɗi da wuta; dan kada mutane su zama suna da wata hujja akan Allah bayan manzanni, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Manzanni mãsu bãyar da bushãra kuma mãsu gargaɗi dõmin kada wata hujja ta kasance ga mutãne a kan Allah bãyan Manzannin. Kuma Allah yã kasance Mabuwãyi, Mai hikima} [al-Nisa'a: 165].
Kuma muna imani cewa Allah Ya aiko manzo a kowace al'umma, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Tabbas mun aiko cikin kowace al'umma wani manzo da ya isar da sakon ku bautawa Allah kuma ku nesanci dagutu (duk wani abin bauta da ba Allah ba} [al-Nahl: 36], Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Banu isra’ila sun kasance Annabawa ne suke shugaban tarsu, aduk sanda annabi ya rasu wani annabine ne zai maye gurbinsa, ku saurara ba wani annabi a bayana". (Bukhari ne ya fitar dashi (3455), da Muslim (1842), da Ibnu Majah (2871).) kai haƙiƙa Allah - Maɗaukakin sarki - Ya bamu labarin cewa Ya aiko da annabawa uku zuwa wata alƙarya daga alƙaryu a lokaci ɗaya, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {A lõkacin da Muka aika (Manzannin) biyu zuwa gare su, sai suka ƙaryata su, sa'an nan Muka ƙarfafa (su) da na uku, sai suka ce: "Lalle mũ, Manzanni ne zuwa gare ku} [Y. S̃:14].
Wanda muka san sunansa daga cikinsu to imani da shi ya zama dole, wanda kuma bamu san sunansa daga cikinsu ba to mu yi imani da shi a dunƙule, to imani yana wajaba da dukkanin annabawa da manzanni - aminci ya tabbata agare su -, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Da wasu Manzanni, haƙĩƙa, Mun bã da lãbarinsu a gare ka daga gabãni, da wasu manzanni waɗanda ba Mu bã da lãbãrinsu ba a gare ka, kuma Allah Yã yi magana da Mũsã, magana sõsai} [al-Nisa'a: 164], kuma Maɗaukakin sarki Ya ce: {Manzon Allah yã yi ĩmãni da abin da aka saukar zuwa gare shi daga Ubangijinsa, da mũminai. Kõwanensu yã yi ĩmãni da Allah, da mala'ikunSa, da littattafanSa, da manzanninSa. Bã mu rarrabẽwa a tsakãnin daya daga manzanninSa. Kuma (mũminai) suka ce: "Mun ji kuma mun yi dã'a; (Muna nẽman) gãfararKa, yã Ubangijinmu, kuma zuwa a gare Ka makõma take } [al-Baƙara: 285], Maɗaukakin sarki Ya ce: {Ka ce: "Mun yi ĩmãni da Allah kuma da abin da aka saukar mana da abin da aka saukar wa Ibrãhĩma da Isma'ĩla da Is'hãƙa da Yãƙũba da jĩkõki, da abin da aka bai wa Mũsã da ĩsã da annabãwa daga Ubangijinsu, bã mu bambantãwa a tsakãnin kõwa daga gare su. Kuma mũ, zuwa gare Shi mãsu sallamãwa ne} [Aal- Imran: 84].
Kuma muna imani cewa Allah Yana aiko manzanninSa ga wanda Ya so cikin bayinSa daidai da abinda hikimarSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - take hukuntawa, Allah sha'aninSa ya buwaya - Ya ce: {Kuma da Mun so, haƙĩƙa dã Mun aika da mai gargaɗi a ciƙin kõwacce alƙarya} [Furƙan: 51], kuma Allah - sha'aninSa ya buwaya Ya ce: {Sannan kuma Muka aika da ManzanninMu jẽre a kõda yaushe Manzon wata al'umma ya jẽ mata, sai su ƙaryata shi, sabõda haka Muka biyar da sãshensu ga sãshe, kuma Muka sanya su lãbãrun hĩra. To, nĩsa ya tabbata ga mutãne (waɗanda) bã su yin ĩmãni!} [al-Mua'Minun: 44]. Babu mai bibiyar hukuncinSa, Yana aikata abinda Yake so, kuma Ya na zaɓa, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma Ubangijinka Yanã halitta abin da Yake so kuma Yake zãɓi. Zãɓi bai kasance a gare su ba. Tsarki ya tabbata ga Allah, kuma (Allah) Ya ɗaukaka daga barin abin da suke yi na shirka} [al-Kasas: 68].
Wanda ya kafircewa wani annabi ɗaya; to haƙiƙa ya kafirta da dukkanin annabawa - aminci ya tabbata agare su -; saboda haka ne Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Mutãnen Nũhu sun ƙaryata Manzanni} [al-Shu'araa: 105]. Waɗannan ayoyin kamar faɗinSa ne - Allah Maɗaukakin sarki -: {Kowannensu ya ƙaryata manzanni sai ƙyacewa Ta ta tabbata} [Qaaf: 14].
Kuma muna imani cewa annabta baiwa ce ta Allah, kuma rahama ce ta Ubangiji Yana bada ita ga wanda Ya so daga bayinSa, Allah Yana zaɓa daga mala'iku haka daga mutane, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Allah nã zãɓen Manzanni daga malã'iku kuma daga mutãne. Lalle Allah, Mai ji ne, Mai gani} [al-Hajji: 75], Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya ce: {Allah shi ne mafi sanin inda Yake ajiye manzancinSa} [al-An'am: 124]. Annabcta ba kokariba ce, kuma bawa ba ya samunta ta hanyar ƙoƙarin biyayya, ko da tsarkake rai da mujahadah da tsarkake zuciya da tsaftatce dabi’u da tace su.
Kuma muna imani cewa annabwa da manzanni - aminci ya tabbata agare su - da fifiko a tsakaninsu, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Waɗancanaka manzanni Mun fifita sashinsu akan sashi daga cikinsu, akwai waɗanda Allah Ya yi magana (da su), kuma Ya ɗaukaka sashinsu a darajoji, Mun bawa (annabi) Isa ɗan Maryam hujjoji kuma Mun ƙarfafe shi da tsarkin Ruhi} [al-Baƙara: 253], Kuma mafifitan annabawa su ne Ulul Azmi, su ne waɗanda aka ambata a cikin faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Kuma a lõkacin da Muka riƙi alkawarin Annabawa daga gare su, kuma daga gare ka, kuma daga Nũhu da Ibrãhĩm da Mũsa da kuma Ĩsã ɗan Maryama, kuma Muka riƙi wani alkawari mai kauri daga gare su} [al-Ahzab: 7], kuma Ya yi nuni gare su a cikin faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Ka yi haƙuri kamar yadda Ulul Azmi daga manzanni suka yi haƙuri} [al-Ahƙaf: 35]. Kuma mafiftan Ulul Azmi su ne badada biyu: (Annabi) Ibrahim da (Annabi) Muhammad - aminci ya tabbata agare su -, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma wãnene ya fi kyau ga addini daga wanda ya sallama fuskarsa ga Allah, alhãli kuwa yanã mai kyautatawa kuma ya bi aƙidar Ibrãhĩm, Yanã mai karkata zuwa ga gaskiya? Allah Yã riƙi Ibrãhĩm badãɗayi} [al-Nisa'a: 125]. Daga Jundub - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Na ji annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - kafin ya rasu da kwana biyar, alhali shi yana cewa: "Lallai ni ina barranta ga Allah ya zama ina da wani badadi daga cikinku, domin cewa Allah haƙiƙa Ya riƙeni badadi kamar yadd da Ya riƙi (annabi) Ibrahim badaɗayi". (Muslim ne ya fitar da shi (532).)
Kuma muna shaida cewa annabinmu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - shi ne mafificin manzanni da Annabawa, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Ni ne shugaban 'ya'yan Adam a ranar Alkiyama ". (Muslim ya fitar da shi (2278), da Abu Dawud (4673).)
Kuma annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi hani daga fifitawa tsakanin annabawa idan ta fuskar ƙabilanci ne da ta'assubanci ko tauye daraja, Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Wasu mutane biyu suka zagi junansu: Wani mutum daga Musulmai da wani mutum daga Yahudawa, Musulmin ya ce: Na rantse da wanda Ya zaɓi (annabi) Muhammad akan talikai, sai Bayahudan ya ce: Na rantse da wanda Ya zaɓi Musa akan talikai, sai Musulmin ya ɗaga hannunsa a nan take, sai ya mari fuskar Bayahudan, sai Bayahuden ya tafi gurin annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, sai ya ba shi labarin abinda ya faru na al'amarinsa, sai annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kira Musulmin, sai ya tambaye shi game da hakan, sai ya ba shi labari, sai annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Kada ku fifitani akan Musa; domin mutane zasu suma a ranar AlKiyama, sai in suma tare da su, sai in zama farkon wanda zai farfaɗo, sai ga Musa yana riƙe da gefen Al'arshi, ban sani ba shin yana daga cikin waɗanda suka suma, sai ya farka kafin ni ko ya kasance daga waɗanda Allah Ya togance?", (Bukhari ne ya fitar da shi (2411), da Muslim (2373), da Abu Dawud (4671), da Tirmizi (3245), da Ibnu Majah (4274).) A wani lafazin: Sai Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi fushi har aka gane fushinsa a fuskarsa, sannan ya ce: "Kada ku fifita tsakanin annabawan Allah". (Muslim ne ya fitar da shi (2373).)
Kamar yadda Allah Ya riƙi (Annabi) Ibrahim da (Annabi) Musa - amnici ya tabbata agare su - badaɗayu, to haƙiƙa Allah Ya zaɓi (Annabi) Musa - aminci ya tabbata agre shi - kuma Ya zaɓe shi akan mutane da saƙonSa da kuma zancenSa da shi, duk da annabinmu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya samu ɗaukakar martabar baɗayantaka, to haƙiƙa Ubangijinsa ya yi magana da shi ta bayan shamaki a daren da aka yi Isra'i da shi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, Maɗaukkain sarki Ya ce: {Sa'an nan ya yi wahayi zuwa ga bãwan Allah (Muhammadu) da abin da ya faɗa (masa)} [al-Najm: 10], sai annabinmu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance ya tara tsakanin ɗaukakar badaɗayantaka, da ɗaukakar zance da shi.
Muna imanin cewa annabawa sun fi mutane, kuma wani ɗaya bai isa ya kai matsayin annabi ba, ba waliyyi ba, ko waninsa, kuma fifita wani ɗaya daga mutane akan wani daga annabawa ba ya halatta, manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Ba ya kamata ga wani ya zama ya fi (annabi) Yunusa ɗan Matta". (Bukhari ne ya fitar da shi (4804).)
Kuma muna imanin cewa Allah Bai aiko wani manzo ba sai namiji, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma ba Mu aiko a gabaninka ba sai mazajen da ake musu wahayi} [al-Anbiyaa: 7].
Kuma muna sanin cewa manzanni da annabawa - aminci ya tabbata agare su - su ne tsarkakan halitta, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Allah nã zãɓen Manzanni daga malã'iku kuma daga mutãne. Lalle Allah, Mai ji ne, Mai gani} [al-Hajji: 75]. Kuma sune mafi cikar mutane a addinsu da hankulansu da ɗabi'unsu, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Ka ce kaɗai ni mutum ne irinku ana yi mini wahayi} [al-Kahf: 110]. Su mutane ne kamar sauran mutane, sai dai ana yi musu wahayi, kuma su ma'asumai ne a cikin abinda suke isarwa daga al'amarin Allah, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce Yana mai bada labari game da annabinSa kuma badaɗayinSa (annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: {Kuma bã ya yin magana daga son zuciyarsa * (Maganarsa) ba ta zamo ba, fãce wahayi ne da ake aikõwa * (Malã'ika) mai tsananin ƙarfi ya sanar da shi} [al-Najm: 3-5].
Idan annbi ya yi ijtihadi a abinda ba'a yi masa wahayi da wani abu ba, kuma bai dace ba; to Allah baYa tabbatar da shi akan ijtihadinsa, kai wahayi yana sauka gare shi dan daidaita shi, kamar yadda yake a cikin faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Bã ya kasancewa ga wani annabi, kãmammu su kasance a gare shi sai (bãyan) yã zubar da jinainai a cikin ƙasa. Kunã nufin sifar dũniya kuma Allah Yanãnufin Lãhira. Kuma Allah ne Mabuwãyi, Mai hikima} [al-Anfal: 67]. Da faɗinSa - yabonSa ya ɗaukaka -: {Yã kai Annabi! Don me kake haramta abin da Allah Ya halatta maka, kanã nẽman yardar mãtanka, alhãli kuwa Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai} [al-Tahrim: 1].
Tare da cewa suna da matsayi babba da daraja maɗaukakiya da matsayi abin yabo a duniya da lahira, to su ba sa mallakawa kansu wani abin amfani ko cuta, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Ka ce: "Ba na mallaka wa kaina wata cũta, haka kuma wani amfãni, sai abin da Allah Ya so. Ga kõwace al'umma akwai ajali, idan ajalinsu ya zo, to, bã zã su yi jinkiri daga gare shi ba, kõ dã sã'ã guda, kuma bã zã su gabãta ba} [Yunus: 49].
Idan sun kasance ba sa mallakawa kansu wani amfani ko cuta to rashin mallakawa waninsu shi ne ya fi, Allah Maɗaukakin sarki Ya faɗa a sha'anin annabinSa kuma badaɗayinSa Muhammada - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: {Bãbu kõme a gare ka game da al'amarin (shiryar da su banda iyar da manzanci). Ko Allah Ya karɓi tũbarsu, kõ kuwa Ya yimusu azãba, to lalle ne sũ, mãsu zãlunci ne} [Aal- Imran: 128], kuma Ya faɗa a sha'anin (annabi Isa) Masihu - aminci ya tabbata agare shi -: {Ka ce waya isa ya mallaki wani abu daga Allah idan Ya yi nufin Ya halaka Masihu ɗan Maryam da babarsa da waɗanda ke cikin ƙasa baki ɗaya} [al-Ma'ida: 17].
Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya cewa baffansa da 'yarsa Faɗimatu - Allah Ya yarda da ita -: "Ya ku jama'ar Kuraishawa - ko wata kalma kwatankwaciyarta - ku ƙwaci kanku, ba na iya wadatar muku da komai daga Allah, ya ku 'ya'yan Abdu Manafi bana iya wadatar muku da komai daga Allah, Ya Abbas ɗan Abdul Muɗɗlib bana iya wadatar maka komai daga gurin Allah, Ya ke Safiyya Yakumbon (Gwaggon) manzon Allah bana iya wadatar miki komai daga Allah, ya ke Faɗimatu 'yar Muhammad ki tambayeni abinda kike so daga dukiyata ba zan iya wadatar miki komai daga Allah ba". (Bukhari ya fitar da shi (2753), da Muslim (206), da Tirmizi (3185), da Nasa'i (3646).) Idan sun kasance basa mallakar komai na amfani ko cuta ga kawunansu ko ga wasunsu - a halin rayuwarsu - to su a wannan lokacin rashin mallakar wani amfani ko cuta ga wasunsu bayan mutuwarsu shi ne ma ya fi.
Kuma muna imani cewa su basa sanin gaibu sai dai gwargwadan abinda Allah Ya tsinkayar musu da shi, kuma Ya yi musu izini a cikinsa, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Ka ce bazan faɗa muku cewa ina da taskokin Allah ba, kuma bana sanin gaibu, kuma bazan ce muku ni mala'ika bane ba wani abu nake biba sai abinda aka yi mini wahayi} [al-An'am: 50], kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Ka ce: "Bã ni mallaka wa raina wani amfãni, kuma haka ban tunkuɗe wata cũta, fãceabin da Allah Ya so. Kuma dã na kasance inã sanin gaibi, dã lalle ne, nã yawaita daga alhẽri kuma cũta bã zã ta shãfe ni ba, nĩ ban zama ba fĩce mai gargaɗi, kumamai bãyar da bishãra ga mutãne waɗanda suke yin ĩmãni} [al-A'araf: 188], kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Shi ɗai ne Masanin fake sabõda haka, bã Ya bayyana gaibinSa ga kowa * Fãce ga wanda Yã yarda da shi, wato wani manzo sa'an nan lalle ne, zai sanya gãdi a gaba gare shi da bãya gare shi} [al-Jinn: 26-27].
Annabawa da manzanni - aminci ya tabbata agare su - suna bautawa Allah ne dan tsoro da kwaɗayi, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Lalle ne su sun kasance suna gudun tsere zuwa ga ayyukan alheri, kuma suna kiranMu dan kwadayi da fargaba. Kuma sun kasance masu kankar da kai gare Mu} [al-Anbiya'a: 90], suna neman wasila (kusanci) zuwa gare shi, kuma suna neman kusanci zuwa gare shi - tsarki ya tabbaatr maSa, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Waɗancan, waɗanda suke kiran, sunã nẽman tsãni zuwa ga Ubangijinsu. Waɗanne ne suke mafĩfĩta a kusanta? Kuma sunã fãtan sãmun rahamarSa, kuma sunã tsõron azãbarSa. Lalle ne azãbar Ubangijinka ta kasance abar tsõro ce} [al-Isra'a: 57].
Annabawa da manzanni - aminci ya tabbata agare su - suna samun abinda mutane suke samu na bala'i da rashin lafiya da mutuwa, Allah Maɗaukain sarki Ya ce: {Lalle kai mai mutuwa ne, kuma su mã lalle mãsu mutuwa ne} [al-Zumar: 30], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya faɗa Yana Mai bada labari game da (annabi) Ayyuba cewa shi cuta ta same shi: {Kuma da Ayyũba a sã'ad da ya yi kiran Ubangijinsa, (ya ce:) "Lalle nĩ, cũta ta shãfe ni, alhãli kuwa Kai ne Mafi rahamar mãsu rahama} [al-Anbiyaa: 83]. kuma suna da mata da zuriya, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Haƙiƙa Mun aiko manzanni a gabaninka kuma Mun sanya musu mata da zuriya} [al-Ra'ad: 38]. kuma suna cin abinci kuma suna shiga cikin kasuwanni, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma baMu aiko a gabaninka daga manzanni ba sai cewa su suna cin abin ci kuma suna tafiya a cikin kasuwanni} [al-Furƙan: 20]. Kuma baƙin ciki yana samunsu, kamar yadda Allah - Maɗaukakin sarki - Ya faɗa Yana mai bada labari game da (Annabi) Ya’akub - aminci ya tabbata agare shi -: {Kuma ya jũya daga gare su, kuma ya ce: "Yã baƙin cikina a kan Yũsufu!" Kuma idãnunsa suka yi fari sabõda huznu sa'an nan yanã ta haɗẽwar haushi} [Yusuf: 84]. A cikin "Bukhari da Muslim' a cikin labarin mutuwar ɗan 'yar manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: Lokacin da ya zauna sai aka miko masa shi, sai ya zaunar da shi a ƙirjinsa, alhali numfashin yaron yana kaikawo, sai idaniyar manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - suka zubar da hawayem sai Sa'ad ya ce: Menene wannan ya manzon Alla? ya ce: "Wannan wata rahama ce wacce Allah Yake sanyata acikin zukatan wanda Ya so daga bayinSa, kaɗai Allah Yana jin ƙan masu jin ƙai ne daga bayinSa". (Bukhari ne ya fitar dashi (6655), da Muslim (923), da Abu Dawud (3125), da Nasa'i (1868), da Ibnu Majah (1588).) (Ma'anar ji'is: Wato ya firgita, ya firgita, shi abin firgitarwa ne. Fathul Bari (8/722), da al-Nihaya fi Garibul Hadis (1/232).)
Kuma muna sanin cewa su haƙiƙi su yi wa halitta nasiha, kuma sun bada amana, sun isar da saƙonnin Ubanigijinsu, ba ya cutar da su cewa wasu daga mabiya basu amsa musu ba, ko kuma cewa manya sun yi musu girman kai, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "An bijiro min da al'ummu, sai na ga annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a tare da shi akwai wasu 'yan mutane, da annabi a tare da shi akwai mutum ɗaya da mutum biyu, da annabi babu kowa tare da shi". (Bukhari ya fitar da shi (5705), da Muslim (220), da Tirmizi (2446).)
Kuma muna imani cewa Allah - Maɗaukakin sarki - haƙiƙa Ya ɗaga (annabi Isa) Masihu - aminci ya tabbata agare shi - a raye lokacin da mutanensa suka so kashe shi, Allah Maɗaukkain sarki Ya ce: {To, a lõkacin da Ĩsa ya gane kãfirci daga gare su, sai ya ce: "Su wãne ne mataimakãna zuwa ga Allah?" Hawãriyãwa suka ce: "Mu ne mataimakan Allah. Mun yi ĩmani da Allah. Kuma ka shaida cẽwa lalle ne mu, mãsu sallamãwa ne * "Yã Ubangijinmu! Mun yi imãni da abin da Ka saukar, kuma mun bi ManzonKa, sai Ka rubũta mu tãre da mãsu shaida * Kuma (Kãfirai) suka yi mãkirci, Allah kuma Ya yi musu (sakamakon) makircin, kuma Allah ne Mafi alhẽrin mãsu sãka wamãkirci} [Aal- Imran: 52-54]. kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma lalle shĩ, haƙĩƙa, wani ilmi ne na Sa'a, sabõda haka, kada ku yi shakka a gare ta, kuma ku bĩ Ni. Wannan ita ce hanya madaidaiciya} [al-Zukhruf: 61], Daga Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su -, da Mujahid, da Katada: Cewa abin nufi da ita (ayar): Saukar (Annabi) Isa ɗan Maryam - aminci ya tabbata agare shi -. (al-Dabari ne ya fitar da shi a cikin Tafsiri (20/631-633).)
Kuma ambatanSa ya ɗaukaka Ya ce: {Kuma bãbu kõwa daga Mutãnen Littafi, fãce lalle yanã ĩmãni da shi a gabãnin mutuwarsa, kuma a Rãnar ¡iyãma yana kasancẽwa mai shaida, a kansu} [al-Nisa'a: 159]. Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su - ya ce: FaɗinSa: {Kafin mutuwarsa} wato: Kafin mutuwar (Annabi) Isa ɗan Maryam". (Tafsirin Dabari (9/380).)
Kuma muna imani cewa zai sauka a ƙarshen zamani yana mai hukunci mai adalci, daga Abu huraira - Allah Ya yarda da shi - cewa shi ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Na rantse da wanda raina yake a hannunSa, Ibnu Maryam (Annabi Isa) ya kusa ya sauka a cikinku yana mai hukunci mai adalci, sai ya karya gicciyayye (cross), ya kashe alade, ya sarayar da jizya, dukiya ta yawaita har babu wanda zai karɓeta". (Bukhari ne ya fitar da shi (2222), da Muslim (155), da Abu Dawud (4324), da Tirmizi (2233), da Ibnu Majah (4078).)
A cikin labarin saukar Masihu - aminci ya tabata agare shi -: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Alhali yana hakan sai Allah Zai aiko Masihu (annabi Isa) ɗan maryam, sai ya sauka a farar manara a gabashin Dimashƙa, tsakanin kayan ado biyu, (Wato a cikin tsagi biyu, ko kayan ado biyu, aka ce tufafi al-Mahrud: Wanda aka rina da wars da kuma za'afaran. al-Nihaya fi Garibul Hadis (5/258).) Yana mai ɗora kafaɗunsa biyu akan fukafukan Mala'iku biyu, idan ya sunkuyar da kansa sai ya ɗigar da ruwa, idan kuma ya ɗagashi sai wasu zinarai kamar lu'ulu'u su gangaro daga gare shi...". (Muslim ne ya fitar dashi (2937), da Abu Dawud (4321), da Tirmizi (2240), da Ibnu Majah (4075).)
BABIN AYOYIN ANNABAWA DA DALILAN ANNABTARSU - AMINCI YA TABBATA AGARE SU -
Muna imani cewa Allah Ya ba kowane annabi a ayoyi da hujjoji abinda a irinsu ne mutum zai yi imani, daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi -: Tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Babu wani annabi daga cikin annabawa face an ba shi daga cikin ayoyi waɗanda mutane za su yi imani da shi, ni kuma abinda aka bani shi ne wahayi, Allah Ya yi mini wahayi ina fatan na fisu yawan mabiya ranar AlKiyama". (Bukhari ne ya fitar da shi (7274), da Muslim (152).)
Kuma muna imani cewa Allah bai aiko wani annabi ba sai a tare da shi akwai ayar da take nuni akan gaskiyarsa, mun santa ko bamu santa ba, haƙiƙa Allah Ya ambata mana wasu jumloli daga garesu a cikin AlKur'ani mai girma, kuma muna sanin cewa a can akwai ayoyi masu yawa Allah Ya ƙarfafi manzanninSa da suka gabata da su, Allah Bai ambata mana su ba, kamar a cikin faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Kuma waɗanda suka kãfirta, kuma suka ƙaryatã, game da ãyõyinMu, waɗannan su ne abõkan wuta} [al-Ma'ida: 10], da faɗinSa - Maɗaukakin sarki: {Kamar al'ãdar mutãnen Fir'auna da waɗanda suke gabãninsu, sun kãfirta da ãyõyin Allah, sai Allah Ya kãma su da zunubansu. Lalle Allah ne Mai ƙarfi, Mai tsananin uƙũba} [Aal- Imran: 11]. Wani lokaci kuma Allah Yana ambatan ayoyi bayyanannu, kuma Yana ambatan hujja, kamar a cikin faɗinSa - yabonSa ya ɗaukaka -: {Kuma haƙĩƙa Mun aiki Mũsã da ãyõyinMu, da dalĩli bayyananne} [Hud: 96], da faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Ya ce: zamu ƙarfafa damuttsanka da ɗan uwanka kuma Zamu sanya hujja gareku ba za su iya kai wa zuwa gareku ba da ayoyinMu} [al-Kasas: 35], Ikramah ya ce; "Duk abinda ya zo a cikin AlKur’ani na Sulɗan to shi: Hujja ne". (Tafsirul al-Dabari (8/30) da (9/337).)
Kuma muna sani cewa ayoyi da hujjojin da Allah Ya ƙarfafi manzanninSa da annabawanSa - aminci ya tabbata agare su - da su masu yawa ne, mafi girman dalilai masu nuni akan gaskiyarsu shi ne abinda suka zo da shi na wahayi, kuma wahayin Allah ga annabawanSa da manzanninSa - aminci ya tabbata agare su -: Ko dai ya zama wahayi ba tare da tsani ba, kamar mafarki kamar faɗinSa -tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Yana mai bada labari game da (Annabi) Ibrahim - aminci ya tabbata agare shi - cewa shi ya ce: {Lokacin da ya isa aiki tare da shi, ya ce: "Ya ƙaramin ɗana! Lallai ni ina gani a cikin barci lallai ina yankaka} [al-Saafat: 102], ko manzon Ya ji zancen Allah - Mai girma da ɗaukaka - kai tsaye sai dai ta bayan shamaki, kamar yadda yake a cikin faɗinSa - yabonSa ya ɗaukaka -: {Ba ya kamata ga wani mutum Allah Ya yi magana da shi sai dai wahayi ko ta bayan shamaki} [al-Shura: 51], haka kamar a cikin zancen Allah da Ya yi da (Annabi) Musa - aminci ya tabbata agare shi - kamar yadda yake a cikin faɗinSa - sha'aninSa ya ɗaukaka -: {Ya ce: "Ya Mũsã! Lalle ne Nĩ, Nã zãɓe ka bisa ga mutãne da manzanciNa, kuma da maganãTa. Sabõda haka ka riƙi abin da Nã bã ka, kuma ka kasance daga mãsu gõdiya} [al-A'araf: 144], ko mala'ika ya yi magana da shi, kamar a cikin faɗinSa - Allah Maɗaukkain sarki -: {Ko Ya aiko wani manzo sai ya yi whayin abinda Ya so da izininSa} [Al-shura: 51].
Kuma muna sanin cewa daga mafi girman dalilai masu nuni akan gaskiyarsu shi ne abinda suke kira zuwa gare shi na tauhidi mai tabbata a cikin ɗabi'u, wanda hankula suka shaida akan kyawunsu, da abinda suka zo da shi na ilimi mai amfani, da aiki na gari, da shiriya da addinin gaskiya da adalci, Daga Ubaidullahi ɗan Abdullahi ɗan Abbas - Allah Ya yarda da su - ya ba shi labari ya ce: Abu Sufyan ya bani labari: "Cewa Hiraƙl ya ce masa: Na tambayeka me yake umartarku? sai ka riya: Cewa shi ya umarceku da sallah, da gaskiya, da kamewa, da cika alƙawari, da mayar da amana, ya ce: Wannan ita ce siffar annabi na". (Bukhari ya fitar da shi (2681), da Muslim (1773), da Tirmizi (2717).)
Najjashi ya ce lokacin da Ja'afar - Allah Ya yarda da shi - ya karanta masa farkon "Suratu Maryam": "Lallai wannan zancen da zancen da (Annabi) Musa ya zo da shi suna fita ne ta alkuki ɗaya". (Ishaƙ ɗan Rahuwaih ne ya fitar dashi (1835), da Ahmad (22498), da Ibnu Khuzaimah (2260), da al-Dahawi a cikin Sharhu Mushkilil Aasar (5598), da Abu Nu'aim a cikin al-Hilyah (1/115), da kuma cikin Dala'il al-Nubuwwah (194).)
Daga cikinsu akwai shaidar Allah ga manzanninSa cewa su suna kan gaskiya, kuma abinda suka zo da shi shi ne gaskiya, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Amma Allah Yanã shaida da abin da Ya saukar zuwa gare ka. Yã saukar da shi da saninSa. Kuma malã'iku sunã shaida. Kuma Allah Yã isa Ya zama shaida} [al-Nisa'a: 166], kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma waɗanda suka kãfirta sunã cẽwa: "Ba a aiko ka ba." Ka ce, "Allah Yã isa zama shaida a tsakãnina da tsakãninku da wanda yake a wurinsa akwai ilmin Littãfi} [al-Ra'ad: 43].
Daga mafi girman ayoyinsu: Wahayin da yake sauka gare su daga Allah, kuma mafi girman wahayi shi ne AlKur'ani mai girma ayar annabinmu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -. Wannan wahayin ba zai yi wu mutum ya zo da kwatankwacinsa ba; domin shi zancen Allah ne kuma wahayinSa ne, dan kuma abinda ke cikinsa na labaran gaibu, dan kuma abinda ke cikinsa na shiriya da haske da rahama da hikima.
Daga ayoyinsu bayyanannu: Hujjoji na hankali waɗanda Allah Yake ƙarar manzanninSa da annabawanSa - aminci ya tabbata agare su - da su, sai aka ƙure kafiri kuma ƙaryarsa ta kare kamar yadda yake a cikin faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Shin, ba ka gani ba zuwa ga wanda ya yi hujjatayya da Ibrãhĩm a cikin (al'amarin) Ubangijinsa dõmin Allah Yã bã shi mulki, a lõkacin da Ibrãhĩm ya ce: "Ubangijina Shi ne Wanda Yake rãyawa kuma Yana matarwa." Ya ce: "Nĩ ina rãyarwa kuma ina matarwa." Ibrãhĩm ya ce: "To, lalle ne Allah Yana zuwa da rana daga gabas: To, ka zo da ita daga yamma." Sai aka ɗimautar da wanda yakãfirta. Kuma Allah ba Ya shiryar da mutãne azzãlumai} [al-Baƙara: 258], da faɗinSa - yabonSa ya ɗaukaka kuma sunayenSa sun tsarkaka -: {To lalle ne, sũ maƙiya ne a gare ni, fãce Ubangijin halittu * Wanda Ya halitta ni, sa'an nan Yanã shiryar da ni * "Kuma Wanda Yake Shĩ ne Yake ciyar da ni, kuma Yanã shãyar da ni * Kuma idan na yi jiyya, to, Shĩ ne Yake warkar da ni * Kuma wanda Yake matar da ni, sa'an nan Ya rãyar da ni * Kuma wanda Yake inã kwaɗayin Ya gãfarta mini kurãkuraina, a rãnar sãkamako} [al-Shu'ara'a: 77-82], da faɗinSa game da (Annabi) Musa - aminci ya tabbata agare shi - cewa shi yacewa Fir'auna: {Ya ce: "Ubangijinmu Shi ne wanda Ya bai wa dukan kõme halittarsa, sa'an nan Ya shiryar} [Daha: 50], daga cikinsu akwai faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Dã waɗansu abũbuwan bautawa sun kasance a cikinsu (sama da ƙasa) fãce Allah, haƙĩƙa dã su biyun sun ɓãci. Sabõda haka tsarki ya tabbata ga Allah Ubangijin Al'arshi daga abin da suke siffantãwa} [al-Anbiya'a: 22], Da faɗinSa - yabonSa ya ɗaukaka -: {Allah bai riƙi wani abin haihuwa ba, kuma bãbu wani abin bautãwa tãre da Shi. Idan haka ne (akwai abin bautawa tare da Shi), lalle ne dã kõwane abin bautawar ya tafi da abin da ya halitta, kuma lalle ne, dã waɗansu sun rinjãya a kan waɗansu, tsarki ya tabbata ga Allah, daga abin da suke siffantãwa} [al-Mua'Minun: 91]. Waɗannan dalilan masu yawa ne sosai mun ambaci wasunsu a cikin babin Rububiyyah da Uluhiyya, saboda ayoyinsu ne labartawarsu da gaibun da Allah Yayi musu izini a cikin labartawarsu.
Daga ayoyinsu mai rinjayarwa: Tsiratar da annabawan da suka gabata - aminci ya tabbata agare su - da tsiratar da mabiyansu daga makircin maƙiyansu, da halakar da masu tsaurin kai masu girman kai, da tinatarwar Allah ga waɗanda aka kira da abinda Ya aikata da waɗanda suka gabata, kuma cewa sunnar Allah mai zarcewace, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya faɗa a farkon suratul Anbiya'u: {Sa'an nan kuma Muka gaskata musu alkawari; sai Muka tsẽrar da su da wanda Muke so, kuma Muka halakar da mãsu yawaitãwa} [al-Anbiya'a: 9], kuma a ƙarshenta Ya ce: {Kuma lalle haƙĩƙa Mun rubũta a cikin Littãfi baicin Ambato (Lauhul Mahfũz) cẽwa ƙasã, bayĩNa sãlihai, sunã gãdonta} [al-Anbiya'a: 105], kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Sun ƙaryata game da ãyõyinMu, dukansu sai Muka kãma su, irin kãmun Mabuwãyi, Mai ĩkon yi * Shin, kãfiranku ne mafi alhẽri daga waɗancan, ko kuwa kunã da wata barã'a a cikin littattafai?} [al-Kamar: 42-43]. A cikin "Suratul Shu'ara" duk lokacin da Allah Ya ambaci tsiratar da annabawan da suka gabata - aminci ya tabbata agare su - da halakar maƙiyansu Allah Yana biyewa kowanne labari daga waɗannan labaran da faɗinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: {Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba} [al-Shu'ara'a: 67], Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {To, idan sun bijire sai ka ce: "Nã yi muku gargaɗi ga wata tsãwa kamar irin tsãwar Ãdãwa da samũdãwa} [Fussilat: 13], Kuma Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Shin, kuma ba su yi tafiya ba, a cikin ƙasã dõmin su gani yadda aƙibar waɗanda ke a gabãninsu ta kasance? Sun kasance mafiya ƙarfi daga gare su kuma suka nõmi ƙasa suka rãya ta fiye da yadda suka raya ta, kuma manzanninsu suka je musu da hujjoji bayyanannu. Sabo da haka Allah ba Ya yiwuwa Ya zãlunce su, amma kansu suka kasance sunã zãlunta} [al-Rum: 9].
Daga ayoyinsu masu nuni akan annabcinsu: Cikar ɗabi'unsu da kyawun halayensu da ayyukansu da tarihinsu, da gaskiyar zantukansu daga abinda zai hana ƙarya tare da su, Allah Ya faɗa Yana Mai bada labari game da mutanen (Annabi) Salihu - aminci ya tabbata agare shi - cewa su sunce: {Suka ce: "Ya Sãlihu! Haƙĩƙa, kã kasance a cikinmu, wanda ake fatan wani alhẽri da shi a gabãnin wannan. Shin kana hana mu bauta wa abin da ubanninmu suke bauta wa? Kuma haƙĩƙa mũ, munã cikin shakka daga abin da kake kiran mu gare shi, mai sanya kõkanto} [Hud: 62], kuma Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Suka ce: "Yã Shu'aibu! Shin sallarka ce take umurtar ka ga mu bar abin da ubanninmu suke bautãwa, kõ kuwa mu bar aikata abin da muke so a cikin dũkiyõyinmu? Lalle, haƙĩƙa kai ne mai haƙuri shiryayye!} [Hud: 87].
Hiraƙl ya ce bayan Abu Sufyan ya tambaye shi game da annabinmu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: "Kuma na tambayeka, shin kun kasance kuna tuhumarsa da ƙarya ne kafin ya faɗa muku abinda ya faɗa? sai ka ce: a'a, haƙiƙa na san cewa shi bai kasance ya bar ƙarya ga mutane sannan ya yi wa Allah ƙarya ba". (Bukhari ne ya fitar da shi (7), da Muslim (1773).)
Daga cikinsu: Hanyoyi masu girma da yawa wurin riwaito ayoyin annabawa, da abinda suka zo da shi na ilimi da shiriya da addinin gaskiya, abinda yake koruwa tare da shi su haɗu akan kawo ƙarya.
Daga cikinsu: Cewa su ba sa neman lada akan saƙonninsu, kuma ba sa neman wani mulki, Allah Maɗaukakin sarki Ya faɗa Yana Mai bada labari game da yawa daga annabawan, cewa kowane ɗaya daga cikinsu ya cewa mutanensa: {Yã ku mutãnena! Bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa, ijãrata ba ta zama ba, fãce ga wanda Ya ƙãga halittata. Shin fa, bã ku hankalta?} [Hud: 51].
Daga cikinsu: Cewa ba'a taɓa samun wanda ya soki annabcin annabawa ba sai jahili wanda bai yi duba ba a cikin abinda suka zo da shi ba na addini da ilimi da shiriya, ko mai tsaurin kai mai girman kai, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Sun yi musun ta kuma rayukansu sun tabbatar da ita sabo da zalunci da girman kai} [al-Naml: 14], Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Lalle ne Muna sani cewa haƙĩƙa, abin da suke faɗa yana ɓãta maka rai. To, lalle ne su, bã su ƙaryata ka (a cikin zukatansu) kuma amma azzãlumai da ãyõyin Allah suke musu} [An'am: 33].
Daga cikinsu: Abinda yake kasancewa dalili a bayyane wanda idanu suke ganinsa, kuma hankula suke sallama masa, kamar dilmiyar da mutanen (annabi) Nuhu, da taguwar (annabi) Salihu, da kalubalantar da (annabi) Hudu ya yi wa mutanensa na su yi masa kaidi baki ɗayansu, da tsiratar da (annabi) Ibrahim daga wuta, da ayoyin (annabi) Musa, daga cikinsu akwai: Sanda, da fari, da kwarkwata, da kwaɗi, da jini, da Dufana, da dilmiyar da Fir'auna da mutanensa, da ayoyin (annabi) Dawud - aminci ya tabbata agare shi -, kamar tasbihin duwatsu da lauya ƙarfe, da ayoyin (annabi) Sulaiman - aminci ya tabbata agare shi -, da hore iska da aljanu gare shi, da yadda ya san maganar tsuntsaye, da ayoyin (annabi Isa) Masihu - aminci ya tabbata agare shi - kamar warkar da kutare da bebaye da makaho, da raya matattu, kuma cewa shi ya kasance yana sawwara tabo (laka) kamar yanayin tsuntsu sain ya yi busa acikinsa da izinin Allah sai ya zama tsuntsu, da ayoyin annabinmu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, su suna da yawa ba su iyakantu ba sai da wahala, kamar tsagewar wata, da Isra'i da Mi'iraji da yawaitar abin ci da zancen dabbobi, da tasbihin tsakawankwani, da shisshiken kututturen dabino, da taimakon Allah gareshi akan makiyansa.
Daga cikinsu: Halin annabi mai kira zuwa gaskiya; domin cewa su mutane suna banbancewa tsakanin mai kira zuwa gaskiya kuma mai gaskiya a maganarsa, da mai da'awa maƙaryaci a maganarsa; saboda haka ne Abdullahi ɗan Salam ya ce: "Lokacin da manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya iso Madina sai mutane suka zabura gare shi, aka ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya zo, sai na zo cikin mutane dan na dube shi, lokacin na bibiyi fuskar manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - na san cewa fuskarsa ba fuskar maƙaryaci ba ne". (Tirmizi ne ya fitar da shi (2485), da Ibnu Majah (1334), da Inu Abi Shaibah (25898), da Ahmad (23784), da Abdu Ibnu Humaid (496).) Da wasunsu na daga ayoyi.
Babu abinda ya rage daga ayoyin annabawa sai AlKur'ani mai girma, da sunnar annabinmu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, su wanzajju ne; domin su wahayi ne, Allah Ya lamunci kiyayesu, Allah - sha'aninSa Ya ɗaukaka - Ya ce: {Lalle Mũ ne, Muka saukar da Ambato (Alƙur'ãni), kuma lale Mũ, haƙĩƙa, Mãsu kiyayẽwane gare shi} [al-Hijr: 9]. A cikinsu akwai mafi girman dalilai da hujjoji akan gaskiyar manzanci, da gaskiyar manzo - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -.
Kuma muna imani cewa Allah Ya ƙarfafi manznninSa - aminci ya tabbata agare su - da abinda hikimarSa take hukunta shi na ayoyi da hujjojin kasancewa da na shari'a, sai Allah Ya shiryar da wanda Ya so da falalarSa, kuma Ya ɓatar da wanda Ya ga dama da adalcinSa, sai dai mai tsaurin kai ayoyin ba sa ƙara masa komai sai tsaurin kai da girman kai, Allah Ya ce: {Kuma lalle ne haƙĩƙa, Mun sarrafa bayãni a cikin wannan Alƙur'ãni dõmin su yi tunãni, kuma bã ya ƙãra musu kõme fãce gudu} [al-Israa: 41], Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Kuma abinda aka saukar zuwa gareka daga Ubangijinka yana ƙara wa da yawa daga cikinsu shisshigi da kafirci} [al-Ma'ida: 68], Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma suka yi rantsuwa da Allah, mafi nauyin rantsuwarsu, "Lalle, idan wani mai gargaɗi ya zo musu tabbas zã su kasance mafi shiryuwa, daga ɗayan al'ummõmi." To, a lõkacin da mai gargaɗi ya jẽ musu, bai ƙarã su da kõme ba fãce gudu} [Faɗir: 42], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma suka yi rantsuwa da Allah iyakar rantsuwõyinsu (cẽwa) lalle ne idan wata ãyã ta jẽmusu, haƙĩƙa, sunã yin ĩmãni da ita. Ka ce: "Abin sani kawai, ãyõyi a wurin Allah suke. Kuma mẽne nezai sanya ku ku sansance cẽwa, lalle ne su, idan ãyõyin sun je, ba zã su yi ĩmãni ba?} [al-An'am: 109], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma Mun baiwa Samudawa taguwa a bayyane sai suka zalinci kansu da ita kuma baMa aiko da ayoyi sai dan tsoratarwa} [al-Isra'a: 59].
Daga ɗan Abbas - Allah Ya yarda da su - ya ce: "Mutanen Makka sun tambayi annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya maida dutsan safa zinare, kuma ya nisantar da duwatsu daga garesu, don su yi noma, sai akace masa: In ka so ka jinkirta musu, idan ka so Mu basu abinda suka tambaya, idan sun kafirce a halaka su kamar yadda Na halakar da waɗanda ke gabansu, ya ce: A'a, kai zan jinkirta musu, sai Allah Ya saukar da wannan ayar: {Kuma ba wani abu ne ya hanaMu Mu aiko musu da ayoyi ba sai dan na farkonsu sun ƙaryata su, kuma Mun bawa samudawa taguwa a bayyane} [al-Isra'a: 59]". (Ahmad ne ya fitar da shi (2333), da al-Bazzar (5036), da Nasa'i a cikin al-Kubra (11226), da Hakim (3437), da al-Baihaƙi a cikin Dala'il al-Nubuwwah (605).)
Kuma muna sanin cewa Allah da Ya ga dama da Ya shiryar da mutane baki ɗaya, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma dã Allah Ya so, haƙĩ ƙa, dã Ya sanya ku al'umma gudã, kuma Yanã ɓatar da wanda Ya so. kuma Yanã shiryar da wanda Ya so. Lalle ne anã tambayarku abin da kuka kasance kunã aikatãwa} [al-Nahl: 93], Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Da Allah Ya ga dama da Ya tarasu akan shiriya, kada ka kasance daga jahilai} [al-An'am: 35].
Kuma muna imani cewa dalilan annabawa da ayoyin da suka zo da su da hujjojin da Allah Ya ƙare su da su, ya koru wani mai da'awar annabta ya zo da su, ko wani matsafi, ko wani maƙaryaci; domin Allah Ya hukunta cewa baZai taimaki mai ɓatarwa ba da wani ingantaccen dalili, kuma baZai gasgata maƙaryaci da wani dalili na gaskiya ba; domin shi Mai hikima ne a cikin shari'arSa da umarninSa, kuma hikimar Allah da sunnarSa masu gudana sun hana hakan, Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya ce: {Kuma dã (Muhammadu) yã faɗi wata maganã, yã jingina ta garẽ Mu * Dã Mun kãma shi da dãma * sa'an nan, lalle ne, dã Mun kãtse masa lakã} [al-Haƙah: 44-46].
BABIN ANNABCIN ANNABIMMU MUHAMMAD - TSIRA DA AMINCIN ALLAH SU TABBATA A GARE SHI -
Muna imani cewa annabinmu Muhammad ɗan Abdullahi shi ne manzon Ubangijin talikai, kuma shi ne cikamakin annabawa da manzanni, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Muhammadu bai kasance baban kõwa ba daga mazanku, kuma amma shĩ yã kasance Manzon Allah kuma cikon Annabãwa. Kuma Allah Ya kasance Masani ga kõme} [al-Ahzab: 40]. Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Lallai kwatankwacina da sauran Annabawa da suka gabaceni kamar mutum ne da ya gina gida sai ya kyautata shi yakawatashi, sai wurin bulo daya a wani lungu sai mutane suka rika kewaye shi suna mamakinsa suna cewa ina ma za'a saka wannan bulo din ? ya ce: To ni ne wannan bulo din, kuma ni ne cikamakin Annabawa". (Bukhari ne ya fitar da shi (3535), da Muslim (2286).)
Kuma shi ne shugaban 'ya'yan (annabi) Adam, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Nine shugaban 'ya'yan Adam ranar Alkiyama, kuma farkon wanda ƙabari zai tsagewa, kuma farkon mai ceto farkon wanda za'a bawa ceto". (Muslim ne ya fitar da shi (2278), da Abu Dawud (4673).) Kuma shi ne badaɗayin Ubangijin talikai, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Da zan riki wani badaɗayi daga al’umata da na riƙi Abubakar badaɗayi sai dai kuma dan’uwa na ne kuma sahabina". (Bukhari ne ya fitar da shi (3656).)
Kuma muna sanin cewa shi an ba shi ayoyin da ba'a bawa wani daga manzanni - aminci ya tabbata agare su - irin sun ba, mafi girman ayoyinsa shi ne AlKur'ani mai girma, kuma farkon abinda aka saukar masa daga gare shi shi ne farkon "Suratul Alaƙ", kamar yadda Hadisi ya ingantar da hakan: Daga A'isha Uwar muminai - Allah Ya yarda da ita - ta ce: farkon abinda aka farawa manzo Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - da shi na wahayi kyakkyawan mafarki a cikin barci, ya kasance ba ya ganin wani mafarki sai ya zo kamar ɓullowar asuba, sannan aka sa masa son kaɗaitaka, ya kasance yana kaɗaitaka a kogon Hira sai ya yi ibada a cikinsa - ita ce ibada - wasu 'yan darare masu adadi kafin ya koma zuwa iyalansa, kuma yana yin guziri saboda hakan, sannan ya dawo zuwa ga Khadija sai ya yi guziri ga irin yadda ya saba, sai gaskiya ta zo masa alhali shi yana kogon Hira, sai mala'ika ya zo masa sai ya ce: "Ka karanta, ya ce: Ni bamai karatu ba ne, ya ce: sai ya kamani, sai ya lullubeni har yakai matukar wahala gareni, sannan ya sakeni, sai ya ce: Ka karanta, na ce: Ni ba mai karatu bane, sai ya kamani sai ya lullubeni karo na biyu har ya kai matukar wahala gareni, sannan ya sakeni, sai ya ce: Ka karanta, sai na ce: Ni bamai karatu bane, sai ya kamani sai ya lullubeni karo na uku, sannan ya sakeni, sai ya ce: Ka karanta da sunan Ubangijinka wanda Ya yi halitta * Ya halicci mutum daga gudan jini * Ka karanta alhali Ubangijinka shi ne mafi girma} [al-Alak: 1-3]", sai manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - zuciyarsa tana rawa. (Bukhari ya fitar da shi (3), da Muslim (160), da Tirmizi (3632).) Kuma bayanta aka saukar masa da "Muddassir", daga Jabir ɗan Abdullahi - Allah Ya yarda da shi - cewa shi ya ji manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana bayani game da lokacin wahayi: "Wataran ina tafiya sai na ji wani sauti daga sama, sai na ɗaga idona wajen sama, sai ga mala'ikan da ya zo min a kogon hira yana zaune akan kursiyyi tsakanin sama da ƙasa, sai na firgita daga gare shi, har na sauko zuwa ƙasa, sai na zo wa iyalaina sai na ce: Ki lulluɓe ni, ki lulluɓeni, ki lulluɓe ni". Sai Allah - Maɗaukakin sarki - Ya saukar da: { Ya kai mai lulluɓa * ka tashi ka yi gargaɗi} [al-Muddassir: 1-2] zuwa faɗinSa: {ka ƙaurace} [al-Muddassir: 5] - Abu Salamah ya ce: al-Rijs: Gumaka - sannan wahayi ya ci gaba da sauka yana bin juna. (Bukhari ne ya fitar da shi (4926), da Muslim (161), da Tirmizi (3325).)
Daga A'isha Uwar muminai - Allah Ya yarda da ita -, cewa Haris ɗan Hisham - Allah Ya yarda da shi - ya tambayi manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai ya ce: Ya manzon Allah, yaya wahayi yake zo maka? sai manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce; "Wani lokaci yakan zo min kwatankwacin ƙararrawa, kuma yafi tsanani a gare ni, sai ya rabu da ni alhali na riƙe abinda ya faɗa, wani lokacin kuma mala'ikan yana yi min kamanceceniya da wani mutum, sai ya yi min magana sai na riƙe abinda yake cewa". A'isha - Allah Ya yarda da ita - ta ce: Haƙiƙa na gan shi wahayi yana saukar masa a yini mai tsananin sanyi sai ya rabu da shi, lallai goshinsa yana zubar da gumi. (Bukhari ya fitar dashi (2), da Muslim (2333), da Tirmizi (3634), da Nasa'i (933).)
Kuma shi ya zauna a Makka shekara goma sha uku yana kiran mutane zuwa Tauhidi, kuma ya zauna a Madina shekara goma yana bayyana shari'un Allah, yana kira zuwa addininSa yana yaƙi a tafarkinSa har Allah Ya karbi rayuwar shi yana da shekaru sittin da uku tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - fansarsa babana da babata.
Muna sanin cewa daga mafi girman ayoyinsa - bayan AlKur'ani mai girma - shi ne Isra'i da Mi'iraji, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Tsarki ya tabbata ga wanda Ya yi tafiyar dare da bãwanSa da dare daga Masallaci mai alfarma zuwa ga Masallaci mafi nĩsa wanda Muka sanya albarka a gefensa dõmin Mu nũna masa daga ãyõyinMu. Lalle ne Shi shĩ ne Mai ji, Mai gani} [al-Isra'a: 1].
Daga Anas - Allah Ya yarda da shi - cewa manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "An zo min da Buraƙa, shi wata dabba ce fara doguwa sama da jaki, ba ta kai alfadari ba, tana sanya kofatanta a inda ganainta ya tiƙe, ya ce: sai na hauta har na zo baitil Maƙdis, ya ce: Sai na ɗaureta da sarƙar da annabawa suke ɗaurewa da ita, ya ce: Sannan na shiga masallaci, sai na yi sallah a cikinsa raka'a biyu, sannan na fita sai Jibrilu - aminci ya tabbata agare shi -ya zo mini da ƙwarya ta giya, da kuma ƙwarya ta nono, sai na zaɓi nono, sai Jibril - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: Ka zaɓi sunna, sannan aka hau da mu zuwa sama, sai Jibril ya nemi a buɗe, sai aka ce: waye kai? ya ce: Jibril ne, aka ce : Wake tare da kai? ya ce: Muhammad, aka ce : Shin an aikoshi ne? ya ce: Haƙiƙa an yi aike gare shi, sai aka buɗe mana, sai gani ga Adam, sai ya yi marhaban da ni, kuma ya yi mini addu;a ta alheri, sannan aka hau da mu zuwa sama ta biyu, sai jibrilu ya nemi a bude masa, sai aka ce: waye kai? ya ce: Jibril, aka ce: wake tare da kai? ya ce: Muhammad, aka ce: shin an yi aike gareshi ne? ya ce: hakika an yi aike gare shi, sai aka bude mana, sai ga 'ya'yan Yakumbo biyu Isa ɗan Maryam da Yahaya dan Zakariyya - aminci ya tabbata agare su -,sai suka yi marhaban da ni kuma suka yi mini addu'a ta alheri, sannan ya hau da ni zuwa sama ta uku, sai Jibril ya nemi a bude, aka ce : waye kai? ya ce: Jibril, aka ce: wake tare da kai? ya ce: Muhammad ne - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, aka ce: an yi aike ne gare shi? ya ce: an yi aike gare shi, sai aka buɗe mana, sai gani ga Yusuf - tsira da amincin su tabbata agare shi - sai ga shi an ba shi rabin kyau, sai ya yi marhaban da ni kuma ya yi mini addu'a ta alheri, sannan aka hau da mu zuwa sama ta huɗu, sai Jibril - aminci ya tabbata agare shi - ya nemi a buɗe ,aka ce : waye wannan? ya ce: Jibril ne, aka ce : wake tare da kai? ya ce: Muhammad, aka ce: An yi aike ne gare shi? ya ce: An yi aike gare shi, sai aka buɗe mana sai gani ga Idris, sai ya yi marhaban da ni kuma ya yi mini addu'a ta alheri, Allah - Mai girma da daukaka - Ya ce: {Mun daukaka shi matsayi maɗaukaki}, sannan aka hau da mu zuwa sama ta biyar, sai Jibril ya nemi a bude, aka ce: waye wannan? sai ya ce: Jibril, aka ce: wake tare da kai? ya ce: Muhammad ne, aka ce: Shin an yi aike ne gare shi? ya ce: an yi aike gare shi, sai aka bude mana sai ga Haruna - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, sai ya yi marhaban, kuma ya yi addu'a ta alheri, sannan aka hau da mu zuwa sama ta shida, sai Jibril ya nemi a bude, aka ce: waye kai? ya ce: Jibril - aminci ya tabbata agare shi -, aka ce: wake tare da kai? ya ce: Muhammad ne, aka ce:shin an yi aikene gare shi? ya ce: An yi aike gare shi, sai aka bude mana sai ga Musa - tsira da amincin su tabbata agare shi -, sai ya yi marhaban, kuma ya yi mini addu'a ta gari, sannan aka hau da mu zuwa sama ta bakwai, sai Jibril ya nemi a buɗe, aka ce: Waye wannan? ya ce: Jibril ne, aka ce: Wake tare da kai? ya ce: Muhammad ne - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, aka ce: shin an yi aike ne gare shi? ya ce: an yi aike gare shi, sai gani ga Ibrahim - tsira da amincin su tabbata agare shi - yana mai jingina bayansa zuwa Baitil Ma'amur, sai ga shi kowace rana mala'iku dubu saba'in ne suke shiga cikinsa kuma ba sa dawowa gare shi, sannan ya tafi da ni zuwa magaryar tikewa, sai ga ganyenta kamar kunnuwan giwa, sai ga 'ya'yan itacenta kamar tukwane, ya ce: lokacin da abinda ya lullubeta daga al'amarin Allah ya lullubeta sai ta canja, babu wani daga hlittar Allah zai iya siffanta maka ita saboda kyanta, sai Allah Ya yi wahayi zuwa gareni abinda Ya yi mini wahayi, sai ya wajabta mini salloli hamsin akowane yini da dare, sai na sauka gurin Musa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, sai ya ce: Me Ubangijinka Ya wajabta akan al'ummarka? na ce: Salloli hamsin, ya ce: Ka koma gurin Ubangijinka ka roƙe shi sauƙi, domin al'ummarka ba za su iya ba, domin cewa ni na jarraba Banu Isra'il, ya ce: Sai na koma gurin Ubangijina, na ce: Ya Ubangiji, ka sauƙaƙawa al'ummata, sai ya cire mini biyar, sai na komawa Musa, sai an ce: Ya sarayar mini da biyar, ya ce: Lallai al'ummarka ba zata iya hakan ba, ka koma zuwa Ubangijinka ka roƙe shi sauƙi, ya ce: Bangushe ba ina komawa tsakanin Ubangijina - alherinSa ya yawaita Ya ɗaukaka - da tsakanin Musa har Ya ce: Ya Muhammad, lallai su biyar ne salloli a kowanne yini da dare, kowace sallah tana da lada goma, to wannan hamsin ke nan wanda ya yi niyyar kyakkyawa bai aikatata ba za'a rubuta masa kyakkyawa, idan ya aikata za'a rubuta masa lada goma, wanda ya yi niyyar mummuna bai aikatata ba ba za'a rubuta masa komai ba, idan ya aikatata za'a rubuta masa mummuna ɗaya, ya ce: Sai na sauka har na tiƙe ga Musa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, sai na bashi labari, sai ya ce: Koma ga Ubangijinka ka roƙe Shi sauƙi, sai manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: Haƙiƙa na komawa Ubangijina har na ji kunyarSa". (Bukhari ne ya fitar da shi (7517), da Muslim (162), kuma lafazin nasa ne, da Tirmizi (3131), da Nasa'i (450), da Ibnu Majah (1399).)
Daga ayoyinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agre shi -: Tsagewar wata, Mai girma da ɗaukaka Ya ce: {Sã'a ta yi kusa, kuma wata ya tsãge} [al-Kamar: 1]. Daga Ibnu Mas'ud - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Wata ya tsage a zamanin manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ɓangare biyu: Wani ɓangaren a saman dutse, wani ɓangaren kuma ƙasansa, sai manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Ku shaida". (Bukhari ne ya fitar da shi (4864), da Muslim (2800), da Tirmizi (3285).)
Kuma Allah Ya keɓantashi da keɓantattun abubuwa da yawa, kamar faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: "An fifita ni akan annabawa da abubuwa shida: An bani matattaran kalmomi, kuma an bani nasara da tsoro, an halatta mini ganimomi, an sanya mini ƙasa ta zama mai tsarkkaewa kuma masallaci, kuma an aikoni zuwa halitta gaba ɗaya, kuma an cike annabawa da ni". (Muslim ne ya fitar da shi (523), da Tirmizi (1553).) Waɗannan keɓantattun abubuwan malamai sun ambacesu a cikin littattafansu wani lokaci, wani lokacin kuma suna ware musu littttafai su kaɗai.
Kuma muna imani cewa imani da shi yana wajaba akan Kowanne mumini namiji da mumina mace, da kuma gasgata shi a cikin abinda ya bada labari da shi, da yi masa biyayya a cikin abinda ya yi umarni da shi, Allh Maɗaukakin sarki Ya ce: {Dõmin ku yi ĩmani da Allah da ManzonSa, kuma ku ƙarfafa shi, kuma ku girmama Shi, kuma ku tsarkake Shi (Allah) sãfiya da maraice} [al-Fath: 9]. Sha'aninSa ya ɗaukaka kuma sunayenSa sun tsarkaka Ya ce: {Sabõda haka ku yi ĩmani da Allah da ManzonSa da hasken nan da Muka saukar. Kuma Allah, ga abin da kuke aikatãwa, Mai labartawa ne} [at-Tagabun: 8].
Kuma muna imani cewa ba'a bautawa Allah sai da abinda annabinmu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya shara'anta, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma duk abinda manzo ya zo muku da shi to ku karɓa kuma duk abinda ya haneku ga barinsa to ku hanu, kuma ku ji tsoron Allah cewa lallai Allah Mai tsananin uƙuba ne} [al-Hashr: 7]. Allah Ya yi gargaɗi daga saɓawa umarninsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, sai sha'aninSa ya ɗaukaka Ya ce: {To waɗanda suke saɓa umarninsa su kiyayi kansu kada musiba ko fitina ta sauka a kansu ko kuma azaba mai raɗaɗi ta same su} [al-Nnur: 63].
Kuma girmama shi yana wajaba da sonsa, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Ka ce: "Idan kun kasance kunã son Allah to, ku bĩ ni, Allah Ya sõ ku, kuma Ya gãfarta muku zunubanku. Kuma Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai} [Aal- Imran: 31].
Kuma soyayyar annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - tana daga tushen imani, haƙiƙa Allah Ya haɗa ta da soyayyarSa, kuma Ya yi narko ga wanda ya gabatar da wani akansa na al'amuran soyayya ko na 'yan uwa ne, ko dukiyoyi, ko ƙasashe ko wanin hakan, sai Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Ka ce: "Idan ubanninku da ɗiyanku da 'yan'uwanku da mãtanku da danginku da dũkiyõyi, waɗanda kuka yi tsiwirwirinsu, da fatauci wanda kuke tsõron tasgaronsa, da gidaje waɗanda kuke yarda da su, sun kasance mafiya sõyuwa a gare ku daga Allah da ManzonSa, da yin jihãdi ga hanyarSa, to, ku yi jira har Allah Ya zo da umurninSa! Kuma Allah bã Ya shiryar da mutãne fãsiƙai} [al-Taubah: 24].
Kuma yana wajaba akan mumini manzo - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya zama mafi soyuwa a gare shi daga kansa da ɗansa da mutane gaba ɗaya, Daga Abdullahi ɗan Hisham - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Mun kasance tare da annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - alhali shi ya riƙe hannun Umar ɗan Khaɗɗab, sai Umar ya ce masa: Ya manzon Allah, lallai kaine mafi soyuwa gareni daga dukkan komai sai kaina, sai annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "A,a na rantse da wanda raina yake a hannunSa, har sai na zama mafi soyuwa gareka daga kanka" sai Umar ya ce masa: Lallai a yanzu - wallahi - kaine mafi soyuwa gareni daga kaina, sai annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "A yanzu ya Umar". (Bukhari ne ya fitar da shi (6632).)
Haƙiƙa Allah - Maɗaukakin sarki - Ya haɗa ambatan annabinmu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - da ambatanSa - tsarki ya tabbatar maSa - a cikin shahada biyu da kiran sallah, haƙiƙa ambatansa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yawaita a cikin littattafan Allah waɗanda suka gabata, da cikin AlKur'ani mai girma, kuma shugabannin musulunci sun wallafa littattafai daban-daban a cikin sunnarsa, da tarihinsa, da halayensa, da ɗabi'unsa, da yaƙe-yaƙensa, zamu iya wadatuwa a nan da abinda yake wajaba a ƙudirce shi a sha'anin annabcinsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -.
Alƙali Iyad - Allah Ya yi masa rahama - Ya ce: "Idan ɗabi'un cika da girma sun kasance abinda muka ambace shi, kuma muka ga ɗaya daga cikinmu yana ɗaukaka da ɗaya daga cikinsu, ko biyu idan sun haɗu a tare da shi a kowane zamani: Ko dai dan nasaba, ko kyau, ko ƙarfi, ko haƙuri, ko gwarzantaka, ko kyauta, har darajarsa ta girmama, kuma ana buga misalai da sunansa, kuma tasiri mai girma yana tabbatuwa da siffantuwa da hakan a cikin zukata, shi tun tsawon zamaninnikan da suka wuce to meye zatanka da mai girman daraja wanda dukkan waɗannan ɗabi'un suka haɗu gare shi , zuwa abinda ƙirguwa basa ɗaukarsa, kuma magana ba ta iya furta shi, kuma ba'a samunsa da aiki, ko dabara, sai da kebantuwar Mai girma Madaukaki, daga falalar annabta, da manzanci, da badadaynataka, da soyayya, dazabi, da Isra'i, da ganin (Allah). (Ganin annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a daren da aka yi Isra'i da shi an yi saɓani a cikinsa, ingantaccen zance shi ne manzanmu - tsira da amicni Allah su tabbata agare shi - bai ga Ubangijin sa ba a daren Isra'i). da kusanci, da kusa, da wahayi, da ceto, da wasila, da fadila, da maɗaukakinyar daraja, da matsayi abin yabo, da Buraƙ, da Mi'iraji, da aiko shi da aka yi zuwa ja da baƙi, da yiwa annabawa sallah, da yin shaida tsakanin annabawa da al'ummu, da shugabancin 'ya'yan Adam, da tuta ta godiya, da albishir, da gargaɗi, da matsayi a wajen Mai Al'arshi, da biyayya, da amana, da shiriya, da rahama ga talikai, da bada yarda da buri, da Alkausara, da jin magana, da cika ni'ima, da afuwa ga abinda aka yi da ba’a yi ba, da buɗewar ƙirji, da dauke nauyi, da ɗaukaka ambato, da buwayar nasara, da saukar nutsuwa, da karfafawar malaa'iku, da bada littafi da hikima, da Fatiha da AlKur'ani mai girma, da tsarkake al'umma, da rokon Allah, da salatin Allah - Madaukakin sarki - da mala'iku, da hukunci a tsakanin mutane da abinda Allah Ya nuna masa, da sauke nauyi da kumakumai daga garesu, da rantsuwa da sunansa, da amsa addu'arsa, da magana da sandararrun abubuwa da abubuwa marasa magana da raya matattu, da jiyar da kurame, da bubbugowar ruwa tsakanin yatsunsa, da yawaita abu kadan, da tsagewar wata, da dawo da rana, da juya abubuwa gaba da gaba, da cin nasara da tsoratarwa, da tsinkaya akan gaibu, da inuwar girgije, da tasbihin tsakwankwani, da warkar da radadi, da tsari daga mutane, har zuwa abinda abinda lissafe su ba zai lissafu ba, kuma kididdige su ba zai kididdigu ba, sai kadai wanda ya ba shi hakan kuma ya fifita shi da su, babu abin bautawa da gaskiya sai shi (Allah), zuwa abinda ya tanadar masa a gidan lahira na masaukan girma, da darajoji masu tsarki, da matakan tsira, da kyakkyawa, da karin da hanukula kaduwa da su, kuma tinani yake dimaucewa daga riskarsu". (Asshifa bi ta'arifi huƙuƙil Musɗafa (1/55-57).)
BABIN GAMEWAR MANZANCINSA - TSIRA DA AMINCIN ALLAH SU TABBATA AGARE SHI - GA HALITTA BAKI DAYA
Muna imani cewa Allah Ya aiko manzanSa (annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - zuwa halitta baki ɗaya, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Ka ce: "Yã kũ mutãne! Lalle ne nĩ manzon Allah nezuwa gare ku, gabã ɗaya. (Allah) Wanda Yake Shĩ ne da mulkin sammai da ƙasa; Bãbu wani abin bautawa fãce Shi, Yanã rãyarwa, kuma Yanã matarwa, sai ku yi ĩmãni daAllah da ManzonSa, Annabi, Ummiyyi, wanda yake yin ĩmãni da Allah da kalmominSa; ku bĩ shi, tsammãninku, kunã shiryuwa} [al-A'araf: 158], Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Kuma ba Mu aika ka ba fãce zuwa ga mutãne gabã ɗaya, kanã mai bãyar da bushãra kuma mai gargaɗi, kuma amma mafi yawan mutãne ba su sani ba} [Saba'i: 28].
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "An bani wasu abubuwa biyar da ba'a bawa wani daga annabawa a gabana ba. An bani nasara da tsoro tsawon tafiyar shekara, kuma an sanya mini ƙasa ta zama masallaci gareni kuma mai tsarkakewa, kowane mutum daga al'uumata sallah ta riske shi to ya yi sallah, kuma an halatta mini ganimomi, annabi ya kasance ana aiko shi zuwa mutanensa akeɓance, ni kuma an aikoni zuwa mutane baki ɗaya, kuma an bani ceto". (Bukhari ne ya fitar da shi (438), da Muslim (521), da Nasa'i (432).)
Kuma annabinmu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - Allah Ya aiko shi zuwa nauyaya biyu: Mutum , da aljani, da haɗuwar musulmai, haƙiƙa aljanu sun ji AlKur'ani kuma sun koma zuwa ga mutanensu suna masu gargaɗi, sai Allah Ya ba manzonSa labari da hakan acikin AlKur'ani da faɗinSa: {Kuma a lõkcin da Muka jũya waɗansu jama'a na aljanu zuwa gare ka sunã saurãren Alƙur'ãni. To, alõkacin da suka halarce shi suka ce: "Ku yi shiru." Sannan da aka ƙãre, suka jũya zuwa ga jama'arsu sunã mãsu gargaɗi * Suka ce: "Ya mutãnenmu! Lalle mũ, mun ji wani littãfi an saukar da shi a bãyãn Mũsã, mai gaskatãwa ga abin da ke a gaba da shi, yanã shiryarwa ga gaskiya da kuma zuwa ga hanya madaidaiciya * Yã mutãnenmu! Ku karɓa wa mai kiran Allah, kuma ku yi ĩmãni da Shi, Ya gãfarta muku daga zunubanku, kuma ya tserar da ku daga azãba mai raɗaɗi * Kuma wanda bai karɓa wa mai kiran Allah ba to bai zama mai buwãya a cikin ƙasa ba, kuma ba ya da waɗansu majiɓinta, baicin Shi. Waɗannnan sunã a cikin ɓata bayyananna} [al-Ahkaf: 29-32].
Kuma Allah Ya riƙi alƙawari da dukkanin annabawa da manzanni - aminci ya tabbata agare su - lallai idan an aiko (annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - alhali suna raye - za su yi imani da shi, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Kuma a lõkacin da Allah Ya riƙi alkawarin Annabãwa: "Lalle ne ban bã ku wani abu ba daga Littãfi da hikima, sa'an nan kuma wani manzo ya je muku, mai gaskatãwa ga abin da yake tãre da ku; lalle ne zã ku gaskata Shi, kuma lalle ne zã ku taimake shi." Ya ce: "Shin, kun tabbatar kuma kun riƙi alkawarĩNa a kan wannan a gare ku?" suka ce: "Mun tabbatar." Ya ce: "To, ku yi shaida, kuma Nĩ a tãre da ku Inã daga mãsu shaida} [Aal- Imran: 81]. Aliyu ɗan Abu Ɗalib - Allah Ya yarda da shi - ya ce: "Allah - Mai girma da ɗaukaka - Bai aiko wani annabi ba, Adam da waɗanda ke bayansa sai ya riƙi alƙawari a sha'anin (Annabi) Muhammad: lallai idan an aikoshi - alhali yana raye - zai yi imani da shi, kuma zai taimake shi, kuma ya umarce shi , sai ya riƙi alƙawarin ga mutanensa, sai ya ce: {Kuma a lokaci da Allah Ya riƙi alƙawarin annabawa lallai ne banbaku wani abuba daga littafi da hikima} karanta ayar zuwa ƙarshe [Aal-Imran: 81]". (Ɗabari ne ya fitar da shi a cikin Tafsiri (5/540).)
Kuma Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Addu'ar babana Ibrahim, da bisharar Isa ga mutanensa, da mafarkin mahaifiyata wacce ta gani cewa wani haske ya fita daga gareta wanda ya haskaka katangun Sham". (Ahmad ne ya fitar da shi (17163), da Usman ɗan Sa'id Darimi a ciki raddi ga Jahamiyya (261), da Ibnu Abi Asim a cikin Sunnah (418), da Abdullahi ɗan Ahmad a cikin Sunnah (865), da Ibnu Hibban (6404), da Ɗabarani a cikin Musnadul Shamiyyin (1455).) Da faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Ni addu'ar babana ce Ibrahim". Yana nufi da ita abinda Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya bamu labari da shi na addu'ar (Annabi) Ibrahim badaɗayi - aminci ya tabbata agagre shi - shi ne faɗinSa: {Ya Ubangijinmu! Ka aiko, a cikinsu, wani manzo daga gare su, yana karanta musu ãyõyinKa, kuma yana karantar da su Littãfin da hikimar, kuma yana tsarkake su. Lalle ne Kai, Kai ne Mabuwãyi Mai hikima} [al-Baƙara: 129].
Kuma muna imani cewa annabawa su yi wa mutanensu albishir da shi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, kuma siffofinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sun zo da siffofin sahabbansa a cikin Attaurada Linjila, Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya ce: {Muhammadu Manzon Allah ne. Kuma waɗannan da ke tãre da shi mãsu tsanani ne a kan kãfirai, mãsu rahama ne a tsakãninsu, kanã ganin su sunã mãsu rukũ'i mãsu sujada, sunã nẽman falala daga Ubangijinsu, da yardarSa. Alãmarsu tanã a cikin fuskõkinsu, daga kufan sujuda. Wannan shĩ ne siffarsu a cikin Attaura. Kuma siffarsu, a cikin Injĩla ita ce kamar tsiron shũka wanda ya fitar da rẽshensa, sa'an nan ya ƙarfafa shi, ya yi kauri, sa'an nan ya daidaita a kan ƙafãfunsa, yanã bãyar da sha'awa ga mãsu shũkar' dõmin (Allah) Ya fusãtar da kãfirai game da su. Kuma Allah Ya yi wa'adi ga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, daga cikinsu, da gãfara da ijãra mai girma} [al-Fath: 29], Kuma Allah - sha'aninSa Yaɗaukaka - Ya ce: {Waɗanda suke sunã bin Manzo, Annabi, Ummiyyi wanda suke sãmun sa rubũce a wurinsu, a cikin Attaura da Linjĩla.yanã umurnin su da alhẽri, kuma yana hana su daga barin abin da bã a so; kuma yana halatta musu abũ- buwa masu dadi, kuma yana haramtarwar mũnana a kansu. Kuma yanã kãyar da nauyinsu daga barinsu, da ƙuƙummai waɗannan da suka kasance a kansu. To, wa- ɗanda suka yi ĩmãni da shi kuma suka ƙarfafa shi, kuma suka tai- make shi, kuma suka bi haske wan- da aka saukar tãre da shi, waɗan- nan ne mãsu cin nasara} [al-A'araf: 157]. Kuma Masihu - aminci ya tabbata agare shi - ya yi wa Banu Isra'ila albishir da shi, Maɗaukakin sarki Ya faɗa Yana mai bada labari game da shi cewa shi ya ce da su: {Kuma a lõkacin da Ĩsã ɗan Maryayama ya ce: "Yã BanĩIsrã'ĩla! Lalle nĩ Manzon Allah ne zuwa gare ku, mai gaskata abin da ke gaba gare ni na Attaura, kuma mai bãyar da bushãra da wani Manzo da ke zuwa a bãyãna, SũnasaAhmad (Mashãyabo)." To, a lõkacin da ya jẽ musu da hujjõji, suka ce: "Wannan sihiri ne, bayyananne} [al-Saaf: 6]. Mazowa littafi (Yahudu da Nasara) sun kasance suna saninsa kamar yadda suke sanin 'ya'yansu, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Waɗanda Muka bã su Littãfi, suna saninsa kamar yadda suke sanin ɗiyansu. Kuma lalle ne wani ɓangare daga gare su, haƙiƙa, suna ɓõyewar gaskiya alhãli kuwa sũ, suna sane} [al-Baƙara: 146].
Kuma daga cikin alamomin annabtarsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - waɗanda sun kasance an san su ga mazowa littafi tambarin annabta akan kafaɗarsa maɗaukakiya, daga Sa'ib ɗan Yazid - Allah Ya yarda da shi - ya ce: "Sannan na tsaya a bayansa, sai na duba tambarin annabci tsakanin kafaɗunsa, tamkar ƙwan tantabara". (Bukhari ne ya fitar da shi (190), da Muslim (2345), da Tirmizi (3643).)
Daga Jabir ɗan samura - Allah Ya yarda da shi - ya ce: "Kuma na ga tambarin annabta a wajen kafaɗarsa tamkar ƙwan tantabara ya yi kama da jikinsa". (Muslim ne ya fitar da shi (2344), da Tirmizi (3644), da Nasa'i (5114).)
Kuma muna imani da gamewar manzancinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, saboda haka ne ya aika wasiku zuwa sarakuna da shugabanni yana kiransu zuwa bautar Allah Shi kaɗai, da imani da saƙonsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - da gasgata shi , daga Abu Burdah daga babansa - Allah Ya yarda da shi - ya ce: "Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya umarcemu mu tafi ƙasar Najjashi - sai ya ambaci Hadisinsa - Najjashi ya ce: Ina shaidawa cewa shi manzon Allah ne - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, kuma cewa shi ne wanda (annabi) Isa ɗan Maryam ya yi albishir da shi, da badan abinda nake a cikinsa na mulki ba da na zo masa har na riƙe masa takalma". (Abu Dawud ne ya fitar da shi (3205), da Ibnu Abi Shaibah (37795), da Abdu Ibnu Humaid (550), da Ibnu Abi Asim a cikin al-Aahad wal Masani (366), da al-Rauyani (502), da Hakim (3268).)
Hiraƙl ya ce bayan sakon manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya je masa: "Haƙiƙa na san cewa shi wanda zo ne, sai dai ban yi zatan cewa shi yana daga cikinku ba, idan abinda ka faɗa gaskiya ne, to ya kusa ya mallaki gurin diga-digan nan nawa waɗannan, da na yi kwaɗayin in tsira gare shi da na yi kwaɗayin haɗuwa da shi, da na kasance agurinsa dan awanke ƙafafuwansa". (Bukhari ne ya fitar da shi (2941), da Abu Dawud (5136).)
Daga Huzaifa - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Aƙibu da Sayyid shugaban nin Najran sun zo gurin manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - suna son su yi tsineneniya da shi, ya ce: Sai ɗayansu ya cewa abokinsa: Kada ka yi, na rantse da Allah idan ya kasance annabi ne sai muka yi tsineneniya ba zamu rabauta ba, haka 'ya'yan mu a bayanmu, suka ce: Mu zamu baka abinda ka tambayemu, to ka aiko mana da wani mutum amintacce tare damu, amma kada ka aiko mana da kowa sai amintacce. Sai ya ce: lallai zan aiki wani mutum amintacce mai gaskiyar amintaka tare da ku, sai sahabban manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - suka dinga leka shi sai ya ce: "Ya Kai Abu Ubaidah Dan Jarrah mike" lokacin da ya mike, sai manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Wannan shi ne amintaccen wannan al'ummar". (Bukhari ne ya fitar da shi (4380), da Muslim (2420), da Tirmizi (3796), da Ibnu Majah (135).)
Kuma muna imani cewa Allah Ya yanƙwanewa annabinmu - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ƙasa, sai ya ga daga gareta inda mulkin al'ummarsa zai kai, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Lallai cewa Allah Ya naɗe min ƙasa, sai naga gabacinta da yammacinta, kuma lallai al'ummata mulkinta zai kai inda aka naɗo mini daga gareta". (Muslim ne ya fitar da shi (2889), da Abu Dawud (4252), da Tirmizi (2176), da Ibnu Majah (3952).)
Daga dalilan gamewar, manzancinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - musuluntar da yawa daga malumman Yahudawa da masu bautar Nasara, kai dubunnai daga waɗanda aka jawo zukatansu zuwa addini daga mazowa litta ne.
Kuma: Haƙiƙa tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya yaƙi Rumawa kuma ya umarci sahabbansa da yaƙar Farisa da Rum a bayansa.
BABIN ZANTUTTUKAN MASU ADAWA DA MANZNCI DA KUMA MANZANNI - AMINCI YA TABBATA AGARE SU -
Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma kamar wancan ne Muka sanya wa kowanne Annabi maƙiyi; shaiɗãnun mutãne da aljannu, sãshensu yanã yin ishãra zuwa sãshe da ƙawãtaccen zance bisa ga rũɗi. Kuma dã Ubangijinka Yã so, dã ba su aikatã shi ba, don haka ka bar su da abin da, suke ƙirƙirãwa} [al-An'am: 112], kuma Allah ambatanSa ya ɗaukaka kuma sunayenSa sun tsarkaka Ya ce: {Kuma kamar haka ne, Muka sanya maƙiyi daga mãsu laifi ga kõwane Annabi. Kuma Ubangijinka Ya isa ga zama Mai Shiryarwa, kuma Mai taimako} [al-Furƙan: 31].
Hikimar Allah ta hukunta cewa Allah Yana shiryar da wanda Yake so da falalarSa, kuma Yana ɓatar da wanda Ya ga dama da adalcinSa, kamar yadda hikimarSa ta hukunta cewa kowane annabi yana da maƙiyi, kuma ya kasance tsakanin waɗannan maƙiyan akwai taimakekeniya akan ƙarya da kuma yadda suka hadu a maganganunsu, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Bã zã a fada maka ba fãce abin da aka riga aka faɗa ga Manzannin da suke a gabãninka. Lalle Ubangijinka, haƙĩƙa, Ma'abũcin gãfara ne, kuma Ma'abũcin azãba mai raɗaɗi ne} [Fussilat: 43]. Maganganun masu fada aji a cikin kowace al'umma iri ɗaya ce, wani lokaci suna cewa: Lallai Shi (annabi) matsafi ne ko boka ne ko maƙaryaci ne, kamar yadda yake a faɗin Fir'auna ga (Annabi) Musa a cikin abinda Allah Ya bada labari game da shi: {Kuma haƙĩƙa Mun aiki Mũsã da ãyõyinMu, da dalĩli bayyananne * Zuwa ga Fir'auna da Hãmãna da Kãrũna, sai suka ce: "Mai sihiri ne, maƙaryaci} [Ghafir: 23-24]. Wani lokacin kuma suna musun ya kasance ya zo musu da wata aya, kamar yadda Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Suka ce: "Yã Hũdu! Ba ka zo mana da wata hujja bayyananna ba, kuma ba mu zama mãsu barin abũbuwan bautawarmu ba dõmin maganarka, kuma ba mu zama mãsu yin ĩmãni da kai ba} [Hud: 53]. Wani lokacin kuma suna da'awar cewa shi yana ƙirƙirar wa Allah ƙarya, Allah Ya faɗa Yana Mai bada labari game da maganarsu mummuna: {Kuma idan an karanta ãyõyinMu bayyanannu a kansu, sai su ce: "Wannan bai zama ba fãce namiji ne yanã son ya kange ku daga abin da ubanninku suka kasance sunã bauta wa." Kuma su ce: "Wannan bai zama ba fãce ƙiren ƙarya da aka ƙãga." Kuma waɗanda suka kãfirta suka ce: ga gaskiya a lõkacin da ta je musu: "Wannan bã kõme ba fãce sihiri ne bayyananne} [Saba'i: 43].
Wani lokaci kuma suna siffanta shi da hauka, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Suka ce: "Yã kai wanda aka saukar da Ambato (Alƙur'ãni) a kansa! Lalle ne kai, haƙĩƙa, mahaukaci ne} [al-Hijr: 6], Tsarki ya tabbatar maSa Ya faɗa Yana Mai bada labari game da maganarsu: {Ya ce: "Lalle ne Manzonku, wanda aka aiko zuwa gare ku, haƙiƙa, mahaukaci ne} [al-Shu'araa: 27]. Ya tsarkaka ga manzannin Allah - aminci ya tabbata agare su -, alhali sune mafi cikar mutane a hankula, kuma mafi tsarkakarsu zukata.
Wani lokaci kuma suna neman girmama abinda suke kiransu gare shi na kira zuwa bautar Allah Shi kaɗai, Allah Maɗaukakin sarki Ya faɗa Yana Mai bada labari game da maganarsu cewa su sunce: {Suka ce: "Shin, kã zo mana ne dõmin mu bautawa Allah Shi kaɗai, kuma mu bar abin da ubanninmu suka kasance sunã bauta wa? To, ka zõ mana da abin da kake yi mana wa'adi da shi idan kã kasance daga mãsu gaskiya} [al-A'araf: 70], kuma suka ce: {Shin, yã sanya gumãka duka su zama abin bautawa guda? Lalle wannan, haƙĩƙa, abu ne mai ban mãmaki!} [Saad: 5].
Wani lokaci kuma suna kin karbar da'awar annabin; domin cewa shi mutum ne irinsu, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Sai manya waɗanda suka kafirta daga mutanensa suka ce bama ganinka sai mutum irinmu} [Hud: 27], kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Sunã mãsu shagaltacin zukãtansu, kuma su asirta gãnãwa: Waɗanda suka yi zãlunce (sunã cẽwa) "Wannan bã Kõwa ba ne fãce mutum misãlinku. Shin, to, kunã jẽ wa sihiri, ahãli kuwa kũ, kunã fahimta?} [al-Anbiya'a: 3].
Wani lokaci kuma suna nemansu da wasu al'amuran da ba sa cikin ikon halitta - sai dai cewa kawai girman kaine da tsaurin kai - haƙiƙa sun nemi annabinmu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - da ya ɓuɓɓugar musu da idan ruwa daga ƙasa, ko ya kasance yana da wata gona, ko ya faɗo musu da sama faɗowa, ko ya zo musu da Allah da kuma mala'iku, ko ya zama annabi yana da gida na zinariya, ko ya hau sama ya sauko musu da wani littafin, kamar a cikin faɗinSa - sha'aninSa ya ɗaukaka kuma mulkinSa ya ɗaukaka -: {Kuma suka ce: "Bã zã mu yi ĩmãni ba dõminka sai kã ɓuɓɓugar da idan ruwa daga ƙasa * Kõ kuma wata gõna daga dabĩnai da inabi ta kasance a gare ka. Sa'an nan ka ɓuɓɓugar da ƙõramu a tsakãninta ɓuɓɓugarwa * Kõ kuwa ka kãyar da sama a kanmu kaɓukka kõ kuwa ka zo da Allah, da malã'iku banga-banga * Kõ kuwa wani gida na zĩnãriya ya kasance a gare ka, kõ kuwa ka tãka a cikin sama. Kuma bã zã mu yi ĩmãni ba ga tãkawarka, sai ka sassaukõ da wani littãfi a kanmu, munã karantã shi." Ka ce: "Tsarki ya tabbata ga Ubangijĩna! Ban kasance ba fãce mutum, Manzo * Kuma bãbu abin da ya hana mutãne su yi ĩmãni, a lõkacin da shiriya ta jẽ musu, fãce sunce, "Shin, Allah zai aiko mutum ya zamo yana Manzo * Ka ce: "Dã malã'iku sun kasance a cikin ƙasa, kuma sunã tafiya, sunã masu natsuwa, lalle ne dã mun saukar da malã'ika daga sama ya zama manzo a kansu} [Al-Isra'a: 90-95].
Wani lokaci kuma suna neman annabi da ya zo musu da abinda ya yi musu aƙawari da shi na azaba, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Suka ce: "Shin, kã zo mana ne dõmin mu bauta wa Allah Shi kaɗai, kuma mu bar abin da ubanninmu suka kasance sunã bauta wa? To, ka zõ mana da abin da kake yi mana wa'adi da shi idan kã kasance daga mãsu gaskiya} [al-A'araf: 70], kuma sha'aninSa ya ɗaukaka Ya ce: {Sai suka sõke rãƙumar, kuma suka kangare daga barin umurnin Ubangijinsu, kuma suka ce: "Yã Sãlihu! Ka zõ mana da abin da kake yi mana wa'adi da shi, idan kã kasance daga manzanni!} [al-A'araf: 77].
Wani lokaci kuma suna tuhumar manzo da ɓata ko wauta, kamar a cikin faɗinsu wanda Allah Ya bamu labari a cikin faɗinSa Mai hikima: {Mashawarta waɗanda suka kãfirta daga mutãnensa suka ce: "Lalle ne mũ, haƙĩƙka, Munã ganin ka a cikin wata wauta! Kuma lalle ne mũ, haƙĩƙa, Munã zaton ka daga maƙaryata} [al-A'araf: 66].
Wani lokaci kuma suna toshe tafarkin Allah, suna cewa mabiyansu: Kada ku ji wannan AlKur'anin, ku yi tayin kuwwa a ciki (lokacin karatunsa), kamar yadda Allah Ya bada labari game da su: {Kuma waɗanda suka kafirta suka ce, "Kada ku saurãra ga wannan Alkur' ãni, kuma ku yi ta yin kuwwa a ckin (lõkacin karãtun) sa, ɗammãninku zã ku rinjaya} [Fussilat: 26].
Wani lokaci kuma suna fuskantar manzon da ƙaryatawa, kamar yadda Allah - Maɗaukakin sarki - Ya bada labari cewa su sunce: {Lallai mu muna zatanka kana daga maƙaryata}, ko kuma suna tuhumar Manzon - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - cewa wanda yake sanar da shi mutum ne, ba wanda yake zo masa da wahayi da daga Allah, Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya ce: {Kuma lalle ne, haƙĩƙa Munã sanin (cẽwa) lalle ne sũ, sunã cẽwa, "Abin sani kawai wani mutum ne yake karantar da shi." Harshen wanda suke karkatar da maganar zuwa gare shi, Ba'ajame ne, kuma wannan (Alƙur'ãni) harshe ne Balãrabe bayyananne} [al-Nahl: 103].
Sukan juyawa manzo baya; da cewa waɗanda suka bishi sune raunana, kamar a cikin faɗinSa - Maɗaukakin sarki - Yana Mai bada labari game da mutanen (Annabi) Nuhu: {Sai mashãwarta waɗanda suka kãfirta, daga mutãnensa, suka ce: "Bã mu ganin ka fãce mutum kake kamarmu, kuma ba mu ganin wani ya bĩ ka fãce waɗanda suke sũ ƙasƙantattunmu ne marasa tunani. Kuma bã mu ganin wata falalã agare ka a kanmu. Ã'a, Munã zaton ku maƙaryata ne} [Hud: 27], Hiraƙl ya ce wa Abu Sufyan: "Kuma na tambayeka: Shin maɗaukakan mutane ne suke binsa ko raunanansu?". (Bukhari ne ya fitar da shi (7), da Muslim (1773).)
Wani lokaci kuma suna yi wa manzanni izgili kamar a cikin faɗinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Ka ce zaku dinga yi wa Allah izgiline da ayoyinSa da manzanSa} [al-Taubah: 65], kuma kamar cikin fadinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Kuma Yanã sassaƙa jirgin cikin natsuwa, kuma a kõ yaushe waɗansu shugabanni daga mutãnensa suka shũɗe a gabansa, sai su yi izgili gare shi. Ya ce: "Idan kun yi izgili gare mu, to, haƙĩƙa mũ mã zã mu yi izgili gare ku, kamar yadda kuke yin izgili} [Hud: 38]. Wani lokaci kuma suna yaudarar manzo, suna kwaɗayi a karkato da shi zuwa garesu, kamar a cikin faɗinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Sunã fatar ka sassauta, su kuma sũ sassauta} [al-Kalam: 9], da faɗinSa Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: {Kuma bã dõmin Mun tabbatar da kai ba, lalle ne, haƙĩƙa, dã kã yi kusa ka karkata zuwa gare su ta wani abu kaɗan} [al-Isra'a: 74].
Wani lokaci kuma suna yi wa manzo girman kai ta hanyar aibanta shi kamar yadda Fir'auna ya cewa (annabi) Musa - aminci ya tabbata agre shi -: {Kõ kuma bã nĩ ne mafĩfĩci ba daga wannan wanda yake shĩ wulakantacce ne kuma bã ya iya bayyanawar magana sai da ƙyar?} [al-Zukhruf: 52].
Da faɗin Abu Sufyan - alhali shi yana Sham - game da annabinmu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: "Sai na cewa sahabbaina lokacin da muka fita: Haƙiƙa al'amrin "Ibnu Abi Kabsha" ya girmama, lallai cewa shi sarkin Banul-Asfar yana jin tsoransa". (Bukhari ne ya fitar da shi (4553), da Muslim (1773), da Tirmizi (2717).)
Wani lokaci kuma masu fada-a ji suna yi wa annabi tsawa da kora daga ƙasa, kamar yadda Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce a sha'anin mutanen (Annabi) Shua'ib: {Mashawarta waɗanda suka yi girman kai daga mutanensa suka ce ga waɗanda aka raunanar, ga waɗanda suka yi ĩmãni daga gare su: "Shin, kunã sanin cẽwaSãlihu manzo ne daga Ubangijinsa?" Suka ce: "Lalle ne mũ, da abin daaka aiko shi, mãsu ĩmãni ne} [al-A'araf: 88].
Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Kafurai suka cewa manzannin su wallahi sai mun fitar daku daga ƙasarmu ko kuma ku dawo addinin mu} [Ibrahim: 13], kuma mutanen (Annabi) Luɗ suka cewa (Annabi) Luɗ da waɗanda suka yi imani tare da shi kamar yadda Allah Ya bada labari game da su: {Ku fitar da su daga alƙaryarku lallai cewa su wasu mutane ne da suke tsarkaka} [al-A'araf: 82]. Kuma kafiran Kuraishawa sun sawa annabinmu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - takunkumi da waɗanda ke tare da shi, da Banu Hashim a cikin kwari shekara uku, kuma suka fitar da shi daga garinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -.
Daga Ibnu Mas'ud - Allah Ya yarda da shi - ya ce: "Lokacin da annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya raba ganimar Hunain, wani mutum daga mutanen Madina ya ce: Ba don Allah ya yi ba, sai na zo wa annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai na ba shi labari, sai fuskarsa ta canja, sannan ya ce: "Rahamar Allah ta tabbata ga (annabi) Musa, haƙiƙa an cutar da shi da mafi yawa daga wannan, sai ya yi haƙuri". (Bukhari ne ya fitar da shi (4335), da Muslim (1062), da Tirmizi (3896).)
Mutanen (Annabi) Ibrahim - aminci ya tabbata agare shi - sun yi ƙoƙarin ƙona shi da wuta, sai Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya tseratar da shi, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Ba wani abu ne amsar mutanensa ba sai sun ce ku kashe shi ko ku ƙonashi} [al-Ankabut: 24], kuma Allah Ya faɗa Yana Mai bada labari daga abinda Banu Isra'ila suka aikata tare da annabawansu: {A duk lokacin da wani manzo ya zo muku da abinda rayukanku ba sa so sai ku yi girman kai, wasu daga ciki kuka ƙaryata wasu kuma kuka kashe} [al-Baƙara: 87].
Wannan shi ne ɗabi'ar masu girman kai tare da manzanni, kuma wannan ita ce sunna mai gudana wacce manya suke binta a cikin kowace al'umma dangane da masu son kawo gyara.
Kuma sunnar Allah ta tabbata da taimakon manzanninSa da annabawanSa - aminci ya tabbata agare su -, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Lalle Mũ, hakĩka, Munã taimakon ManzanninMu da waɗanda suka yi ĩmãni, a cikin rãyuwar dũniya da rãnar da shaidu ke tsayãwa} [Ghafir: 51], kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Sa'an nan kuma Muka gaskata musu alkawari; sai Muka tsẽrar da su da wanda Muke so, kuma Muka halakar da mãsu yawaitãwa} [al-Anbiya'a: 9].
KUNDIN RANAR LAHIRA
Kundin a taƙaice
Muna imani da ranar lahira, kuma cewa shi rukuni ne daga rukunan imani guda shida, an ambaceta ranar lahira; domin cewa ita ce ƙarshen kwanukan duniya, babu wata rana a bayanta, kuma - tana da wasu sunayen masu yawa daga sunayenta: Ranar Alkiyama, da ranar tashi, da ranar hisabi, da ranar sakamako, da masifa, da Haƙƙah, da mai afkuwa, da ihu, da mai lulluɓewa, haƙiƙa Allah Ya ambaci ranar lahira agurare masu yawa daga littafinSa mai girma.
Daga cikin imani da ranar lahira: Yin imani da alamominta - wato alamomin Alkiyama - kuma: Da imani da abinda yake faruwa bayan mutuwa, zamu fara magana akan alamomin Alkiyama, sannan abinda yake faruwa bayan mutuwa; dan kasancewarsu suna afkuwa ne kafin ranar lahira.
Alamomin Alkiyama: Su ne alamomi masu nuni akan kusancin ranar lahira, su suna daga gaibun da Allah Ya yi mana umarni dayin imani da shi.
Su sun kasu kashi uku:
Na farkonsu: Abinda ya bayyana daga alamomin Alkiyama, kuma ya ƙare, to wadannan suna da yawa sosai:
Na biyu: Abinda ya bayyana daga alamomin Alkiyama, sai dai bai ƙare ba, kawai bai gushe ba yana ta bayyana.
Na uku: Abinda bai afku ba daga cikinsu, kawai zasu kasance ne kusa da tashin Alkiyama.
Daga cikin imani da ranar lahira: Imani da cewa kowane abu mai halane sai zatin Sa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -, kuma cewa mala'ikan mutuwa yana ɗaukar rayuka, da kuma imani da abinda yake faruwa bayan mutuwa na tambayar mamaci, da azabar ƙabari da ni'imarsa.
Muna imani da cewa Allah idan Ya yi izini da gushewar wannan duniyar da ƙarewarta, Allah Zai umarci mala'ika, sai ya yi busa ta farko a cikin ƙaho, sai dukkan wanda ke cikin sammai da wanda ke cikin ƙasa su suma sai wanda Allah Ya so, sannan Allah Zai saukar da wani ruwa sai jikkunan halitta su tsiro, sannan Allah Zai yi izni ga mala'ika sai ya yi busa ta biyu a cikin ƙaho, sai a tashesu daga ƙaburburansu, kuma mutane zasu tashi gaba ga Ubangijin talikai, farkon wanda ƙasa zata tsage daga gare shi (shi ne) annabinmu tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, kuma farkon wanda zai farka (shi ne) annabinmu - tsira da a mincin Allah su tabbata agare shi -, kuma farkon wanda za'a tufatar shi ne annabin Allah Ibrahim badadayin Ubangiji Arrahman, mutane zasu tashi marasa takalma tsirara marasa kaciya, kuma kasar tahin kiyama fara ce.
Kuma muna imani da ceton annabinmu - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, kuma muna imani da bujuro da al’umma, da hisabi, da sakamako, kuma cewa Shi - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Mai gaggawar hisabi ne. Kuma hisabin Allah ga bayinSa yana da matakai da halaye mabanbanta, daga bayi akwai wanda za’a yi wa hisabi hisabi mai tsanani, daga cikinsu akwai wanda za’a yi wa hisabi hisabi sassauƙa, daga cikin muminai akwai wanda zai shiga aljanna ba tare da hisabi ba.
Ba'a zalintar wani a wannan ranar, farkon wanda za'a fara yi wa hisabi a ranar lahira al'ummar (Annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, kuma farkon abinda za’a fara yin hukunci a tsakanin mutane a sha'anin jinane ne.
Kuma muna imani cewa shi a wannan ranar za’a zo da shahidai, sai mala'iku su yi shaida, kuma ƙasa ta yi shaida da abinda bayi suka aikata akanta, kuma gaɓɓai su yi shaida.
Muna imani cewa Allah - Maɗaukkain sarki - Zai sanya ma'aunai dan auna ayyukan bayi.
Muna imani cewa manzon Allah - tsira da aminci su tabbata agare shi - yana da wani tafki wanda al'ummarsa zasu gangaro masa, sannan akoro bayi: Kodai zuwa aljanna, ko zuwa wuta - muna neman tsarin Allah - kuma za'a shinfida gada akan Jahannama, yana da arabsakai kamar ƙayar Sa'adana, sai su fauce mutane saboda ayyukansu, farkon wanda zai ƙetare siraɗi shi ne annabinmu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -.
BABIN DALILAN IMANI DA RANAR LAHIRA
Muna imani da ranar lahira, shi rukuni ne daga rukunan imani guda shida waɗanda aka ambata a cikin faɗinSa -Allah Maɗaukakin sarki -: {Ba wai juya fuskoki ɓangaren gabas ko yamma shi ne biyayayya da ɗa'a ba, amma aikin ɗa'a shi ne wanda ya yi imani da Allah da ranar Lahira} [Baƙara: 177], da faɗinSa - Allah yabonSa ya ɗaukaka -: {Amma tabbatattu a cikin ilmi daga gare su, da mũminai, suna ĩmani da abin da aka saukar zuwa gare ka, da abin da aka saukar daga gabãninka, madalla da masu tsai da salla, da mãsu bãyar da zakka, da mãsu ĩmãni daAllah da Rãnar Lãhira. Waɗannan zã Mu bã su lãda mai girma} [Nisa'a: 162].
Kuma Hadisin Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya yi nuni cewa shi ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance ya fito ga mutane wata rana, sai wani mutum ya zo masa, sai ya ce: Ya manzon Allah mene ne imani? ya ce: "Ka yi imani da Allah, da mala'ikunSa, da littafinSa, da haɗuwa daShi, da manzanninSa, kuma ka yi imani da tashin ƙarshe". (Bukhari ne ya fitar da shi (4777), da Muslim (9), da Ibnu Majah (64).)
Kuma dalilai na hankali sun yi nuni akansa, kamar a cikin faɗinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Kuma ya buga Mana wani misãli, kuma ya manta da halittarsa, ya ce: "Wãne ne ke rãyar da ƙasũsuwa alhãli kuwa sunã rududdugaggu * Ka ce: "Wanda ya ƙãga halittarsu a farkon lõkaci Shĩ ke rãyar da su, kuma Shi, game da kõwacce halitta, Mai ilmi ne} [Y. S̃: 78-79], da kuma cikin faɗinSa - Allah sha'aninSa ya buwaya -; {Ya ku mutãne! Idan kun kasance a cikin shakka a Tãshin kiyama, to, lalle ne Mũ, Man halittaku daga turɓaya, sa'an nan kuma daga gudãjin jini, sa'an nan kuma daga taõka wadda ake halittãwa da wadda ba a halittawa dõmin, Mu bayyana muku. Kuma Munã tab batar da abin da Muke so a cikin mahaifa zuwa ga wani ajali ambatacce, sa'an nan kuma Munã fitar da ku kunã jãrĩri, sa'an nan kuma dõmin ku kai ga cikar ƙarfinku. Kuma daga cikin ku akwai wanda ke mutuwa, kuma daga gare ku akwai wanda ake mayarwa zuwa ga mafi ƙasƙancin rãyuwa dõmin kada ya san kõme a bãyan ya sani. Kuma kanã ganin ƙasa shiru, sa'an nan idan Muka saukar da ruwa a kanta, sai ta girgiza kuma ta kumbura, kuma ta tsirar da tsirrai daga kõwane nau'i mai ban sha'awa. [al- Hajj: 5], kuma da faɗin Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka kuma sunayenSa sun tsarkaka -: {Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta} [al-Nazi'at: 27], da faɗinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: {Kuma akwai daga ãyõyinSa cẽwa lalle kai kanã ganin ƙasã ƙẽƙasasshiya, to, idan Mun saukar da ruwa a kanta, sai ta girgiza kuma ta kumbura. Lalle wannan da Ya rãya ta, haƙĩƙa, Mai rãyar da matattu ne. Lalle Shĩ Mai ĩkon yi ne a kan kõwanne abu} [Fussilat: 39], da faɗinSa - Allah sha'aninSa ya buwaya kuma sunayenSa sun tsarkaka -: {Kuma Shi ne wanda Yake fara yin halitta sannan Ya dawo da ita, kuma (dawowar) ta fi sauki a gare Shi} [Rum: 27], da faɗinSa - Allah Ya buwaya -: {Zamu dawo da shi kamar yadda muka fareshi a farkon halitta alƙawarinMune lallai ne Mu Masu aikatawa ne} [al-Anbiyaa: 104].
An ambaceta da ranar lahira; domin cewa ita ce ƙarshen kwanukan duniya, babu wata rana a bayanta, kuma ita - tana da sunaye masu yawa. Daga sunayenta: Ranar Alkiyama, da ranar tashi, da ranar hisabi, da ranar sakamako, da tashin hankali, da Haƙƙah, da mai afkuwa, da kururuwa, da mai lulluɓewa, haƙiƙa Allah Ya ambaci ranar lahira a wurare da yawa daga littafinSa mai girma. Kamar faɗinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Yinin da mutãne ke tãshi zuwa ga Ubangijin halitta?} [al-Muɗaffifin: 6]. Da faɗinSa - Allah yabonSa ya ɗaukaka -: {Rãnar da suke fitowa daga kaburbura da gaugãwa, kamar sũ, zuwa ga wata kafaffiyar (tuta), suke yin gaugãwa} [al-Ma'arij: 43], Da faɗinSa - Allah yabonSa ya ɗaukaka -: {To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo} [al-Nazi'at: 34]. Da faɗiinSa: {To, idan mai tsãwa (busa ta biyu) ta zo * Rãnar da mutum yake gudu daga ɗan'uwansa * Da babarsa da babansa * Da mãtarsa da ɗiyansa * Ga kõwane mutum daga cikinsu, a rãnar nan akwai wani sha'ani da ya ishe shi} [Abasa: 33-37], da faɗinSa: {Yã ku mutãne! Ku bi Ubangijinku da taƙawa. Lalle ne girgizar ƙasa ta tsayuwar Sa'a wata aba ce mai girma * A rãnar da kuke ganin ta dukan mai shãyar da mãma tanã shagala daga abin da ta shãyar, kuma dukan mai ciki tanã haihuwar cikinta, kuma kanã ganin mutãne sunã mãsu mãyẽ alhãli kuwa su bã mãsu mãye ba, amma azãbar Allah ce mai tsanani} [ Hajj: 1-2]. Da faɗinSa - Allah girmanSa ya ɗaukaka kuma sarautarSa ta ɗaukaka -: {Ranar da Zai taraku dan ranar taruwa wancananka ita ce ranar kamunga} [Tagabun: 9].
BABI A CIKIN IMANI DA ALAMOMIN ALKIYAMA
Yana daga cikin imani da ranar ƙarshe: Yin imani da alamominta - wato alamomin tashin Alkiyama- sune alamomi masu nuni akan kusantowar ranar lahira, kamar yadda Allah tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya ce: {Shin sunã jiran wani abu ne? sai dai Sa'a ta jẽ musu bisa ga kwatsam, alhãli kuwa ba su sani ba} [Muhammad: 18], Suna daga gaibun da aka umarcemu da yin imani da shi.
Daga alamomin tashin Alkiyama abinda ya bayyana ya kuma wuce, suna da yawa sosai, daga hakan akwai faɗinSa - annabi tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: "An aikoni ni da Alkiyama kamar wannan daga wannan, ko kamar waɗannan biyun, ya haɗa tsakanin ɗan yatsa na nuni da kuma na tsakiya". (Bukhari ne ya fitar da shi (5301), da Muslim (2950).) Da faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: "Ka ƙirga abubuwa shida kafin Alkiyama: Mutuwata, sannan buɗe Baitil Maƙdis, sannan annobar da zata faru a cikinku kamar rashin lafiyar dabbobi, sannan kwararar dukiya har sai an ba mutum zinari ɗari, sai ya gushe yana mai fushi"... (Bukhari ne ya fitar da shi (3176), da Ibnu Majah (4042).) Da faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi: "Alkiyama ba za ta tashi ba har sai ƙungiyoyi biyu masu girma sun yi yaƙi, za'a samu kisa mai girma tsakaninsu, kuma da'awarsu ɗaya ce, kuma har sai maƙarayata sun bayyana kusan su talatin, dukkaninsu suna da'awar cewa su manzannin Allah ne, kuma har sai an ɗauke ilimi, girgizar ƙasa zata yawaita, zamani zai kusanto, fitinu zasu bayyana, Haraj: zai yawaita, shi ne: Kisa kuma har sai dukiya ta yawaita a cikinku, sai ta kwaranya har sai mai dukiya ya shagalta da wanda zai karɓi sadakarsa, kuma har sai ya kawo masa ita, sai wanda ya kawo masa ita ya ce: bani da wata buƙata da ita, kuma har sai mutane sun yi gasa wajen tsawaita gine-gine...". (Bukhari ya fitar da shi (7121), da Muslim (157), da Tirmizi (2218).)
Kuma yana daga cikin alamomin tashin Alkiyama wanda shi ya afku, saidai cewa bai ƙare ba, kuma bai gushe yana ci gaba ba da faruwa ba, daga cikin hakan afkuwar fitintinu a cikin al'umma (A cikin Bukhari da Muslim akwai Hadisai masu yawa akan fitintinu, sai dai su ba a bayyane suke ba, cewa fitintinu suna daga alamomin Alkiyama; saboda haka ne muka ambaci Hadisai biyu masu zuwa daga Littattafan Sunan; domin a cikinsu akwai bayyanarwa da hakan.) suna da yawa, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Lallai kafin Alkiyama akwai fitintinu kamar wani yanki na dare mai duhu, mutum yana wayar gari a cikinsu yana mumini kuma ya yammanta kafiri, kuma ya yammanta yana mumini ya wayi gari yana kafiri, wanda ke zaune shi ne mafi alheri ga wanda ke tsaye, mai tafiya shi ne mafi alheri ga mai gaggawa, to ku karya gwafunfunanku, ku yanyanke tsirgiyoyinku, ku daki takubbanku da duwatsu, idan an shiga - wato - ga ɗayanku, to ya zama kamar mafi alherin 'ya'yan (annabi) Adam biyu" (Abu Dawud ya fitar da shi (4259), da Tirmizi (2204), da Ibnu Majah (3961), da Ibnu Abi Shaibah (30978), da Ahmad (19662), da al-Rauyani (585).)
kuma tsira da amincin Allah su abbata a gare shi ya ce: "Wasu fitintinu zasu faru kafin Alkiyama kamar wani yanki na dare mai duhu, mutum zai wayi gari a cikinsu yana mumini ya yammanta yana kafiri, kuma zai yanmanta yana mumini ya wayi gari yana kafiri, wasu mutane zasu saida addininsu da wata haja ta duniya". (Tirmizi ne ya fitar da shi (2197), da Ibnu Abi Shaibah a cikin al-Musannaf (31053), da kuma cikin al-Iman (64), da al-Faryani a cikin Siffar munafunci d zargin munafukai (97).)
Kuma tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Alkiyama ba zata tashi ba har sai maƙaryata sun bayyana kusan talatin, dukkaninsu suna da'awar cewa su manzannin Allah ne". (Bukhari ya fitar da shi (7121), da Muslim (157), da Tirmizi (2218).)
Abu Hurairah - Allah ya yarda da shi - ya ce: yayin da Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yake a wani majlisi yana zantar da mutane, sai wani baƙauye ya zo masa, sai yace: Yaushe ne Alkiyama, sai Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yaki ci gaba da maganar sa, sai wasu mutane suka ce: Ya ji abunda ya faɗa, sai yaƙi abinda ya ce. Wasu suka ce: A'a bai jiba, har saida ya gama maganarsa sa, sai ya ce: Ina - ina zatansa - mai tambaya game da Alkiyama ? Sai ya ce gani nan Ya Manzon Allah, sai Manzon Allah Ya ce masa, Idan aka tozartar da amana to ku jirayi alkiyama", sai ya ce, ta yaya ake tozartar da alkiyama, sai Manzon Allah Ya ce, idan aka mika al’amari ga wadanda ba ma’abotansa ba, to ku jira kiyama. (Bukhari ne ya fitar da shi (59).)
kuma tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Daga alamomin Alkiyama, Za'a ɗauke ilimi, jahilci ya tabbata, kuma asha giya, zina ta bayyana". (Bukhari ne ya fitar da shi (80), da Muslim (2671), da Tirmizi (2205), da Ibnu Majah (4045).)
kuma tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Lallai akwai wasu kwanuka kafin Alkiyama, jahilci zai sauka a cikinsu, za'a ɗauke ilimi a cikinsu, kuma kisa zai yawaita a cikinta". (Bukhari ne ya fitar da shi (7062), da Muslim (2672), da Tirmizi (2200), da Ibnu Majah (3959, 4050).)
Daga cikin alamomin tashin Alkiyama waɗanda ba su afku ba har zuwa yanzu, kawai zasu afku kafin tashin Alkiyama Amma za su bayyana kusa da ita, daga cikinsu akwai: Saukar Masihu (annabi) Isa ɗan Maryam - aminci ya tabbata agare shi -, Allah Maɗaukkain sarki Ya ce: {Kuma bãbu kõwa daga Mutãnen Littafi, fãce lalle yanã ĩmãni da shi a gabãnin mutuwarsa, kuma a Rãnar kiyãma yana kasancẽwa mai shaida, a kansu} [al-Nisa'a: 159], da fitowar Yajuju da majuju, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Har sa'ad da aka bũde Yãjũju da Mãjũju alhãli kuwa sunã gaggãwa daga kõwane tudun ƙasa} [Anbiya'a: 96], da fitowar Dabba, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma idan magana ta auku a kansu, Munã fitar musu da wata dabba daga ƙasa, tanã yi musu magana, cẽwa "Lalle mutãne sun kasance game da ayoyinMu, ba su yin ĩmãnin yaƙĩni} [Naml: 82].
Ya zo a cikin Hadisin Huzaifa Dan Usaid al-Gifari ya ce: Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya tsinkaya garemu, alhali mu muna muzakara, sai ya ce: "Me kuke muzakara?" suka ce: Muna tina AlKiyama, ya ce: "Lallai cewa ita (AlKiyama) ba za ta tsaya ba har kafin ta sai kun ga alamomi goma: sai ya ambaci - hayaƙi, da Jujal, da Dabba, da hudowar rana ta mafaɗarta, da saukar (annabi) Isa ɗan Maryam - tsira da amincin Allah su tabbata aagre shi -, da Yajuju da Majuju, da kusufi uku, kusufi a gabas, da kusufi a yamma, da kusufi a tsibirin larabawa, na ƙarshen wata wuta ce da zata fito daga Yaman, tana koro mutane daga mahadarsu". (Muslim ne ya fitar da shi (2901), da Abu Dawud (4311), da Tirmizi (2183), da Ibnu Majah (4041).
kuma tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Alkiyama ba zata tsaya ba har sai rana ta hudo ta mafaɗarta, idan ta hudo daga mafaɗarta mutane za su yi imani gaba ɗayansu, a wannan lokacin {Wani rai imaninta ba zai amfaneta ba wacce dama ba ta kasance ta yi imani ba kafi nan ko ba ta aikata wani alheri ba a cikin imaninta} [al-An'am: 158]". (Bukhari ne ya fitar da shi (4635), da Muslim (157), da Abu Dawud (4312), da Ibnu Majah (4068).)
kuma tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Na rantse da wanda raina yake a hannunSa, Ibnu Maryam (Annabi Isa) ya kusa ya sauka a cikinku yana mai hukunci mai adalci, sai ya karya gicciyayye (cross), ya kashe alade, ya dauke jizya, dukiya ta yawaita har babu wanda zai karɓeta". (Bukhari ne ya fitar da shi (2222), da Muslim (155), da Abu Dawud (4324), da Tirmizi (2233), da Ibnu Majah (4078).)
kuma tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Allah Bai aiko wani annabi ba sai ya gargaɗar da mutanensa (daga sharrin) mai ido ɗaya kuma maƙaryaci, lallai shi (Jujal) mai ido ɗaya ne, kuma Ubanigijinku ba mai ido ɗaya bane - an rubuta tsakanin idanuwansa - Kafiri ne". (Bukhari ne ya fitar da shi (7408), da Muslim (2933), da Abu Dawud (4316), da Tirmizi (2245).)
BABI A CIKIN IMANI DA ABINDA ZAI KASANCE BAYAN MUTUWA
Muna imani cewa yana daga cikin imani da ranar lahira: Yin imani da cewa kowane abu mai halaka ne sai zatinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -, kamar yadda Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kowanne abu mai halaka ne face Fuskarsa} [Kasas: 88], Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya ce: {Dukkan wanda ke kanta mai ƙãrẽwa ne * Kuma Fuskarar Ubangijinka, Mai girman Jalala da karimci, ita ce take wanzuwa} [al-Rahman: 26-27]. Kuma cewa mala'ikan mutuwa yana karɓar rayuka, Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Ka ce: "Mala, ikin mutuwa ne. wanda aka wakkala a gare ku, shĩ ne ke karɓar rãyukanku. Sa'an nan zuwa ga Ubangijinku ake mayar da ku} [al-Sajda: 11].
Muna imani da abinda yake faruwa bayan mutuwa, na tambayar mamaci, da azabar ƙabari da ni'imarsa, kamar yadda yake a cikin faɗinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Wutã, anã gitta su a kanta, sãfe da maraice, kuma a rãnar da Sa'a take tsayuwa, anã cẽwa, "Ku shigar da mutãnen Fir'auna a mafi tsananin azãba} [Ghafir: 46], da faɗinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Za Mu yi musu azaba sau biyu, sa’annan Mu mayar da su zuwa ga azaba mai girma} [al-Taubah: 101], da kuma faɗinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Kuma dã kã gani, a lõkacin da Malã'iku suke karɓar rãyukan waɗanda suka kãfirta, sunã dukar fuskõkinsu da ɗuwãwunsu, kuma suna cẽwa: "Ku ɗanɗani azãbar Gõbara * "Wannan (azãbar) kuwa sabõda abin da hannuwanku suka gabãtar ne. Kuma lalle ne Allah bai zama mai zãlunci ga bãyinsa ba} [al-Anfal: 50-51], Da faɗinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Kuma da zaka ga lokacin da azzalumai a cikin magagin mutuwa kuma mala'iku suna shimfiɗe da hannayensu ku futo da kawunanku (rayukanku), yau ne za'a saka muku da azabar wulaƙanci saboda abinda kuka kasance kuna faɗa wa Allah wanda bana gaskiya ba da kuma abinda kuka kasance kuna girman kai da ayoyinSa}. [al-An'am: 93], da faɗinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Lallai akwai wata azaba koma bayan haka ga waɗanda suka zalinci kansu} [al-Ɗur: 47].
Daga Barra’u ɗan Azib - Allah Ya yarda da shi -, daga annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: {Allah Yana tabbatarwa waɗanda suka yi imani da tabbatacciyar magana} [Ibrahim: 27] ya ce: "Ta sauka ne a azabar ƙabari, sai a ce masa: Waye Ubangijinka? sai ya ce: Ubangijina (Shi ne) Allah, kuma annabina (shi ne) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, wannan kuwa shi ne faɗinSa - Mai girma da ɗaukaka -: {Allah Yana tabbatarwa waɗanda suka yi imani da tabbatacciyar magana a cikin rayuwar duniya da kuma lahira} [Ibrahim: 27]". (Bukhari ne ya fitar da shi (1369), da Muslim (2871), kuma lafazin nasa ne, da Tirmizi (3120), da Nasa'i (2056-2057), da Ibnu Majah (4750, 4269).)
Daga Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su -; Cewa manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance yana sanar da su wannan addu'ar kamar yadda yake sanar da su sura daga AlKur'ani, yana cewa: "Ku ce: Ya Allah mu muna neman tsarinKa daga azabar Jahannama, kuma ina neman tsarinKa daga azabar ƙabari, ina neman tsarinKa daga fitinar Masihul Dajjal, ina neman tsarinKa daga fitinar rayuwa da mutuwa". (Muslim ne ya fitar da shi (590), da Abu Dawud (1542), da Tirmizi (3494), da Nasa'i (2063), da Ibnu Majah (3840).)
Daga Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su - ya ce: Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya fito daga wani sashi na shingayen Madina, sai ya ji sutin wasu mutum biyu ana yi musu azaba acikin ƙaburburansu, sai ya ce: "Ana musu azaba, kuma ba ana musu azaba a wani abu mai girma ba, kuma lalle babba ne, ɗayansu ya kasance ba ya tsarkaka daga fitsari, ɗayan kuma ya kasance yana tafiya da annamimanci", sannan ya ce akawo masa itace na dabino, sai ya karya shi gida biyu, sai ya sanya ɓangare a ƙabarin wannan, ɓangare ɗayan kuma a cikin ƙabarin wannan, sai ya ce: "Watakila a yi musu sauƙi muddin dai ba su bushe ba". (Bukhari ne ya fitar da shi (6055), da Muslim (292), da Abu Dawud (20), da Tirmizi (70), da Nasa'i (31), da Ibnu Majah (347).)
Daga Abu Sa'id - ya ce: Zaid ɗan sabit - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Yayin da Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana cikin shingen Bani Najjar, a kan wani alfadarin sa, kuma muna tare da shi, yayin da ta karkace da shi, ta kusa ta fadar da shi, sai ga wasu ƙaburbura shida, ko biyar, ko huɗu - ya ce: Haka nan al-Jurairi yake faɗa - sai ya ce: "Waye ya san masu waɗannan ƙaburburan?" wani mutum ya ce: Nine, ya ce: Yaushe waɗannan suka mutu? Ya ce: Sun mutu ne a cikin shirka, don haka ya ce: “Wannan al’ummar za’a jarabceta ta tana cikin kabarinta, kuma ba don kada ku binne junanku ba, da na roki Allah da ya jiyar daku wani abu na azabar kabari da nake ji. "Sa'annan ya fuskanto mu da fuskarsa. ya ce:" Ku nemi tsarin Allah daga azabar kabari. "Suka ce:" Muna neman tsarin Allah daga azabar kabari. Ya ce: "Ku nemi tsarin Allah, daga fitintinu, na abin da ya bayyana daga gare ta da abin da yake boye." »Suka ce:" Muna neman tsarin Allah daga fitinar dujal. " (Muslim ne ya fitar da shi (2867).)
Daga Abu Ayub - Allah Ya yarda da shi - ya ce : Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya fito a lokacin rana ta faɗi, sai ya ji wani sauti ,sai ya ce : Wata Bayahudiya ce ake azabtar da ita a cikin ƙabarinta". (Bukhari ne ya fitar da shi (1375), da Muslim (2869), da Nasa'i (2059).)
Daga Aisha -Allah Ya yarda da ita- ta ce: Wasu tsoffin mata guda biyu daga cikin tsoffin Yahudawan Madina sun zo wurina, sai suka ce da ni: Lallai ma'abota ƙabari ana yi musu azaba a cikin ƙaburburansu, sai na ƙaryata su, kuma ban so na gasgata su ba, sai suka fita, sai annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya shigo gurina, sai na ce da shi: Ya Manzon Allah, wasu tsoffin mata biyu kuma na gaya masa labarin, sai ya ce: "Sun yi gaskiya, lallai su ana yi musu azaba, azabar da dabbobi suke ji baki dayansu". Kuma ban taba ganinsa a wata sallah ba face sai ya nemi tsari daga azabar ƙabarin. (Bukhari ne ya fitar da shi (6366), da Muslim (586), da Nasa'i (2067).)
Kamar yadda kafiri da munafiki da wasu daga amsu saɓo daga musulmai ake yi musu azaba a cikin ƙaburburansu, haka nan mumini ana ni'imtashi a cikin ƙabari. Daga Anas ɗan Malik - Allah Ya yarda da shi -cewa shi ya zantar da su: Cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Lallai bawa idan aka sanya shi a cikin ƙabarinsa mutanansa suka juya suka tafi, yana jin sautin takalmansu, mala’iku biyu za su zo masa sai su zaunar da shi su ce da shi me ka kasance kana cewa kan wannan mutumin Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi -? amma mumini sai ya ce : Ina shaida cewa shi bawan Allah ne kuma Manzon Sa ne, Sai a ce masa: Kalli mazauninka a wuta Allah Ya canja maka da wani mazaunin a aljanna, sai ya gansu baki ɗaya”. Y ce: "Amma munafiki da kafiri sai su ce musu : Me kuka kasance kuna cewa kan wannan mutumin? sai ya ce: Ban sani ba, na kasance ne ina fadar abinda mutane suke fada, sai a ce: Baka sani ba kuma baka karanta ba, sai a dake shi da wasu gudumu na karfe duka daya, sai ya yi kara karar da duk wanda biye da shi zai ji ta banda mutum da aljan". ! (Bukhari ne ya fitar da shi (1374), da Muslim (7318).)
BABIN IMANI DA TASHI BAYAN MUTUWA DA ABINDA KE BAYANSA
Muna imani cewa Allah idan Ya yi izini na gushewar wannan duniyar da ƙarewarta, Allah Zai umarci mala'ika sai ya yi busa a cikin ƙaho, sai dukkan wanda ke cikin sammai da wanda ke cikin ƙasa su suma sai wanda Allah Ya so, Allah Maɗaukkain sarki Ya ce: {Kuma aka busa a cikin ƙaho, sai waɗanda ke a cikin sammai da ƙasã suka sũma sai wanda Allah Ya so (rashin sumansa) sannan aka hũra a cikinsa, wata hũrãwa, sai gã su tsaitsaye, sunã kallo} [al-Zumar: 68], kuma tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "...Sannan a yi busa a cikin ƙaho, babu wanda zai ji shi sai ya karkatar da fatar wuya, kuma ya ɗaga fatar wuya, ya ce: Farkon wanda zai ji shi wani mutum ne wanda yake gyara tafkin raƙuminsa, ya ce: Sai ya suma, sai mutane su suma...". (Muslim ne ya fitar da shi (2940).) ("Warafa'a litan", wato ya karkatar da fatar wuyansa gare shi. al-Nihaya fi garibul hadis (3/33).)
kuma tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "...Lallai Alkiyama zata tsaya alhali mutum biyu sun shinfiɗa tufansu a tsakaninsu, ba za su saida su ba, kuma ba za su ninkesu ba, kuma lallai Alkiyama zata tashi alhali mutum ya juya da nonon taguwarsa amma ba zai sha shi ba, lallai Alkiyama zata tashi alhali shi yana gyara tafkinsa amma ba zai shayar a cikinsa ba, lallai Alkiyama zata tsaya alhali ɗayanku ya ɗaga abincinsa zuwa bakinsa amma ba zai ɗanɗane shi ba".
Sai Allah Ya halakar da wanda Ya so daga halittarSa cikin wanda Allah Ya rubuta masa ƙarewa da halaka, har babu wanda zai wanzu sai Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Dukkan wanda ke kanta mai ƙãrẽwa ne * Kuma Fuskarar Ubangijinka, Mai girman Jalala da karimci, ita ce take wanzuwa} [al-Rahman: 26-27], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kada ka kira wani abin bautãwa na dabam tãre da Allah. Bãbu abin bautãwa fãce Shi. Kõwane abu mai halaka ne fãce fuskarSa. Shi ne da hukunci kuma zuwa gare Shi ake mayar da ku} [al-Kasas: 88], kuma Maɗaukakin sarki Ya ce: {Rãnar da suke bayyanannu, bãbu wani abu daga gare su wanda yake iya bõyuwa ga Allah. "Mulki ga wa ya ke a yau?" Yana ga Allah, Makaɗaici, Mai tĩlastãwa} [Gafir: 16].
Sannan Allah Ya saukar da wani ruwa wanda jikkunan halitta zasu tsiro daga gare shi, kamar yadda tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "...Sannan Allah Zai aiko - ko cewa ya yi: Allah zai saukar da - wani ruwa kai kace yayyafi ne - ko: Inuwa - Nu'uman (ɗaya daga maruwaita Hadisin.) ya yi kokwanto - sai jikkunan mutane su tsiro daga gare shi, sannan a sake yin wata busar daban, sai gasu a tsattsaye suna saurare...". (Muslim ne ya fitar da shi (2940).)
Sannan Allah Ya umarci mala'ika sai ya yi busa ta biyu a cikin ƙaho, kamar yadda Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Sannan sai a yi wata busar ta daban a cikin kaho sai gasu a tsaitsaye suna sauraare} [al-Zumar: 68].
Kuma tsira da amincin Allah su tabbata aagre shi ya bayyana gwargwadan abinda ke tsakanin busa biyun, daga Abu Hurairah - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Tsakanin busa biyun arba'in ne, ya ce: Kowane abu daga mutum zai dandaƙe sai ƙashin guringwitsi a cikinsa ne ake hauhawar da halitta". (Bukhari ne ya fitar da shi (4814), da Muslim (2955).)
Kuma muna imani da abinda annabinmu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya bamu labari na halayen sammai da ƙasa a ranar lahira, kamar yadda ya zo a cikin Hadisin Ibnu Mas'ud - Allah Ya yarda da shi - ya ce: "Wani malami daga maluman Yahudawa ya zo wurin manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai ya ce: Ya Muhammad, mu muna samun: Cewa Allah Zai sanya sammai akan yatsa, ƙassai ma akan yatsa, bishiyoyi akan yatsa, ruwa da ƙasa akan yatsa, sauran halittu akan yatsa, sai Ya ce: Nine Sarki. Sai annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi dariya har haƙoransa na gaba suka bayyana dan gasgata maganar malamin Yahudawa, sannan manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya karanta: {Kuma ba su ƙaddara Allah a kan haƙĩƙanin ĩkon yinsa ba: kasã duka damƙarSa ce, a Rãnar kiyãma, kuma sammai abũbuwan naɗewa ne ga dãmanSa. Tsarki ya tabbata a gare Shi, kuma Ya ɗaukaka daga barin abin da suke shirki da shi} [al-Zumar: 67]". (Bukhari ya fitar da shi (4811), da Muslim (2786), da Tirmizi (3238).)
Kuma muna imani cewa mutane za'a tashe su daga ƙaburburansu, sai Allah - Maɗaukakin sarki - Ya raya matattu lokacin da za’a yi busa ta biyu a cikin ƙaho; sai mutane su mike ga Ubangijin talikai, kamar yadda Allah Maɗaukkain sarki Ya ce: {Sa'an nan kuma ku, bãyan wannan, lalle ne masu mutuwa ne * Sa'an nan kuma lalle ne kũ a Rãnar kiyãma, za a tayar da ku} [al-Mua'Minun: 15 - 16], kuma Allah Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma aka yi bũsa a cikin ƙaho, to, sai gã su, daga kaburbura zuwa ga Ubangijinsu, sunã ta gudu * Suka ce: "Yã bonenmu! Wãne ne ya tãyar da mu daga barcinmu?" "Wannan shi ne abin da Mai rahama ya yi wa'adi da shi, kuma Manzanni sun yi gaskiya * Ba ta kasance ba fãce wata tsãwa ce guda, sai gã su duka, sunã abin halartarwa a gare Mu} [Y. S̃: 51-53].
kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma lalle ne Mu Muke rãyarwa, kuma Muke kashẽwa kuma Mũ ne magada * Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun san mãsu gabãta daga cikinku, kuma Mun san mãsu jinkiri * Kuma lalle ne Ubangijinka Shĩ ne Yake tãra su, lalle Shĩ ne Mai hikima, Masani} [al-Hijr: 23-25].
kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma suka ce: "Shin, idan mun kasance ƙasũsuwa da, niƙaƙƙun gaɓãɓuwa ashe, lalle ne mũ haƙĩƙa, waɗanda ake tãyarwa ne a wata halitta sãbuwa? * Ka ce: "Ku kasance duwãtsu ko kuwa baƙin ƙarfe * Kõ kuwa wata halitta daga abin da yake da girma a cikin ƙirazanku." To zã su ce "Wãne ne zai mayar da mu?" Ka ce: "Wanda Ya ƙaga halittarku a fabkon lõkaci." To, zã su gyaɗa kansu zuwa gare ka, kuma sunã cẽwa, "A yaushene shi?" Ka ce: "Akwai tsammãninsa ya kasance kusa * A rãnar da Yake kiran ku, sa'an nan ku riƙa karɓãwa game dã gõde Masa, kuma kunã zaton ba ku zauna ba fãce kaɗan} [al-Isra'a: 49-52], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma wanda Allah Ya shiryar, to, shĩ ne shiryayye, kuma wanda Ya ɓatar to bã zã ka sãmi waɗansu masõya gare su ba baicinSa. Kuma Munã tãra su a Rãnar kiyãma a kan fuskõkinsu, sunã makãfi, kuma bẽbãye da kurãme. Matattararsu Jahannama ce, kõ da yaushe ta bice, sai Mu ƙãra musu wata wuta mai tsanani * Wancan ne sãkamakonsu sabõda lalle sũ, sun kãfirta da ãyõ yinMu, kuma suka ce: "Shin idan muka kasance ƙasũsuwa da nĩƙaƙƙun gaɓũɓuwa, shin lalle mũ, haƙĩ ka, waɗanda ake tãyarwa ne a cikin wata halitta sãbuwa? * Shin, kuma ba su ganĩ ba (cẽwa) lalle ne Allah, wandaYa halicci sammai da ƙasa, Mai ikon yi ne a kan Ya halicci misãlinsu? Kuma Ya sanya wani ajali wanda bãbu kõkwanto a cikinsa? Sai azzãlumai suka ƙi fãce kãfirci} [al-Isra'a: 97-99], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Idan aƙawarin ƙarshe ya zo zamuzo daku jama'a-jama'a} [al-Isra'a: 104], Ayoyi masu girma a cikin tabbatar da tashi daga ƙabari masu yawa ne sosai.
Farkon wanda ƙasa zata tsage masa shi ne annabinmu tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, daga Abu Hurairah - Allah Ya yarda da shi - cewa annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Ni ne shugaban 'ya'yan Adam ranar Alkiyama, kuma farkon wanda ƙabari zai tsagewa, kuma farkon mai ceto farkon wanda za'a bawa ceto". (Muslim ya fitar da shi (2278), da Abu Dawud (4673).)
Kuma farkon wanda zai farka shi ne annabinmu tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ; inda tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Kada ku fifitani akan Musa; domin mutane zasu suma a ranar Alkiyama, sai in suma tare da su, sai in zama farkon wanda zai farfaɗo, sai ga Musa yana riƙe da gefen Al'arshi, ban sani ba shin yana daga cikin waɗanda suka suma, sai ya farka kafin ni ko ya kasance daga waɗanda Allah Ya togance?", (Bukhari ne ya fitar da shi (2441), da Muslim (2373).)
Kuma farkon wanda za'a tufatar shi ne annabin Allah Ibrahim badaɗayin Allah ArRahman, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Farkon wanda za'a tufatar a ranar lahira (shi ne) (Annabi) Ibrahim". (Bukhari ya fitar da shi (3349), da Muslim (2860), da Tirmizi (2423), da Nasa'i (2082).)
Za'a tashi mutane marasa takalma tsirara marasa kaciya, kamar yadda tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Za'a tashi mutane ranar Alkiyama marsa takalma tsirara marasa kaciya". (Bukhari ne ya fitar da shi (6527), da Muslim (2859), da Nasa'i (2083), da Ibnu Majah (4276).)
Kuma muna imani cewa ƙasar da za’a tashi bayi akanta wata ƙasa ce ba wannan ƙasar ba, kamar yadda Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {A rãnar da ake musanya ƙasa bã ƙasar nan ba, da sammai kuma su bayyana ga Allah Makaɗaici, Mai tanƙwasãwa} [Ibrahim: 48].
Kasar taruwa fara ce, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Za'a tashi mutane ranar AlKiyama akan wata ƙasa fara jaja-jaja kamar tatacciyar gurasa". (Bukhari ne ya fitar da shi (6521), da Muslim (2790).)
Daga Abu Said al-Khudiri cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Kasa zata kasance ranar Alkiyama gurasa ɗaya, Ubangiji AlJabbar Zai jujjuyata da hannunSa kamar yadda ɗayanku yake jujjuya gurasarsa a halin tafiya...". (Bukhari ne ya fitar da shi (6520), da Muslim (2792).)
Haƙiƙa Hadisai ingantattu sun zo a cikin bayanin ina mutane zasu kasance a lokacin canji: Daga Sauban Baran manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - cewa wani malami daga maluman Yahudawa ya zo wurin manzo yana tambayarsa a cikinsa: "...Sai Bayahude ya ce: Ina mutane zasu kasance ranar da za'a canza ƙasa ba wannan ƙasar ba da sammai? sai manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: Su suna cikin duhu bayan gada". (Muslim ne yafitar da shi (315).)
Daga A'isha - Allah Ya yarda da ita - ta ce: "Na tambayi manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - game da faɗinSa - Mai girma da ɗaukaka -: {Ranar da za'a canja ƙasa ba wannan ƙasar ba da sammai} to ina mutane zasu kasance a wannan ranar ya manzon Allah? sai ya ce: Akan siraɗi". (Muslim ne ya fitar da shi (2791).)
Kuma muna sanin cewa wannan ranar mai girma ce sosai, kamar yadda Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Ashe! Waɗancan bã su tabbata cẽwa lalle sũ, ana tãyar da su ba * Domin yini mai girma} [al-Muɗaffifin: 4- 5]. Sha'aninSa ya ɗaukaka Ya ce: {Yã ku mutãne! Ku bi Ubangijinku da taƙawa. Lalle ne girgizar ƙasa ta tsayuwar Sa'a wata aba ce mai girma} [al-Hajj: 1].
Kuma cewa gwargwadanta shekara dubu hamsin ne, kamar yadda Hadisi ya inganta da hakan, daga Abu Hurairah - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Babu wani ma'abocin taska ba ya bada zakkartsa har zuwa inda ya ce: Har Allah Ya yi hukunci tsakanin bayinSa a cikin wani yinin da gwargwadansa shekara dubu hamsin ne daga abinda kuke ƙirgawa, sannan ya ga tafarkinsa kodai zuwa aljanna ko kuma zuwa wuta". (Bukhari ne ya fitar da shi (2371), da Muslim (987), da Abu Dawud (1658), da Tirmizi (1636), da Nasa'i (3563), da Ibnu Majah (2788).)
A cikinta ne rana zata kusantowa ƙasa, daga Abu Umamah - Allah Ya yarda da shi - cewa manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Za'a kusantowa halitta rana a yinin Alkiyama har sai ta kusa kamar gwargwadan mil daga gare su" - Sulaim ɗan Amir ya ce: Na rantse da Allah ban sani ba me yake nufi da mil? Shin faɗin ƙasa ne, ko kuma mil ɗin da ake wa ido kwalli? - ya ce: "Sai mutane su zama akan gwargwadan ayyukansu cikin gumi, daga cikinsu akwai wanda zai kasance zuwa idanun sawunsa, daga cikinsu akwai wanda zai kasance zuwa guwoyinsa, daga cikinsu akwai wanda zai kasance zuwa kwankwasonsa, daga cikinsu akwai wanda zai yi masa linzmi linzami". (Muslim ne ya fitar da shi (2864), da Tirmizi (2421).)
Muminai zasu kare zafin rana da abinda ya rigaya garesu na kyawawan (ayyuka), daga cikinsu akwai wanda yake inuwantuwa da inuwar Al'arshi, kamar yadda tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Mutum bakwai Allah Zai inuwantar da su a cikin inuwarSa, ranar da babu wata inuwa sai inuwarSa". (Bukhari ne ya fitar da shi (660), da Muslim (1031).)
Daga cikinsu akwai wanda "Baƙara" da "Aal-Imran" za su yi masa inuwa, kuma su yi kariya gare shi, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Ku karanta Alkur’ani domin zai zo ranar Alkiyama yana mai ceton ma'abotansa. Ku karanta surori biyu Baƙara da Al-Imran cewa su za su zo a ranar al-Kiyama kamar giza-gizai ko kamar wata tawagar tsuntsaye sun yi sahu suna kare ma'abocinsu, ku karanta Surat al-Baƙara don haddace ta albarka ne, kuma barinta asara ne, kuma matsafa ba zasu iya ta ba". (Muslim ne ya fitar da shi (804).) Daga cikinsu akwai wanda zai inuwanta da inuwar sadakarsa, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Kowane mutum (yana) cikin inuwar sadakarsa har sai an yi hukunci tsakanin mutane". (Ahmad ne ya ruwaito shi (17333), da Abu Ya'ala (1766), da Ibnu Khuzaimah (2431), da Ibnu Hibban (3310), kuma Ibnu Khuzaimah da Ibnu Hibban sun inganta shi).)
BABI AKAN CETO RANAR ALKIYAMA DA ZUWAN UBANGIJI DA KUMA ZUWANSA DAN RABE HUKUNCI TSAKANIN BAYINSA
Muna imani cewa ceto na Allah ne - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Ka ce: "Cẽto gabã ɗaya ga Allah yake. Mulkin sammai da ƙasã Nãsa ne. Sa'an nan zuwa gare Shi ake mayar da ku} [al-Zumar: 44].
Muna imani cewa babu wani da zai yi ceto a wurinSa (Allah) sai da izninSa, Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Wane ne wanda yake iya yin ceto a warinSa, in bada da Izininsa?} [Baƙara: 255], Kuma masu ceto ba zai yi ceto ba sai ga wanda Allah ArRahman Ya yarda da maganarsa da kuma aikinsa, Allah - sha'aninSa Ya buwaya - Ya ce: {Kuma ba za su yi ceto ba sai ga wanda Ya yarda, kuma su masu sauna ne saboda tsoronSa} [al-Anbiya'a: 28], kuma Allah Maɗaukaki Ya ce: {A yinin nan cẽto bã ya yin amfãni fãce wanda Mai rahama Ya yi masa izni kuma Ya yarda da shi, da magana} [Daha: 109].
Kuma muna imani cewa mafi cancantar mutane da ceton masu ceto sune masu ikhlasi da tauhidi, ya zo a cikin Hadisi daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - cewa shi ya ce: An ce: Ya manzon Allah, waye mafi cancanta da cetonka ranar AlKiyama? manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Haƙiƙa ya Abu Hurairah yi zatan babu wanda zai rigaka tambayata game da wannan Hadisin; dan abinda na gani na kwaɗayinka akan Hadisi, mafi cancanta da cetona ranar AlKiyama, wanda ya ce: Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah yana mai tsarkakewa daga zuciyarsa, ko ransa". (Buhari ne ya fitar da shi (99, 6570).)
Kuma muna imani cewa kafirai ceton masu ceto ba ya samunsu, Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Sabõda haka cẽton mãsu cẽto bã zai amfãne su ba} [al-Mudathir: 48].
Kuma muna imani cewa Allah Zai yi izini da ceto ga wanda Ya so daga bayinSa; dan girmamawa ga mai ceton da kuma rahama ga wanda za'a ceta. Kuma muna sanin cewa mafi girman masu ceto ranar AlKiyama shi ne annabinmu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, zai yi ceto da yawa, kuma mafi girmansu mafi ɗaukakarsu ceto ga wadanda suke tsaye, domin yin hukunci tsakaninsu, wannan shi ne matsayi abin yabo, shi ne wanda Allah Ya ambace shi a cikin littafinSa, sai sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Kuma da dare, sai ka yi hĩra da shi (Alƙur'ãni) akan ƙãri gare ka. Akwai tsammãnin Ubangijinka Ya tãyar da kai a wani matsayi gõdadde} [al-Isra'a: 79], kuma a ciin Hadisin Ibnu Umar - Allah Ya yarda da su - a wurin Bukhari: "...Sai ya yi ceto dan yin hukunci tsakanin halitta, sai ya tafi har sai ya yi riƙo da kewayen ƙofa a wannan lokacin Allah Zai tashe shi a matsayi abin yabo dukkan waɗanda ke cikin taro zasu yaba masa". (Bukhari ne ya fitar da shi (1475)). A wannan Hadisin sai ya ambaci ceto a cikin rabe hukunci, kuma Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - cewa shi Zai zo domin rabe hukunci kamar yadda yake a cikin faɗinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Shin suna jira, fãce dai Allah Ya je musu a cikin wasu inuwõyi na girgije, da malã'iku, kuma an hukunta al'amarin? Kuma zuwa ga Allah al'amurra ake mayar da su} [al-Baƙara: 210]. Da faɗinSa - Allah sha'aninSa ya ɗaukaka -: {Kuma Ubangijinka Ya zo, alhãli malã'iku na jẽre, sahu- sahu} [al-Fajr: 22]. Da faɗinSa - Allah sha'aninSa ya buwaya -: {Shin suna jiran (wani abu) face dai mala'iku suje musu, ko kuwa Ubangijinka Yaje, ko kuwa sashen ayoyin Ubangijinka} [al-an'am: 158].
Sannan ceto na shigar 'yan aljanna aljanna, haƙiƙa Hadisai masu yawa mutawatirai sun yi nuni akan waɗannan ceton, daga cikinsu Hadisin Anas - Allah Ya yarda da shi - shahararre cewa shi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Idan ranar AlKiyama ta zo mutane zasu rikice sashinsu a cikin sashi, sai su zo wa (annabi) Adam, sai suce: ka nemamana ceto ga Ubangijinka, sai ya ce: ni bani ne mai ita ba, sai dai kuje gurin (annabi)Ibrahim, domin shi ne badaɗayin ArRahman, sai su zo wa (annabi) Ibrahim, sai ya ce: ba nine mai ita ba, sai dai kuje wa (annabi) Musa; domin cewa shi ne wanda ya yi zance da Allah, sai su zo wa (annabi) Musa, sai ya ce: bani da ita, sai dai kuje wa (annabi) Isa; domin cewa shi ne Ruhin Allah kuma kalmarSa, sai su zo wa (annabi) Isa, sai ya ce: bani da ita, sai dai kuje wurin (annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, sai su zo min, sai in ce: Nike da ita, sai in nemi izinin Ubangijina, sai a yi mini izini, kuma ya yi mini ilhamar wasu kalmomin yabo da zan yabeShi da su baz zasu halarto min yanzu ba, sai in yabeShi da waɗancan kalmomin yabon, sai in faɗi ina mai sujjada, sai ya ce: Ya Muhammad, ka ɗago kanka, ka faɗa za'ajika, ka yi tambaya za'a baka, ka nemi ceto za'a baka ceto, sai in ce: Ya Ubangiji al'ummata, al'ummata, sai ya ce: Ka tafi ka fitar da wanda ya kasance a cikin zuciyarsa akwai gwargwadan gashi na imani, sai intafi, sannan in dawo, sai in yabe shi da wadancan kalmonin yabon, sanna in fadi ina mai sujjada, sai a ce: Ya Muhammad ka ɗago kanka ka faɗa za’a ji ka ka yi tambaya za'a baka shi, ka nemi ceto za'a baka ceto, sai in ce: Ya Ubangiji al'ummata al'ummata, sai Ya ce; Ka tafi kafitar da wanda ya kasance acikin zuciyarsa akwai mafi kasan mafi kasan mafi kasan kwatankwacin kwayar komayya na imani, sai infitar da su daga wuta, sai in tafi sai in aikata". lokacin da muka fita daga gurin Anas na cewa wasu daga abokananmu; da zamu je wurin Hassan alhali shi yana boye a gidan Abu Khalifa, mu zantar da shi da abinda Anas Dan Malik ya zantar damu sai muka je wurinsa, sai muka yi masa sallama sai ya yi mana izini, sai mukace masa: Ya kai Abu Sa'id, mun zo maka daga wurin dan uwanka Anas ɗan Malik, bamu taba ganin kwatankacin abinda ya zantar da mu ba dangane da ceto, sai ya ce: ku faɗa, sai muka zantar da shi da Hadisin, sai ya tiƙe zuwa wannan gurin, sai ya ce: To ku ƙaro, sai muka ce bai ƙara mana ba akan wannan, sai ya ce: Haƙiƙa ya zantar da ni - shi gaba ɗaya - tun tsawon shekara ashirin, ban saniba shin ya manta ne ko ya ƙi ne don kada ku dogara? muka ce: Ya kai Abu Sa'id, ka zantar da mu, sai ya yi dariya, ya ce: An halicci mutum mai gaggawa, abnida zan zantar daku sai ina nufin in zantar da ku, ya zantar da ni kamar yadda ya zantar da ku shi, ya ce: "Sannan in koma karo na hudu sai in yabe shi da wadancan kalmomin yabon, sanna in fadi ina mai sujjada, sai a ce: Ya Muhammad ka dago kanka, ka fada za’a ji, ka tambaya za'a baka shi, ka nemi ceto za'a baka ceton, sai in ce: Ya Ubangiji ka yi min izini ga wanda ya ce: Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, sai ya ce: na rantse da buwayaTa da girmaNa, da burinkasaTa, duk wanda ya ce: babu abin bautawa da gaskiya sai Aallah zan fitar da shi daga cikinta". (Bukhari ne ya fitar da shi (7510), da Muslim (193), da Ibnu Majah (4312).)
Daga cikinsu akwai Hadisin Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - shi kwatankwacin Hadisin Anas ne - Allah Ya yarda da shi -, kuma a ƙarshensa ya ce: "...Ku tafi wurin Muhammad, sai su zo min sai su ce: Ya Muhammad, kai ne manzon Allah, cikamakin annabawa, Allah Ya gafarta maka abinda ya gabata daga zunubinka da abinda ya jinkirta, ka nemamana ceto ga Ubangijinka, shin baka ganin abinda muke ciki? baka ganin inda muka kai? sai in tafi, sai in zo ƙarƙashin Al'arshi, sai in faɗi ina mai sujjada ga Ubangijina, sannan Allah Ya buɗe min sai Ya yi mini ilhama daga kalmomin yabonSa, da kyakkyawan yabo gareShi wani abu wanda bai buɗewa wani ba kafinni, sannan a ce: Ya Muhammad, ka ɗaga kanka, ka yi tambaya za'a baka shi, ka nemi ceto za'a baka ceto, sai in ɗaga kaina, sai in ce: Ya Ubangiji al'ummata al'ummata, sai a ce: Ya Muhammad, ka shaigar da wanda babu wani hisabi akansu aljanna daga al'ummarka daga kofar dama daga kofofin aljanna, su masu tarayya da mutanene a kofofin da ba wadannan ba, na rantse da wanda ran muhammad yake a hannunSa, lallai tsakanin ginshikai biyu daga ginshikan aljanna kamar tsanain Makka ne da ijr, ko kamar tsakani Makka da Busrah. (Bukhari ne ya fitar da shi (3340), da Muslim (194).)
Daga cikinsu akwai Hadisin Anas ɗan Malik - Allah Ya yarda da shi -: Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Ni ne faron wanda zai yi ceto a cikin aljanna, ba'a gasgata wani annabi ba cikin annabawa irin yadda aka gasgatani, lallai cikin annabawa akwai wani annabi babu wanda ya gasgata shi daga al'ummarsa sai mutum ɗaya". (Muslim ne ya fitar da shi (196), da al-Darimi (52).)
kuma tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Kowane annabi yana da addu'ar da ya roƙa sai aka amsa masa, sai na sanya addu'ata ceto ga al'ummata ranar Alkiyama". (Bukhari ne ya fitar da shi (6305)). kuma tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Kowane annabi yana da addu'ar da aka amsa masa ita wacce ya roƙa, Ina son in ɓoye addu'ata ta zama ceto ga al'ummata a lahira". (Bukhari ne ya fitar da shi (6304), da Muslim (199), da Tirmizi (3602), da Ibnu Majah (4307).)
Kuma muna imani cewa Allah kamar yadda Ya girmama annabinmu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - da ceto, haka nan Yake girmama annabawa da mala'iku da muminai, daga Abu Sa'id Khudr - Allah Ya yarda da shi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "...Sai Allah - Mai girma da ɗaukaka - Ya ce: Mala'iku za su yi ceto, annabawa ma za su yi ceto, muminai ma za su yi ceto, babu wanda ya rage sai Mafi jin ƙan masu jin ƙai, sai Ya yi damƙa damƙa ɗaya daga wuta, sai Ya fitar da wasu mutanen da ba su aikata alheri ba ko sau ɗaya". (Bukhari ne ya fitar da shi (7439), da Muslim (183).)
BABIN BUJUROWA DA HISABI DA RABA TAKARDU
Muna imani cewa kowane mutum za'a ba shi littafinsa, sai ya karɓi littafinsa, Allah Ya ce - alhali maganarSa gaskiya ce: {To, amma wanda aka bai wa littãfinsa a dãmansa, sai ya ce wa (makusantansa), "Ku karɓa, ku karanta littafina} [al-Haƙah: 19].
Da mai karɓar littafinsa da hagunsa, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma wanda aka bai wa littãfinsa ga hagunsa, sai ya ce: "Kaitona, ba a kãwo mini littãfina ba!} [al-Haƙah: 25], Ko ya karɓeshi ta bayan bayansa, Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya ce: {Kuma amma wanda aka bai wa littãfinsa, daga wajen bãyansa} [al-Inshiƙaƙ: 10], sai a ce masa: {Karanta Littãfinka. Ranka ya isa ya zama mai hisãbi a kanka a yau] [al-Isra'a: 14], Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Kuma aka aza littãfin ayyuka, sai ka ga mãsu laifi sunã mãsu jin tsõro daga abin da ke cikinsa, kuma sunã cẽwa "Kaitonmu! Mẽne ne ga wannan littãfi, bã ya barin ƙarama, kuma bã ya barin babba, fãce yã ƙididdige ta?" Kuma suka sãmi abin da suka aikata halarce. Kuma Ubangijinka bã Ya zãluntar kõwa} [Kahf: 49].
Kuma muna imani da bujurowa, Allah Ya ce - alhali maganarSa gaskiya ce: {A rãnar nan zã a bijirã ku (dõmin hisãbi), bãbu wani rai, mai ɓoyewa, daga cikinku, wanda zai iya ɓõyẽwa} [al-Hakah: 18], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma a gittã su ga Ubangijinka sunã sahu guda, (Mu ce musu), "Lalle ne haƙĩƙa kun zo Mana, kamar yadda Muka halitta ku a farkon lõkaci. Ã'a, kun riya cẽwa bã zã Mu sanya mukuwani lõkacin haɗuwa ba} [al-Kahf: 48]. Daga Adi ɗan Hatim ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: ‘’Babu wani daga cikinku face sai ya yi magana da Ubangijinsa babu wani tafinta a tsakaninsu, sai ya yi duba zuwa daman sa ba zai ga komai ba face abinda ya aikaata, sai ya yi duba zuwa hagu shima ba zai ga komai ba face abinda ya aikata, sai ya yi duba zuwa gabansa ba zai ga komai ba sai wuta wajen fuskarsa, to ku ji tsoron wuta koda kuwa da gutsiren dabino ne". (Bukhari ne ya fitar da shi (6539), da Muslim (1016).)
Muna imani da hisabi, kuma cewa Allah Zai yi wa bayinSa hisabi, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Lalle ne, zuwa gare Mu kõmõwarsu take * Sa'an nan lalle ne aikinMu ne Mu yi musu hisãbi} [al-Gashiya: 25-26], wanda ya sami alheri to ya godewa Allah, wanda ya sami wanin hakan kada ya zargi kowa sai kansa, kamar yadda hadisi ya inganta daga annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - da hakan: "...Yaku bayiNa kaɗai sune ayyukanku ina kiyaye muku su, sannan in cika muku su, wanda ya sami alheri to ya godewa Allah, wanda ya sami wanin hakan to kada ya zargi kowa sai kansa". (Muslim ne ya fitar da shi (2577).)
Shi - tsarki ya tabbatar maSa - Mai saurin hisabi ne, sha'aninSa Ya ɗaukaka Ya ce; {Yau anã sãka wa kõwane rai a game da abin da ya aikata, bãbu zãlunci a yau. Lalle Allah Mai gaggawar hisãbi ne} [Ghafir: 17].
Muna imani cewa wasu daga cikin muminai zasu shiga aljanna babu hisabi, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Mutum dubu saba'in daga al'ummata zasu shiga aljanna ba tare da hisabi ba...". (Bukhari ne ya fitar da shi (5811), da Muslim (216), kuma lafazin nasa ne).
Hisabin Allah ga bayinSa matakaine da halaye mabanbanta, daga bayi akwai wanda za’a yi masa hisabi mai tsanani, daga cikinsu kuma akwai waɗanda za’a yi wa hisabi mai sauƙi, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {To, amma wanda aka bai wa littãfinsa da damansa * To, za a yi masa hisãbi, hisãbi mai sauƙi} [al-Inshiƙaƙ: 7-8].
Daga A'isha - Allah Ya yarda da ita - daga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Babu wani da za’a yi masa hisabi ranar lahira sai ya halaka". (Bukhari ne ya fitar da shi (6537), da Muslim (2876).) sai na ce: Ya manzon Allah, shin Allah - Maɗaukkain sarki ba ya ce ba: {To, amma wanda aka bai wa littãfinsa da damansa * To, za a yi masa hisãbi, hisãbi mai sauƙi}? [al-Inshiƙaƙ: 7-8], sai manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Wannan kaɗai bijurowa ne, babu wani da za'a yi masa hisabi ranar lahira sai an yi masa azaba". (Bukhari ne ya fitar da shi (6537)). Kuma ba za'a zalinci wani ba a wannan ranar, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma ku ji tsõron wani yini wanda ake mayar da ku a cikinsa zuwa ga Allah, sa'an nan kuma a cika wa kõwane rai abin da ya sanã'anta, kuma sũ bã a zãluntar su} [al-Baƙara: 281].
Farkon wanda za’a yi wa hisabi ranar lahira daga al'ummu, al’ummar (annabi) Muhammad; saboda faɗinSa -tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: "...Mune na ƙarshe daga mutanen duniya, kuma na farko ranar AlKiyama, waɗanda za’a yi wa hukunci kafin halittu". (Muslim ne ya ruwaito shi (856).)
Farkon abnida za'a yi hukunci akan shi tsakanin mutane a jinane ne; saboda faɗin annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: "Farkon abinda za’a yi huknci a tsakanin mutane a ranar Alkiyama akan jinane ne". (Bukhari ne ya fitar da shi (6864), da Muslim (1678).)
Kuma muna imani cewa shi a wannan ranar za’a zo da masu shaida, sai mala'iku su yi shaida, kuma ƙasa ta yi shaida da abinda bayi suka aikata akanta, kuma gaɓɓai su yi shaida, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Lalle Mũ, hakĩka, Munã taimakon ManzanninMu da waɗanda suka yi ĩmãni, a cikin rãyuwar dũniya da rãnar da shaidu ke tsayãwa} [Ghafir: 51], kuma Allah Ya ce; {Kuma ƙasã ta yi haske da hasken Ubangijinta, kuma aka aza littãfi, kuma aka zo da Annabãwa da mãsu shaida, kuma aka yi hukunci a tsakãninsu, da gaskiya, alhãli kuwa, sũ, bã zã a zãlunce su ba} [al-Zumar: 69], Kuma Allah - sh'aninSa ya buwaya - Ya ce: {A rãnar nan, zã ta faɗi lãbãrinta] [al-Zalzalah: 4], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {A yau, Munã sanya hãtimin rufi a kan bãkunansu, kuma hannãyensu su yi Mana magana, kuma ƙafãfunsu su yi shaidu da abin da suka kasance sunã aikatãwa} [Y. S̃: 65].
A cikin "Ingantaccen Hadisi' daga Hadisin Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - akwai ambatan shaidar gaɓɓai akan bayi, a cikinsa: "...Sannan za'a ce masa: a yanzu zamu aiko maka mai mana shaida akanka, sai ya yi tinani a ransa: Waye zai yi min shaida? sai a rufe bakinsa, sai a cewa cinyarsa da namansa da ƙasusuwansa: Ku yi magana, sai cinyarsa da namansa da ƙasusuwansa su furta ayyukansa, hakan dan ya yi wa kansa hanzari, wannan kuwa munafiki ne, wannan kuwa wanda Allah Ya yi fushi akansa ne". (Muslim ne ya fitar da shi (2968).)
Kuma daga Anas ɗan Malik ya ce: Mun kasance a wurin manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai ya yi dariya, sai ya ce: "Shin kun san abinda nakewa dariya?" ya ce: Muka ce: Allah da manzonSa ne mafi sani, ya ce: "Cikin tattaunawar bawa ga Ubangijinsa, zai ce: Ya Ubangiji, shin baka tseratar dani ba daga zalinci? ya ce: sai ya ce: Eh, ya ce: Sai ya ce: Lallai ni ba zan halastawa kaina mai shaida ba sai daga gareNi, ya ce: Sai ya ce: Kanka ya isheka ya zama mai shaida a gareka, da kuma masu girma marubuta su zama amsu shaida, ya ce: Sai arufe bakinsa, sai acewa gaɓɓansa: Ku yi magana, ya ce: Sai su furta ayyukansa, ya ce: Sannan abarshi tsakaninsa da zance, ya ce: Sai ya ce: Nisanta ya tabbata gareku, akanku ne nake fafutika". (Muslim ne ya fitar da shi (2969).)
BABIN IMANI DA MA'AUNAI
Muna imanin cewa Allah Zai sanya ma'aunai dan auna ayukan bayi, kamar yadda Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma Munã aza ma'aunan ãdalci ga Rãnar ¡iyãma, sabõda haka ba a zãluntar rai da kõme. Kuma kõ dã ya kasance nauyin ƙwãya daga kõmayya ne Mun zo da ita. Kuma Mun isa zama Mãsu hisãbi] [al-Anbiya'a: 47], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma awo a rãnar nan ne gaskiya. To, wanda sikẽlansasuka yi nauyi, to, waɗannan sũ ne mãsu cin nasara * Kuma wanda sikẽlansa suka yi sauƙi, to, waɗannan ne waɗanda suka yi hasarar rayukansu, sabõda abin da suka kasance, da ãyõyinMu, sunã yi na zãlunci} [al-A'araf: 8-9], shi ma'aunine na haƙiƙa yana da ma'aunai guda biyu da harshe ana auna ayyukan bayi da shi.
kuma muna imani cewa ayyukan bayi za'a ɗorasu a kan ma'aunai, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Kalmomi biyu masu sauƙi a harshe, masu nauyi a cikin ma'auni, masu soyuwa zuwa ga Mai jin ƙai: Tsarki ya tabbatar wa Allah da godiyar Sa, tsarki ya tabbatar wa Allah Mai girma". (Bukhari ne ya fitar da shi (6682), da Muslim (2694), da Tirmizi (3467), da Ibnu Majah (3806).)
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Tsarki tsagi ne na imani, (faɗin) godiya ta tabbata ga Allah yana cika ma'auni...". (Muslim ne ya fitar da shi (223), da Tirmizi (3517), da Nasa'i (2437), da Ibnu Majah (280).)
Kuma muna sanin cewa mai aiki ana ɗora shi tare da aikinsa a cikin ma'auni, daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - daga annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Lallai cewa babban mutum zai zo ranar lahira, a wurin Allah ba zai yi nuyin fiffikan sauro ba", ya ce: Ku karanta: {A ranar lahira ba zamu tsayar musu da awo ba} [al-Kahfi: 105], (Bukhari ne ya fitar da shi (4729), da Muslim (2785).) Haka nan za’a ɗora takardun ayyuka akan ma'auni kamar yadda Hadisin kati ya yi nuni. (Tirmizi ne ya fitar da shi (2639), da Ibnu Majah (4300), da Ibnul Mubarak a cikin al-Musnad (100), da kuma cikin al-Zuhd (2/109), da Ahmad (6994).)
BABIN IMANI DA TAFKI.
Muna imani cewa manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata aagre shi - yana da wani tafki wanda al'ummarsa zasu gangaro masa, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Lalle ne Mu, Mun yi maka kyauta mai yawa} [al-Kausar: 1].
Daga Anas - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Wata rana manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana cikinmu lokacin da ya yi gynagyaɗi gyangyaɗi sannan ya ɗaga kansa yana murmushi, sai muka ce: Me ya saka dariya ya manzon Allah ya ce: "Ɗazu-ɗazun nan an saukar mini da wata sura" sai ya karanta: "Da sunan Allah Mai rahama Mai jin ƙai {Lallai ne Mu Mun baka al-Kausara * to ka yi sallah ga Ubangijinka kuma ka soke. Lallai maƙiyin ka shi ne mai yankakken baya} [al-Kausar: 1-3]". Sannan ya ce: "Shin kun san menene al-kausara?" sai muka ce: Allah da manzonSa ne mafi sani, ya ce: "Lallai wata korama ce Ubangijina ya yi mini alkawarinta, yana da alheri mai yawa, shi wani tafki ne wanda al'ummata zasu gangaro masa ranar AlKiyama, kofinsa adadin taurari ne, sai kuri bawa daga cikinsu, sai in ce; Ya Ubangiji, lallai cewa shi daga al'ummata yake sai Ya ce: Bakasan abinda ya farar ba a bayanka". (Muslim ne ya fitar da shi (400).)
kuma tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Tafkina tafiyar wata ne, ruwansa ya fi nono fari, ƙamshinsa ya fi almiski ƙanshi, kofunansa kamar taurarin sama ne, wanda ya sha daga gare shi ba zai yi ƙishirwa ba har abada". (Bukhari ne y fitar da shi (6579), da Muslim (2292).)
kuma tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Lallai tafkina shi ne mafi nisa daga Ailata (Ilat) daga Adn, lallai ya fi ƙanƙara fari, kuma ya fi nonon da akasa masa zuma zaƙi, kuma lallai kofin shi sunfi taurari yawa, kuma lallai cewa ni zan hana mutane daga gare shi, kamar yadda mutum yake hana mutane tafkinsa". Suka ce: Ya manzon Allah, shin zaka ganemu a wannan lokacin? ya ce: "Kawarai kuwa, kuna da wata alamar da babu wanda yake da ita daga al'ummu, zaku zo min kuna masu fararen fuskoki, masu fararen gaɓɓai saboda gurbin alwala". (Muslim ne fitar da shi (247).)
kuma tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Wata rana ina tsaye (abakin tafki) sai ga wasu jama'a, har sai da na ganesu, sai wani mutum (mala'ika a surar mutum) ya fito tsakanina da su, sai ya ce: Ku zo, sai na ce: Ina? ya ce: Zuwa wuta wallahi, na ce: Mene ne lamarinsu? ya ce: Lallai su sun juya a bayanka da baya-da baya. Sannan sai ga wasu jama'a, har sai da na ganesu sai wani mutum ya fito a tsakanina da su, sai ya ce: Ku zo, na ce: Ina? ya ce: Zuwa wuta wallahi, na ce: Menene lamarinsu? ya ce: Lallai su sun yi ridda, sun koma inda suka baro, bana zatan cewa zai tsira daga cikinsu sai kamar takarkace harawar dabbobi". (Bukhari ne ya fitar da shi (6587)).
Daga Anas - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Lokacin da aka yi mi'iraji da annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - zuwa sama ya ce: ‘’Na je ga wata ƙorama sasanninta ƙubba ce ta tataccen lu’u lu’u, sai na ce: Mene ne wannan ya Jibril? sai ya ce wannan shi ne alkausara’’. (Bukhari ne ya fitar da shi (4964).)
BABIN SIRAƊI DA SAKAMAKO
Muna imani cewa siraɗi za'a kafa shi akan bayan Jahannama, shi mai santsi ne mai sa a zame, bayi zasu wuce ta kansa gwargwadan ayyukansu, kuma yana da arabsakai kamar ƙayar Sa'adan, sai su fauce mutane da ayyukansu, farkon wanda zai ƙetare siraɗi (shi ne) annabinmu tsira da amincin Allah su tabbata agare shi, daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "...Za'a tara mutane ranar lahira, sai ya ce: Wanda ya kasance yana bautawa wani abu to ya bi (shi), daga cikinsu akwai wanda yake bin rana, daga cikinsu akwai wanda yake bin wata, daga cikinsu akwai wanda yake bin ɗagutai. Sai wannan al'ummar ta tsaya a cikinta akwai munafukanta, sai Allah Ya zo musu sai Ya ce: Ni ne Ubangijinku, sai su ce: Wannan wurinmu ne (munanan) har Ubangijinmu Ya zo mana, idan Ubangijinmu Ya zo mana zamu ganaeShi, sai Allah Ya zo musu sai Ya ce: Ni ne Ubangijinku, sai su ce: Kaine Ubangijinmu, sai ya kirasu, sai a buga siraɗi a gadan bayan Jahannama, sai in zama farkon wanda zai ƙetare siraɗi daga manzanni da al'ummarsa, kuma wani da zai yi magana ba a wannan ranar sai manzanni, zancen mazanni awannan ranar: Ya Allah Ka kubutar ka kubutar". (Bukhari ne ya fitar da shi (806), da Muslim (182), da Abu Dawud (4730), da Tirmizi (2554), da Ibnu Majah (178).)
Daga Abu Sa'id al-Kudri - Allah Ya yarda da shi - ya ce: "...Sannan za’a zo da gada (siradi), sai a sanyata agadan bayan Jahannama" muka ce: Ya manzon Allah, mece ce gada? ya ce: "mazamiya ne mai santsi, akansa akwai flayoyi da arabsakai, da aduwa mai faɗi, tana da ƙaya mai lanƙwasasshen kai, ana samunsu a Najd, ana ce musu Sa'adan, mumini akansu kamar ƙiftawar ido ne, kuma kamar walƙiya ne, kuma kamar iska ne, kuma kamar sukuwar dawakai ne da ayari, a kwai mai tsira wanda za'a kuɓutar da shi, da wanda za'a tirmusa a cikin wutar Jahannama, har na ƙarshensu ya wuce ana jansa ja...". (Bukhari ne ya fitar da shi (7439)).
kuma tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "...A gefen siraɗi akwai arabsakai (kugiyoyi) a rataye abar umarta da riƙe wanda aka yi musu umarni da shi, (daga cikinsu akwai) wanda ya ji raunuka amma ya tsira, da wanda aka wurga a cikin wuta". (Muslim ne ya fitar da shi (195).)
Daga Abuz Zubair shi ya ji Jabir ɗan Abdullahi - Allah Ya yarda da su - ana tambayarsa game da gangarowa (wuta), sai ya ce: "Zamu zo a ranar Alkiyama game da kaza da kaza, ka duba wato wancan a saman mutane? ya ce: Sai akirawo al'ummu da gumakansu, da abinda suke bautawa, na farko sai na farko, sannan Ubangijinmu ya zo bayan nan, sai ya ce: Wa kuke jira? sai su ce: Muna jiran Ubangijinmu, sai ya ce: Ni ne Ubangijinku, sai su ce: har sai mun kalleKa, sai Ya yi musu tajalli Yana dariya, ya ce: sai Ya tsinkaya da su suna binSa, sai abawa kowane mutum haske daga cikinsu munafiki ko mumini haske, sannan su bi shi kuma akn gadar Jahannama akwai Arabiasakai da aduwa, suna kama wanda Allah Ya so, sannan aka kashe hasken munafukai, sannan muminai su tsira...". (Muslim ne ya fitar da shi (191).)
Idan muminai suka tsira daga siraɗi za'a tsaresu akan wata gada tsakanin aljanna da wuta, daga Abu Sa'idul Khudr - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Muminai zasu tsira daga wuta, sai a tsaresu akan wata gada tsakanin aljanna da wuta, sai a yi wa sashinsu sakayyar zalincin da ya faru tsakaninsu a duniya, har idan an tsarkakesu an wankesu sai a yi musu izini da shiga aljanna, na rantse da wanda ran Muhammad yake a hannunSa, ɗayansu ya fi gane gidansa na aljanna akan gidansa na duniya". (Bukhari ne ya fitar da shi (6535).)
BABIN ALJANNA DA WUTA
Muna imani cewa aljanna da wuta su ne gidajen sakamako, kuma siffar 'yan aljanna da wuta ya zo a cikin Alkur’ani da sunnah, da ambatan gidajansu da abubuwan shansu da abubuwan cinsu da tufafinsu.
Kuma muna imani cewa su an halicce su yanzu, kuma (Annabi) Adam - aminci ya tabbata agare shi - ya kasance a cikin aljannar dawwama, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma ya Ãdam! Ka zauna kai da matarka a Aljanna sai ku ci daga inda kuka so; kuma kada ku kusanci wannan itãciya, har ku kasance daga azzãlumai} [al-A'araf: 19]. Daga Abu Huraira -Allah Ya yarda da shi - cewa annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "(Annabi) Adam da (Annabi) Musa sun yi jayayya, sai (Annabi) Musa ya ce da shi: Ya Adam kai ne babanmu ka taɓar da mu ka fitar da mu daga aljanna, sai Adam ya ce da shi: Ya Musa Allah Ya zaɓeka da zancenSa, kuma Ya zana maka da hannunSa, zaka zargeni ne akan wani al'amarin da Allah Ya ƙaddara shi akaina kafin Ya halicceni da shekara arba'in? sai (Annabi) Adam ya rinjayi (Annabi) Musa, sai Adam ya rinjayi Musa'. sau uku. (Bukharin ne ya fitar da shi (6614), da Muslim (2652), da Abu Dawud (4701), da Tirmizi (2134), da Ibnu Majah (80).)
Aljanna ita ce gidan ni'ima tabbatacciya, Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya ce: {Waɗannan sakamakonsu gãfara ce daga Ubangijinsu, daga Gidajen Aljanna (waɗanda) ƙõramu na gudana daga ƙarƙashinsu, suna madawwama a cikinsu. Kuma mãdalla da ijãrar mãsu aiki} [Aal- Imran: 136]. Kuma Allah Maɗaukkain sarki Ya ce Yana Mai kwaɗaitar da abinda ke cikinta na ni'ima: {Sabõda haka wani rai bai san abin da aka ɓõye musu ba, na sanyin idãnu, dõmin sakamako ga abin da suka kasance sunã aikatãwa} [al-Sajda: 17].
Muna imani cewa mafi girman ni'imar aljanna shi ne duba zuwa fuskar Allah - Maɗaukakin sarki - a cikin aljannar ni'ima, Allah Maɗaukkain sarki Ya ce: {Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu annuri ne * Zuwa ga Ubangijinsu mãsu kallo ne} [al-Kiyama: 22-23]. Kuma Ya ce: {A'aha! Haƙĩƙa, lalle ne sũ daga Ubangijinsu, rãnar nan, waɗanda ake shãmakancẽwa ne} [al-Muɗaffifin: 15]. Daga Suhaib al-Rumi - Allah Ya yarda da shi - cewa manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Idan 'yan aljanna suka shiga aljanna, ya ce: Allah -Maɗaukakin sarki - zai ce: Kuna san wani abu ne da zan ƙaro muku shi? sai su ce: Ba ka haskaka fusokinmu ba? kuma ba Ka shigar da mu aljannah ba, kuma ka tseratar da mu daga wuta? ya ce: Sai a yaye hijabi, ba'a basu wani abu mafi soyuwa a gare su ba kamar ganin Ubanginsu - Mai girma da ɗaukaka -". (Muslim ne ya fitar da shi (181).)
Kuma muna imani cewa aljanna matakai ce, haƙiƙa tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya bada labarin mafi ƙasan 'yan aljanna a gida da mafi ɗaukakarsu, sai tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "(annabi) Musa ya tambayi Ubangijinsa: Menene mafi ƙasan 'yan aljanna a gida? ya ce: Shi wani mutum ne da zai zo bayan an shigar da 'yan aljanna aljanna, sai a ce masa: Ka shiga aljanna, sai ya ce: Ya Ubangiji, ta yaya alhali mutane sun sauka a masaukansu, sun ɗauki abubuwansu, sai a ce masa: Shin ka yarda ka sami kwatankwacin mulkin wani sarki daga sarakunan duniya? sai ya ce: Na yarda ya Ubangiji, sai ya ce: Kana da hakan, da kwatankwacinsa da kwatankwacin kwatankwacinsa, sai ya ce ana biyar: Ya Ubangiji na yarda, sai ya ce: wannan naka ne duka tamkarsa agoma, kuma kana da duk abinda ranka ya yi sha'awa, kuma idanka ya ji dadi, sai ya ce: Ya Ubangiji na yarda, ya ce: Ya Ubangiji, to mafi daukakarsu masauki? Ya ce: wadannan sune wadanda na yi nufi, na dasa girmansu da hannuNa, kuma Na yi mata sitamfi, wani ido bai taba gani ba, wani kunne bai taba ji ba, kuma bai taba darsuwa a zuciyar wani mutum ba". Ya ce: Gaskiyar hakan a cikin littafin Allah - Mai girma da ɗaukaka -: {Wata rai bata sanin abinda aka ɓoye mata daga abinda rayuka suke farin ciki} zuwa ƙarshen ayar. [Sajdah: 17]. (Muslim ne ya fitar da shi (189).)
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Lallai mafi ƙan kantar gidan ɗayanku a cikin aljanna shi ne ace da shi: Ka yi buri, sai ya yi buri, kuma ya yi buri, sai Ya ce da shi: Shin ka yi burin kuwa? sai ya ce: Eh, sai Ya ce da shi: To kana da abin da ka yi burin da wani kwatankwacin sa tare da shi". (Muslim ne ya fitar da shi (182).)
Kuma muna sanin cewa ƙofofin aljanna guda takwas ne, tsira da amincin Allah su ta agare shi ya ce: "Wanda ya ce: Ina shaida cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah Shi kaɗai baShi da abokin tarayya, kuma (Annabi) Muhammad bawanSa ne kuma manzanSa ne, kuma cewa (Annabi) Isa bawan Allah ne, ɗan baiwarSa ne, kuma kalmarSa ce Ya jefata ga Maryam kuma Ruhi ne daga gareShi, kuma aljanna gaskiya ce, wuta gaskiya ce; Allah Zai shigar da shi daga ƙofofin aljanna takwas wacce ya so". (Bukhari ne ya fitar da shi (3435), da Muslim (28).)
Kuma muna imani cewa gidan ni'ima gidajan aljanna ne masu yawa, kamar yadda Allah Maɗaukkain sarki Ya ce: {Kuma wanda ya ji tsõron tsayãwa a gaba ga Ubangijinsa yanã da Aljanna biyu} [al-Rahman: 46], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma baicinsu akwai waɗansu gidãjen Aljanna biyu} [al-Rahman: 62], tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Aljannatai guda biyu kofinansu na azurfa ne, da abinda yake cikinsu, da kuma aljannatai guda biyu kofinansu na zinariya ne da abinda ke cikinsu, kuma abinda yake tsakanin mutane da abinda yake tsakanin su ga Ubangijinsu, babu komai sai wani mayafi na girma akan fuskarSa a cikin aljanna madawwama".
Kuma muna imani cewa ni'imar aljanna madawwamiya ce ba ta yankewa, daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi -, daga annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Wanda ya shiga aljanna zai ni'imtu bazai yanke ƙauna ba, tufansa ba zai dandaƙe ba, kuma samartakarsa ba zata ƙare ba".
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi -, daga annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Mai kira zai yi kira: Lallai cewa ku zaku yi lafiya ba zaku yi masassara ba har abada, kuma ku zaku rayu ba zaku mutu ba har abada, kuma ku zaku kasance ne a samari ba zaku tsufaba har abada, kuma cewa ku zaku ni'imtu ba zaku yanke ƙauna ba har abada, wannan shi ne faɗinSa - Allah Mai girma da ɗaukaka -: {Za’a kira cewa waccan aljannar an gadar muku da ita saboda abinda kuka kasance kuna aikatawa} [al-A'araf: 43]".
Kuma Allah Ya bada labari game da wuta da abinda ke cikinta na nau'ikan azaba da masifa, sai Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Lallai Mu mun yi tanadi domin azzalumai wata wuta wadda shamakunta suna kewaye da su, kuma idan sun nemi taimako sai a taimakesu da wani ruwa kamar dabzar mai, yana soye fuskokinsu. Tir da abin shansu, kuma wutar ta yi munin zama mahutarsu} [al-Kahf: 29], Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Da shĩ ake narkar da abin da yake a cikin cikunansu da fãtun jikinsu * Kuma sunã da waɗansu gwalmõmin dũka na baƙin ƙarfe} [al- Hajj: 20-21], Kuma Allah -sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Lalle ne waɗanda suka kãfirta da ayõyinMu za Mu ƙõne su da wuta, kõ da yaushe fãtunsu suka nuna, sai Mu musanya musu wasu fãtun, dõmin su ɗanɗani azãba. Lalle ne Allah Yã kasance Mabuwãyi, Mai hikima} [al-Nisa'a: 56].
Muna imani cewa wuta matakan azaba ce mabanbanta, haƙiƙa Allah Ya bayyana cewa munafukai suna cikin matakan azaba na Jahim, sai Allah Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Lalle ne, manãfukai sunã a magangara mafi ƙasƙanci daga wuta. Kuma bã zã ka sãma musu mataimaki ba} [al-Nisa'a: 145]. Kuma ya zo a cikin AlKur'ani mai girma cewa tana da ƙofofi bakwai, sai Allah - Maɗaukaki - ya ce: {Tanã da ƙõfõfi bakwai, ga kõwace ƙõfa akwai wani juz'i daga gare su rababbe} [al-Hijr: 44]. Ita ce gidan azaba matabbaciya, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Lalle ne waɗanda suka kãfirta, kuma suka yi zãlunci, Allah bai kasance Yana yi musu gãfara ba, kuma bã Ya shiryar da su ga hanya * Fãce hanyar Jahannama, sunã mãsu dawwama a cikinta har abada, kuma wannan yã kasance, ga Allah, mai sauƙi} [al-Nisa'a: 168-169].
KUNDIN IMANI DA KADDARA
Kundin a taƙaice
Muna imani da hukunci da ƙaddara, kuma muna sani na sakankancewa cewa imani da hukunci da ƙaddara shi ne rukuni na shida daga rukunan imani, imani da ƙaddara yana daga imani da Allah; domin cewa ƙaddara tana daga sanin Allah da ƙaddarawarSa da shiryawarSa da ganin damar Sa da halittarSa.
Musulmai sun haɗu akan cewa imani da ƙaddara rukuni ne daga rukunan imani.
Kuma muna sanin cewa imani da hukunci da ƙaddara yana ƙunsar imani da sanin Allah wanda yake gamamme wanda ya kewaye komai, kuma cewa Allah haƙiƙa Ya kewaye komai da sani, kuma cewa iliminSa ya kewayewa dukkan al'amura manya maɗaukaka, da babba da ƙarami, babu wani abin da ke samamme ko wanda za'a samar, kuma ba'a samar da shi ba sai shi tabbatacce ne acikin Lauhul mahfuz, abin rubutawa a cikinsa kuma adadinsa a rubuce yake da inda zai kai da lokacin da za'a samar da shi, da halin da zai ƙare a cikinsa.
Kuma cewa Shi - tsarki ya tabbatar maSa - Ya san abinda ya kasance, da wanda zai kasance, da wanda da zai kasance to yaya zai kasance, kuma Allah Ya rubuta ƙaddarorin halittu tun kafin Ya halicci sammai da ƙasa da shekara dubu hamsin, Al'arshinSa ya kasance akan ruwa.
Muna imani cewa Allah Ya rubuta dukkan kasantaccen abu a cikin wani littafi abin kiyayewa.
Kuma muna imani cewa Allah Yana rubuta abinda Yake so, kuma Yana shafe abinda Yake so Yana tabbatarwa, kuma asalin Littafin yana wurinSa.
Muna imani da cewa wani abu ba ya kasancewa sai da hukuncin Allah da ƙaddararSa, kuma ba'a tunkuɗe wani al'amari sai da hukuncin Allah da ƙaddararSa, abinda Ya ƙaddaraShi mai afkuwa ne babu wata dabara, abinda kuma Ya juyar da shi babu wani ɗaya da ya isa ya tabbatar da shi, halittu gaba ɗayansu ba sa iya aikata wani abinda Allah bai rubuta shi ba, kuma babu tunkuɗe abinda Ya rubutaShi - tsarki ya tabbatar maSa kumka Ya daukaka -, abinda ya kuskurewa bawa to bai kasance zai same shi ba, abinda kuma ya same shi bai kasance zai kuskure masa ba.
Kuma muna imani cewa abinda Allah Ya ga dama shi zai kasance, abinda kuma bai ga dama ba ba zai kasance ba, kuma ganin damar Sa cikakkiya ce, ikonSa tabbacce ne, kuma babu wani abu a cikin mulkinSa da zai kasance sai abinda Ya ga dama, muna imani cewa bayi suna da wani ganin dama na haƙiƙa, kuma shi mai bi ne ga ganin damar Allah - Maɗaukakin sarki -.
Kuma muna imani cewa Allah Ya shiryar da wanda Ya so da falalarSa, Ya taɓar da wanda Ya ga dama da adalcinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -, ba'a tambaya game da abinda Yake aikatawa su (bayi) ake tambaya, kowace biyayya daga mai biyayya to da taufiƙin Allah ne gare shi , kuma kowane saɓo daga mai saɓo to da taɓarwar Allah ne gare shi da ta gabata, mai arziƙi shi ne wanda arziƙi ya rigaye shi, taɓaɓɓe shi ne wanda taɓewa ta rigaye shi, kuma ayyukan bayi na alheri ne ko sharri aikinsu ne, kuma halitta ne ga Ubangijinsu.
Kuma muna imani cewa Allah Yana son ayyukan biyayya da masu biyayya, kuma muna imani cewa Allah Ya na ƙin fasiƙanci da fasiƙai, kuma Allah idan Ya yi nufin wani alheri ga bawa Zai datar da shi ga abinda Yake so da kuma biyayyarSa, da kuma abinda Ya yarda da shi game da shi, wanda Ya yi nufin wanin hakan da shi Zai tsaida hujja akansa, sannan Ya azabtar da shi batare da ya zalince shi ba.
Muna imanin cewa Allah ba ya umarni da alfasha, kuma bai yarda da kafirci ga bayinSa ba.
Muna imani cewa Allah (Shi ne) Mahaliccin kowane abu, kuma Allah Ya halicci bayi, kuma Ya halicci ayyukansu, wani ba ya tarayya da Shi a cikin halittarSa. Allah Ya kafawa bayinSa hujja akan halitta cewa Shi ne Mahalicci Shi kaɗai, wanda Ya kaɗaita da halitta to babu wani da zai yi da'awar tarayya daShi a halitta.
Kuma muna imani cewa babu karo tsakanin shari'a da al’amari da kuma halitta, Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - halitta taSa ce, kuma umarni naSa ne, kamar yadda Yake aikata abinda Yake so, kuma ba'a tambaya game da abinda yake aikatawa, to Shi Yana umarni kuma babu mai juyar da hukuncinSa, kuma babu mai bibiyar umarninSa.
Muna imani cewa Allah Ya ƙaddara ƙaddarorin halittu kafin Ya halicci sammai da ƙasa da shekara dubu hamsin, tare da hakan Ya yi umarni da yi maSa biyayya da yi wa manzanninSa da annabawanSa biyayya, kuma Ya yi hani daga saɓa maSa da saɓawa manzanninSa da annabawanSa, sai tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya haɗa a cikin littafinSa tsakanin bada labari daga ƙaddarawarSa, da kuma umarni da bin wahayinSa da umarninSa. Kuma Allah Ya bayyana cewa wajibi shi ne bin shiriya, kuma cewa Shi Ya shiryar da wanda ya so da falalarSa, kuma Ya ɓatar da wanda Ya ga dama da adalcinSa, kuma Allah Ya haɗa tsakanin labartawarSa daga gamammiyar Shari’ar Sa, da kuma tsawatarwarSa ga masu sabawa, da kuma umarninSa ga bayinSa muminai da bautarSa da dogaro gareShi. Da kuma hadawa tsakanin imani da kaddara da kuma aiki da shari'a mai yi wu wa ne kuma abin kaddarawa ne, kuma Allah - saha'aninSa ya buwaya - Ya bayyana cewa baYa dorawa wata rai sai abinda zata iya.
Kuma muna imani cewa kamar yadda babu karo tsakanin halitta da umarni da kuma sharai'a, to babu karo tsakanin shari'a da umarni da kuma hankali, dukkan abinda Allah Ya yi umarni da shi da manzonSa - tsira da a mincin Allah su tabbata agare shi -, ko Allah da manzonSa suka yi hani daga gare shi , ko Allah Ya ƙaddara shi, ko ya bada labarinsa, to ba ya karo da hankali, kai shi ne mahukuntar abinda hankula suka yi umarni da shi, kuma shi ne maƙarar hikima.
Kuma muna imani cewa Allah Ya saukar da littattafai, kuma Ya aiko manzanni - aminci ya tabbata agare su - dan hujja ta tsaya akan halitta, shari'a da umarni da ƙaddara dukkanin wadannan masu cikawa ne sashin su yana cike sashi, shi yana cikin ƙololuwar kyau, kai babu mafi kyau daga gare shi.
Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya yi yabo ga littafinSa wanda Ya siffanta shi da cewa shi ne mafi kyan zancen da ya ƙunshi shari'a da umarni - abinda Allah Ya shara'antashi ko Ya ƙaddar shi, to yana cikin ƙololuwar cika da kyau; daidai ne hankula sun riske shi ko sun gajiya ga riskarsa da fahimtarsa, kada mu sanya hankulanmu da ra'ayukanmu masu hukunci akan shari'ar Allah da ƙaddararSa, wani lokaci da kyautatawa, wani lokaci kuma da munanawa, kai dukkan abinda Allah Ya ƙaddara shi Ya kuma shar’anta shi to shi mai cikakken kyau ne da cika.
Kuma muna imani cewa shari'a da ƙaddara dukkaninsu alheri ne, Allah ba Ya ƙaddara tsantsan sharri, sai dai Yana shigar da sharri cikin gamewar abinda aka ƙaddara, kuma a cikin AlKur’ani yana zuwa abin raɓawa zuwa ga wanda ya tsaya da shi, daga babin ladabi kada a jingina sharri ga Allah - Maɗaukakin sarki -.
Muna imani cewa aikata sabubba ba ya kore imani da ƙaddara, kai aikata sababi yana daga cikar imani da hukunci da ƙaddara, kuma Ubangijinmu Ya yi umarni da aikata sabubba, daga mafi girman sabubba shi ne addu'a, kuma Ya umarcemu da addu'a haƙiƙa hukunci ya rigaya.
Kuma muna imani Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Yana umarni da adalci kuma Yana hukunci da shi a Shari'a da ƙaddarawa da sakayya, kuma Ya korewa kanSa zalinci, kuma Ya tabbatar da cikar adalci.
Kuma muna imani cewa rigayar ƙaddara ba ya lazimtar zalincin bayi daga gare shi; domin cewa Allah Ya saukar da littattafai, kuma Ya aiko da manzanni; dan kada hujja ta tsayu akan Allah bayan manzanni, kuma Ya sanya ƙaddara wani ɓoyayyen sirri, kuma Ya sanyawa bayi mashi'a da zaɓi, wanda ya shiriya to ladan yana kansa, wanda kuma ya ɓata to zunubin ɓatan yana kansa.
Kuma muna imani cewa ba ya halatta kafa hujja da ƙaddara akan aikata saɓo ko akan barin ayyukan biyayya, kuma cewa mushrikan da suke kafa hujja da ƙaddara akan afkawarsu cikin shirka, Allah Ya bayyana ƙaryarsu kuma Ya ɗanɗana musu tsananinSa, da ace ƙaddara ta kasance hujja garesu akan shirkarsu da Allah bai ɗanɗana musu tsananinSa ba.
Kuma muna imani cewa yana halatta ga bawa ya kafa hujja da ƙaddara akan zunubai bayan tuba daga zunuban, kuma ya kafa hujja da ƙaddara akan masifu.
Kuma muna imani cewa idan mumini ya miƙa al'amari zuwa ga Allah, kuma ya tuba ya yi istirja'i a lokacin musiba, za'a rubuta masa ɗabi'u uku na alheri: Tsira daga Allah, da rahama, da tabbatar da shiriya.
BABIN WAJABCIN IMANI DA KADDARA
Muna imani da hukunci da kuma ƙaddara, Shi - Allah tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya san abinda ya kasance da abinda zai kasance, kuma Ya rubuta dukkanin hakan kuma Ya so shi Ya kuma ƙaddara shi ƙaddarawa.
Kuma muna sani na sakankancewa cewa imani da hukuncin (Allah) da ƙaddara shi ne rukuni na shida daga rukunan imani, Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya ce: {Lalle Mũ, kõwane irin abu Mun halitta shi a kan tsãri} [al-Kamar: 49], Allah - Maɗaukakin - Ya ce: {Kuma umarnin Allah ya kasance abin ƙaddarawa tabbatacce} [al-Ahzab: 38], Kuma Allah - sha'ninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Kuma Ya halicci kowane abu, sai Ya ƙaddara shi ƙadartawa} [al-Furƙan: 2], Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Manzo ya yi imani da abin da aka saukar daga Ubangijinsa zuwa gare shi hakanan muminai ma, kowa ya yi imani da Allah da mala'ikunSa da littattafanSa da manzanninSa} [al-Baƙara: 285]. Imani da ƙaddara yana daga imani da Allah; domin cewa ƙaddara tana daga ilimin Allah da ƙaddarawarSa da jujjuya al'amarin mulkinSa.
Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Shi ne Wanda ke rayarwa kuma Yana kashewa. To, idan Ya hukunta wani al'amari, to, Yana cewa kawai gare shi, ka kasance sai yana kasancewa (kamar yadda ake buƙatar sa.)} [Gafir: 68], Kuma Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Kuma a wurinSa mabũdan gaibi suke, babu wanda yake sanin su fãce Shi, kuma Yanã sanin abin da ke a cikin tudu da ruwa, kuma wani ganye ba ya fãɗuwa, fãce Yã san shi, kuma bãbu wata ƙwãya a cikin duffan ƙasã, kuma babu ɗanye, kuma babu ƙẽƙasasshe, fãce yanã a cikin wani Littãfi mai bayyanãwa} [al-An'am: 59].
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - daga Hadisin Jibril - aminci ya tabbata agare shi - ya ce: To ka bani labari game da imani, ya ce: "Ka yi imani da Allah da mala’ikunSa da littattafanSa da manzanninSa, da ranar lahira, kuma ka yi imani da ƙaddara alherinsa da sharrinsa'. Ya ce: Ka yi gaskiya. (Muslim ne ya fitar da shi (8), da Abu Dawud (4695), da Tirmizi (2610), da Ibnu Majah (63).)
Haƙiƙa musulmai sun haɗu akan cewa imani da ƙaddara rukuni ne daga rukunan imani, al-Hafiz Abul Kasim al-Lakal'i ya ce: "Idan haɗuwa da yaɗuwa ta kasance a duniya ba tare da inkari ba, to shi a wannan mas'alar "Wato ƙaddara", wanda ya saɓa faɗarsa a cikinta, to shi mai tsaurin kai ne mai saɓawa Allah, narko zai riske shi, kuma shi ya shiga ƙarƙashin faɗinSa: {Wanda ya saɓawa manzo bayan shiriya ta bayyana gare shi kuma ya bi wanin tafarkin muminai Zamu jiɓinta masa abinda ya jiɓinta kuma Zamu ƙona shi da Jahannama makoma ta munana} [al-Nisa'i: 115]". (Sharhi Usulul I'itiƙadi Ahlus Sunnah Wal jama'ah (4/726).)
Daga Amr ɗan Shuaib daga babansa, daga kakansa: Cewa wasu mutane suna zaune a ƙofar annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - sai sashinsu suka ce: Shin Allah Bai ce kaza da kaza ba? Wasunsu kuma suka ce: Shin Allah Bai ce kaza da kaza ba? Sai Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ji haka, sai ya fita kamar an ji kaunar rumman a fuskarsa, sai ya ce: «Da wannan ne aka umurce ku? Ko da wannan aka aiko ku? Don buga Littafin Allah sashinsa da sashi? kaɗai al'ummun da ke gabanku sun bata ne a irin wannan, ku ba komai bane daga abinda ke nan, ku duba abinda aka umarceku da shi, ku yi aiki da shi, abinda kuma aka haneku da shi, to ku hau". (Ibnu Majah ne ya fitar da shi (85), da Ahmad (6845), kuma lafazin nasane, da Haris ɗan Abi Usama a cikin al-Musnad - kamar yanda yake a cikin Bugyatul bahis (735), da Ibnu Abi Asim a cikin al-Sunnah (406).)
Daga Abdul Malik - wato ɗan Juraij - daga Aɗa'u ɗan Abi Rabah ya ce: " Nazm zo wa Ibnu Abbas, alhali shi yana debo Zamzam, haƙiƙa ƙasan tufansa sun jiƙe, sai na ce da shi: Haƙiƙa an yi magana a ƙaddara, sai ya ce: Shin sun aikata ta ? Na ce: Eh, ya ce: Wallahi wannan ayar bata sauka ba sai a cikinsu: {Ku ɗanɗani shafar wutar Saƙar * Lallai ne kowane abu mun halittashi akan tsari} [al-Kamar: 48-49], Kada ku gaida marasa lafiyansu, kuma kada ku yi wa mamatansu sallah, da zaka nuna mini ɗaya daga cikinsu, da na fasa idansa". (Sharhi Usulul I'itiƙadi Ahlus Sunnah Wal jama'ah (3/597).)
Ubadata ɗan Samit - Allah Ya yarda da shi - ya ce wa ɗansa: Ya ɗan ƙaramij ɗana, kai ba zaka ɗanɗani haƙiƙanin imani ba har sai ka san cewa abinda ya sameka bai kasance zai kuskure maka ba, kuma abinda ya kuskure ka bai kasance zai sameka ba, na ji manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana cewa: "Lallai farkon abinda Allah Ya halitta shi ne alƙalami, sai Ya ce masa: Ka rubuta, ya ce: Ya Ubangiji, me zan rubuta? ya ce: Ka rubuta ƙaddarorin kowane abu har tashin Alkiyama", Ya kai ɗan ƙaramin ɗana na ji manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana cewa: "Duk wanda ya mutu akan wanin hakan to ba ya tare da ni". (Abu Dawud ne ya fitar da shi a cikin Sunan nasa (4700), da kuma Sunnah, na Abu Asim (1/51).)
Daga Yahya ɗan Ya'amur ya ce: "Ma'abad Juhani ya kasance farkon wanda ya fara faɗin magana a sha'anin ƙaddara a Basrah, sai na tafi ni da Humaid ɗan AbdurRahman al-Himyari muna masu aikin Hajj - ko masu Umarah - sai muka ce: Da mun haɗu da wani daga sahabban manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai mu tambaye shi game da abinda waɗannan suke fada akan ƙaddara, sai muka dace cewa Abdullahi ɗan Umar ɗan al-Khadɗab yana cikin Masallaci, sai muka kewayeshi ni da abokina: Ɗayanmu a damansa, ɗayan kuma ahagunsa, sai na zaci cewa abokina zai barni in yi magana, sai na ce: Ya Abu Abdurrahman, lalai wasu mutane a bangarenmu sun bayyana suna karanta AlKur'ani kuma suna bibiyar ilimi. Ya kuma ambata daga sha'aninsu, kuma cewa su suna riyawa cewa babu kaddara, kuma al'amari mai afkuwa da kansa ne, ya ce: Idan ka hadu da wadancan to ka basu labari cewa babu ruwana da su, kuma suma babu ruwansu da ni, wanda Abdullahi yake rantsuwa da shi, da a ce dayansu yana da kwatankwacin dutsen Uhud na zinari sai ya ciyar da shi, Allah ba Zai karba ba har sai ya yi imani da kaddara...". (Muslim ne ya fitar da shi a cikin Muƙaddimar Sahih (8), da al-Shari'ah na al-Ajurri (2/851).)
Daga Abu Haruna al-Abali - ya kasance daga waɗanda suka abokanci Sahl ɗan Abdullahi - kuma ya kasance mutum ne na gari, ya kasance yana karantar da mu AlKur'ani a cikin Masallacin juma'a, ya ce: "An tambayi Sahl ɗan Abdullahi game da ƙaddara, sai ya ce: Yin imani da ƙaddara farilla ne, kuma ƙaryata shi kafirci ne, magana a cikinsa bidi'a ne, yin shuru daga gare shi Sunna ce". (Sharhi Usulul I'itiƙadi Ahlus Sunnah Wal jama'ah (4/786).)
Daga Alhasanul Basri ya ce: "Alƙalami ya bushe, an gama hukunci, ƙaddara ta cika da tabbatar da littafi, da gasgata manzanni, da tsiran wanda ya yi aiki kuma ya ji tsoron Allah, da taɓewar wanda ya yi zalinci kuma ya yi shisshigi, da kuma jibinita daga Allah ga muminai, da kuma barranta daga Allah ga mushrikai". (Al-Shari'ah, na al-Ajurri (2/881).)
Ibnu Baɗɗah al-Akbari ya ce: "Sannan bayan nan imani da ƙaddara alherinsa da sharrinsa, da zaƙinsa da ɗacinsa, da ƙanƙaninsa da mai yawansa abin ƙaddarawa ne daga Allah - Mai girma da ɗaukaka - akan bayi, da kuma lokacin da Ya yi nufin ya afku, ba ya gabatuwa ba kuma ya jinkirtuwa, ga abinda sanin Allah ya rigaya da hakan, kuma abinda ya samu bawa bai zama zai kuskure shi ba, abinda ya kuskure shi bai zama zai same shi ba, abinda ya gabata bai zama zai jinkirta ba, kuma abinda ya jinkirta bai zama zai gabata ba... yin imani da wannan gaskiya ne kuma wajibi ne, farillah ne daga Allah - Mai girma da ɗaukaka - akan halittarSa, wanda ya saɓa wa hakan, ko ya fita daga gare shi, ko ya yi suka a cikinsa, kuma bai tabbatar da kadara wa ga Allah - Mai girma da daukaka ba -, kuma ya rabata, kuma ya raba mashi'ah gare shi , to shi ne farkon zindikai". (al-Sharhu wal Ibanah ala Usul Sittah wal Diyanah, na Ibnu Baɗɗah (shafi na 213-216).)
BABIN ABINDA IMANI DA KADDARA YAKE KUNSARSA
Muna imani cewa imani da ƙaddara yana ƙunsar imani da sanin Allah wanda ke kunshe da game komai, kuma cewa Shi - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Yana sanin abinda ke cikin sammai da abinda ke cikin ƙasa, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Ashe, ba ka sani ba, lalle ne Allah Yanã sanin abin da yake a cikin sama da ƙasa? Lalle ne wancan yanã cikin Littafi lalle wancan ga Allah mai sauƙi ne} [al- Hajj: 70], Kuma cewa Allah haƙiƙa Ya kewaye kowane abu da sani, Allah - sha'ninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Allah, wanda Ya halitta bakwai ɗin sammai kuma daga ƙasã kwatankwacinsu, umuruinSa yanã ta sauka a tsakaninsu dõmin ku san lalle Allah Mai ĩkon yi ne akan dukan kõme, kuma lalle Allah, haƙĩƙa Ya kẽwaye ga dukan kõme da sani} [al-Ɗalak: 12].
Kuma cewa saninSa wanda ya game al'amura masu girma da maɗaukaka, da manya da ƙanana, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma a wurinSa mabũdan gaibi suke, babu wanda yake sanin su fãce Shi, kuma Yanã sanin abin da ke a cikin tudu da ruwa, kuma wani ganye ba ya fãɗuwa, fãce Yã san shi, kuma bãbu wata ƙwãya a cikin duffan ƙasã, kuma babu ɗanye, kuma babu ƙẽƙasasshe, fãce yanã a cikin wani Littãfi mai bayyanãwa} [al-An'am: 59]. Ibnu Jarir - Allah Ya yi masa rahama - ya ce a tafasirin wannan ayar: "Babu komai - kuma - daga abinda yake samammai, ko daga abinda za'a samar kuma ba'a samar ba bayan nan, sai shi tabbatacce ne a cikin Lauhul Mahfuz, abin rubuta hakan a cikinsa, kuma abin zana adadinsa da ma'isarsa, da lokacin da za'a samar da shi a cikinsa, da halin da zai ƙare a cikinsa, yana nufi da faɗinSa: {Mabayyani}: cewa shi yana bayyana ingancin abinda ke cikinsa da samuwar abinda aka zana a cikinsa ga abinda aka zana". (Tafsir al-Ɗabari (11/403).)
Allah Tsarki ya tabbatar maSa Ya Ya ɗaukaka Ya ce: {Yã san abin da yake shiga a cikin ƙasã da abin da yake fita daga gare ta, da abin da yake sauka daga sama da abin da yake hawa a cikinta, kuma Shĩ ne Mai jin ƙai, Mai gãfara * Kuma waɗanda suka kãfirta suka ce: "Sã'a bã zã ta zo mana ba." Ka ce: "Kayya! Na rantse da Ubangijĩna, lalle, zã ta zõ muku." Masanin gaibi, gwargwadon zarra bã ta nĩsanta daga gare Shi a cikin sammai kuma bã ta nĩsanta a cikin ƙasã, kuma bãbu mafi ƙaranci daga wancan kuma bãbu mafi girma fãce yanã a cikin Littãfi bayyananne} [Saba'i: 2-3].
Daga Imran dan Husain - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Ni ina wajen Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yayin da wasu mutane daga Banu Tamim suka zo , sai ya ce: "Ku karɓi bushara yaku Banu Tamim", suka ce: Ka yi mana bushara to ka bamu. Sai wasu mutane daga mutanen Yaman suka shigo, sai ya ce: "Ku karbi bushara ya ku mutanen Yaman, dan Banu Tamim ba su karɓeta ba" sai suka ce: Mun karɓa, mun zo maka dan mu fahimci addini, kuma dan mu tambayeka daga farkon al'amari: Meye ya kasance? sai ya ce: "Allah Ya kasance alhali babu wani abu kafinSa, kuma Al'arshinSa ya kasance akan ruwa, sannan ya halicci sammai da kassai, ya kuma rubuta kowanne abu a cikin Lauhul Mahfuz. (Bukhari ne (7418), da Tirmizi (3951).) suka ruwaito.
Haƙiƙa Tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya san abin da ya kasance, da abinda zai kasance, da abinda da ya kasance ta yaya zai kasance, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce - Yana Mai bada labari game da munafukai cewa su da sun fita tare da muminai ba abinda zasu ƙara musu sai ɓarna, alhali su basu fita tare da su ba -: {Dã sun fita a cikinku bã zã su ƙãre ku da kõme ba fãce da ɓarna, kuma lalle dã sun yi gaggãwar sanya annamĩmanci a tsakãninku, sunã nẽma muku fitina. Kuma a cikinku akwai 'yan rahõto sabõda su. Kuma Allah ne Masani ga azzãlumai} [Taubah: 47].
kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce game da 'yan wuta: {Kuma da kana gani, a lokacin da aka tsayar da su akan wuta, sai suka ce: "Ya kaicanmu! da ana mayar da mu, kuma ba zamu ƙaryata ba daga ayoyin Ubangijinmu, kuma zamu kasance daga muminai * A' aha abinda suka kasance suna ɓoyewa, daga gabani, ya bayyana a gare su. Kuma da an mayar da su, lallai da sun koma ga abinda aka hanasu daga barinsa. Kuma lallai ne su, haƙiƙa maƙaryata ne} [al-An'am: 27-28]. Sai Ya ambaci cewa su da andawo da su duniya da sun koma ga kafircinsu, alhali su ba'a bijiro da su akan wuta ba bayan nan, Allah Maɗaukkain sarki Ya ce: {Kuma waɗanda suka kãfirta suka ce: "Sã'a bã zã ta zo mana ba." Ka ce: "Kayya! Na rantse da Ubangijĩna, lalle, zã ta zõ muku." Masanin gaibi, gwargwadon zarra bã ta nĩsanta daga gare Shi a cikin sammai kuma bã ta nĩsanta a cikin ƙasã, kuma bãbu mafi ƙaranci daga wancan kuma bãbu mafi girma fãce yanã a cikin Littãfi bayyananne} [Saba'i: 3].
Kuma muna imani cewa Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya rubuta dukkan kasantaccen abu acikin wani littafi abin kiyayewa, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Bubu wani abu da yake ɓoyewa Ubangijinka daga kwatankwacin ƙwayar zarra a ƙasa ne ko a sama ko mafi ƙanƙanta daga hakan ko mafi girma sai yana cikin wani littafi bayyananne} [Yunus: 61], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Ashe, ba ka sani ba, lalle ne Allah Yanã sanin abin da yake a cikin sama da ƙasa? Lalle ne wancan yanã cikin Littafi lalle wancan ga Allah mai sauƙi ne} [al- Hajj: 70], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Wata masifa bã zã ta auku ba a cikin ƙasã kõ a cikin rayukanku fãce tanã a cikin littãfi a gabãnin Mu halitta ta. Lalle wannan, ga Allah, mai sauƙi ne} [al-Hadid: 22].
Daga Abdullahi ɗan Amr ɗan Aas - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Na ji manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana cewa: "Allah Ya rubuta abinda ya kaddara wa halittu kafin Ya halicci sammai da ƙasa da shekara dubu hamsin, ya ce: Al’ArshinSa yana kan ruwa". (Muslim ne ya fitar da shi (2653), da Tirmizi (2156).)
kuma tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Lallai farkon abinda Allah Ya halitta (shi ne) alƙalami, sai ya ce: Ka rubuta, sai ya ce: Me zan rubuta? ya ce: Ka rubuta ƙaddarar abinda ya kasance da abinda zai kasance har abada". (Abu Dawud ne ya fitar da shi (4700), da Tirmizi (2155, 3319), da Dayalisi (578), da Ahmad (22705, 22707), da Ibnu Abi Asim a cikin sunnah (115).)
Daga Abu Huraira - Allah ya yarda da shi - daga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Lokacin da Allah Ya gama halitta, Ya rubuta wani littafi a warinSa: Ta rinjaya, ko Ya ce: Rahamata ta rigayi fishi Na, shi (Littafin) yana wajenSa a birbishin Al'arshi"." (Bukhari ne ya fitar da shi (7553), da Muslim (2751), da Tirmizi (3543), da Ibnu Majah (189).)
Kuma muna imani cewa Allah Yana rubuta abinda Yake so, kuma Yana shafe abinda Yake so Yana tabbatarwa, kuma akwai asalin littafin yana wurinSa, Allah Ya ce - kuma zancenSa gaskiya ne -: {Allah Yanã shafe abin da Yake so, kuma Yanã tabbatarwa kuma a wurinsa asalin Littãfin yake} [al-Ra'ad: 39].
Kuma muna imani cewa wani abu ba zai kasance ba sai da hukuncin Allah da ikonSa, kuma ba'a tunƙuɗe wani al'amari sai da hukuncin Allah da ikonSa, abinda ya ƙaddara shi mai afkuwa ne babu dabara, abinda ya juyar da shi babu wanda ya isa ya afkar da shi, halitta baki ɗayansu ba sa iya aikata dukkan abinda Allah Bai rubuta shi ba, ko tunkuɗe abinda tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya rubuta shi, abinda ya kuskurewa bawa bai zama zai same shi ba, abinda kuma ya same shi bai zama zai kuskure masa ba, daga Abdullahi ɗan Abbas - Allah Ya yarda da su - ya ce: Na kasance a bayan manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - wata rana, sai ya ce: "Ya kai yaro, zan sanar da kai wasu kalmomi, ka kiyaye Allah Zai kiyayeka, ka kiyaye Allah zaka same shi a daura da kai, idan za ka yi roƙo, to, ka roƙi Allah, idan za ka nemi taimako, to, ka nemi taimakon Allah*, ka sani cewa da al'umma za su taru a kan su amfaneka da w abu, ba za su amfaneka ba sai da abin da tabbas Allah Ya rubuta maka, da za su taru a kan su cutar da kai da wani abu, ba za su cutar da kai ba, sai da abin da tabbas Allah Ya rubuta a kanka, an ɗauke alƙaluma kuma takardu sun bushe". (Tirmizi ne ya fitar da shi (2516), da Ibnu Wahb a cikin al-Kadr (28), da Ahmad (2669), da Abdu Ibnu Humaid (636).)
Kuma muna imani cewa abinda Allah Ya so ne yake kasancewa, abinda kuma bai so ba to ba zai kasance ba, kuma mashi'arSa cikakkiya ce, Allah - Maɗaukkain sarki - Ya ce: {Kuma Ubangijinka Yanã halitta abin da Yake so kuma Yake zãɓi. Zãɓi bai kasance a gare su ba. Tsarki ya tabbata ga Allah, kuma (Allah) Ya ɗaukaka daga barin abin da suke yi na shirka} [al-Kasas: 68], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda} [al-Takweer: 29]. Kuma ikonSa mai zartarwa ne, Allah Ya ce: {Kuma Allah bai kasance wani abu na iya rinjayarSa ba acikin Sammai da kuma qasa, lallai shi ne Ya kasance Masani,Mai ikon yi} [Faɗir: 44], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Da Ubangijinka Ya so da basu aikata shi ba ka barsu da abinda suke ƙirƙira} [al-an'am: 112].
Kuma babu abinda yake kasancewa a cikin mulkinSa sai abinda Yake nufi, Allah Ya ce: {Da Allah Ya ga dama da waɗanda suke daga bayansu, ba su yi yaƙi ba, bayan hujjoji bayyanannu sun je musu. Kuma amma sun saɓawa juna, saboda haka daga cikinsu akwai wanda ya yi imani, kuma daga cikinsu akwai wanda ya kafirta. Kuma da Allah Ya so da ba za su yi yaƙi da juna ba, kuma Allah Yana aikata abinda Yake nufi} [al-Baƙara: 253].
kuma muna imani cewa bayi suna da Mashi'a ta hakika, kuma ita mai bi ce ga Mashi'ar Allah, Allah - sha'aninSa ya daukaka - Ya ce: {Kuma, bã zã ku so ba, sai Allah Ya so, lalle ne Allah Yã kasance Masani' Mai hikima} [al-Insan: 30], Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu * Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda} [al-Takweer: 28-29], kuma Allah sha'aninSa ya ɗaukaka Ya ce: {Lalle ne, wannan wata tunãtarwa ce, sai dai wanda ya so, ya kãma hanyar ƙwarai zuwa ga Ubangijinsa} [al-Insan: 29]. Allah tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya ce: {Wancan, shi ne yini na gaskiya; to wanda ya so, ya riƙa makõma zuwa ga Ubangijinsa} [al-Naba: 39].
kuma muna imani cewa Allah Ya shiryar da wanda Ya so da falalarSa, kuma ya tabar da wanda Ya so da adalcinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -, ba'a tambaya game da abinda Yake aikatawa su ake tambaya, Maɗaukkain sarki ya ce: {Kuma waɗanda suka ƙaryata gameda ãyõyinMu, kurãme ne kuma bebãye, acikin duffai. Wanda Allah Ya so Yanã ɓatar da shi, kuma wanda Ya so zai sanya shi a kan hanya madaidaiciya} [al-An'am: 39], kuma Allah sha'aninSa ya ɗaukaka Ya ce: {Domin haka wanda Allah Ya yi nufin Ya shiryar da shi sai Ya buɗa ƙirjinsa domin Musulunci,kuma wanda Ya yi nufin ɓatar da shi sai Ya sanya ƙirjinsa mai ƙunci matsattse kamar dai yana takawa ne acikin sama} [al-An'am: 125], Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma dã Mun so dã Mun bai wa kõwane rai shiriyarsa to, amma magana ta tabbata daga gare Ni! Lalle ne Inã cika Jahannama daga aljannu da mutãne gabã ɗaya} [al-Sajda: 13].
Daga Abubakr al-Mirwazi ya ce: "Na ji Abu Abdullahi - yana nufin: Ahmad ɗan Hanbali - yana cewa: Sun tambayi Abdurrahman ɗan Mahdi game da ƙaddara, sai ya ce musu: Alheri da sharri da ƙaddara ne". (al-Ibanah al-Kubra, na Ibnu Baɗɗah (4/261).)
Abubakar ɗan Abu Asim ya ce: "Ka yi tambaya game da sunnah mece ce? Sunnah: Sunane mai tattaro ma'anoni da yawa a cikin hukunce-hukunce da wanin hakan, daga abinda ma'abota ilimi suka haɗu akan danganta shi ga sunna: Magana da tabbatar da ƙaddara, kuma iko yana tare da aiki dan aiki, da imani da ƙaddara alherinsa da sharrinsa, da zaƙinsa da ɗacinsa, kuma dukkanin biyayya daga mai biyayya to da dacewar Allah gare shi ne, kuma dukkanin saɓo daga mai saɓo to da taɓewar Allah ne wanda rigaya daga gareShi, mai arziƙi shi ne wanda arziƙi ya rigaya gare shi , taɓaɓɓe kuwa shi ne wanda taɓewa ta rigaya gare shi, abubuwa basa fita daga mashi'ar Allah da nufinsa, kuma ayyukan bayi na alheri da sharri aikinsu ne, kuma halitta ne ga Mahaliccinsu". (Al-Sunnah Na Ibn Abi Asim (2/645).)
Kuma muna imani cewa Allah Yana son ayyukan biyayya da masu biyayya, yabonSa ya ɗaukaka Ya ce: {Kuma amma Allah Ya soyar muku da imani a gare ku, kuma Ya ƙawata shi a cikin zukatanku, kuma Ya ƙyamatar da kafirci da fasiƙanci da saɓo, waɗancananka sune masu shiriya} [al-Hujurat: 7], Tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya ce: {Kuma waɗannan da suka yi ɗã'a ga Allah da Mazonsa, to, waɗannan sunã tãre da waɗanda Allah Ya yi ni'ima a kansu, daga annabãwa da mãsu yawan gaskatãwa, da masu shahãda da sãlihai. kuma waɗannan sun kyautatu ga zama abõkan tafiya} [al-Nisa'a: 69], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Ku kyautata lallai Allah yana son masu kyautatawa} [al-Baƙara: 195], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Lallai Allah Yana son masu yawan tuba kuma Yana son masu yawan son tsarkaka} [al-Baƙara: 222], kuma tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Lallai Allah Yana son atishawa, kuma Yana ƙin hamma". (Bukhari ne ya fitar da shi (6223), da Muslim (2994), da Abu Dawud (5028), da Tirmizi (2746), da Ibnu Majah (968).)
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda dashi - daga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Idan Allah Ya so wani bawa sai Ya kira (mala'ika) Jibril: Lallai Allah Yana son wane to kaima ka so shi...". (Bukharin ya fitar da shi (46040), da Muslim (2637), da Tirmizi (3161).)
Kuma muna imani cewa Allah Yana ƙin fasiƙanci da fasiƙai, Allah - tsarki ya tabbatar maSa - Ya ce: {Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Kada waɗansu mutãne su yi izgili game da waɗansu mutãne, mai yiwuwa ne (abin yi wa izgilin) su kasance mafifita daga gare su (mãsu izgilin), kuma waɗansu mãtã kada su yi izgili game da waɗansu mãtã mai yiwuwa ne su kasancc mafĩfĩta daga gare su. Kuma kada ku aibanta kanku, kuma kada ku jẽfi jũna da miyãgun sunãye na laƙabõbĩ. Tir da sũna na fãsicci a bãyãn ĩmãni. Kuma wanda bai tũba ba, to, waɗannan sũ ne azzãlumai} [al-Hujurat: 11], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Lallai Allah baYa son masu wuce gona da iri} [al-Baƙara: 190], kuma Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya ce: {Allah ba Ya son ɓarna} [al-Baƙara: 205].
Daga Usman al-Batti ya ce: na shiga wirin Ibnu Sirin, sai ya ce da ni: "Me mutane suke cewa a sha'anin ƙaddara? ya ce: ban san abinda zan mayar masa ba, ya ce: sai ya ɗaga wani abu daga ƙasa, ya ce: Bana nufin kwatankwacin wannan kan abinda zan faɗa, (FishShari'a na al-Ajurri (2/887).) Lallai Allah idan Ya yi nufin alheri ga wani bawa sai Ya datar da shi ga sonSa da biyayyarSa, da abinda Yake yarda da shi. Wanda kuma ya yi nufin wanin hakan sai Ya riƙi hujja akansa, sannan Ya azabtar da shi ba tare da Ya zalince shi ba". (al-Kadr na al-Furayyani shafi na 263).)
Kuma muna imani cewa Allah ba Ya umarni da alfahsa, kuma bai yarda da kafirci ga bayinSa ba, Allah Maɗaukakin sarki ya ce: {Lallai Allah ba Ya umarni da alfasha} [al-A'araf: 28], Kuma Allah sha'aninSa ya buwaya kuma sarautarSa ta ɗaukaka Ya ce: {Kuma bai Yardawa bayinSa kafirci ba idan kun gode maSa Zai yardar muku da shi} [al-Zumar: 7].
Muna imni cewa Allah ne Mahaliccin kowane abu, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Allah ne Mai halitta dukkanin kõme, kuma Shĩ ne Wakĩli a kan kõme} [al-Zumar: 62], kuma Allah Ya halicci bayi, kuma Ya halicci ayyukansu, Allah - Maɗaukkain sarki - Ya ce: {Alhãli, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatãwa} [al-Saafat: 96], kuma babu wani mai tarayya da shi a cikin halittarSa kamar yanda babu wani mai tarayya da shi a cikin mulkinSa, Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Wanda Yake da mulkin sammai da ƙasa kuma bai riƙi abin haihuwa ba, kuma abõkin tãrayya bai kasance a gare Shi ba a cikin mulkinSa kuma Ya halitta dukan kowane abu, sa'an nan Ya ƙaddara shi ƙaddarãwa} [al-Furƙan: 2].
Allah Ya kafawa halitta hujja da cewa Shi ne Mahalicci Shi kaɗai, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Mũ ne Muka halitta ku, to, don me bã zã ku gaskata ba? * Shin kuma kun ga abin da kuke fitarwa na maniyyi? * Shin kũ ne kuke halitta shi, kõ kuwa mũ ne Mãsu halittãwa?} [al-Waƙi'ah: 57-59]. Shi koda ya kasance dalili ne akan tashi, to shi daliline akan kaɗaitakarSa - tsarki ya tabbatar maSa - da halitta - alherinSa ya yawaita kuma Ya ɗaukaka -.
BABI BABU KARO TSAKANIN UMARNI DA SHARI'A DA HALITTA HA HANKALI
Kuma muna imani cewa babu karo tsakanin shari'a da umarni da halitta, Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - halitta taSa ce, kuma umarni naSa ne, kamar yadda Yake aikata abinda Yake so, kuma ba'a tambaya game da abinda yake aikatawa, to Shi Yana umarni kuma babu mai juyar da hukuncinSa, kuma babu mai bibiyar umarninSa, Allah - tsarki ya tabbatar maSa - Ya ce: {Lalle ne Ubangijinku Allah ne, wanda Ya halitta sammai da ƙasa a cikin kwãnaki shida, sa'an nan kuma Ya daidaita a kan Al'arshi, Yanã sanya dare ya rufa yini, yanã nẽman sa da gaggawa, kuma rãnã da watã da taurãri hõrarru ne da umurninSa. To, Shĩ ne da halittar kuma da umurnin. Albarkar Allah Ubangijin halittu tã bayyana!} [al-A'araf: 54].
Kuma muna imani cewa Allah Ya ƙaddara ƙaddarorin halittu kafin Ya halicci sammai da ƙasa da shekara dubu hamsin, tare da hakan Ya yi umarni da biyayyarSa da kuma biyayyar manzanninSa da annabawanSa, kuma Ya yi hani daga saɓo da saɓawa manzanninSa da annabawanSa, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka, kuma sunayenSa sun tsarkaka - Ya ce: {Kuma idan Allah Ya shãfe ka da wata cũta, to, bãbu mai yãyẽ ta fãce shi, kuma idan Yanã nufin ka da wani alhẽri, to, bãbumai mayar da falalarSa. Yanã sãmun wanda Yake so daga cikin bãyinSa da shi. Kuma Shĩ ne Mai gãfara, Mai jin ƙai * Ka ce: "Yã ku mutãne! Lalle ne gaskiya, ta zo muku daga Ubangijinku. To, wanda ya shiryu, yã shiryu ne dõmin kansa kawai, kuma wanda ya ɓace yana ɓacewa ne a kansa kawai. Kuma ban zama wakĩli a kanku ba * Kuma ka bi abin da ake yin wahayinsa zuwa gare ka, kuma ka yi haƙuri har Allah Ya yi hukunci. Kuma Shĩ ne Mafi alhẽrin mãsu hukunci} [Yunus: 107-109]. Sai Allah tsarki ya tabbatar maSa ya ɗaukaka Ya haɗa a wannan ayar tsakanin labartawa game da ƙaddarawarSa, da umarni da bin wahayinSa da umarninSa, Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Ka bi abin da aka yi wahayi zuwa gare ka daga Ubangijinka; babu wani abin bautãwa fãce Shi, kuma ka bijire daga mãsu shirki * Kuma dã Allah Yã so, dã ba su yi shirki ba, kuma ba Mu, sanya ka mai tsaro a kansu ba, kuma ba kai ne wakĩli a kansu ba} [al-An'am: 106-107], sai Allah Ya bayyana cewa wajibi shi ne bin shiriya, kuma cewa Shi Ya shiryar da wanda Ya so da falalarSa, kuma Ya ɓatar da wanda Ya so da adalcinSa, tsarki ya tabatar maSa Ya ɗaukaka, tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya ce: {Kuma dã Ubangijinka Ya so, dã Yã sanya mutãne al'umma guda. Kuma bã zã su gushe ba sunã mãsu sãɓã wa jũna * Sai wanda Ubangijinka Ya yi wa rahama, kuma dõmin wannan ne Ya halicce su. Kuma kalmar "Ubangijinka" Lalle ne zã Ni cika Jahannama da aljannu da mutãne gaba ɗaya" ta cika * Kuma dũbi dai Munã bã da lãbãri a gare ka daga lãbarun Manzanni, abin da Muke tabbatar da zuciyarka da shi. Kuma gaskiya ta zo maka a cikin wannan da wa'azi da tunãtarwã ga mãsu ĩmãni * kuma kace wa waɗanda bã su yin ĩmãni, "Ku yi aiki a kan hãlinku, lalle mũ mãsu aiki ne * Kuma ku yi Jiran dãko, lalle mu mãsu Jiran dãko ne * Kuma ga Allah gaibin sammai da ƙasa yake. Kuma zuwa gare Shi ake mayar da dukan al'amari. Sabõda haka ku bauta Masa kuma ku dõgara a kanSa. Kuma Ubangijinka bai zama Mai gafala daga abin da kuke aikatãwa ba} [Hud: 118-123]. A cikin waɗannan ayoyin - kuma - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya haɗa tsakanin labartawarSa game da Mashi'arSa mai gamewa, da kuma tsawatawarSa ga masu saɓawa, da umarninSa ga bayinSa muminai da dogaro gareShi.
Haɗawa tsakanin imani da ƙaddara da aiki da shari'a mai yiwuwa ne kuma abin ƙaddarawa ne; saboda haka ne Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya ce: {Allah ba Ya ɗorawa wani rai sai iyawarta} [al-Baƙara: 286], Kuma Allah - tsarki ya tabbatar masa ya ɗaukaka - Ya ce: {ba ma ɗorawa wani rai sai iyawarta} [al-Mua'Minun: 62].
Kuma Allah Ya umarce mu da haƙuri akan ƙaddarorinSa masu raɗaɗi, sai Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Kuma lalle ne, Muna jarrabar ku da wani abu daga tsõro da yunwa da naƙasa daga dũkiya da rãyuka da 'ya'yan itãce. Kuma ka yi bishãra ga mãsu haƙuri} [al-Baƙara: 155], Kuma Allah tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya ce: {Lallai kaɗai ana cikawa masu haƙuri ladansu ba tare da hisabi ba} [al-Zumar: 10].
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Lallai mafi tsananin mutane bala'i (su ne) annabawa, sannan waɗanda suke biye musu, sannan waɗanda suke biye musu, sannan waɗanda suke biye musu". (Ishaƙ ɗan Rahuwaihu ne ya fitar da shi (2413), da Ahmad a cikin al-Musnad (27079), da Ibnu Abid Duniya a cikin al-Mard wal Kaffarat (6), da al-Nasa'i a cikin al-Kubra (7440).)
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Bala'i ba zai gushe da mumini da mumina ba a kansa da ɗansa da dukiyarsa har sai ya gamu da Allah ba shi da wani laifi". (Tirmizi ne ya fitar da shi (7859), da Ibnu Abi Shaibah (10916), da Ahmad a cikin al-Musnad (7859), da Hannad ɗan Surri a cikin Zuhdu (402).)
Daga Aliyu - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Mun kasance a cikin wata jana'iza a cikn Baƙi'ul Gargaɗ, sai annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya zo mana sai ya zauna muka zauna a gefansa, a tare da shi akwai wata sanda, sai ya sunkuyar da kai, sai ya fara yana tona ƙasa da sandarsa, sannan ya ce: "Babu wani daga cikinku, babu wani rai da aka busawa rai sai an rubuta mata gurinta a aljanna ko a wuta, kuma sai an rubutata 'yar wuta ce ko 'yar aljanna", sai wani mutum ya ce: ya manzon Allah, shin ba ma dogara akan littafina ba, kuma mubar aiki? wanda a cikinmu ya kasance daga 'yan aljanna, to zai kasance ga aikin 'yan aljanna, amma wanda ya kasance daga 'yan wuta, to zai kasance ga aikin 'yan wuta. ya ce; "Amma 'yan aljanna sai a tafiyar adsu ga aikin tsira, amma 'yan wuta sai asawwaka musu aikin 'yan wuta" sannan ya karanta: {Amma wanda aka ba shi kuma ya ji tsoron Allah * kuma ya gasgata da kyakkyawa} zuwa ƙarshen ayar. (Bukhari ne ya fitar da shi (1362), da Muslim (2647), da Abu Dawud (4694), da Tirmizi (3344).)
Daga Imran ɗan Husain - Allah Ya yarda da shi - ya ce; Wani mutum ya ce: Ya manzon Allah, Shin za'a gane 'yan aljanna daga 'yan wuta? ya ce: "Eh", ya ce: To me yasa masu aiki suke aiki? ya ce: 'Kowanne yana aiki ga abinda aka halitta masa, ko: Ga abinda aka sawwaƙa masa". (Bukharine ya fitar da shi (6596), da Muslim (2649), da Abu Dawud (4709).)
Daga Jabir - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Suraƙat ɗan Malik ɗan Ju'usham ya ce: Ya manzon Allah, bayyana mana addininmu kamar an haliccemu a yanzu, ame za’a yi aiki a yau? a me alƙaluma suka bushe kuma ƙaddarori suka gudana da shi, ko a abinda zamu fuskanta?" ya ce: A'a, kai a abinda alƙaluma suka bushe da shi kuma ƙaddarori suka gudana da shi" ya ce: To dan me za’a yi aiki? Zuhair ya ce: Sannan Abuz Zubair ya yi magana da wani abinda ban fahimce shi ba, sai na yi tambaya: Me ya ce: sai ya ce: "Ku yi aiki kowa abi sawwakawane". (Muslim ne ya fitar da shi (2648).)
Daga Sahlu ɗan Sa'ad - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Lallai bawa zai yi aiki - a abinda mutane suke gani - irin aikin 'yan aljanna, lallai cewa shi yana daga 'yan wuta, kuma yana aiki - a binda mutane suke gani - irin aikin 'yan wuta, alhali shi yana daga 'yan aljanna, kaɗai ayyuka (abin la'akari) da ƙarshensu ne". (Bukhari ne ya fitar da shi (6493), da Muslim (112).)
Imam al-Ajurri ya ce yana mai bada labari game da Allah cewa Shi: "Ya so biyayya daga bayinSa kuma Ya yi umrani da ita, sai ta gudana daga waɗanda ya yi masa biyayya da gamkatarɗinSa gare su, kuma Ya yi hani daga saɓo, Ya yi nufin kasancewarsa ba tare da sonSa daga gareShi ba, ba tare da Ya yi umarni da shi ba, Allah Ya ɗaukaka - Mai girma da ɗaukaka - da Ya yi umarni da alfasha, ko Ya sota, kuma Ubangijnmu Ya ɗaukaka Ya buwaya abinda Bai yi nufin gudana a mulkinSa ya gudana ba, ko wani abinda iliminSa bai kewaye da shi ba kafin kasancewarsa, Ya san abinda halitta suke aikatawa kafin Ya haliccesu, da bayan Ya haliccesu, kafin su aikata hukunci da ƙaddara, haƙiƙa alƙalami ya gudana da umarninSa - Allah Maɗaukakin sarki - a cikin Lauhul Mahfuz da (al-Shari'ah, na al-Ajurri (2/702).)
Kuma muna imani cewa kamar yadda babu karo tsakanin halitta da umarni da sharai'a, to babu karo tsakanin shari'a da umarni da kuma hankali, dukkan abinda Allah Ya yi umarni da shi da manzonSa - tsira da a mincin Allah su tabbata agare shi -, ko Allah da manzonSa suka yi hani daga gare shi, ko Allah Ya ƙaddarashi, ko ya bada labarinsa, to ba ya karo da hankali, kai shi ne mahukuntar abinda hankula suka yi umarni da shi, kuma shi ne matuƙar hikima, Mai hikima Masani Ya ce: {Wancan yãnã daga abin da Ubangijinka Ya yi wahayi zuwa gare ka na hikima. Kuma kada ka sanya wani abin bautãwa na daban tãre da Allah har a jẽfa ka a cikin Jahannama kanã wanda ake zargi, wanda ake tunkuɗẽwa} [al-Isra'a: 39], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Hikima cikakka! Sai dai abũbuwan gargaɗi bã su amfãni} [al-Kamar: 5], kuma Allah Ya ce; {Kuma Allah Ya saukar maka da littafi da hikima} [al-Nisa'a: 113], Kuma da shi ne hujja take tsayuwa akan halitta, Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya ce: {Ka ce: "To Allah ne da hujja isasshiya, sabõda haka: Dã Yã so, dã Yã shiryar da ku gabã ɗaya} [al-An'am: 149]. Wannan shari'ar da umarnin da ikon shi yana cikin matuƙar kyau, kai babu mafi kyau sama da shi, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Shin, hukuncin Jãhiliyya suke nema? Kuma wane ne mafi kyau ga hukunci daga Allah sabõda mutãne waɗanda suke yin yaƙĩni (tabbataccen ĩmãni)?} [al-Ma'ida: 50].
Daga Ibnu al-Dailami ya ce; "Na zo wa Ubayyu ɗan Ka’ab, sai na ce masa: Wani abu ya afku a cikin raina na ƙaddara, to ka zantar dani da wani abu wataƙila Allah Ya tafiyar da shi daga zuciyata, ya ce: Da Allah Zai azabtar da ma'abota sammanSa da ma'abota ƙasanSa Ya azabtar da su to Shi bai zalince su ba, kuma da Ya yi musu rahama da rahamarSa ta zama alheri garesu daga ayyukansu, da ka ciyar da zinare kwatankwacin (dutsen) Uhud a tafarkin Allah , to Allah ba Zai karɓa daga gareka ba har sai ka yi imani da ƙaddara, kuma kasan cewa abinda ya sameka bai zama zai kuskure maka ba, kuma abinda ya kuskure maka bai zama zai sameka ba, da ace ka mutu akan wanin hakan da ka shiga wuta. Ya ce: Sanann na zo wa Abdullahi ɗan Mas'ud, sai fadi kwatankwacin hakan, ya ce: sannan na zo wa Huzaifa dan Yaman, sai ya fadi kwatankwacin hakan, ya ce: Sannan na zowa Zaid dan Sabit, sai ya a zantar da ni daga annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi kwatankwacin hakan". (Abu Dawud ne ya fitar da shi (4699), da Ibnu Majah (77), da Ahmad (21589), da Abdu Ibnu Humaid (247), da al-Furayyani a cikin al-Kadr (190), da Sharhu Usul i'itiƙadi Ahlissunnah wal jama'ah (4/676).)
Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce Yana mai yabo ga littafinSa wanda ya ƙunshi shari'a da umarni cewa shi ne mafi kyan zance, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Allah ne Ya saukar da mafi kyan zance wani littafi} [al-Zumar: 23]. Abinda Allah Ya shara'anta shi ko Ya ƙaddara shi to shi yana cikin matuƙar cika da kyau; daidai ne hankula sun riskeshi ne ko sun gajiya daga riskarsa da fahimtarsa, ba ma sanya hankulanmu da ra'ayukanmu masu hukunci akan shari'ar Allah da ikonSa, wani lokaci mu ce ya yi kyau, wani lokaci kuma mu ce ya yi muni, kai dukkan abinda Allah Ya ƙaddara shi Ya kuma shara’anta shi to shi mai cikakken kyaune da cika.
Muna imani cewa shari'a da ƙaddara dukkansu alheri ne, Allah ba Ya ƙaddara sharri tsantsa, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Alheri gaba ɗayansa ahannunKa yake, kuma sharri ba ya gunKa". (Muslim ya fitar da shi (771), da Abu Dawud (761), da Nasa'i (266), da Nasa'i (897).)
Kuma sharri yana shiga ƙunshin gamewar abin da aka ƙaddara, kamar yadda Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Lalle Mũ, kõwane irin abu Mun halitta shi a kan tsãri} [al-Kamar: 49], Sharri yana zuwa a cikin AlKur'ani abin raɓawa zuwa ga wanda ya tsaya da shi, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Ka ce ina neman tsari daga Ubangijin safiya * {Daga sharrin abin da Ya halitta} [al-Falaƙ: 1-2].
Yana daga babin ladabi kada a raɓa sharri zuwa ga Allah - Maɗaukakin sarki -, Allah - Maɗaukaki Ya faɗa Yana Mai bada labari game da aljanu cewa su sun ce: {Kuma lalle ne mũ ba mu sani ba, shin, sharri ne aka yi nufi ga waɗanda ke cikin ƙasa, ko Ubangijinsu Yã yi nufin shiriya a gare su ne?} [al-Jinn: 10], Kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce game da (Annabi) Ibrahim badaɗayi - aminci ya tabbata a gare shi - cewa shi ya ce: {Kuma idan na yi jiyya, to, Shĩ ne Yake warkar da ni} [al-Shu'ara'a: 80], sai ya danganta rashin lafiya ga kansa, waraka kuma ga Allah - GirmanSa ya ɗaukaka -.
BABIN AIKATA SABUBBA YANA CIKIN KADDARA
Muna imani cewa aikata sabubba ba ya kore imani da ƙaddara, kai yin sabubba daga cikar imani ne da hukunci da kuma ƙaddara, kuma Ubangijinmu Ya umarce mu da neman arziƙi, haƙiƙa Ya bamu labari cewa Shi Ya rubuta shi garemu, Allah Ya ce: {Shi, (Allah), Yã sanya muku ƙasa hõrarriya, sai ku tafi cikin sãsanninta, kuma ku ci daga arzikinSa, kuma zuwa gare shi ne tãshin yake} [al-Mulk: 15].
Tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya ce: {Sa'an nan idan an ƙarẽ salla, Sai ku wãtsu a cikin ƙasã kuma ku nẽma daga falalar Allah, kuma ku ambaci sũnan Allah da yawa ɗammãninku, ku sãmi babban rabo} [al-Juma'a: 10].
Kuma Allah Ya faɗa Yana Mai bada labari game da (Annabi) Ya'aƙub cewa shi ya cewa 'ya'yansa: {Kuma ya ce: "Yã ɗiyana! Kada ku shiga ta ƙõfa guda, ku shiga ta ƙõfõfi dabam-dabam, kuma bã na wadãtar muku kõme daga Allah. Bãbu hukunci fãce daga Allah, a gare Shi na dõgara, kuma a gare Shi mãsu dõgara sai su dõgara} [Yusuf: 67]. Daga sa'ib ɗan Yazid: "Cewa annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ɗauki silke biyu ranar Uhud, kamar cewa ya haɗa tsakaninsu". (Ibnu Majah ne ya fitar da shi (2886), da Sa'id ɗan Mansur (2858), da Ahmad (15722), da al-Nasa'i a cikin al-Kubra (8529).) Kuma Allah Ya umarci (Annabi) Nuhu - aminci ya tabbata agare shi - da yin jirgin ruwa, kamar yadda Ya umarci (Annabi) Musa - aminci ya tabbata agare shi - da ya daki kogi, kuma Ya umarci Maryam - aminci ya tabbata agareta - da ta girgiza kututturen dabino dan ɗanyen dabinai su farfaɗo, zuwa wanin hakan daga abinda Allah Ya umarci bayinSa da shi na riƙon sabubba.
Daga mafi girman sabubba: Addu'a, daga Nu'uman ɗan Bashir "Daga annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a cikin faɗinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Kuma Ubangijinku Ya ce ku roƙeNi in amsa muku} Ya ce: Addu'a ita ce ibada, kuma ya karanta: {Ubangijinku Ya ce ku roƙeNi in amsa muku} [Gafir: 60] zauwa faɗinSa: {Kasƙantattu}". (Abu Dawud ne ya fitar da shi (1479), da Tirmizi (2969), da Ibnu Majah (3828).)
Daga sabubba: Magani da tawaida, Daga Abu Khizama, daga babansa - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Na tambayi manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai na ce: Ya manzon Allah, shin kana ganin tawaidar da muke yinta da maganin da muke yin sa da kariyar da muke yi, shin suna maida wani abu daga ƙaddarar Allah? Ya ce: "Suma suna daga ƙaddarar Allah". (Tirmizi ne ya fitar da shi (2065), da Ibnu Majah (3437), da Ibnu Wahb a cikin al-Jami fil Hadith (699), da Ahmad (15472), da Ibnu Abi Asim a cikin al-Ahad wal Masani (2610).)
BABIN KADDARA BA TA KARO DA ADALCI
Muna imani cewa Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Yana umarni da adalci, kuma Yana hukunci da shi a shari'a da ƙaddarawa da sakayya, Allah Maɗaukkain sarki Ya ce: {Lallai Allah Yana umarni da adalci da kyautatawa} [al-Nahl: 90], kuma Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya ce: {Kuma Allah Ya buga wani misãli, maza biyu, ɗayansu bẽbe ne, ba ya iya sãmun ikon yin kõme, kuma shi nauyi ne a kan mai mallakarsa, inda duk ya fuskantar da shi, bã ya zuwa da wani alhẽri. Shin, yanã daidaita, shi da (namiji na biyu) wanda yake umurni da a yi ãdalci kuma yanã a kan tafarki madaidaici?} [al-Nahl: 76], Daga Abu Zarr - Allah Ya yarda da shi - daga annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - cikin abinda ya ruwaito daga Allah - alherinSa ya yawaita kuma Ya ɗaukaka - cewa Shi Ya ce: "Yaku bayi Na, lallai Ni Na haramta zalinci akan kaiNa, kuma Na sanya shi abin haramtawa a tsakaninku, kada ku yi zalinci". (Muslim ne ya fitar da shi (2577), da Tirmizi (2495).)
Kuma Ya korewa kanSa zalinci, sai Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Wanda ya aikata aiki na ƙwarai to sabõda kansa ne, kuma wanda ya mũnanã, to, yanã akansa. Kuma Ubangiwinka, bã Mai zãlunci ga bãyinSa ne ba} [Fussilat: 46], kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Lallai Allah ba Ya zalintar kwatankwacin ƙwayar zarra idan ta kasance kyakkyawa ce Zai ninkata} [al-Nisa'a: 40], Tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya ce: {Kuma wanda ya yi aiki daga ayyukan ƙwarai, namiji ne ko kuwa mace, alhãli kuwa Yanã mũmini, to, waɗannan sunã shiga Aljanna kuma bã zã a zãlunce su da gwargwadon hancin gurtsun dabĩ no ba} [al-Nisa'a: 124], kuma Allah sha'aninSa ya ɗaukaka Ya ce: {Lalle ne Allah ba Ya zãluntar mutãne da kõme, amma mutãnen ne ke zãluntar kansu} [Yunus: 44], Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Wanda ya zo da kyakkyãwan aiki guda, to, yanã da gõma ɗin misãlansa. Kuma wanda ya zo da mũgun aiki gũda, to, bã zã a sãka masa ba fãce da misãlinsa. Kuma sũ bã a zãluntar su} [al-An'am: 160], Zuwa wanin haka daga ayoyi masu nuni akan cikar adalcinSa, da kore zalinci akan kanSa.
Muna imani cewa rigayar hukunci da ƙaddara ba sa lazimtar zalinci ga bayi daga gareShi; domin cewa Allah Ya saukar da littattafai, kuma Ya aiko manzanni; dan kada hujja ta zama ga mutane akan Allah bayan manzanni, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Manzanni mãsu bãyar da bushãra kuma mãsu gargaɗi dõmin kada wata hujja ta kasance ga mutãne a kan Allah bãyan Manzannin. Kuma Allah yã kasance Mabuwãyi, Mai hikima} [al-Nisa'a: 165].
Kuma Ya sanya ƙaddara sirri abin ɓoyewa, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: [Shi ɗai ne Masanin fake sabõda haka, bã Ya bayyana gaibinSa ga kowa} [al-Jinn: 26], kuma Ya sanya wa bayi ganin dama da zaɓi, Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya ce: {Ka ce gaskiya daga Ubangijiku take, wanda ya ga dama ya yi imani wanda ya ga dama ya kafirta} [al-Kahf: 29], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Lalle ne, Mũ, Mun shiryar da shi ga hanyar ƙwarai, ko ya zama mai gõdiya, kuma ko ya zama mai kãfirci} [al-Insan: 3], kuma Allah Ya ce; {Sa'an nan ya yi masa Ilhamar fãjircinsa da shiryuwarsa} [al-Shamsu: 8].
BABIN KAFA HUJJA DA KADDARA
Muna imani cewa Allah Ya aiko manzanni, kuma Ya saukar da littattafai; dan kada hujja ta zama ga mutane akan Allah, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Manzanni mãsu bãyar da bushãra kuma mãsu gargaɗi dõmin kada wata hujja ta kasance ga mutãne a kan Allah bãyan Manzannin. Kuma Allah yã kasance Mabuwãyi, Mai hikima} [al-Nisa'a: 165], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya faɗa Yana Mai bada labari game da mushrikai cewa su sun kafa hujja da ƙaddara akan afkawa cikin shirka, sai Allah Ya bayyana ƙaryarsu, kuma Ya ɗanɗana musu tsananinSa, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Waɗanda suka yi shirki zã su ce: "Dã Allah Yã so dã ba mu yi shirki ba, kuma dã ubanninmu ba su yi ba, kuma dã ba mu haramta wani abu ba." Kamar wannan ne mutãnen da suke a gabãninsu suka ƙaryata, har suka ɗanɗani azãbarMu. Ka ce: "Shin, kunã da wani ilmi a wurinku dõmin ku fito mana da shi? Bã ku bin kõme fãce zato kuma ba ku zama ba fãce ƙiri-faɗi kawai kuke yi} [al-An'am: 148]. Da a ce ƙaddara ta kasance hujja garesu akan shirkarsu da bai ɗanɗana musu tsananinSa ba.
Daga Aliyu- Allah Ya yarda da shi - ya ce: Mun kasance muna zaune tare da manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a tare da shi akwai itace da yake karta ƙasa, ya ce: "Babu wani daga cikinku sai haƙiƙa an rubuta masa mazauninsa a wuta ko a aljanna", sai wani mutum daga mutanen ya ce: Shin ba ma dogara ba ya manzon Allah? ya ce: "A'a, ku yi aiki kowanne abin sawwaƙawa ne". Sannan ya karanta: {Amma wanda ya bayar kuma ya ji tsoron Allah} [al-Lail: 5] zauwa ƙarshen ayar". (Bukhari ne ya fitar da shi (6605), da Muslim (2647), da Tirmizi (2136), da Ibnu Majah (78).) Sai annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi umarni da aiki, kuma ya yi hani daga dogara ga ƙaddara.
Kuma muna imani cewa yana halatta ga bawa ya kafa hujja da ƙaddara akan zunubai bayan tuba daga garesu, Daga Humaid ɗan Abdurrahman cewa Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "(Annabi) Adam da (Annabi) Musa sun yi jayayya, sai (Annabi) Musa ya ce masa: kaine Adamun da kurakuranka suka fitar da kai daga aljanna, sai (Annabi) Adam ya ce masa: Kaine Musan da Allah Ya zaɓeka da saƙonSa da kuma zancenSa, sannan kake zargina akan wani al'amarin da aka ƙaddara akaina kafin a halicceni", sai amnzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata aagre shi - ya ce: "Sai Adam ya kafa wa Musa hujja". (Bukhari ne ya fitar da shi (6614), da Muslim (2652), da Abu Dawud (4701), da Tirmizi (2134), da Ibnu Majah (80).)
Muɗarrif ɗan Abdullahi ɗan al-Shikkir - Allah Ya yi maSa rahama - ya ce: "A AlKur'ani ba'a wakilta mu zuwa ƙaddara ba, haƙiƙa ya bamu labari a cikin AlKur'ani cewa mu masu taimako ne gareshi". (Littafin Sunnah, na Abdullahi ɗan Ahmad (2/412).) Muhammad ɗan Sirin - Allah Ya yi masa rahama - Ya ce: "Idan ma'abota ƙaddara ba su zama daga waɗanda suke kutsawa a cikin ayoyin Allah - Mai girma da ɗaukaka - ba ban san akan abinda suke ba?". (al-Sunnah na Abdullahi ɗan Ahmad (2/432), da Sharhu usuli i'itiƙadi Ahlis Sunnah Wal Jama'ah (4/696).)
Ibnu Wahb, da mutane da yawa sun ce: "An tambayi Malik game da ma'abota ƙaddara: Shin za'a kame daga zancensu? ya ce: Eh, idan ya kasance masani da abinda shi yake akansa. Ya ce: Kuma yana umartarsa da aikin alheri, kuma yana hana shi daga munkari, kuma yana ba su labari da saɓaninsu, ba ya ajiye magana, kuma ba ya sallah garesu, ba'a halartar jana'izojinsu, kuma bana ganin a'auresu, ya yi ƙari a cikin riwayar waninsa: Allah Ya ce: {Bawa mumini shi ne mafi alheri daga mushriki}. [al-Baƙara: 221], ya faɗa a cikin riwayar Ash’habu: ba'a sallah a bayansu, kuma ba'a ɗaukar hadisi a garesu, idan kuka samesu a wata madakata to ku fitar da su daga gare shi". (Tartibul Madarik Wa Taƙribul Masilk)
Kuma muna imani cewa yana halatta ga bawa ya kafa hujja da ƙaddara akan masifu, daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Mumini ƙaƙƙarfa ya fi alheriri da soyuwa a wajen Allah sama da mumini rarrauna, akwai alheri a kowanne, ka yi kwaɗayin yin abinda zai amfane ka, kuma ka nemi taimakon Allah, kada ka gaza, idan wani abu ya sameka kada ka ce: Dana aikata da kaza da kaza ya kasance, sai dai ka ce : Kaddarar Allah abinda Ya so zai aikata, domin cewa (da a ce) tana buɗe aikin Shaiɗan". (Muslim ne ya fitar da shi (2664), da Ibnu Majah (79).)
Daga dan Abbas - Allah Ya yarda da su - faɗinsa a cikin tafsirin faɗinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Su ne waɗanda idan wata musiba ta samesu suka ce mu ga Allah muke kuma mu gare Shi zamu koma} [al-Baƙara: 156]: Ya ce: Allah Ya bada labarin cewa mumini idan ya miƙa al'amari zuwa ga Allah kuma ya yi istirja'i a lokacin musiba, za'a rubuta masa ɗabi'u uku na alheri: Sallah daga Allah da rahama, da tabbatar da hanyar shiriya. Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Wanda ya yi istirja'i a lokacin musiba Allah Zai nashi ladan musibarsa, kuma Zai kyautata ƙarshensa, kuma Zai sanya masa baya na gari wanda zai yarda da shi". (al-Dabari ne ya fitar da shi a cikin al-Tafsir (2/707), (3/223), da Ibnu Abi Hatim a cikin al-Tafsir (1421), da al-Dabarani a cikin al-Kabir (13027), da al-Baihaƙi a cikin al-Shu'ab (9240).)
KUNDIN IBADAH
Kundin a taƙaice
Muna imani cewa Allah Ya halicci halitta dan su bauta masa, ibadar da Allah ya yi umarni da ita ita ce miƙaƙƙiya, ita ce tafarkin (Annabi) Ibrahim - aminci ya tabbata agare shi -, ita ce wacce Allah Ya umarci dukkan nauyaya biyu (mutum da aljan) da ita. Ibadah nau'o'ice da yawa, kuma juyar da wani abu daga gareta ga wanin Allah - Maɗaukakin sarki - ba ya halatta. Daga nau'o'inta: Addu'a, da dogaro ga Allah, da tsoro, da tsoro, da kwaɗayi, da neman tsari, da yanka, da neman taimako, da neman agaji.
Kuma muna imani cewa Allah Ya halicci halitta dan su bauta masa, kuma muna sanin cewa farkon umarnin da ya zo a cikin AlKur'ani shi ne umarni da bautar Allah Shi kaɗai banda waninSa, kuma kowane annabi yana cewa mutanensa: {Ku bautawa Allah, ba ku da wani abin bauta da gaskiya wanda ba shi ba} [al-A'araf: 65].
Kuma muna sanin cewa ibada ba ta kasancewa abar karɓa har sai ta zama tsarkakakkiya ga Allah Ubangijin talikai, mai dacewa da shiriyar shugaban manzanni - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -.
Yana wajaba cewa abin nufi da ibada ya kasance Shi ne Allah Shi kaɗai ba Shi da abokin tarayya, kuma tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya yi gargaɗi daga shirka gaba ɗayanta babbarta da ƙaramarta, wanda ya aikata wani aiki yana mai tsarkake wa saidai cewa shi ba mai dacewa ne da shiriyar manzo - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ba; to aikinsa abin juyarwa ne akansa, wanda ya aikata wani aiki mai dac da shiriyar manzo - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai dai cewa shi ba mai tsarkakewa ne ga Allah ba; to shi abin juyarwane gare shi.
Kuma muna sani cewa tushen ibada uku ne su ne: Cikar so, da cikar ƙauna, da cikar tsoro, kuma cewa annabawa da manzanni sun rabauta daga hakan da mafi yawan rabo.
Mafi girman abinda muminai suke ƙaunarsa shi ne ganin fuskar Allah Mai girma, kuma ganin Allah shi ne mafi ɗaukakar ni'imar 'yan aljanna, kai shi ne ƙarin ni'ima akan ni'imarsu, idan 'yan aljanna suka shiga aljanna, Allah Zai ƙarawa muminai girma da kyautatawa zuwa kyautatawarsu dan falala daga gareShi dan samuwa da izininSa garesu da kallo zuwa gare Shi, kuma mafi girman abinda ma'abota imani suke tsoronsa shi ne haramta musu wannan ni'imar da ya keɓanci masoyanSa da ita daga cikin muminai, kuma ya hana maƙiyanSa daga gare shi, kuma ya shamakance dukkan maƙiyanSa daga duba zuwa gare Shi daga mushrikai da Yahudawa da Nasara da Majusawa da Munafukai.
Kamun ƙafa shi ne neman kusanci zuwa ga Allah da dukkan abinda zai yardar da Shi na wajibi ko mustahabbi. (Kuma wasila tana zuwa da wata ma'anar daban, ita ce abin ambata a cikin faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: "Ku roƙa min Allah al-Wasila".)
Muna imani cewa Allah Ya umarci bayinSa da addu'a, kuma Ya yi musu alƙawari da amsawa, kuma muna sani cewa kamun ƙafa zuwa ga Allah yana kasancewa ne da sunayenSa kyawawa da siffofinSa maɗaukaka; saboda haka ne Da'awar annabawa da manzanni ta kasance mafi yawa suna kasancewa ne da kamun ƙafa da sunayen Allah ne kyawawa. Daga wuraren addu'a (akwai) bayan salloli, da sulusin dare na ƙarshe, da lokacin buɗa baki, da lokacin ɗawafi, da kan Safa da Marwa, da lokacin Arafat da Muzdalifa, da bayan jifan Jamrori.
Kamar yadda kamun ƙafa yake kasancewa da imani da Allah, kamun ƙafa yana kasancewa zuwa ga Allah da aiki na gari da nau'ikan ibadu. Kuma kamun ƙafa zuwa ga Allah yana kasancewa da ambatan hali, da bayyanar da buƙatuwa zuwa ga Allah, kuma cewa bawa mai buƙatuwa ne zuwa taimakon Allah da rahamarSa. Kuma kamun ƙafa yana kasancewa da cewa musulmi ya nemi wani mutum na gari rayayye mahalarci ya yi masa addu'a, kamar yadda 'yan uwan (annabi) Yusuf suka nemi babansu ya nema musu gafara, kuma sahabbai - Allah Ya yarda da su - sun kauce daga neman shayarwa da kamun ƙafa da manzo - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - bayan wafatinsa zuwa kamun kafa da Abbas - Allah Ya yarda da shi -; domin cewa su suna sanin cewa wannan yana daga kamaun kafa abin shara'antawa.
Kamun kafa ba ya halatta da abinda Allah bai shara'anta shi ba; Haƙiƙa mutanen Jahiliyya sun kasance suna neman kusanci zuwa ga Allah ta hanyar kamun ƙafa zuwa gare Shi da gumakansu da allolinsu.
BABIN FADIN ALLAH - MADAUKKAIN SARKI -: {BAN HALICCI ALJANI DA MUTUM BA SAI DAN SU BAUTA MINI}
Muna imani cewa Allah Ya halicci nauyaya biyu (mutum da aljan) dan bautarSa, Mabuwayi Ya ce: {Kuma Ban halicci aljannu da mutãne ba sai dõmin su bauta Mini} [al-Zariyat: 56]; wato: Ba'a umarce su ba sai dan su tsarkake bauta ga Allah Ubangijin talikai. Ibadar da Allah Ya yi umarni da ita, ita ce miƙaƙƙiya, kuma ita ce tafarkin (Annabi) Ibrahim - aminci ya tabbata agare shi - Allah Mabuwayi Ya ce: {Ka ce: "Lalle nĩ, Ubangijina Yã shiryar da ni zuwa ga tafarki madaidaici, addĩni, ƙĩmantãwa (ga abũbuwa), mai aƙĩdar Ibrãhĩm, mai karkata zuwa ga gaskiya, kuma bai kasance daga mãsu shirki ba} [al-An'am: 161].
Ibadar da Allah Ya yi umarni da ita nau'o'i ce da yawa, kuma ba ya halatta juya wani abu daga cikinta ga wanin Allah, Allah Maɗaukakin sarki ya ce: {Kuma lalle ne wurãren sujada na Allah ne, saboda haka kada ku kira kõwa tãre da Allah (da su, a cikinsu)} [al-Jinn: 18].
Daga nau’ukanta: Addu'a, Allah Mabuwayi Ya ce: {Kuma wanda ya kira, tãre da Allah, waɗansu abũbuwan bautãwa na dabam, bã yanã da wani dalĩli game da shĩ (kiran) ba, to hisãbinsa yanã wurin Ubangijinsa kawai. Lalle ne, kãfirai bã su cin nasara} [al-Mua'Minun: 117], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma Ubangijinku ya ce: "Ku kira Ni in karɓa muku. Lalle waɗannan da ke kangara daga barin bauta Mini, za su shiga Jahannama sunã ƙasƙantattu} [Ghafir: 60].
Daga cikinsu dogaro, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce; {Kuma ga Allah to ku dogara in kun kasance muminai} [al-Ma'ida: 23], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: ‘{Wanda duk ya dogara ga Allah to shi Ya isar masa} [al-Dalak: 3].
Daga cikinsu tsoro (wanda ya ginu akan ilimi) Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kada ka ji tsoronsu ku ji tsoroNa} [al-Baƙara: 150].
Daga cikinsu tsoro, Allah - sha'aninSa Allah ya ɗaukaka - Ya ce: {Kada ku ji tsoransu kuma ku ji tsoroNa in kun kasance muminai} [Aa-Imran: 175].
Daga cikinsu kwaɗayi, Allah - yabonSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Waɗancan, waɗanda suke kiran, sunã nẽman tsãni zuwa ga Ubangijinsu. Waɗanne ne suke mafĩfĩta a kusanta? Kuma sunã fãtan sãmun rahamarSa, kuma sunã tsõron azãbarSa. Lalle ne azãbar Ubangijinka ta kasance abar tsõro ce} [al-Isra'a: 57], Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya ce: {Ka ce: "Nĩ, mutum ne kawai kamarku, anã yin wahayi zuwa gare ni cewa: Lalle ne, Abin bautawarku, Abin bautawa Guda ne, sabõda haka wanda ya kasance yanã fãtan haɗuwa da Ubangijinsa, to, sai ya yi aiki na ƙwarai. Kuma kada ya haɗa kõwa ga bauta wa Ubangijinsa} [al-Kahf: 110].
Daga cikinsu neman tsari, Allah yabonSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Ka ce ina neman tsari daga Ubangijin mutane} [al-Nas: 1].
Daga cikinsu yanka, Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Ka ce: "Lalle ne sallãta, da baikõna, da rãyuwãta, da mutuwãta, na Allah ne Ubangijin tãlikai} [al-an'am: 162].
Daga cikinsu neman taimako, Allah Maɗaukkain sarki Ya ce: {Kai kaɗai muke bautawa, kuma Kai kaɗai muke neman taimakonKa} [al-Fatiha: 5].
Daga cikinsu neman agaji, Allah - sha'aniSa ya ɗaukaka - Ya ce: {A lõkacin da kuke nẽman Ubangijinku tairnako, sai Ya karɓa muku cẽwa: "Lalle ne Nĩ, Mai taimakon ku ne da dubu daga malã'iku, jẽre} [al-Anfal: 9].
Kuma muna sanin cewa farkon umarnin da aka ambata a cikin AlKur'ani shi ne umarni da bautar Allah Shi kaɗai banda waninSa, yabonSa ya ɗaukaka kuma sunayenSa sun tsarkaka - Ya ce: {Yã ku mutãne! Ku bauta wa Ubangjinku, Wanda Ya halicce ku, kũ da waɗanda suke daga gabãninku, tsammãninku ku kãre kanku}! [al-Baƙara: 21]. Kuma kowane annabi yana cewa mutanensa: {Ku bautawa Allah ba ku da wani abin bauta da gaskiya wanda ba shi ba}, kamar yadda Allah Ya faɗa a sha'anin farkon manzanni - aminci ya tabbata agare su -: {Lalle ne, haƙĩƙa Mun aika Nũhu zuwa ga mutãnẽnsa, sai ya ce: "Yã mutãnẽna! Ku bauta waAllah! Bã ku da wani abin bautãwa waninSa. Lalle ne nĩ, inã yimuku tsõron azãbar wani Yini mai girma} [al-A'araf: 59], Allah Ya faɗa Yana Mai bada labari game da na ƙarshensu - tsira da aminci ya tabbata agare shi - cewa shi ya cewa mutanensa: {Ku bautawa Allah kada kuyi masa shirka da wani abu} [al-Nisa'a: 36], Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Tabbas mun aiko cikin kowace al'umma wani manzo da ya isar da sakon ku bautawa Allah kuma ku nesanci ɗagutu (duk wani abin bauta da ba Allah ba} [al-Nahl: 36].
Kuma muna sanin cewa ibada ba ta kasancewa abar karɓa har sai ta zama tsarkakakkiya ga Allah Ubangijin talikai, mai dacewa da shiriyar shugaban manzanni - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -. {Saboda haka wanda ya kasance yana fatan haduwa da Ubangijinsa, to ya yi aiki na kwarai, kuma kada ya hada kowa ga bauta wa Ubangijinsa} [al-Kahf: 110].
Kuma muna sani cewa yana wajaba abin nufata da ibada ya kasance Shi ne Allah Shi kaɗai ba Shi da abokin tarayya, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Dukkan ayyuka sai da niyya kuma kowane mutum (yana samun ladan) abinda ya niyyata, to wanda ya yi hijira saboda Allah da ManzonSa to ladan sa yana ga Allah da manzonSa, kuma wanda ya yi hijira dan duniya ko wata mata da zai aura to ladan hijirarsa yana ga abinda ya yi hijira gare shi". (Bukhari ne ya fitar da shi (6689), da Muslim (1907), da Abu Dawud (2201), da Tirmizi (1647), da Nasa'i (75), da Ibnu Majah (4227).)
Kuma tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka ya yi gargaɗi daga shirka gaba ɗayanta babbarta da ƙaramarta, sai Mai girma da ɗaukaka Ya ce: {Lalle ne, Allah ba Ya gãfarta a yi shirki game da Shi, kuma Yana gãfarta abin da yake bãyan wannan ga wanda Yake so, kuma wanda ya yi shirki da Allah, to, lalle ne ya ƙirƙiri zunubi mai girma} [al-Nisa'a: 48]. Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Allah - alherinSa ya yawaita Ya girmama - Ya ce: Ni ne mafi wadatar abokanan tarayya daga shirka, duk wanda ya aikata wani aiki ya hada ni da wani a aikin to Zan bar shi da shirkarsa". (Muslim ne ya fitar da shi (2985).)
Wanda ya aikata wani aiki yana mai tsarkake niyya sai dai cewa shi bai dace da shiriyar manzo - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ba to aikinsa abin juyarwa ne, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Lalle, abin kõyi mai kyau ya kasance gare ku daga Manzon Allah, ga wanda ya kasance yanã fãtan rahamar Allah da Rãnar Lãhira, kuma ya ambaci Allah da yawa} [al-Ahzab: 21]. Kuma tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Wanda ya yi wani aiki wanda babu umarninmu a cikinsa to wannan aikin abun mayarwa ne". (Muslim ne ya fitar da shi (1718).) Kuma Allah - Mabuwayi - Ya ce: {To waɗanda suke saɓa umarninsa su kiyayi kansu kada musiba ko fitina ta sauka a kansu ko kuma azaba mai raɗaɗi ta same su} [al-Nnur: 63], Kuma Allah - Mabuwayi - Ya ce: {Ka ce: "Idan kun kasance kunã son Allah to, ku bĩ ni, Allah Ya sõ ku, kuma Ya gãfarta muku zunubanku. Kuma Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai} [Aal- Imran: 31].
Kuma muna sanin cewa tushen ibadu uku ne, su ne: Cikar so, da cikar ƙauna, da cikar tsoro, haƙiƙa annabawa da manzanni sun rabauta daga hakan da mafi gwaggwaɓan rabo, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya faɗa Yana Mai bada labari game da halinsu: {Lalle ne, su sun kasance suna gudun tsere zuwa ga ayyukan alheri, kuma suna bauta mana dan kwadayi da fargaba. Kuma sun kasance masu kankar da kai gare Mu} [al-Anbiya'a: 90], Kuma Allah - Mabuwayi - Ya ce: {Da waɗanda ke bãyar da abin da suka bãyar, alhãli kuwa zukãtansu sunã tsõrace dõmin sunã kõmãwa zuwa ga Ubangijinsu * Waɗancan sunã gaggãwar tsẽre a cikin ayyukan alhẽri, alhãli kuwa sunã mãsu tsẽrẽwa zuwa gare su (ayyukan alhẽri)} [al-Mu'Minun: 60-61], Tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya ce: {Sãsanninsu nã nĩsanta daga wurãren kwanciya, sunã kiran Ubangijinsu bisa ga tsõro da ɗammãni, kuma sunã ciryawa daga abin da Muka azurta su} [al-Sajda: 16], Allah - Maɗaukakin - Ya ce: {Shin, wanda yake mai tawali'u sa'o'in dare yana mai sujjada kuma yana mai tsayawa ga sallah, yana tsoron lahira, kuma yana fatan rahamar Ubangijinsa} [al-Zumar: 9].
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Allah Yana cewa: Ni Ina inda bawaNa yake zatoNa, kuma Ni Ina tare da shi idan ya ambace Ni, idan ya ambace Ni a cikin ransa zan ambace shi a cikin raiNa, idan ya ambaceNi acikin wasu jama'a, zan ambace shi a cikin wasu jama'a mafi alheri daga garesu, idan ya yi kusanci zuwa gareNi taku ɗaya zan yi kusanci gare shi zira'i, idan ya yi kusanci gareNi zira'i, zan yi kusanci gare shi gaba guda, idan ya zo mini yana tafiya zan zo masa ina gaggawa". (Bukhari ne ya fitar da shi (7405), da Muslim (2675), da Tirmizi (3603), da Ibnu Majah (3822).)
Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Kuma daga cikin mutane akwai wanda yake riƙon kinaye baicin Allah suna sonsu kamar son Allah , kuma waɗanda suka yi imani ne mafiya tsananin so ga Allah} [al-Bakara: 165], kuma tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Abu uku wanda suka kasance tare da shi ya samu zaƙin imani: Allah da Manzansa su kasance mafi soyuwa a gare shi daga waninsu, kuma ya so mutum ba yana sonsa ba ne sai dan Allah, kuma ya ki komawa cikin kafirci bayan Allah Ya tserar da shi daga cikinsa kamar yadda yake ƙin a jefa shi cikin wuta". (Bukhari ne ya fitar da shi (16), da Muslim (43), da Tirmizi (2624), da nasa'i (4987), da Ibnu Majah (4033).)
Daga Abu huraira - Allah Ya yarda dashi - cewa manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Na rantse da wanda raina yake a hannunSa, ɗayanku ba za yi imani ba har sai na zama mafi soyuwa gare shi daga mahaifansa da ɗansa". (Bukhari ne ya fitar da shi (14), da Nasa'i (5015).) Bawa ba zai samu soyayyar Allah ba har sai ya bi manzo - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Ka ce: "Idan kun kasance kunã son Allah to, ku bĩ ni, Allah Ya sõ ku, kuma Ya gãfarta muku zunubanku. Kuma Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai} [Aal- Imran: 31].
Kuma mafi girman abinda muminai suke ƙaunarsa shi ne ganin fuskar Allah Mai girma, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu annuri ne * Zuwa ga Ubangijinsu mãsu kallo ne} [al-Kiyama: 22-23].
Kuma ganin Allah shi ne mafi ɗaukakar ni'imar 'yan aljanna, kai shi ne ƙarin ni'ima akan ni'imarsu, Allah Maɗaukkain sarki Ya ce: {Waɗanda suka kyautata yi, sunã da abu mai kyãwo kuma da ƙari)1), wata ƙũra bã ta rufe fuskõkinsu, kuma haka wani ƙasƙanci. waɗancan ne abokan Aljanna, sunã madawwama a cikinta} [Yunus: 26].
Daga Suhaib - Allah Ya yarda da shi - daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Idan 'yan aljanna suka shiga aljanna, ya ce: Allah -Maɗaukakin sarki - zai ce: Kuna san wani abu ne da zan ƙaro muku shi? sai su ce: Ba ka haskaka fusokinmu ba? kuma ba Ka shigar da mu aljannah ba, kuma ka tseratar da mu daga wuta? ya ce: Sai a yaye hijabi, ba'a basu wani abu mafi soyuwa a gare su ba kamar ganin Ubanginsu - Mai girma da ɗaukaka -". (Muslim ya fitar da shi (181), da Tirmizi (2552), da Ibnu Majah (187).
BABIN TAWASSULI (KAMUN KAFA) DA WASILA
Wasila ita ce neman kusanci zuwa ga Allah da dukkan abinda yake yardar da Shi na wajibi ko mustahabbi.
Mun imanai cewa Allah Ya umarci bayinSa da addu'a, kuma Ya yi musu alƙawari da amsawa, sai Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Kuma Ubangijinku ya ce: "Ku kira Ni in karɓa muku. Lalle waɗannan da ke kangara daga barin bauta Mini, za su shiga Jahannama sunã ƙasƙantattu} [Ghafir: 60], Allah - Maɗaukaki kuma sunayenSa sun tsarkaka Ya ce: {Kuma idan bãyiNa suka tambaye ka daga gare Ni, to, lalle Ni Makusanci ne. Ina karɓa kiran mai kira idan ya kirã Ni. Sabõda haka su nẽmi karɓawaTa, kuma su yi ĩmãni da Ni: tsammãninsu, su shiryu} [al-Baƙara: 186].
Kuma muna sanin cewa kamun ƙafa zuwa ga Allah yana kasancewa ne da sunayenSa kyawawa, da siffofinSa maɗaukaka, kamar yadda Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Allah Yana da sunaye kyawawa to ku kiraShi da su, kubar waɗanda suke ilhadi a cikin sunayenSa, za'a yi musu sakayya da abinda suka kasance suna aikatawa} [al-A'araf: 180], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Ka ce: "Ku kirayi Allah kõ kuwa ku kirãyi Mai rahama. Kõwane kuka kira to Yanã da sũnãye mafi kyau. Kuma, kada ka bayyana ga sallarka, kuma kada ka ɓõye ta. Ka nẽmi hanya a tsakãnin wancan} [al-Isra'a: 110].
Saboda haka ne addu'o'in annabawa da manzanni sun kasance mafi yawa kamun ƙafa ne da sunayen Allah kyawawa, kamar yadda Allah Ya faɗa Yana Mai bada labari game da (Annabi) Adam da matarsa cewa su sunce: {(Ya) Ubangijin mu ! Mun zalinci kawunan mu, kuma idan ba Ka gafarta mana ba ba Ka yi mana rahama ba tabbas za mu kasance cikin masu asara)} [al-A'araf: 23], kuma badaɗayi - aminci ya tabbata agare shi ya ce: {Yã Ubangijina! Ka sanyã ni mai tsayar da salla. Kuma daga zũriyyata. Yã Ubangijinmu! Kuma Ka karɓi addu'ata} [Ibrahim: 40], kuma (Annabi) Musa - aminci ya tabbata agare shi ya ce: {Ya ce: "Yã Ubangijina! Ka gãfarta mini, nĩ da ɗan'uwana, kuma Ka shigar da mu a cikin rahamarKa, alhãli kuwa Kai ne Mafi rahamar mãsu rahama} [al-A'araf: 151].
Kamar yadda kamun ƙafa yake kasancewa da yin imani da Allah, Allah Maɗaukakin sarki ya ce: {Yã Ubangijinmu! Mun yi imãni da abin da Ka saukar, kuma mun bi ManzonKa, sai Ka rubũta mu tãre da mãsu shaida} [Aal- Imran: 53].
Kuma kamun ƙafa yana kasancewa da aiki na gari, kamar yadda yake a cikin ƙissar mutum ukun nan da kogo ya rufe da su, Daga Abdullahi ɗan Umar - Allah Ya yarda da su - ya ce: Na ji manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana cewa: Wasu mutum uku sun tafi daga waɗanda ke gabanku har suka zowa makwanci a wani kogo, sai suka shige shi , sai wani kurman dutse ya gangaro daga dutsen, sai ya toshe musu kogon, sai suka ce: Lallai cewa ba abin da zai tseratar da ku daga wannan kurman dutsen sai ku roƙi Allah da ayyukanku na gari, sai wani daga cikinsu ya ce: Ya Allah ina da iyaye biyu tsofaffi, na kasance bana karya kumallo ko iyalai kafinsu, ko dukiya (bayi ko dabbobi), sai neman wani abu ya nisasantar da ni wata rana, ban dawo garesu ba har suka yi bacci, sai na tatsar musu nonansu, sai na samesu sun yi bacci, kuma naki in shayar da iyalai ko dukiya kafinsu, sai na jira alhali kwaryar tana hannuna ina jiran farkawarsu har alfijir ya bullo, sai suka farka, sai suka sha nonansu. Ya Allah idan na kasance na aikata hakan dan neman yardarKa to ka yaye mana abinda muke ciki na wannan kurman dutan. Sai ya dan buda kadan, ba za su iya fita ba daga cikin wannan kurman dutsen ba, ". Sai Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: dayan kuma ya ce: Ya Allah ! Ya kasance ina da 'yar baffana, ta kasance mafi soyuwar mutane gareni, sai na yi nufinta, sai ta hana ni kanta, har wani fari daga shekaru suka sauka gareta, sai ta zo wurina sai na bata dinare ɗari da ashirin akan ta bani kanta, sai ta aikata, har sai da na sami iko akanta, sai ta ce: Ban halatta maka ka farka rufafen abu ba sai da haƙƙinsa, sai na damu daga afka mata, sai na juya daga gareta alhali ita ce mafi soyuwar mutane gareni, na bar mata zinaren da na bata. Ya Allah in na kasance na aikata hakan dan neman yardarKa to Ka yaye mana abinda muke cikinsa. Sai kurman dutsen ya ɗan buɗe sai dai cewa su ba za su iya fita daga agreshi ba. Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: Na ukun ya ce: Ya Allah ni na hayi wasu 'yan haya, sai na basu ladansu banda mutum daya ya bar min abinda na ba shi ya tafi, sai na yi kasuwanci da ladansa har suka yi yawa na dukiya, sai ya zo mini bayan wani lokaci sai ya ce: Ya bawan Allah Ka bani ladana, sai na ce:Duk abinda kake gani to ladanka ne na rakuma da shanu da tumakai da bayi, sai ya ce: ya bawan Allah, kada ka yi mini izgili! sai na ce: Ni ba na maka izgili, sai ya karbe shi gabadayansa, sai ya korasu, baibar komai ba daga gare shi. Ya Allah idan na kasance na aikata hakan dan nemn zatinKa to Ka yaye mana abinda muke cikinsa. Sai kurman dutsen ya bude sai suka fita suna tafiya. (Bukhari ne ya fitar da shi (2272), da Muslim (2743).)
Kuma kamun ƙafa zuwa ga Allah yana kasancewa da nau'ikan ibadu, daga mafi muhimmancinsu addu'a, kamar yadda yabonSa ya ɗaukaka Ya faɗa a sha'anin annabawanSa: {Lalle ne su sun kasance suna gudun tsere zuwa ga ayyukan alheri, kuma suna kiranMu dan kwadayi da fargaba. Kuma sun kasance masu kankar da kai gare Mu} [al-Anbiya'a: 90]. Daga guraren addu'a (akwai) bayan salloli, da sulusin dare na ƙarshe, da lokacin buɗa baki, da a cikin Dawafi, da kan Safa da Marwa, da Arafat, da Muzdalifa, da bayan jifan Jamrori.
Kuma kamun ƙafa yana kasancewa da ambatan hali, da bayyanar da buƙatuwa zuwa ga Allah, kuma cewa bawa mai buƙatuwa ne ga taimakon Allah da rahamarSa, Allah Maɗaukakin sarki Ya faɗa Yana Mai bada labari game da (Annabi) Musa - aminci ya tabbata agare shi - cewa shi Ya ce: {(Ya) Ubangijina lallai ni mabukacine dangane da abinda Ka saukar zuwa gareni na alheri} [al-Kasas: 24], kuma yabonSa ya ɗaukaka Ya faɗa a sha'anin Annabin Allah Ayyuba - aminci ya tabbata agare shi cewa shi yayi addu'a sai ya ce: {Lallai cewa ni cuta ta same ni kuma Kaine mafi jin ƙan masu jin ƙai} [al-Anbiya'a: 83].
Kuma kamun ƙafa yana kasancewa (mutum) musulmi ya nemi wani mutum na gari rayayye halartacce ya yi masa addu'a, kamar yadda 'yan uwan (Annabi) Yusuf - aminci ya tabbata agare shi - suka nemi baba su ya roka musu gafara, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya faɗa Yana mai bada labari game da hakan: {Suka ce: "Yã ubanmu! ka nẽma mana gãfara ga zunubanmu, lalle ne mũ, mun kasance mãsu kuskure} [Yusuf: 97], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Da a ce su lokacin da suka zalinci kansu sun zo maka sun nemi gafarar Allah kuma manzo ya nema musu gafara, da sun sami Allah Mai yawan karɓar tuba ne kuma Mai yawan rahama ne} [al-Nisa'a: 64]. Daga Anas ɗan Malik, daga innarsa Ummu Hiram 'yar Milhan, ta ce: Wata rana annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi bacci kusa da ni, sannan ya farka yana murmushi, sai na ce: Me yasaka dariya? ya ce: "Wasu mutane ne daga al'ummata aka bijiro mini su, suna hawa wannan koren kogin kamar sarakuna akan gadaje", ta ce: To ka roƙi Allah Ya sanyani daga cikinsu sai ya roƙi Allah, sannan ya yi bacci na biyu, sai ya aikata kwatankwacinsa, sai ta faɗi kwatankwacin abinda ta faɗa, sai ya amsa mata kwatankwacin abinda ya amsa mata, sai ta ce: Ka roki Allah Ya sanya ni daga cikinsu, sai ya ce: "Ke kina daga na farko". (Bukharin ne ya fitar da shi (2799), da Muslim (1912), da Abu Dawud (2490), da Nasa'i (3172), da Ibnu Majah (2776).)
Yayin da annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya fassara siffar (mutum) dubu saba'in waɗanda zasu shiga aljanna ba tare da hisabi ba, sai Ukasha - Allah Ya yarda da shi - ya miƙe, sai ya ce: "Ka roƙi Allah Ya sanyani daga cikinsu". (Muslim ne ya fitar da shi (218).)
Daga Anas - Allah Ya yarda da shi - cewa Umar ɗan Khaɗɗab - Allah Ya yarda da shi - "Ya kasance idan sukai fari sai su roƙi ruwa da tawassuli da Abbas ɗan Abdulmuɗɗalib, sai ya ce: Ya Ubangiji mu mun kasance muna tawassuli gareKa da annabinmu sai Ka shayar da mu, kuma mu muna tawassuli zuwa gareKa da baffan annabinmu Ka shayar da mu, ya ce: Sai a shayar da su". (Bukhari ne ya fitar da shi (1010).) Sai shabbai - Allah Ya yarda da su - suka kauce daga neman shayarwa da kamun ƙafa da addu'ar manzo - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - dan kasancewarsa ya rasu zuwa kamun ƙafa da addu'ar Abbas - Allah Ya yarda da shi -; dan kasancewarsu suna sanin cewa wannan yana daga tawassulin da aka shara'anta, Umar - Allah Ya yarda da shi - yana nufin kamun ƙafa da addu'ar Abbas, ba da Abbas ɗin ba shi da kansa ba; domin cewa shi da a ce ana nufin kamun ƙafa da Abbas shi da kansa da annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya fi cancanta da hakan.
Kamun ƙafa ba ya halatta da abinda Allah bai shara’anta shi ba; Haƙiƙa mutanen Jahiliyya sun kasance suna neman kusanci zuwa ga Allah ta hanyar kamun ƙafa zuwa gare Shi da gumakansu da allolinsu, Allah - Maɗaukakin sarki Ya fada Yana Mai bada labari daga mummunan aikinsu: {Waɗanda suka riƙi masoya koma bayanSa (suna cewa) ba ma bauta musu sai dan su kusanto da mu zuwa ga Allah kusanci} [al-Zumar: 3].
KUNDIN ABINDA YAKE KISHIYANTAR ASALIN IMANI KO YAKE KISHIYANTAR CIKARSA
Kundin a taƙaice
Muna sanin cewa daga abinda yake kishiyantar imani da Allah: Kafirciwa Allah.
Kafirci yana kasancewa babba da ƙarami, babban mai fitarwa ne daga tafarki, kuma Allah ba Ya karɓar farilla ko nafila daga mai shi, shi mai ɓata dukkanin ayyuka ne, kuma kafiri madawwami ne abin dawwamarwa a cikin wuta, amma ƙarami to yana kishiyantar cikar imani ne.
Kuma muna sanin cewa kafirci babba nau'o'i ne, Allah Ya bada labari game da su a cikin littafinSa, kuma Ya ambaci cewa kafircin kafirai wani lokaci yana kasancewa musantawa, wani lokaci kuma hanuwa da girman kai daga gaskiya, wani lokaci kuma yana kasacewa da ƙaryatawa, babu banbanci tsakanin ƙaryatawa da harshe, da kuma ƙaryatawa da zuciya, wani lokaci kuma yana kasancewa kokwanto da zato, shi mai kaikawone a cikin umarnin Allah mai kokwanto ne a tashin alƙiyama da haɗuwa da Allah, wani lokaci yana kasancewa zagi da izgili, wani lokaci kuma yana kasancewa bijirewa da hanawa daga tafarkin Alla, wani lokaci kuma yana kasancewa da kin gaskiya.
Kuma muna sani cewa daga kafirci akwai kafirci koma bayan kafirci babba, shi ne kafirci ƙarami, ba ya kishiyantar asalin imani, sai dai cewa shi yana kishiyantar cikarsa, shi ba ya dawwamar da mai shi a cikin wuta, kuma ba ya ɓata dukkan ayyuka, kuma shi nau'o'ine da yawa.
Yana daga gare cikin shi : Akwai yakar musulmi, wannan kafirci ne ba ya fitarwa daga tafarki, kuma ba ya dawwamar da mai shi a cikin wuta; domin cewa Allah Ya ambaci muminai masu yaƙi tsakaninsu 'yan uwa sai Ya ambacesu muminai, alhali su suna yaƙi tsakaninsu.
Kuma muna sanin cewa daga abinda yake kishiyantar imani da Allah: Yi wa Allah Mai girma shirka - shi ne mafi girman zalinci - kuma shirka tana ɓata dukkanin ayyuka, shirka Allah ba Ya yin gafara ga mai yinta idan ya mutu bai tuba ba, kuma mushriki idan ya mutu bai tuba ba to aljanna haramun ce gareshi, kuma makomarsa ita ce Jahannama, yana madawwami a cikinta.
Haƙiƙa Allah ya ɓata shirka, Ya siffantawa mushrikai shirkarsu, kuma Ya bayyana ɓacin riƙonsu kishiyoyi, kuma cewa su ba sa anfanarwa kuma ba sa cutarwa, wani lokaci yana bayyana cewa waɗannan abokanan tarayyar ba sa ji, da sun ji ma ba zasu iya amsawa wanda ya kirasu ba. Wani lokaci kuma Allah Yana bayyana cewa waɗannan abokanan tarayyar ba sa anfanarwa ba sa cutarwa, kuma ba sa mallakar mutuwa ko rayuwa, wani lokaci kuma Allah Yana bayyana cewa waɗannan abubuwan da ake bautawa koma bayan Allah sune mafiya tawaya daga wanda ya bauta musu; domin cewa su ba sa tafiya, basa damka, basa ji. Wani lokaci kuma Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Yana bayyana gajiyawar wadannan abubuwan bautar da rauninsu, wani lokaci kuma Allah - sha'aninSa ya buwaya - Yana hukunci akansu da bukatuwa da karanci, kuma cewa su basa mallakar kwatankwacin kwayar zarra a cikin sammai da kasa cikakkiyar mallaka, kuma basa mallakar tarayya acikin wani abu daga hakan, kuma babu wani abu daga garesu mai taimako ga Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya daukaka - ko masu ceto gareShi, wani lokaci Allah Yana bayyana cewa samuwar alloli tare da Allah mai hanuwa ne a hankalce, kuma mai koruwane a kasancewa, kuma bataccene a shari'ance.
Kuma muna sanin cewa shirka babba nau'o'i ce da yawa:
Daga cikinta: A sanya abokin tarayya tare da Allah a cikin RububiyyarSa da halittarSa da mulkinSa da arziƙinSa da tsarinSa, kuma Allah Ya bayyana cewa Shi ne Mai kaɗaitaka tsarki ya tabbatar maSa - da halitta da umarni.
Daga cikinsu: Bawa ya sanyawa Allah ɗa - Allah Ya ɗaukaka daga hakan ɗaukaka mai girma.
Daga cikinta: Yin imani da taurari da bauta musu, daga hakan - kuma - neman shayar da ruwa da taurari, da ƙudirce cewa su suna jawo arziƙi.
Daga cikinta: Ya sanya wani abokin tarayya tare da Allah a cikin sunayenSa ko siffofinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -, kamar wanda yake riya cewa wani wanda ba Allah ba yana sanin gaibu, haƙiƙa narko mai tsanani yazo akan wanda ya ambaci kansa, ko ya ambaci waninsa da wani suna daga sunayen Allah waɗanda basa kamatuwa sai ga Allah kamar lafazin ɗaukaka "Allah", ko "ar-Rahman".
Daga cikin ta : Ya ƙudirce cewa wani daga halitta mai siffantuwa ne da cikar Allah, ko cewa shi mai iko ne akan dukkan komai, tayaya?! haƙiƙa tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya bayyana cikakkiyar gajiyawa ga masu yin bautar da kuma waɗanda ake bautawa koma bayanSa.
Daga cikinsu: Ya sanya wasu allolin daban tare da Allah.
Daga cikinsu: Ya juyar da bauta ko wani yanki daga gareta ga wanin Allah.
Daga cikinta: Yanka ga wanin Allah ta hanyar neman kusanci, kamar wanda yake yanka ga gumaka ko matattu dan neman kusanci garesu.
Daga cikinsu: Bakance ga wanin Allah, bakance bautace ga Allah juyar da shi ba ya halatta ga wanin Allah; saboda haka ne Allah Ya yabi muminai waɗanda suke cika bakance.
Daga cikinta: Neman taimako da wanin Allah.
Daga cikin ta: Neman agaji da neman taimako da wanin Allah a cikin abinda babu mai iko akansa sai Allah, ko kiran wanin Allah - Maɗaukakin sarki -.
Daga cikinta: Tarayya ta biyayya ga wanin Allah, Allah Ya ambaci cewa mazowa littafi sun riƙi malumman yahudawansu da masu bautar kiristancinsu iyayen giji suna shara'anta musu, kuma suna haramta musu abinda Allah Ya halatta musu.
Daga cikinta: Yin shirka a cikin sallah da ruku'u da sujjada da ɗawafi; cewa waɗannan ibadun da makamantansu juyasu ga wanin Allah ba ya halatta, kuma Allah Ya umarci badaɗayinSa - aminci ya tabbata agare shi - ya tsarkake ɗakinSa dan masu ɗawafi da masu Itikafi da amsu ruku'u masu sujjada, kuma Allah Ya ambaci cewa ba mai hanuwa daga bautarSa sai masu girman kai, kuma Allah Ya ambaci cewa dukkan ababen halitta sunawa Allah sujjada.
Daga cikinsu: Hukunci da abinda Allah bai saukar ba, da neman hukunci ga wanin Allah, kamar yadda mazowa littafi da wasunsu suka aikata; inda suka sanya abokanan tarayya ga Allah suna shara'anta musu shari'u, wannan wani lokaci yana zama kafirci, wani lokaci kuma yana zama zalinci, wani lokaci kuma yana zama fasiƙanci.
Daga cikinsu: Shirka ta soyayya, ita ce mutum ya so abin halitta soyayya mai haɗuwa da ƙasƙanci da girmamawa da ƙanƙar da kai.
Daga cikinta: Shirkar tsoro, ita ce ya ji tsoron abin halitta tsoro mai gwamuwa da ƙanƙar da kai da ƙasƙanci da girmamawa, kamar ya ji tsoron saukar da bala'i akansa, ko ya hana alheri daga gare shi, ko yabar wajibi saboda shi, ko saboda shi ya aikata wani abinda aka haramta ta hanyar neman kusanci, kuma Allah - Maɗaukaki - Ya bayyana cewa ma'abota soyayyrSa ba sa jin tsoron kowa sai Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -.
Daga cikinta: Shirka ta ƙauna, ita ce kamar ya ƙaunata daga wani abin halitta rayayye wanda yake nan ko wanda ba ya nan abinda ba mai iko akansa sai Allah, ko ya ƙaunaci yaye baƙin ciki da biyan buƙatu da ceto daga matattu ranar alƙiyama.
Daga cikinta: tsafi.
Daga cikinta: Bokanci, da duba; domin wanda yake da'awarsu yana da'awar sanin gaibu.
Kuma muna sani cewa daga shirka akwai shirka ƙarama, ba ta fitarwa daga Musulunci, kuma ba ta kishiyantar asalin imani, sai dai cewa ita tana kishiyantar cikarsa, ita ba ta dawwamar da mai ita a cikin wuta, kuma ba ta ɓata dukkan ayyuka, kuma ita nau'o'ice da yawa.
Daga cikinta: Canfi, ma’anar canfi - kamar yadda ya zo a cikin hadisi - abinda ya sa ka tafi ko ya dawo da kai.
Daga cikinta: Rataya layu.
Daga cikinta: Akwai karamar riya, amma wanda zuciyarsa ta cika da riya, ya kasance yana aikata ayyuka na gari ba tare da niyya ko imani, ko tsoro ba, to shi munafiki ne tsantsa, kuma aikinsa ɓatacce ne abin juyarwa ne ba abin karɓa ba ne, manzo - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ambace shi boyayyiyar shirka, kuma tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya bayyana cewa riya ɓoyayya ce sosai, kuma cewa shi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance yana jin tsoronta ga al'ummarsa mafi tsanani sama da tsoronsa akanta daga Dujal.
Daga cikinta: Nufin mutum duniya da aikinsa (na lahira), wannan mai kai kawone tsakanin ya kasance babbar shirka, ko ya kasance ƙarama gwargwadan abinda yake tsayuwa a cikin zuciyar bawa.
Daga cikinsa: Ilimin taurari, ilimin taurari yakan kasance babbar shirka, kuma yakan kasance ƙaramar shirka gwargwadan abinda yake tsayuwa a zuciya.
Daga cikinta: Faɗin mutum: Allah Ya so kaso da abinda ke kama da su na lafazuka.
Daga cikinta: Rantsuwa da wanin Allah.
Kuma muna sani cewa daga abinda yake kishiyantar imani da Allah: Munafunci, shi ne bayyanar da musulunci, da ɓoye kafirci, shi akwai babba da ƙarami, munafunci shi ne kafirci, ya kafircewa Allah ya bautawa waninSa, ya bayyanar da musulunci a bayyane, misalin munafukan da suka kasance a zamanin manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, munafunci babba mai fitarwa ne daga tafarki, muna shaidawa da shaidawar Allah cewa munafukai maƙaryata ne a da'awarsu ta imani.
Kuma Allah ba Ya karɓar farillar munafiki ko nafilarsa, kuma makomar munafukai - idan sun mutu akan munafunci - (ita ce) dawwama a cikin wuta.
Kuma muna sani cewa munafunci babba yana kasancewa da ƙin gaskiya, da ƙyamarta, kuma yana kasancewa da farin ciki da rashin nasar musulunci da ma'abotansa, da baƙin ciki idan sun ga nasara ga musulunci, kuma yana kasancewa da kfirci bayan imani, da bijirewa daga karɓar neman hukunci zuwa ga shari'a, kuma yana kasancewa zato ga Allah mummunan zato cewa Shi ba zai taimaki annabinSa ba - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - da addininSa, kuma yana zama izgili daga gaskiya da ma'abotanta, da zaginsu, da yi musu izgili - kuma yana kasancewa yafice ga musulmai - kuma yana kasancewa yaudara ga masu imani da riyar ayyuka.
Allah Ya umarci annabinSa - tsira da amincin Allah su tabbata aagre shi - da muminai da yaƙar munafikai.
Kuma muna sani cewa munafunci ƙarami ba ya fitarwa daga tafarki, kuma ba ya ɓata aiki, ba ya dawwamar da mai shi a cikin wuta, kuma ba ya kishiyantar asalin imani, sai dai cewa shi yana kishiyantar cikarsa, kuma cewa munafunci nau'o'ine huɗu, wanda ya kasance a cikinsu ya zama munafuki, wanda ya zama akwai wata ɗabi'a daga waɗannan huɗun ya kasance akwai ɗabi'a ta munafunci a cikinsa har sai ya barta: idan yai zance ya yi ƙarya, idan ya yi alƙawari ya saɓa, idan aka yi alƙawari da shi sai ya yi yaudara, idan ya yi husuma sai ya yi fajirci.
*Bidi'a dukkanta ɓata ce.
Muna imani cewa Allah Ya cika mana addini, kuma Ya cika ni'ima garemu. Daga abinda yake kishiyantar cikar imani bidi'o'i a cikin addini, kuma muna sanin cewa Allah Ya yi hani daga rarrabuwa da saɓani.
Kuma muna sani cewa daga bidi'o'i akwai girmama ƙaburbura da gini akansu, sukan kai zuwa ga shirka, daga bidi'o'i hotunan mutanen kirki dan ƙaunar koyi da su bayan mutuwarsu.
Kuma muna sanin cewa daga bidi'o'i ababen ƙi: Tarukan bidi'o'i da tarayya da kafirai a idinansu.
Kuma muna sanin cewa daga bidi'o'i ababen ƙi: Neman albarka daga abinda Allah bai sanya shi sababi mai albarka ba, wannan yakan kasance sababi zuwa ga shirka.
BABIN KAFIRCEWA ALLAH
Muna sanin cewa daga abinda yake kishiyantar imani da Allah: Kafircewa Allah, kuma shi babba ne da ƙarami, babban kafirci yana kishiyantar asalin imani, ƙaramin kafirci kuma yana kishiyantar cikarsa, babban mai fitarwa ne daga tafarki, Allah ba Ya karɓar farilla da nafila daga ma'abocinsa, Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma wanda ya nẽmi wanin Musulunci ya zama addini, to, bã zã a karɓa daga gare shi ba. Kuma shi a Lãhira yana daga cikin mãsu hasãra} [Aal- Imran: 85], kuma Maɗaukakin sarki Ya ce: {Lalle ne wanɗanda suka kãfirta, kuma suka mutu alhãli kuwa suna kãfirai to bã zã a karɓi cike da ƙasa na zinãri daga ɗayansu ba, kõ dã ya yi fansa da shi, waɗannan sunã da azãba mai raɗaɗi, kuma bã su da wasu mataimaka} [Aal- Imran: 91], kuma Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Kuma ku ji tsron wani yini, (a cikinsa) rai bã ya Wadãtar da wani rai da kõme, kuma bã a karɓar cetõ daga gareshi, kuma ba a karɓar fansa daga gare shi, kuma bã su zama ana taimakon su ba} [al-Baƙara: 48]. Kafirci mai ɓata dukkanin ayyuka ne, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Wanda ya kafirce da imani to haƙiƙa ya ɓata aikinsa kuma shi a lahira yana daga taɓaɓɓu} [al-Ma'ida: 5], Daga Dan Abbas - Allah Ya yarda da su - faɗinSa: {Wanda ya kafirce da imani to haƙiƙa ya ɓata aikinsa}, ya ce: "Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya bada labari cewa imani shi ne igiya mafi aminci, kuma cewa Shi baYa karɓar wani aiki sai da shi, kuma ba Ya haramta aljanna sai ga wanda ya bar shi". (Tafsir al-Dabari (3/113) da (9/593), kuma Ibnu Abi Hatim ya fitar da shi a cikin al-Tafsir (1307), sai dai a cikin Tafsirin faɗinSa: {Idan suka yi imani da kwatankwacin abida kuka yi imani da shi}.)
Kafiri madawwamine kuma abin dawwamarwa ne a cikin wuta, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Lallai waɗanda suka kafirta suka zalinci kawunansu Allah baZai kasance Zai gafarta musu ba ko kuma ya shiryar da su hanya * Sai dai hanyar Jahannama suna masu dawwama a cikinta har abada kuma hakan mai sauƙine ga Allah} [al-Nisa'a: 169].
Kafirci babba nau'o'i ne, Allah Ya bada labari game da su a cikin littafinSa, kuma Ya ambaci cewa kafircin kafirai wani lokaci yana zamowa musantawa ne, Maɗaukkain sarki Ya ce: {Lalle ne Muna sani cewa haƙĩƙa, abin da suke faɗa yana ɓãta maka rai. To, lalle ne su, bã su ƙaryata ka (a cikin zukatansu) kuma amma azzãlumai da ãyõyin Allah suke musu} [al-An'am: 33], Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Babu mai musanta ayoyinmu sai dukkanin mai yawan yaudara mai yawan kafirci} [Luƙman: 32], Kuma Allah - Mabuwayi - Ya ce: {Kuma suka yi musunsu, alhãli zukãtansu sun natsu da su dõmin zãlunci da girman kai. To, ka dũbi yadda ãƙibar maɓarnata ta kasance} [al-Naml: 14].
Wani lokaci kuma kafirci yana kasancewa hanuwa da kuma girman kai daga gaskiya, Allah Maɗaukakin sarki Ya faɗa a cikin sha'anin Iblis - kuma shi ne jagoran kafirai: {Kuma a lõkacin da Muka ce ga malã'iku: "Ku yi sujada ga Ãdam," Sai suka yi sujada, fãce Ibilĩsa ya ƙi, kuma ya yi girman kai, kuma ya kasance daga kãfirai} [al-Baƙara: 34]. (Annabi) Nuhu ya ce: {Kuma lalle ne ni, kõ da yaushe na kirãye su dõmin Ka gãfarta musu, sai su sanya yatsunsu a cikin kunnuwansu, su lulluɓe da tufãfinsu, su dõge ga yin laifi. Sun yi girman kai iyãkar girman kai} [Nuhu: 7].
Wani lokaci kafirci yana kasancewa ƙaryatawa, kamar yadda Allah Ya faɗa a cikin sha'anin al'ummomin da suka gabata: {Kamar ɗabi'ar mutãnen Fir'auna da waɗanda ke a gabãninsu, sun ƙaryata ãyõyinMu, sai Allah Ya kãmã su sabõda zunubansu, kuma Allah Mai tsananin uƙũba ne} [Aal- Imran: 11], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Ba haka ba! waɗanda suka kãfirta, sai ƙaryatãwa suke yi} [al-Inshiƙaƙ: 22]. Babu banbanci tsakanin ƙaryatawa ta zama da harshe, da kuma zuciya, Allah Ya faɗa a cikin sha'anin munafukai: {Ashe, ba ka ga waɗanda suka yi munãfinciba, sunã cẽwa ga 'yan'uwansu, waɗanda suka kãfirta daga Mazõwa Littafi, "Lalle idan an fitar da ku, lalle zã mu fita tãre da ku, kuma bã zã mu yi ɗã'a ga kõwa ba game da ku, har abada, kuma lalle idan an yãƙe ku, lalle zã mu taimake ku haƙĩƙatan?" Alhãli kuwa Allah na shaidar cẽwa lalle sũ tabbas, maƙaryata ne} [al'hashr: 11], kuma Allah sha'aninSa ya ɗaukaka Ya ce: {Idan munãfukai suka jẽ maka suka ce: "Munẽ shaidar lalle kai haƙĩƙa Manzon Allah ne," Kuma Allah Yanã sane da lalle Kai, haƙĩƙa ManzonSa ne, kuma Allah Yanã shaida lalle munafukan haƙĩƙa, maƙaryata ne} [al-Munafiƙun: 1].
Wani lokaci kuma kafirci yana kasancewa kokwanto da zato, to shi mai kai kawo ne a cikin umarnin Ubangiji, mai kokwanto a cikin tashin alƙiyama da gamuwa da Allah, Maɗaukakin sarki Ya faɗa Yana Mai bada labari game da ma'abocin gona cewa shi ya ce: {Kuma bã ni zaton sa'a mai tsayuwa ce, kuma lalle ne, idan an mayar da ni zuwa ga Ubangijiĩna, to, lalle ne, zan sãmi abin da yake mafi alhẽri daga gare ta ya zama makõma} [al-Kahf: 36], sai abokinsa mumini ya ce masa: Shin yanzu ka kafirta da wanda Ya halicceka daga turɓaya sannan daga ɗigon maniyyi sannan Ya daidaitaka a matsayin mutum} [al-Kahf: 37].
Wani lokaci kuma kafirci yana kasancewa zagi da izgili, Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya faɗa Yana Mai bada labari game da kafirai: {Kuma lalle ne, haƙĩƙa, an yi izgili ga waɗansu Manzanni daga gabãninka, sai abin da suka kasance sunã izgili da shi ya auku ga waɗanda suka yi izgilin daga gare su} [al-an'am: 10], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya faɗa Yana Mai bada labari game da mutanen (Annabi) Nuhu da izgilinsu da shi: {Kuma Yanã sassaƙa jirgin cikin natsuwa, kuma a kõ yaushe waɗansu shugabanni daga mutãnensa suka shũɗe a gabansa, sai su yi izgili gare shi. Ya ce: "Idan kun yi izgili gare mu, to, haƙĩƙa mũ mã zã mu yi izgili gare ku, kamar yadda kuke yin izgili} [Hud: 38].
Wani lokaci kuma kafirci yana kasancewa bijirewa da hanawa daga tafarkin Allah, Allah Maɗaukakin sarki Ya faɗa Yana Mai bada labari game da bijirewar kafirai: {Kõ sun riƙi waɗansu abũbuwan bautãwa baicinSa? Ka ce: "Ku kãwo hujjarku, wannan shi ne ambaton wanda yake tãre da ni, kuma shi ne ambaton wanda yake a gabãnĩna. Ã'a, mafi yawansubã su sanin gaskiya, sabõda haka sũ mãsu bijirẽwa ne} [al-Anbiyaa: 24], Kuma Allah Sha'aninSa ya ɗaukaka kuma sunayenSa sun tsarkaka Ya ce: {Ba Mu halitta sammai da ƙasa ba, da abin da ke tsakãninsu, fãce da gaskiya da wani ajali ambatacce, kuma waɗanda suka kãfirta, mãsu bijirẽwa ne daga abin da aka yi musu gargaɗi (da shi)}. [al-Ahƙaf: 3].
Wani lokaci kuma kafirci yana kasancewa ƙin gaskiya, Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya ce: {Wannan, sabõda lalle sũ, sun ƙi abin da Allah Ya saukar dõmin haka Ya ɓata ayyukansu} [Muhammad: 9].
Kuma muna sani cewa daga kafirci akwai kafirci koma bayan kafirci babba, shi ne kafirci ƙarami, ba ya kishiyantar asalin imani, sai dai cewa shi yana kishiyantar cikarsa, shi ba ya dawwamar da mai shi a cikin wuta, kuma ba ya ɓata dukkan ayyuka, kuma shi nau'o'ine da yawa.
Daga cikinsa faɗinsa -annabi tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: "Zagin musulmi fasiƙanci ne, kuma yaƙarsa kafirci ne". (Bukhari ne ya fitar da shi (48), da Muslim (64), da Tirmizi (1983), da Nasa'i (4108), da Ibnu Majah (69).) Daga cikinsa faɗinsa - annabi tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: "Abu biyu acikin mutane su daga kafirci ne: Sukar nasaba, da kukan kera ga mamaci". (Muslim ne ya fitar da shi (67).) Da faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: "Kada ku koma kafirai a bayana, sashinku yana dukan wuyayen sashi". (Bukhari ne ya fitar dashi (121), da Muslim (65), da Nasa'i (4131), da Ibnu Majah (3942).)
Wannan kafircin ba ya fitarwa daga Musulunci, kuma ba ya dawwamarwa a cikin wuta; domin cewa Allah Ya ambaci muminai masu yaƙar juna 'yan uwa, sai Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Idan ƙungiyoyi na muminai suka yi faɗa to ku yi sulhu a tsakaninsu} [al-Hujurat: 9], sai Ya ambacesu muminai alhali su suna yaƙar juna. Jagoran Ahlus Sunnah Imam Ahmad - Allah Ya yi masa rahama - ya ce bayan ya koro jumla daga waɗannan hadisan da ire-irensu: "Waɗannan hadisan da suka zo: "Abu uku wanda ya kasance a cikinsa to shi munafuki ne", wannan akan kaurarawane, muna ruwaitosu kamar yadda suka zo, amma ba zamu fassarasu ba... da makamancinsa daga hadisai daga abinda ya inganta aka hardace, mu muna miƙa wuya gare shi , koda ba'asan fassararsu ba, kuma ba'a magana a cikinsa, ba'a jayayya a cikinsa, kuma ba'a fassara waɗannan hadisan sai da kwatankwacin yadda suka zo". (Sharhi Usulul I'itiƙadi Ahlus Sunnah Wal jama'ah (1/182).)
BABIN SHIRKA DA ALLAH
Muna sani cewa daga abinda yake kishiyantar imani da Allah: Yi wa Allah Mai girma shirka, shirka babba tana kishiyantar asalin imani, shirka ƙarama kuma tana kishiyantar cikarsa, shirka babba ita ce mafi girman zalinci, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma a lõkacin da Luƙmãn ya ce wa ɗansa, alhãli kuwa yanã yi masa wa'azi, "Yã ƙaramin ɗãna! Kada ka yi shirki game da Allah. Lalle shirki wani zãlunci ne mai girma} [Luƙman: 13]. Shirka babba tana ɓata dukkan ayyuka, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce {Kuma an yi wahayi zuwa gare ka da kuma zuwa ga waɗanda suke a gabãninka, "Lalle idan ka yi shirki haƙĩƙa aikinka zai ɓãci, kuma lalle zã ka kasance daga mãsu hasãra} [al-Zumar: 65], Kuma Allah - Mabuwayi - Ya ce: {Wancan ne shiryarwar Allah, Yanã shiryar da wanda Yake so daga bayinSa. Kuma dã sun yi shirki dã haƙĩƙa abin da suka kasance sunã, aikatãwa yã lãlãce} [al-An'am: 88].
Shirka babba Allah ba Ya gafartawa mai yinta idan ya mutu bai tuba daga gareta ba, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Lalle ne, Allah ba Ya gãfarta a yi shirki game da Shi, kuma Yana gãfarta abin da yake bãyan wannan ga wanda Yake so, kuma wanda ya yi shirki da Allah, to, lalle ne ya ƙirƙiri zunubi mai girma} [al-Nisa'a: 48]. Mushriki idan ya mutu bai tuba ba to aljanna haramun ce gare shi, kuma makomarsa Jahannama yana mai dawwama a cikinta, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma wanda ya yi shirka da Allah to haƙiƙa Allah Ya haramta aljanna a gare shi kuma makomarsa wuta ce} [al-Ma'ida: 72].
Daga Jabir - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Wani mutum ya zo wurin annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai ya ce: Ya manzon Allah, waɗanne abubuwa biyu ne masu wajabtawa? sai ya ce: "Wanda ya mutu ba ya taranya wani abu da Allah zai shiga aljanna, wanda ya mutu yana taranya wani abu da Allah zai shiga wuta". (Muslim ne ya fitar da shi (93).)
Haƙiƙa Allah Ya ɓata shirka, kuma Ya siffantawa mushrikai shirkarsu, kuma Ya bayyana ɓacin riƙonsu kishiyoyi, kuma cewa su ba sa anfanarwa ba sa kuma cutarwa, wani lokaci yana bayyana cewa waɗannan abokanan tarayyar ba sa ji, koda sun ji ba za su iya amsawa wanda ya kirasu ba, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Waɗanda kuke kira waninSa, basu mallakar ko fatar gurtsin dabino * Idan kun kira su, bã zã su ji kiranku ba, kuma kõ sun jiya, bã zã su karɓa muku ba, kuma a Rãnar ¡iyãma zã su kãfirce wa shirkinku, kuma bãbu mai bã ka lãbãri, kamar wanda ya sani} [Faɗir: 13-14]. Sai Allah Ya bayyana cewa su ba sa mallakar kowane abu, kuma ba sa jin wanda ya kirasu, kuma a ranar lahira zasu kafirta da shirkarsu.
Wani lokaci Allah Yana bayyana cewa waɗannan abokanan tarayyar ba sa anfanarwa basa cutarwa, kuma basa mallakar mutuwa ko rayuwa, kamar yadd da Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma suka riƙi abũbuwan bautawa, baicin Shi, bã su yin halittar kõme alhãli sũ ne ake halittãwa kuma bã su mallakar wa kansu wata cũta ko wani amfãni, kuma bã su mallakar mutuwa kuma bã su mallakar rãyarwa, kuma bã su mallakar tãyarwa} [al-Furƙan: 3], kuma Allah sha'aninSa ya ɗaukaka Ya ce: {Ya ce: "Shin, sunã jin ku, a lõkacin da kuke kira? * Kõ kuwa sunã amfãnin ku, kõ sunã cũtar ku?} [al-Shu'araa: 72-73].
Wani lokaci Allah Yana bayyana cewa waɗannan abubuwan bautar koma bayan Allah su ne mafi girman tawaya daga wanda ya bauta musu; domin cewa su ba sa tafiya, ba sa kamu (damka), ba sa ji, ba sa gani, to su: "Sun wofinta daga dukkanin waɗannan abubuwan waɗanda dasu ne ake kaiwa zuwa jawo anfani da tunkuɗe cuta". (Tafsirin Dabari (13/322).) Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Shin sunã da ƙafãfu da suke yin tafia da su? Kõ sunã da hannãye da suke damƙa da su? Kõ sunã da idãnu da suke gani da su? Ko sunã da kunnuwa da suke saurãre da su? Ka ce: "Ku kirãwo abũbuwan shirkinku sa'an nan kuma ku yi mini kaidi, sa'an nan kada ku saurãra mini} [al-A'araf: 195].
Wani lokaci kuma Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Yana bayyana gajiyawar waɗannan abubuwan bautar da kuma rauninsu, Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Ya ku mutãne! An buga wani misãli, sai ku saurãra zuwa gare shi. Lalle ne waɗanda kuke kira baicin Allah, bã zã su halitta ƙudã ba, kõ da sun tãru gare shi, kuma idan ƙudãn ya ƙwãce musu wani abu, bã zã su kuɓutar da shi ba daga gare shi. Mai nẽma da wanda ake nẽman gare shi sun raunana} [al- Hajj: 73], Kuma Allah - Mabuwayi - Ya ce: {Kuma waɗanda kuke kira, baicinSa, bã su iya taimakõn ku, kuma kansu ma, bã su iya taimaka} [al-A'araf: 197].
Wani lokaci kuma Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Yana hukunci akansu da buƙatuwa da ƙaranta, kuma cewa su ba sa mallakar kwatankwacin ƙwayar zarra a cikin sammai ko a cikin ƙasa na cikakken mulki, kuma ba sa mallakin tarkon a cikin wani abu daga hakan, kuma Allah ba Shi da wasu mataimaka daga cikinsu, ko mai bada agaji, kuma babu mai ceto a wurinSa, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Ka ce: "Ku kirãyi waɗanda kuka riya (cẽwa abũbuwan bautãwa ne) baicin Allah, bã su Mallakar ma'aunin zarra a cikin sammai, kuma bã su Mallakarsa a cikin ƙasa kuma bã su da wani rabon tãrẽwa a cikinsu (sammai da ƙasa), kuma bã Shi da wani mataimaki daga gare su * Kuma wani ceto ba ya amfani a wurinSa face fa sai ga wanda Ya yi izni gare shi} [Saba'i: 22-23].
Wani lokaci kuma Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Yana bayyana cewa samuwar alloli tare da Allah mai hanuwa ne a hankalce, kuma mai koruwane a kasance, kuma ɓatacce ne a shari'ance, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Dã waɗansu abũbuwan bautawa sun kasance a cikinsu (sama da ƙasa) fãce Allah, haƙĩƙa dã su biyun sun ɓãci. Sabõda haka tsarki ya tabbata ga Allah Ubangijin Al'arshi daga abin da suke siffantãwa} [al-Anbiyaa: 22], kuma Allah - sha'aninSa ya buwaya kuma girmanSa da sarautarSa sun ɗaukaka - Ya ce: {Ka ce: "Dã akwai waɗansu abũbuwan bautãwa tãre da shi, kamar yadda suka faɗa, a lõkacin, dã (abũbuwan bautãwar) sun nẽmi wata hanya zuwa ga Ma'abũcin Al'arshi} [al-Isra'a: 42]. Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya ce: {Allah bai riƙi wani abin haihuwa ba, kuma bãbu wani abin bautãwa tãre da Shi. Idan haka ne (akwai abin bautawa tare da Shi), lalle ne dã kõwanne abin bautawar ya tafi da abin da ya halitta, kuma lalle ne, dã waɗansu sun rinjãya a kan waɗansu, tsarki ya tabbata ga Allah, daga abin da suke siffantãwa} [al-Mua'Minun: 91].
Kuma muna sanin cewa shirka babba nau'o'i ce da yawa:
Daga nau'o'inta: A sanya wani abokin tarayya tare da Allah acikin RububiyyarSa da halittarSa da mulkinSa da arziƙinSa da tsarin mulkinSa, Allah Ya faɗa Yana Mai bada labari game da shirkarsu: {Ko sun sanya masa abokan tarayya ne da suka halicce su kamar halittarSa, sai halittun suka yi kamanceceniya gare su ? Ka ce: Allah Shi ne Mahaliccin komai kuma Shi ne Makaɗaici Mai rinjaye} [al-Ra'ad: 16], Allah Maɗaukakin sarki Ya faɗa Yana Mai inkari akan wanda Ya sanwa Allah abokin tarayya daga halitta, alhali shi abin halitta ne ba ya halitta: {Wannan shĩ ne halittar Allah. To ku nũna mini, "Mẽne ne waɗanan da ba Shi ba suka halitta? Ã'a, azzalumai sunã a cikin ɓata bayyananna} [Luƙman: 11], kuma Allah Ya bayyana cewa Shi ne (kadai) Mai kaɗaitaka - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - da halitta da umarni, sai Allah sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Lalle ne Ubangijinku Allah ne, wanda Ya halitta sammai da ƙasa a cikin kwãnaki shida, sa'an nan kuma Ya daidaita a kan Al'arshi, Yanã sanya dare ya rufa yini, yanã nẽman sa da gaggawa, kuma rãnã da watã da taurãri hõrarru ne da umurninSa. To, Shĩ ne da halittar kuma da umurnin. Albarkar Allah Ubangijin halittu tã bayyana!} [al-A'araf: 54].
Daga nau'ukan ta: A sanya ɗa ga Allah - Allah Ya ɗaukaka daga hakan ɗaukaka mai girma - Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya ce: {Kuma Yahũdãwa suka ce: "Uzairu ɗan Allah ne."Kuma Nasãra suka ce: "Masĩhu ɗan Allah ne." Wancan zancensu ne da bãkunansu. Sunã kamã da maganar waɗanda suka kãfirta daga gabãni. Allah Yã la'ance su! Yãya aka karkatar da su?} [al-Taubah: 30], Kuma Allah - Mabuwayi - Ya ce: {Kuma suka sanya wa Allah abõkan tãrayya, aljannu, alhãli kuwa (Shi) Ya halitta su. Kuma sun ƙirƙira masa ɗiya da 'yã'ya, bã da ilmi ba. TsarkinSa yã tabbata! Kuma Ya ɗaukaka daga abin da suke sifantãwa} [al-An'am: 100], Kuma Allah - tsarki ya tabbatar masa Ya ɗaukaka - Ya ce: {Kuma suka sanya Masa wani yanki daga bãyinsa. Lalle ne mutum, haƙĩƙa, mai yawan kãfirci ne, mai bayyanãwar kãfircin * Kõ zã Ya ɗauki 'ya'ya mãtã daga abin da Yake halittawa ne, kuma Ya zãɓe ku da ɗiya maza?} [al-Zukhruf: 15-16].
Daga nau’ukanta: Yin imani da taurari da bauta musu, Allah Maɗaukkain sarki Ya faɗa Yana Mai bada labari game da (Annabi) Ibrahim badaɗayi - aminci ya tabbata agare shi - cewa shi ya kafawa mutanensa hujja a cikin bautarsu ga taurari: {Kuma kamar wancan ne, Muke nũna wa Ibrãhĩma mulkin sammai da ƙasa, kuma dõmin ya kasance daga mãsu yaƙĩni * To, a lõkacin da dare ya rufe a kansa, ya ga wani taurãro, ya ce: "Wannan ne, ubangijina?" Sa'an nan a lõkacin da ya faɗi, ya ce: "Ba ni son mãsu fãɗuwa * Sa'an nan a lõkacin da ya ga watã yanã mai bayyana, ya ce: "Wannan ne Ubangijina?" Sa'an nan a lõkacin da ya fãɗi, ya ce: "Lalle ne idan Ubangijina bai shiryar da ni ba, haƙĩƙa, inã kasancẽwa daga mutãne ɓatattu * Sa'an nan a lõkacin da ya ga rãnã tanã bayyana, ya ce: "Wannan shĩ ne Ubangijina, wannan ne mafi girma?" Sa'an nan a lõkacin da ta fãɗi, ya ce: "Ya mutãnena! Lalle ne ni barrantacce nake daga abin da kuke yi na shirki * "Lalle ne nĩ, na fuskantar da fuskata ga wanda, Ya ƙãga halittar sammai da ƙasa, inã mai karkata zuwa ga gaskiya, kuma bã ni cikin mãsu shirki * Kuma mutãnensa suka yi musu da shi. Ya ce: "Shin kunã musu da ni a cikin sha'anin Allah, alhãli kuwa Yã shiryai da ni? Kuma bã ni tsõron abin da kuke yin shirki da shi, fãce idan Ubangijina Yã so wani abu. Ubangijina Ya yalwaci dukkan kõme da ilmi. Shin, ba zã ku yi tunãni ba? * Kuma yãyã nake jin tsõron abin da kuka yi shirki da shi, kuma ba ku tsõron cẽwa lalle ne kũ, kun yi shirki da Allah, abin da (Allah) bai saukar da wata hujja ba game da shi? To, wane ɓangare daga sãshen biyu ne mafi cancanta da aminci, idan kun kasance kunã sani?} [al-An'am: 75-81].
Daga hakan - kuma -: Neman shayar da ruwa da taurari, da ƙudirce cewa su suna jawo arziƙi, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce; {Kuma kunã sanya arzikinku (game da shi) lalle kũ, ku ƙaryata (shi)?} [al-Waƙi'ah: 82]. Daga Dan Abbas - Allah Ya yarda da su - ya ce: An yi wa mutane ruwa a zamanin Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, sai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce-: "Daga mutane akwai wanda ya wayi gari mai godiya, daga cikinsu akwai mai butulcewa", suka ce: Wannan rahamar Allah ce, wasunsu suka ce: Haƙiƙa tauraro kaza da kaza na cikin taurari ya yi gaskiya, ya ce: "Sai wannan ayar ta sauka: {To ba sai na yi rantsuwa ba da lokutan faɗuwar taurari ba} [al-Waƙi'ah: 75], har ya kai {Kuma kuna sanya arziƙinku (game da shi) lallai ku, ku ƙaryata (shi)} [al-Waƙi'ah: 82]. (Muslim ne ya fitar da shi (73), da al-Dabari a cikin al-Tafsir (23/154).)
kuma annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Abubuwa huɗu a cikin al'umma ta suna daga cikin al'amuran Jahiliyya kuma ba zasu taba iya barin su ba: Alfahari da dangi, da sukar nasaba, da roƙon ruwa da taurari, da kukan mutuwa". (Muslim ne ya fitar dashi (934), da Ibnu Majah (1581).)
Daga Zaid ɗan Khalid al-Juhani - Allah Ya yarda da shi - cewa shi ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya yi mana sallar Asuba a Hudaibiyya bayan saukar ruwa a darannan, lokacin da ya juya sai ya fuskanci mutane, sai ya ce: "Shin kun san mai Ubangijinku ya ce?" suka ce: Allah da manzonSa ne mafi sani, ya ce: "Daga bayiNa akwai wanda ya wayi gari yana mai imani da Ni kuma yana mai kafircewa taurari, amma wanda ya ce: An yi mana ruwa da falalar Allah da rahamarSa, to wannan shi ne mai imani da Ni kuma mai kafircewa taurari, amma wanda ya ce: Da masaukin tauraro kaza da kaza, to wannan mai kafircemin ne kuma mai imani da taurari ne". (Bukhari ne ya fitar da shi (846), da Muslim (71), da Abu Dawud (3906), da Nasa'i (1525).)
Daga nau'o'ita shirka: A sanya wani abin tarayya tare da Allah a sunayenSa ko siffofinSa - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - kamar wanda yake riya cewa akwai wani da yasan gaibu koma bayn Allah, Allah Ya umarci annabinSa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: {Ka ce: "Ba zan ce muku, a wurina akwai taskõkin Allah ba. Kuma ba ni sanin gaibi, kuma ba ni gaya muku cẽwa ni malã'ika ne. Ba ni bi, fãce abin da ake yiwo wahayi zuwa gare ni." Ka ce: "Shin, makãho da mai gani sunã daidaita? Shin fa, ba ku yin tunãni?} [al-An'am: 50], Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Kaɗai (sanin) gaibu ga Allah ne} [Yunus: 20]. Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - cewa manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Wanda ya zo wa boka - Musa ya ce a cikin Hadisin sa - sai ya gasgata shi da abinda yake faɗa - sannan suka haɗu - ko ya zo wa wata mace - Musaddad ya ce: Matarsa - alhali tana haila, ko ya zo wa wata mace - Musadad ya ce: Matarsa - ta duburarta, to haƙiƙa ya barranta da abinda aka saukarwa (Annabi) Muhammad". (Abu Dawud ne ya fitar da shi (3904), da Tirmizi (135), da Ibnu Majah (639), da Fadlu ɗan Dakin a cikin Sallah (15), da Ishaƙ ɗan Rahuwaih (482), da Ahmad (9536).) Haƙiƙa narko mai tsanani ya zo akan wanda ya ambaci kansa, ko ya ambaci waninsa da wani suna daga sunayen Allan da ba sa kamata sai ga Allah, kamar lafazin ɗaukaka "Allah" ko "al-Rahman", Allah - Maɗaukakin sarki - Yana cewa: {Kuma Allah Yanã da sũnãye mãsu kyau. Sai ku rõƙe shi da su, kuma ku bar waɗanda suke yin ilhãdi a cikin sũnãyenSa: zã a sãka musu abin da suka kasance sunã aikatãwa} [al-A'araf: 180], Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya ce: {Allah bãbu abin bautãwa fãce Shi. Yanã da sunãye mafiya kyau} [Daha: 8], kuma annabi tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Mafi ƙasƙanci sunaye ranar lahira a wurin Allah mutumin ake kiransa sarkin sarakuna". (Bukhari ne ya fitar da shi (6205), da Muslim (2143), da Abu Dawud (4961), da Tirmizi (2837).)
Abu Ubaid - Allah Ya yi masa rahama - ya ce: "Sufyan ɗan Uyaynah ya kasance yana fassara faɗinsa: "Sarkin sarakuna", ya ce: Shi ne kamar faɗinsu: Shahin Shah, wato: Cewa shi ne sarkin sarakuna, wanin Sufyan ya ce: Kai shi ne a ambaci mutum da sunayen Allah, kamar faɗinsa: al-Rahman, da al-Jabbar, da al-Aziz. Ya ce: Allah Shi ne sarkin sarakuna, ba ya halatta a ambaci waninSa da wannan sunan". (Garibul Hadith, na al-Kasim ɗan Sallam (2/18).)
Daga cikin nau’ukan shirka: A ƙudirce cewa akwai wani daga halitta yana siffantuwa da cikar Ubangiji, ko cewa shi mai iko ne akan dukkan komai, Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Kuma babu ɗaya da ya kasance kini a gare Shi} [al-Ikhlas: 4], Tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya ce: {Shi ne Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu. sai ka bauta Masa, kuma ka yi haƙuri ga bautarsa. Shin kã san wani takwara a gare shi} [Maryam: 65], kuma Allah Maɗaukkain sarki Ya faɗa Yana Mai bada labari game da cikar ikonSa: {Lallai Allah Mai ikone akan dukkan komai} [al-Baƙara: 148], Kuma Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya ce: {Kuma Allah bai kasance wani abu na iya gajiyar da Shi ba acikin Sammai da kuma kasa, lallai shi Ya kasance Masani, Mai ikon yi} [Faɗir: 44]. Kuma tsarki ya tabbatar maSa Ya bayyana cikakkiyar gajiyawa ga masu bautar da kuma waɗanda ake bautawa koma bayanSa, sai sha'aninSa ya buwaya kuma sarautarSa ta ɗaukaka - Ya ce: {Ya ku mutãne! An buga wani misãli, sai ku saurãra zuwa gare shi. Lalle ne waɗanda kuke kira baicin Allah, bã zã su halitta ƙudã ba, kõ da sun tãru gare shi, kuma idan ƙudãn ya ƙwãce musu wani abu, bã zã su kuɓutar da shi ba daga gare shi. Mai nẽma da wanda ake nẽman gare shi sun raunana} [al-Hajji: 73].
Daga cikin nau’ukan shirka: A sanya wasu allolin daban tare da Allah, kamar yadda Allah Ya bada labari game da mutanen (Annabi) Ibrahim - aminci ya tabbata agare shi - cewa su sun riƙi wasu iyayen giji koma bayan Allah, sai Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma a lõkacin da Ibrãhĩma ya ce wa ubansa Ãzara: "Shin, kanã riƙon gumãka abũbuwan bautãwa? Lalle nĩ, inã ganin ka kai damutã- nenka, a cikin ɓata bayyananniya} [al-An'am: 74], kuma Allah Ya bada labari game da ma'abota kogo cewa su sun ƙauracewa mutanensu; domin cewa su sun riƙi wasu allolin koma bayan Allah, Allah - Ya ɗaukaka Ya tsarkaka - Ya ce: {Ga waɗannan mutãnenmu sun riƙi waninSa abin bautãwa! Don me bã su zuwa da wata hujja bayyananna a kansu (waɗanda ake bautawar)? To, wãne ne mafi zãlunci daga wanda ya ƙãga ƙarya ga Allah?} [al-Kahf: 15], Tsarki ya tabbatar maSa Ya faɗa a cikin sha'anin (Annabi) Musa - aminci ya tabbata a gare shi - cewa su sun nemi annabi Musa ya sanya musu wani allan kamar yadda mushrikai suke da alloli: {Kuma Muka ƙẽtarar da Banĩ Isra'ila ga tẽku, sai suka jẽ a kan wasu mutãne waɗanda sunã lizimta da ibãda a kan wasu gumãka, nãsu suka ce: "Yã Mũsã! Ka sanya mana wani abin bautawa kamar yadda suke da abũbuwan bautãwa " Ya ce: "Lalle ne kũ, mutãne ne kunã jahilta * Lalle ne waɗannan, abin da suke a cikinsa halakakke ne, kuma abin da suka kasance sunã aikãtawa ƙarya ne} [al-A'araf: 138-139], kuma Allah - Maɗaukkain sarki - Ya faɗa Yana Mai ɓata bautar kowane abin bauta koma bayan Allah: {Allah bai riƙi wani abin haihuwa ba, kuma bãbu wani abin bautãwa tãre da Shi. Idan haka ne (akwai abin bautawa tare da Shi), lalle ne dã kõwanne abin bautawar ya tafi da abin da ya halitta, kuma lalle ne, dã waɗansu sun rinjãya a kan waɗansu, tsarki ya tabbata ga Allah, daga abin da suke siffantãwa} [al-Mua'Minun: 91].
Daga cikin nau’ukan shirka: Juyar da ibada ko wani yanki daga gareta ga wanin Allah, Allah Maɗaukakin sarki Ya faɗa Yana Mai bayyana halin mushrikai: {Kuma sun sanya wani rabõ ga Allah daga abin da Ya halitta daga shũka da dabbõbi, sai suka ce: "Wannan na Allah ne," da riyãwarsu "Kuma wannan na abũbuwan shirkinmu ne." Sa'an nan abinda yake na shirkinsu baya kaiwa zuwa ga Allah, abinda yake na Allah ne to shi yana kaiwa zuwa shirkinsu abinda suke hukuntawa ya munana} [al-An'am: 136], kuma annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Allah - alherinSa ya yawaita Ya girmama - Ya ce: Ni ne mafi wadatar abokanan tarayya daga shirka, duk wanda ya aikata wani aiki ya hada ni da wani a aikin to Zan bar shi da shirkarsa". (Muslim ne ya fitar da shi (2985).)
Daga cikin nau’ukan shirka: Yanka ga wanin Allah ta hanyar neman kusanci, kamar wanda yake yanka ga gumaka ko matattu dan neman kusanci garesu, Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya faɗa Yana Mai bayyana cewa yanka ba ya kasancewa sai ga Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: {Ka ce: "Lalle ne sallãta, da baikõna, da rãyuwãta, da mutuwãta, na Allah ne Ubangijin tãlikai} [al-An'am: 162], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Abin sani kawai (Allah) Ya haramta muku mussai da jini da nãman alade da abin da aka ambaci sũnan wanin Allah game da shi. Sa'an nan wanda aka tĩlastaa kan jama'a kuma baicin mai zãlunci, to, lalle Allah ne Mai gãfara, Mai jin ƙai} [al-Nahl: 115]. Daga Abu Dafail ya ce: Mun ce wa Aliyu ɗan Abi Dalib - Allah Ya yarda da shi -: Ba mu labarin wani abinda manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi maka sirrinsa, sai ya ce: "Babu wani abu da ya yi mini sirrinsa kuma ya ɓoyewa mutane shi, sai dai cewa ni na ji shi yana cewa: Allah Ya la'anci wanda ya yi yanka ga wanin Allah". (Muslim ne ya fitar da shi (1978), da Nasa'i (4422).) Kuma domin cewa wannan al'amarin mai girma ne sosai, annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi hani daga yanka a wurin da ake yin yanka ga wanin Allah, Daga Sabit ɗan Dahhak - Allah Ya yarda da shi - ya ce: "Wani mutum ya yi bakancen yanka wani raƙumi a zamanin manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a Buwanah - wani tudune a bayan Yanbu'u kusa da gefen kogi - sai ya zo wa annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai ya ce: Lallai ni na yi bakancen yanka wani raƙumi a Buwanah, sai annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Shin a wurin akwai wani gunkin da ake bautawa daga gumakan Jahiliyya?" suka ce: A'a, ya ce: "Shin a wurin akwai wani idi daga idunansu?", suka ce: A'a, manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Ka cika bakancenka, domin cewa shi babu cikawa ga wani bakance a sabon Allah, ko a abinda dan Adam ba ya mallaka". (Abu Dawud ne ya futar da shi (3313).)
Daga cikin nau’ukan shirka: Bakance ga wanin Allah; bakance bauta ne ga Allah dan haka juyar da shi ga wanin Allah ba ya halatta; saboda haka Allah Ya yabi muminai waɗanda suke cika bakance, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Suna cikãwa da alwãshin (da suka bãkanta), kuma suna tsõron wani yini wanda sharrinsa ya kasance mai tartsatsi ne} [al-Insan: 7], kuma Allah Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma abin da kuka ciyar daga ciyarwa, kõ kuka cika alwãshi daga wani bãkance, to, lalle ne, Allah Yana sanin sa. Kuma azzãlumai bã su da wasu mataimaka} [al-Baƙara: 270]. Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Duk wanda ya yi bakancen bin Allah to ya bi Shi, wanda ya yi bakancen saɓonSa to kada ya saɓa maSa". (Bukharin ne ya fitar da shi (6696), da Abu Dawud (3289), da Tirmizi (1526), da Nasa'i (3806), da Ibnu Majah (2126).)
Daga nau’ukan shirka: Neman tsari da wanin Allah, daga Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su - ya ce: "Wasu mazaje daga mutane sun kasance ɗayansu yana kwana a kwari a (lokacin) Jahiliyya, sai ya ce: Ina neman tsari da mabuwayin wannan kwarin, sai hakan ya ƙara musu zunubi". (al-Dabari ne ya fitar da shi a cikin Tafsiri (23/ 322).) Allah maɗaukakin sarki Ya faɗa Yana Mai bada labari game da mutanen Jahiliyya; {Kuma cewa shi wasu maza daga cikin mutane sun kasance suna neman tsari da wasu maza daga aljanu, sabo da haka suka ƙara musu girman kai} [al-Jin: 6]. Kuma annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bada labarin cewa wanda ya sauka wani masauki sai ya ce: "Ina neman tsari da kalmomin Allah cikakku daga sharrin abin da Ya halitta. To, babu abin da zai cutar da shi har ya bar wannan masaukin". (Muslim ne ya fitar dashi (2708), da Tirmizi (3437), da Ibnu Majah (3547).
Daga nau'ikanta: Neman agaji da neman taimako daga wanin Allah a cikin abinda babu mai iko akansa sai Allah, ko kiran wanin Allah, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma lalle ne wurãren sujada na Allah ne, saboda haka kada ku kira kõwa tãre da Allah (da su, a cikinsu)} [al-Jinn: 18], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Idan kun kira su, bã zã su ji kiranku ba, kuma kõ sun jiya, bã zã su karɓa muku ba, kuma a Rãnar ¡iyãma zã su kãfirce wa shirkinku, kuma bãbu mai bã ka lãbãri, kamar wanda ya sani} [Faɗir: 14], kuma Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya faɗa Yana Mai bayyana cewa mushrikai suna neman agajin Allah idan cuta ta samesu, sannan suna komawa zuwa shirkarsu idan Allah Ya tseratar da su: {To, a lõkacin da suka shiga cikin jirgin ruwa, sun kirãyi Allah sunã mãsu tsarkake addini a gare shi, to, a lõkacin da Ya tsĩrar da su zuwa ga tudun ƙasã, sai gã su sunã shirki} [al-Ankabut: 65], kuma sha'aninSa ya ɗaukaka Ya ce: {Kuma wãne ne mafi ɓata daga wanda ke kiran wanin Allah wanda da bã zai karɓa masa ba, bar Rãnar Kyama, alhãli sũ (waɗanda ake kiran) shagaltattu ne daga kiransu?} [al-Ahƙaf: 5], kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya faɗa Yana Mai bayyana cewa Shi ne Yake taimakon wanda ke cikin baƙin ciki kuma Yake yaye cuta: {Kõ wãne ne yake karɓã, kuma ya sanya ku mamãyan ƙasa? Shin akwai wani abin bautawa tãre da Allah? Kaɗan ƙwarai kuke yin tunãni} [al-Naml: 62].
Daga nau'ikanta: Shirka ta biyayya ga wanin Allah, Allah Maɗaukakin sarki Ya faɗa Yana Mai bada labari game da mazowa littafi (Yahudu da Nasara) cewa su sun riƙi maluman Yahudawansu da masu bauta cikin kiristocin su iyayen giji suna shara'anta musu, kuma suna haramta musu abinda Allah Ya halatta musu: {Sun riƙi mãlamansu (Yahũdu) da ruhubãnãwansu (Nasãra) Ubannangiji, baicin Allah, kuma sun riƙi Masĩhu ɗan Maryama (haka). Kuma ba a umurce su ba fãce da su bautã wa Ubangiji Guda. Bãbu abin bautãwa fãce Shi. TsarkinSa ya tabbata daga barin abin da suke yin shirki da shi} [al-Taubah: 31], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Ko suna da wasu abokan tarayya ne da suke shar'anta musu addini abin da Allah bai musu Izini da shi ba} [al-Shura: 21]. Kuma Allah Ya umarci bayinSa da imani da Shi da kai ƙara ga sharai'arSa, kuma Ya bayyana cewa Shaiɗan yana nufinsu sukai ƙara zuwa ga ɗagutu, sai Maɗaukaki Ya ce: {Shin, ba ka gani ba, zuwa ga waɗanda suke riyãwar cẽwa sunã ĩmãni da abin da aka saukar zuwa gare ka da abin da aka saukar daga gabãninka, sunã nufin su kai ƙãra zuwa ga ¦ãgũtu alhãli kuwa, lalle ne, an umurce su da su kãfirta da shi, kuma Shaiɗan yanã nẽman ya ɓatar da su, ɓatarwa mai nĩsa} [al-Nisai'i: 60]. Daga Adi ɗan Hatim - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Na zo wa annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a wuyana akwai wani gicciyayye (cross) na zinare, sai ya ce: Ya Adi, ka jefar da wannan gunkin daga gareka, kuma na ji shi yana karantawa a cikin "Surat Bara'ah": {Sun riƙi maluman yahudawansu da masu bauta a kiristocin su iyayen giji koma bayan Allah} [al-Taubah: 31], Ya ce: "Ai cewa su ba su kasance sun bauta musu ba, sai dai cewa su sun kasance idan sun halatta musu wani abu sai su halatta shi, idan kuma sun haramta musu wani abu sai su haramta shi". (Tirmizi ne ya fitar da shi (3095), da Ibnu Sa'ad (6/219), da Ibnu Abi Hatim a cikin al-Tafsir (10057), da Dabarani a cikin al-Kabir (17/92/218).)
Daga Nau’ukan shirka: Shirka a cikin sallah da ruku'u da sujjada da ɗawafi; hakan cewa waɗannan ibadun da makanmantansu karkatar da su ga wanin Allah ba ya halatta, kuma Allah Ya umarci badaɗayinSa - aminci ya tabbata agare shi - ya tsarkake ɗakinSa dan masu ɗawafi da masu Itikafi da masu ruku'u masu sujjada, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma a lõkacin da Muka iyãkance wa Ibrãhim wurin ¦akin (Muka ce masa), "Kada ka haɗa kõme da Ni ga bauta, kuma ka tsarkake ¦ãkiNa dõmin mãsu ɗawãfi da mãsu tsayuwa da mãsu ruku'u da mãsu sujada} [al-Hajj: 26], kuma Allah Ya yi umarni da sujjada ta kasance saboda Shi ne kawai Shi kaɗai - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -, sai Allah Maɗaukaki Ya ce: {Kada ku yi sujjada ga rana ko ga wata ku yi sujjada ga Allah wanda Ya haliccesu in kun kasance Shi kaɗai kuke bautawa} [Fussilat: 37]. Kuma babu mai hanuwa daga bautarSa sai masu girman kai, Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya ce: {(Allah) Ya ce, "Yã Ibilis! Mẽ ya hana ka, ka yi sujada ga abin da Nã halitta da HannayeNa biyu? Shin, kã yi girman kai ne, kõ kuwa kã kasance daga maɗaukaka ne?} [Saad: 75], kuma Allah Ya ambata cewa ragowar halittu suna maSa sujjada, sai Mabuwayi Ya ce: {Kuma ga Allah, abin da yake a cikin sammai da ƙasa na dabba da mala'iku, suke yin sujada, kuma bã su kangara} [al-Nahl: 49]. A cikin labarin Ja'afar - Allah Ya yarda da shi lokacin da ya shiga gurin Najjashi, sai Ja'afar ya ce: "Ni ne mai magana a madadinku yau, sai suka bi shi har suka shiga gurin Najjashi ba su yi masa sujjada ba sai ya ce: Me yasameku bakwa yi wa sarki sujjada? sai ya ce; Lallai Allah - Mai gima da ɗaukaka - Ya aiko mana annabinSa - tsira da a mincin Allah su tabbata agare shi - sai Ya umarcemu da kada mu yi sujjada sai ga Allah". (al-Dayalisi ne ya fitar dashi (344), da Sa'id ɗan Mansur (2481), da Ahmad (4400), da Luwain a cikin Juzu'insa (4), da al-Dahawi a cikin Ahkamul Kur'ani (418).)
Daga nau’ikanta: Hukunci da wanin abinda Allah Ya saukar, da kai ƙara zuwa ga wanin Allah, Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya bayyana hukuncin wanda ya yi hukunci da wanin abinda Allah Ya saukar, sai Allah yabonSa ya ɗaukaka kuma sunayenSa sun tsarkaka - Ya ce: {Kuma wanda bai yi hukunci ba da abin da Allah Ya saukar ba, to waɗannan su ne kafirai} [al-Ma'ida: 44]. Kuma Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Kuma wanda bai yi hukunci da abin da Allah ya saukar ba, to waɗannan su ne azzalumai} [al-Ma'ida: 45]. kuma Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya ce: {Kuma wanda bai yi hukunci ba da abin da Allah Ya saukarba, to waɗannan su ne fasiƙai} [al-Ma'ida: 47]; Hakan domin cewa umarni dukkansa na Allah ne, Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Ku saurara ! Halitta da umarni nasa ne) Allah - alherinSa ya yawaita - Ubanigijin talikai} [al-A'araf: 54], kuma Allah Maɗaukaki Ya ce: {Kuma waɗanda suka yi shirki suka ce: "Dã Allah Yã so, dã bamu bautã wa kõme ba, baicinSa, mũ ko ubannimmu kuma dã ba mu haramta kõme ba, baicin abin da Ya haramta." Kamar wancan ne waɗanda suke a gabãninsu suka aikata. To, shin, akwai wani abu a kan Manzanni, fãce iyarwa bayyananniyã?} [al-Nahl: 35].
Haƙiƙa Allah Ya aibatawa mazowa littafi (Yahudu da Nasara) riƙonsu ga malumman yahudawansu da masu bauta cikin kiristocinsu iyayen giji suna shara'anta musu (shari'u), Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Sun riƙi mãlamansu (Yahũdu) da ruhubãnãwansu (Nasãra) Ubannangiji, baicin Allah, kuma sun riƙi Masĩhu ɗan Maryama (haka). Kuma ba a umurce su ba fãce da su bautã wa Ubangiji Guda. Bãbu abin bautãwa fãce Shi. TsarkinSa ya tabbata daga barin abin da suke yin shirki da shi} [al-Taubah: 31]. Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Ko suna da wasu abokan tarayya ne da suke shar'anta musu addini abin da Allah bai musu Izini da shi ba} [al-Shura: 21]. Daga Adi ɗan Hatim - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Na zo wa annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a wuyana akwai wani gicciyayye (cross) na zinare, sai ya ce: Ya Adi, ka jefar da wannan gunkin daga gareka, kuma na ji shi yana karantawa a cikin "Surat Bara'ah": {Sun riƙi maluman yahudawansu da masu bauta cikin kiristocin su iyayen giji koma bayan Allah} [al-Taubah: 31], ya ce: "Ai cewa su ba su kasance sun bauta musu ba, sai dai cewa su sun kasance idan sun halatta musu wani abu sai su halatta shi, idan kuma sun haramta musu wani abu sai su haramta shi". (Tirmizi ne ya fitar da shi (3095), da Ibnu Sa'ad (6/219), da Ibnu Abi Hatim a cikin al-Tafsir (10057), da Dabarani a cikin al-Kabir (17/92/218).)
Mazowa littafi suna kamanceceniya da mushrikai waɗanda Allah Ya faɗa game da su: {Kuma waɗanda suka yi shirki suka ce: "Dã Allah Yã so, dã bamu bautã wa kõme ba, baicinSa, mũ ko ubannimmu kuma dã ba mu haramta kõme ba, baicin abin da Ya haramta." Kamar wancan ne waɗanda suke a gabãninsu suka aikata. To, shin, akwai wani abu a kan Manzanni, fãce iyarwa bayyananniyã?} [al-Nahl: 35].
kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {To, a'aha! Ina rantsuwa da Ubangijinka, ba za su yi ĩmãni ba, sai sun yarda da hukuncinka ga abin da ya sãɓa a tsakãninsu, sa'an nan kuma ba su sãmi wani ƙunci a cikin zukãtansu ba, daga abin da ka hukunta, kuma su sallama sallamãwa} [al-Nisa'a: 65]. Kuma Allah - Mabuwayi - Ya ce: {Ko suna da wasu abokan tarayya ne da suke shar'anta musu addini abin da Allah bai musu Izini da shi ba} [al-Shura: 21]. kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Shin, hukuncin Jãhiliyya suke nema? Kuma wane ne mafi kyau ga hukunci daga Allah sabõda mutãne waɗanda suke yin yaƙĩni (tabbataccen ĩmãni)?} [al-Ma'ida: 50].
Daga nau’ukan su: Shirkar soyayya, ita ce ya so wani abin halitta soyayya mai gwamuwa da ƙasƙanci da girmamawa da ƙanƙar da kai, Allah Maɗaukakin sarki Ya faɗa a sha'anin soyayyar mushrikai ga kishiyoyinsu (allolinsu): {Kuma daga mutane akwai wanda yake riƙon wasu kishiyoyi koma bayan Allah suna son su kamar son Allah} [al-Baƙara: 165]. Daga Abdullahi - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Na tambayi annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: Wanne zunubi ne mafi girma? ya ce: "Ka sanya kishiya ga Allah alhali Shi Ya halicceka...". (Bukhari ne ya fitar da shi (4477), da Muslim (86), da Abu Dawud (2310), da Tirmizi (3182) da Nasa'i (4013).)
Daga nau’ukanta: Shirkar tsoro, shi ne ya ji tsoron wani abin halitta tsoro mai gwamuwa da ƙanƙar da kai da ƙasƙanci da girmamawa, kamar ya ji tsoron kada ya saukar masa da bala'i, ko ya hana masa alheri, ko ya aikata wani abin haramtawa saboda shi ta hanyar neman kusanci, Allah Mabuwayi Ya ce: {Wancan, Shaiɗan ne kawai yake tsõratar da, ku masõyansa. To, kada ku ji tsõronsu ku ji tsõro Na idãn kun kasance mãsu ĩmãni} [Aal- Imran: 175]. Mushrikai suna ƙudirce cewa allolinsu suna cutarwa kuma suna anfanarwa, saboda haka suka zaci cewa allolinsu ne suka shafi annabin Allah Hudu - aminci ya tabbata agare shi - da mummunan abu inda suka ce: {Bã mu cẽwa, sai dai kurum sashen abũbuwan bautawarmu ya sãme ka da cũtar hauka." Yace: "Lalle ne nĩ, inã shaida waAllah, kuma ku yi shaidar cẽwa" lalle ne nĩ mai barranta ne dagb abin da kuke yin shirki da shi} [Hud: 54]. Mujahid ya ce: " {Ba mu cewa sai dai kurum sashin abubuwan bautar mu sun shafeka da mummuna}, ya ce: "Gumaka sun shafeka da hauka". (Tafsirin Dabari (15/361).) Allah Ya faɗa a cikin sha'anin ma'abocin addini miƙaƙƙe - aminci ya tabbata agare shi - cewa shi ya ce: {Kuma yãyã nake jin tsõron abin da kuka yi shirki da shi, kuma ba ku tsõron cẽwa lalle ne kũ, kun yi shirki da Allah, abin da (Allah) bai saukar da wata hujja ba game da shi? To, wane ɓangare daga sãshen biyu ne mafi cancanta da aminci, idan kun kasance kunã sani?} [al-An'am: 81].
Mutanen Jahiliyya sun kasance suna neman tsari da shugabannin aljanu dan tsoron wawayensu, Allah Mabuwayi Ya ce: {Kuma cewa shi wasu maza daga cikin mutane sun kasance suna neman tsari da wasu maza daga aljanu, sabo da haka suka ƙara musu girman kai} [al-Jin: 6].
kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {To a lokacin da aka wajabta musu yaƙi, sai ga wani ɓangare daga cikinsu suna tsoron mutane kamar tsoron Allah, ko mafi tsanani ga tsoronSa} [al-Nisa'i: 77]. Kuma Allah - Maɗaukaki - Ya bayyana cewa ma'abota waliccinSa ba sa jin tsoron kowa sai Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - kamar yadda sha'aninSa ya buwaya Ya ce: {Waɗanda ke isar da Manzancin Allah, kuma sunã tsõronSa, kuma bã su tsõron kõwa fãce Allah, Kuma Allah Ya isa Ya zama Mai hisabi} [al-Ahzab: 39], kuma Allah Ya ce: {Abin sani kawai, mai rãya masallãtan Allah, shĩ ne wanda ya yi ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira, kuma ya tsayar da salla kuma ya bãyar da zakka, kuma bai ji tsõron kõwa ba fãce Allah. To, akwai tsammãnin waɗannan su kasance daga shiryayyu} [al-Taubah: 18]. Kuma Ya bada labarin cewa matsafa bayan imninsu sun fifita tsoro daga Allah akan tsoro daga Fir'auna da azabarsa, Allah Maɗaukakin sarki Ya faɗa Yana Mai bada labari game da maganarsu: {Suka ce: "Bã zã mu fĩfĩta ka ba faufau a kan abin da ya zo mana na hujjõji. Munã rantsuwa da wanda Ya ƙãga halittarmu sai ka hukunta abin da kake mai hukuntãwa, ai kanã ƙãre wannan rãyuwar dũniya kawai ne * Lalle mũ, mun yi ĩmãni da Ubangijinmu dõmin Ya gãfarta mana laifuffukanmu da abin da ka tĩlasta mu a kansa na sihiri. Kuma Allah ne Mafi alhẽri, kumaMafi wanzuwa} [Daha: 72-73].
Daga Nau’ukanta : Shirkar fata, ita ce ya yi fata daga wani abin halitta rayayye mahalarci (Wato wanda yake a nan) ko wanda ba ya nan abinda babu wanda yake da iko akansa sai Allah, ko ya yi fatan yaye baƙin ciki da biyan buƙatu, da ceto a ranar lahira daga matattu, Allah Ya faɗa Yana Mai bada labari game da zagin mushrikai ga allolinsu: {Ba ma bauta musu face sai don su kusantar da mu zuwa ga Allah kusanci} [al-Zumar: 3], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Idan kun kira su, bã zã su ji kiranku ba, kuma kõ sun jiya, bã zã su karɓa muku ba, kuma a Rãnar ¡iyãma zã su kãfirce wa shirkinku, kuma bãbu mai bã ka lãbãri, kamar wanda ya sani} [Faɗir: 14], kuma Allah Ya bayyana cewa waɗannan abokanan tarayyar basa mallakar komai, Allah Mabuwayi Ya ce: {Ka ce: "Shin, kun ga abũbuwan shirkinku, waɗanda kuke kira, wasun Allah? Ku nũna mini, mẽne ne suka halitta daga ƙasã? Kõ sunã da tãrayya ne a cikin sammai? Kõ kuma Mun bã su wani littãfi ne sabõda haka sunã a kan wata hujja ce daga gare shi? Ã'a, azzãlumai bã su yin wani wa'adi, sãshensu zuwa ga sãshe, fãce rũɗi} [Faɗir: 40], kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya faɗa ga sha'anin mabiya cewa su za’a ce musu a ranar alƙiyama: {Kuma a ce ku kirãwo abõkan tãrayyar ɗinku, sai su kira su, sai ba su amsa ba, kuma su ga azãbar. Dã dai lalle su sun kasance snnã shiryuwa!} [al-Kasas: 64]. dukkan abinda ya zo a cikin AlKur'ani daga ambaton kiran mushrikai ga allolinsu to shi dalili ne akan shirkar fata, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Haƙƙan ne abin da kawai kuke kira na zuwa gare shi, bã ya da wani kira a cikin dũniya, kuma bã shi da shi a Lãhira kuma lalle makomarmu zuwa ga Allah take, kuma lalle mabarnata sũ ne 'yan wutã} [Ghafir: 43]. Da a ce ba su zama suna ƙudirce cewa su suna amsa musu ba da muminin nan na iyalan Fir'auna bai kore ta ba.
Daga nau’ukan sa: Tsafi (Asiri), Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Saidai cewa Shaiɗanu sun kafirta suna koyawa mutane tsafi da abinda aka saukar da shi akan mala'iku biyu a Babila, Haruta da Maruta, kuma basu sanar da kowa ba face sun ce: "Mu fitina kawai ne, saboda haka kada ku kafirta} [al-Baƙara: 102]. Daga Abu Huraira -Allah Ya yarda da shi - daga annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Ku gu jiya abubuwa bakwai masu halakarwa" suka ce: Ya Ma'aikin Allah! waɗanne ne su? ya ce: Yin shirka da Allah, da sihiri, da kashe rai wacce Allah Ya haramta face da gaskiya, da cin riba, da cin dukiyar maraya, da juyawa ranar yaƙi, da kuma yi wa katangaggiya marafkaniya mumina ƙazafi". (Bukhari ne ya fitar da shi (2766), da Muslim (89), da Abu Dawud (2874), da Nasa'i (3671).)
Daga Amr ɗan Dinar, ya ji Bajalata yana zantar da Amr ɗan Aus, da Abu al-Sha'asa'u, ya ce: "Na kasance marubuci ga Jar'i ɗan Mu'awiya baffan Ahnaf ɗan Kais sai ga littafin Umar ya zo mana kafin mutuwarsa da shekara: Ku kashe kowane matsafi...". (Abu Dawud ne ya fitar da shi (3043), da Abdurrazaƙ (9972), da Said ɗan Mansur (2180), da Ahmad (1657).)
kuma annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Dukkan wanda ya ɗosani wani yanki na ilimin taurari, to, haƙiƙa ya ɗosani wani yanki na tsafi, ya ƙara abin da ya ƙara". (Abu Dawud ne ya fitar da shi (3905), da Ibnu Majah (3726), da Inu Abi Shaibah (26159), da Ahmad (2000), da Abdu Ibnu Humaid (714).)
Daga nau’ukan sa: Bokanci da duba; domin cewa wanda yake da’warsu (bokanci da duba) yana da'awar sanin gaibu, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Shi kaɗai ne Masanin fake sabõda haka, bã Ya bayyana gaibinSa ga kowa * Fãce ga wanda Yã yarda da shi, wato wani manzo sa'an nan lalle ne, zai sanya gãdi a gaba gare shi da bãya gare shi} [al-Jinn: 26-27]. Daga Safiyya daga wasu daga matan Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: Wanda ya je wurin Ɗan duba (malamin duba) sai ya tambaye shi wani abu, to, ba za a karɓi sallarsa ta darare arba’in ba" (Muslim ne ya fitar da shi (2230).)
Daga Abu Huraira da Hassan - Allah Ya yarda da su -, daga annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Duk wanda ya je wajen boka, ko ɗan duba sai ya gasgata shi cikin abinda yake cewa; to haƙiƙa ya kafirta da abinda aka saukarwa (Annabi) Muhammad". (Ahmad ne ya fitar da shi (9536), daga Abu Huraira, da Hassan, kuma Abu Dawud ya fitar da shi (3904), da Tirmizi (135), da Ibnu Majah (639), da Ibnu Abi Shaibah (17077), da Ishaƙ ɗan Rahuwaih (482), da Ahmad (9290), daga hadisin Abu Huraira).
Kuma muna sanin cewa daga shirka akwai shirka ƙarama ba ta fitarwa daga tafarki (Musulunci), kuma ba ta dawwamar da mai ita a cikin wuta, kuma ba ta ɓata dukkanin ayyuka, ita kuma nau’uka ce da yawa:
Daga cikinta: Canfi, abinda ake nufi da camfi: Abinda ya zartar da kai ko ya dawo da kai, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Sa'an nan idan wani alhẽri ya jẽ musu, sai su ce: "Masĩfa ta sãme su, sai su yi shu'umci da Mũsã da wanda yake tãre da shi, To, shu'umcinsu a wurin Allah yake, kuma amma mafi yawansu bã su sani!} [al-A'araf: 131], Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Suka ce: "Shu'umcinku, yanã tãre da ku. Ashe, dõmin an tunãtar da ku? Ã'a, kũ dai mutãne ne mãsu ƙẽtare haddi} [Y. S̃:19]. kuma annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: {Babu adwa(harbin cututtuka ta kashin kansu) babu shu’umci babu camfi da mujiya, ba camfa watan safar". (Bukhari ne ya fitar da shi (5707), da Muslim (2220), da Abu Dawud (3911).)
Daga Urwa ɗan Amir - Allah Ya yarda da shi - ya ce: An ambaci camfi a wurin annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai ya ce: Mafi kyansu kyakkyawan fata, kuma ba ya komar da musulmi, to idan ɗayanku ya ga abinda yake ƙi to ya ce: Ya Allah ba wanda yake zuwa da kyakkyawa sai Kai, kuma ba wanda zai kawar mummuna sai Kai, babu dabara babu ƙarfi sai daga gareka". (Abu Dawud ne ya fitar da shi (3919), da Ibnu Abi Shaibah a cikin al-Musannaf (26920), da kuma a cikin al-Adabul Mufrad (162), da Khallal a cikin (1405).)
Daga Abdullahi ɗan Amr - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Wanda camfi ya dawo da shi daga wata buƙata, to haƙiƙa ya yi shirka". Suka ce: Ya manzon Allah, menene kaffarar hakan? ya ce: "Ɗayansu ya ce: Ya Allah babu wani alheri sai alherinKa, kuma babu canfi sai canfinKa, kuma babu wani abin bauta da gaskiya sai Kai". (Ibnu Wahb ne ya fitar da shi a cikin al-Jami'u (658), da Ahmad (7045), kuma lafazin na sane, da al-Ɗabarani a cikin al-Kabir (14622), da Ibnu Sunni a cikin Amalul yaum wal lailah (292).)
Daga cikinsa: Rataya layu: Daga Abu Bashir al-Ansari - Allah Ya yarda da shi - "Cewa shi ya kasance tare da manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a sashin tafiye-tafiyensa, Abdullahi ya ce: Na yi zatan cewa shi ya ce: Mutane suna makwancinsu, sai manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya aiko wani ɗan aike: Cewa kada wani rataye na tsirgiya ya kasance a wuyan wani raƙumi, ko wani rataye sai an yanke shi". (Bukhari ne ya fitar da shi (3005), da Muslim (2115), da Abu Dawud (2552).)
Daga Abdullahi - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Na ji Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana cewa: "Lallai cewa tawaida da layu da tiwala (tsafin juyar da tunani musamman tsakanin ma'aurata) shirka ne". (Abu Dawud ne ya fitar da shi (3883), da Ibnu Majah (3530), da Ma'amar a cikin al-Jami (20343), da Ibnu Abi Shaibah (23924), da Ahmad (3615).)
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Wanda ya rataya wani abu za'a jiɓinta shi gare shi". (Tirmizi ne ya fitar da shi (2072), da Ibnu Abi Shaibah a cikin al-Musannaf (23923), da kuma a cikin al-Musnad (786), da Ahmad (18781).)
Daga cikin shi : Sassauƙar riya: Amma wanda zuciyars ta cika da riya har ya kai yana aikata ayyuka na gari ba tare da niyya ko imani ko tsoro ba to shi munafiki ne tsantsa, kuma aikinsa ɓatacce ne abin juyarwa ne ba karɓaɓɓe ba ne, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Saboda haka wanda ya kasance yana fatan haduwa da Ubangijinsa, to ya yi aiki na kwarai, kuma kada ya hada kowa ga bauta wa Ubangijinsa} [al-Kahf: 110], kuma tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Allah - alherinSa ya yawaita Ya girmama - Ya ce: Ni ne mafi wadatar abokanan tarayya daga shirka, duk wanda ya aikata wani aiki ya haɗa Ni da wani a aikin to Zan bar shi da shirkarsa". (Muslim ne ya fitar da shi (2985).)
kuma tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Lallai farkon mutumin da za'a fara yi wa hukunci ranar lahira mutumin da ya yi shahada, sai a zo da shi sai Ya sanar da shi ni'imominsa sai ya sansu, ya ce: To me ka yi da su? ya ce: Na yi yaƙi saboda Kai har na yi shahada, Ya ce: Ka yi ƙarya, sai dai cewa kai ka yi yaƙi ne; dan a ce: Sadauki ne, to an faɗa, sannan a yi umarni da shi sai a jawoshi akan fuskarsa har a jefa shi a cikijn wuta. Da mutumin da yakoyi ilimi, kuma ya sanar da shi kuma ya karanta AlKur'ani, sai a zo da shi sai Ya sanar da shi ni'imominsa sai ya sansu, Ya ce: To meka yi da su? ya ce: Na koyi ilimi, kuma na koyar da shi, kuma na karanta AlKur'ani saboda Kai, ya ce: Ka yi ƙarya, sai dai cewa kai ka koyi ilimi, kuma ka koyara dan ace maka: Masani. Kuma ka karanta AlKur'ani; dan ace: Shi makaranci ne, to an fada, sannan a yi umarni da shi sai a jawo shi akan fuskarsa har a jefa shi a cikin wuta. Da mutumin da Allah Ya yalwata masa, kuma Ya ba shi nau’ukan dukiya gaba dayanta, sai a zo da shi sai ya sanar da shi ni'imominsa, sai yasansu. Ya ce: To mekayi da su? ya ce: Ban bar wata hanyar da kake son a ciyar a cikinta ba har sai da na ciyar a cikinta saboda kai, ya ce: ka yi karya, saidai cewa kai ka aikata ne dan a ce: Mai yawan kyauta ne to an fada, sannan a yi umarni da shi sai ajawo shi akan fuskarsa har a jefa shi acikin wuta". (Muslim ne ya fitar da shi (1905), da Tirmizi (2382), da Nasa'i (3137).)
kuma Annabi tsira da amincin Allah su kara tabbata a gare shi ya ce: "Duk wanda ya jiyar Allah Zai kunyata shi, wanda ya yi riya, Allah Zai yi riya da shi". (Bukhari ne ya fitar da shi (6499), da Muslim (2987), da Ibnu Majah (4207).)
Daga Ɗan Umar - Allah Ya yarda da su - annabi tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Wanda ya jiyar da mutane aikinsa Allah Zai jiyar Mai jin halittarSa da shi, kuma Zai wulaƙanta shi kuma Zai ƙasƙantar da shi". (Dan Mubarak ne ya fitar da shi a cikin al-Zuhd (141), da Ibnu Abi Shaibah (36448), da Hannad a cikin al-Zuhd (872), da Ahmad (6509), da kuma a cikin al-Zuhd (238).)
Daga Abu Musa - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Wani mutum ya zo wurin annabi - tsira da a mincin Allah su tabbata agare shi - sai ya ce: Ya manzon Allah, mene ne yaƙi a tafarkin Allah? domin cewa ɗayanmu yana yaƙi dan fushi, kuma yana yaƙi dan ƙabailanci, sai ya ɗaga kansa gare shi - ya ce: Bai ɗago kansa ba sai dai cewa shi ya kasance a tsaye - sai ya ce: "Wanda ya yi yaƙi dan kalmar Allah ta zama ita ce maɗaukakiya, to shi ne saboda Allah - Mai girma da ɗaukaka -". (Bukhari ne ya fitar da shi (123), da Muslim (1904), da Abu Dawud (2517), da Tirmizi (1646), da Nasa'i (3136), da Ibnu Majah (2783).)
Kuma muna sanin cewa manzon Allah - tsira da a mincin Allah su tabbata agare shi - ya ambace shi shirkar ɓoye, Daga Mahmud ɗan Labid ya ce: Manzon Allah - tsira da a mincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Na haneku na haneku da boyayyiyar shirka" suka ce: Mece ce shirkar ɓoye? ya ce: "Ɗayanku ya tashi yana ƙawata sallarsa yana mai ƙoƙari; dan mutane su dinga kallonsa, to wanccan ita ce boyayyiyar shirka". (Ibnu Abi Shaiba ne ya fitar da shi (8489), da Ibnu Khuzaimah (937), da al-Ɗabarani a cikin la-Kabir (4301), da al-Baihaƙi a cikin al-Sunan al-Kubra (3629), da kuma a cikin al-Shu'ab (2872).)
Kuma tsira da a mincin Allah su tabbata agare shi ya bayyana cewa riya ɓoyayyace sosai, kuma cewa shi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance yana jin tsoranta akan al'ummarsa mafi tsananin tsoronsa akan Masihul Dajjal, inda ya ce: "Shin ba na baku labari ba da abinda shi ne mafi tsoro gareku a wurina daga Masihul Dajjal ba?", ya ce: Muka ce: Eh, sai ya ce: "Boyayyar shirka, mutum ya tashi yana sallah, sai ya ƙawata sallarsa, dan abinda yake gani daga kallon wani mutum". (Ibnu Majah ne ya fitar da shi (4204), da Ahmad (11252), da Hanbali ɗan Ishaƙ a cikin al-Fitan (30), da al-Ɗabarani a cikin Tahzibul Aasar (1117).)
Daga cikin ƙaramar shirka: Nufatar mutum duniya da aikinsa (na lahira), Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Wanda ya kasance yanã nufin nõman Lãhira zã Mu ƙãra masa a cikin nõmansa, kuma wanda ya kasance yanã nufin nõman dũniya, zã Mu sam masa daga gare ta, alhãli kuwa bã shi da wani rabo a cikin Lãhira} [al-Shura: 20], Kuma Allah yabonSa ya ɗaukaka ya ce: {Wanda ya kasance yã yi nufin rãyuwar dũniya da ƙawarta, Munã cika musu ayyukansu zuwa gare su a cikinta, kuma a cikinta bã zã a rage su ba} [Hud: 15]. Wannan mai kaikawo ne tsakanin ya zama babbar shirka, da tsakanin ya zama ƙarama gwargwadan abinda ya tsaya a cikin zuciyar bawa, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Wanda ya kasance yanã nufin mai gaggãwa, sai Mu gaggauta masa a cikinta, abin da Muke so ga wanda Muke nufi, sa'an nan kuma Mu sanya masa Jahannama, ya ƙõnu da ita, yanã abin zargi kuma abin tunkuɗewa} [al-Isra'a: 18].
Daga Abu Musa - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Wani mutum ya zo wurin annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai ya ce: Mutum ne yake yaƙi saboda ganima, da mutumin da yake yaƙi dan a ambace shi, da mutumin da yake yaƙi dan aga matsayinsa, to waye saboda Allah? ya ce: "Wanda ya yi yaƙi dan kalmar Allah ta kasance ita ce maɗaukakiya to shi ne saboda Allah". (Bukhari ne ya fitar da shi (2810), da Muslim (1904), da Abu Dawud (2517), da Nasa'i (3136), kuma manzon Allah - tsira da a mincin Allah su tabbata agare shi - ya yi mummunar addu'a akan wanda duniya ta zama ita ce himmarsa kuma manufarsa, daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Bawan kwabo da ɗari ya wahala, da bawan riga da sutura, idan aka ba shi sai ya yarda idan ba'a ba shi ba ba zai yarda ba". (Bukhari ne ya fitar da shi (2886), da Ibnu Majah (4135).)
Daga nau’ukan shirka karama: Faɗin mutum: Allah Ya so, kai ma ka so, da abinda ke kama da su na lafazi, daga Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su -: Cewa wani mutum ya cewa annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: Allah Ya so kaima ka so, sai annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce masa: "Zaka sanyani daidai da Allah, kawai Allah Ya so Shi kaɗai". (Ibnu Abi Shaibah ne ya fitar da shi (27227), da Ahmad (1839), da Bukhari a cikin al-Adabul Mufrad (783), da Ibnu Abid Duniya a cikin al-Samt (342), da Bagindi a cikin Amali ɗinsa (36).) Wannan lafazin yana kama da faɗinsu: Wannan daga Allah ne da kai, da badan Allah da kai ba da abu kaza bai kasance ba.
Daga ire-irensa: Rantsuwa da wanin Allah, annabi tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Wanda ya kasance zai yi rantsuwa to kada ya rantse sai da Allah, Kuraishawa sun kasance suna rantsuwa da iyayensu, sai ya ce: Kada ku rantse da iyayenku". (Bukhari ne ya fitar dashi (3836), da Muslim (1646), da Nasa'i (3764).) Daga Ɗan Umar - Allah Ya yarda da su -annabi tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Wanda ya rantse da wanin Allah to haƙiƙa ya kafirta ko ya yi shirka". (Tirmizi ne ya fitar da shi (1535), da Ahmad (6072), da Abu Awanah (6401), da Hakim (7895).)
BABIN MUNAFUNCI
Daga abinda yake kishiyantar imani da Allah: Munfunci babba; shi ne bayyanar da musulunci da ɓoye kafirci, munafunci babba ne da ƙarami. Munafunci babba yana kishiyantar asalin imani, munafunci ƙarami kuma yana kishiyantar cikarsa, Imam Ahmad ya faɗa a cikin "Usulus Sunnah": "Munafunci shi ne kafirci, wato ya kafircewa Allah, ya bautawa waninSa, ya bayyanar da musulunci a bayyane, misalin munafukan da suka kasance a zamanin manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -". (Usulus Sunnah na Ahmad ɗan Hanbali (Shafi na: 55).) Babban kuma mai fitarwa ne daga tafarki. (Musulunci).
Muna shaidawa da shaidar Allah cewa munafukai maƙaryata ne a cikin da'awarsu, Allah sh'aninSa ya buwaya kuma sarautarSa ta ɗaukaka - Ya ce: {Kuma waɗanda suka riƙi wani masallãci dõmin cũta da kãfirci da nẽman rarrabẽwa a tsakãnin muminai da fakẽwã ga taimakon wanda ya yãƙi Allah da ManzonSa daga gabãni, kuma haƙĩƙa sunã yin rantsuwa cẽwa, "Ba mu yi nufin kõmai ba fãce alhẽri", alhãli kuwa Allah Yanã yin shaida cẽwa, su, haƙĩƙa, maƙaryata ne} [al-Taubah: 107]. Kuma Allah - Mabuwayi - Ya ce: {Allah Yana shaidawa cewa munafukai maƙaryata ne} [al-Munafiƙun: 1].
Allah ba Ya karɓar farilla ko nafila daga munafuki, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Ka ce: "Ku ciyar a kan yarda kõ kuwa a kan tĩlas. Bã zã a karɓa daga gare ku ba. Lalle ne kũ, kun kasance mutãne fãsiƙai * Kuma bãbu abin da ya hana a karɓi ciyarwarsu daga gare su fãce dõmin sũ, sun kãfirta da Allah da ManzonSa, kuma bã su zuwa ga salla fãce Luma sunã mãsu kasãla, kuma bã su ciyarwa fãce sunã mãsu ƙyãma} [al-Taubah: 53-54].
Makomar munafiki - idan ya mutu akan munafunci - dawwama a ciKin wuta, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Lalle ne, manãfukai sunã a magangara mafi ƙasƙanci daga wuta. Kuma bã zã ka sãma musu mataimaki ba} [al-Nisa'i: 145]. kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Allah yã yi wa'adi ga munãfukai maza da munãfukai mãtã da kãfirai da wutar Jahannama, sunã madawwama a cikinta. Ita ce ma'ishiyarsu. Kuma Allah Yã la'ance su, kuma sunã da azãba zaunanniya} [al-Taubah: 68].
Muna sanin cewa munafunci babba yana kasancewa ƙin gaskiya da ƙyamarta, Allah Maɗaukakin sarki ya faɗa Yana Mai bada labari game da halin munafukai: {Wannan, dõmin lalle sũ sun bi abin da ya, fusãtar da Allah kuma sun ƙi yardarSa, sabõda haka Ya ɓãta ayyukansu * Ko kuwa waɗanda ke da wata cũta a cikin zukatansu suna zaton cẽwa Allah ba zai fitar da mugun ƙulle-ƙullen su (ga Musulunci) ba? * Kuma dã Munã so, dã lalle Mun nũna maka su. To, lalle kanã sanin su game da alãmarsu. Kuma lalle kanã sanin su ga shaguɓen magana, alhali kuwa Allah Yanã sanin ayyukanku} [Muhammad: 28-30].
Kuma yana zamowa da farin ciki da rashin samun nasarar Musulinci da Musulmai, da nadama idan sun ga nasara ga Musulunci, Allah - Maɗaukaki - Ya faɗa Yana Mai bayyana abinda ƙirazansu suke ɓoyewa: {Idan wani alhẽri ya sãme ka, zai ɓãta musu rai, kuma idan wata masifa ta sãme ka sai su ce: "Haƙĩƙa, mun riƙe al'amarinmu daga gabãni."Kuma sujũya, alhãli kuwa sunã mãsu farin ciki} [al-Taubah: 50].
Kuma yana zamowa kafirci bayan imani, da juya baya daga karɓar kai ƙara zuwa ga shari'ar Allah, Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya ce: {Kuma sunã cẽwa, "Mun yi ĩmãni da Allah da kuma Manzo, kuma mun yi ɗã'ã." Sa'an nan kuma wata ƙungiya daga gare su, su jũya daga bãyan wancan. Kuma waɗancan ba mũminai ba ne * Kuma idan aka kirã su zuwa ga Allah da ManzonSa, dõmin Ya yi hukunci a tsakãninsu, sai gã wata ƙnngiya daga gare su sunã mãsu bijirewa * [al-Nur: 47-48].
Kuma yana zamowa da yi wa Allah mummunan zaton cewa ba zai taimaki annabinSa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ba, da addininSa, Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Kuma a lõkacin da munafukai da waɗanda akwai cũta a cikin zukãtansu ke cẽwa, Allah da ManzonSa, "Ba su yi mana wa'adin kõme ba, fãce rũɗi} [al-Ahzab: 12].
Kuma yana zamowa da yi wa gaskiya da ma'abotanta izgili, da zaginsu da yi musu habaici, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Munãfukai sunã tsõron a saukar da wata sũra a kansu, wadda take bã su lãbãri ga abin da yake cikin zukãtansu. Ka ce: "Ku yi izgili. Lalle ne, Allah ne Mai fitai da abin da kuke tsõro * Kuma lalle ne, idan ka tambaye, su haƙĩƙa, sunã cẽwa, "Abin sani kawai, mun kasance munã hĩra kuma munã wãsã. Ka ce: "Shin da Allah, da kuma ãyõyinSa da ManzonSa kuka kasance kunã izgili?} [al-Taubah: 64-65].
Kuma yana zamowa yafice ga Musulmai, Allah - sha'aninSa ya buwaya - Ya ce: {Waɗanda suke aibanta mãsu yin alhẽri daga mummunaia cikin dũkiyõyin sadaka, da waɗanda ba su sãmu fãce iyãkar ƙõƙarinsu, sai sanã yi musu izgili. Allah Yanã yin izgili gare su. Kuma sunã da azãba mai raɗaɗi} [al-Taubah: 79].
Kuma yana zamowa yaudarar ma'abota imani da kuma riya a ayyuka, Allah - Ya ɗaukaka Ya tsarkaka - Ya ce: {Suna yaudarayya da Allah da waɗanda suka yi ĩmãni, alhãli bã su yaudarar kõwa fãce kansu, kuma bã su sakankancẽwa!} [al-Baƙara: 9], Ya ce kuma: {Lalle ne munãfukai sunã yaudarẽwa da Allah, alhãli kuwa Shi ne mai yaudarasu; kuma idan sun tãshi zuwa ga salla, sai su tãshi sunã mãsu kasãla. Suna nũnawa mutãne, kuma ba su ambatar Allah sai kaɗan} [al-Nisa'a: 142]. daga Annabi - tsira da Amincin Allah su tabbata agareshi - ya ce: "Waccan ita ce sallar munafuki, yana zama yana sauraron rana har idan ta zama tsakanin ƙahon shaiɗan biyu, sai ya tashi, sai ya yi ta raka'a huɗu kukan kurciya, ba ya ambatan Allah sai kaɗan". (Muslim ya fitar da shi (622), da Abu Dawud (413), da Nasa'i (160), da Nasa'i (511).)
Abdullahi ɗan Mas'ud - Allah Ya yarda da shi - ya ce: "Haƙiƙa muna ganin mu ba mai kin yin ta (a lokacinta) sai munafuki sanannen munafunci". (Muslim ne ya fitar dashi (654), da Abu Dawud (550), da Nasa'i (849), da Ibnu Majah (777).)
Daga Abu huraira - Allah Ya yarda da shi - daga Annabi - tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Na rantse da wanda raina yake a hannunSa ba zaku takura a ganin Ubangijinku ba, sai dai kamar yadda kuke takura a ganin ɗayansu, ya ce: Sai ya haɗu da bawa, sai ya ce... har zuwa inda ya ce: Sannan ya haɗu da na uku, sai ya faɗa masa irin hakan, sai ya ce: Ya Ubangiji, na yi imani da Kai, da littafinKa, da manzanninKa, na yi sallah, na yi azumi, na yi sadaka, sai ya yi yabo da alheri daidai gwargwado, sai ya ce: Nan a lokacin, ya ce: Sannan a ce masa; A yanzu zamu aiko da mai yi maka shaida, sai ya yi tinani a cikin ransa: Waye zai yi mini shaida? sai a yi yumƙi a bakinsa, kuma acewa cinyarsa da namansa da ƙashinsa: Ku yi magana, sai cinyarsa da namansa da kashinsa su furta aikinsa, hakan dan ya yi wa kansa uzuri, wancan munafuki, wancan wanda Allah Yake fushi da shi". (Muslim ne ya fitar da shi (2968).)
Kuma Allah Ya umarci annabinSa - tsira da a mincin Allah su tabbata agare shi - da muminai da yaƙarsu, sai Allah Mabuwayi Ya ce: {Ya kai Annabi! Ka yãƙi kãfirai da munãfukai kuma ka tsaurara a kansu. Kuma matattararsu Jahannama ce. Tir da ta zama makõmar! * Sunã rantsuwa da Allah, ba su faɗa ba, alhãli kuwa lalle ne, haƙĩƙa, sun faɗi kalmar kãfirci, kuma; sun kãfirta a bãyan musuluntarsu, kuma sun yi himma ga abin da ba su sãmu ba. Kuma ba su zargi kõme ba fãce dõmin Allah da ManzonSa Ya wadãtar da su daga falalarSa. To, idan sun tũba zai kasance mafi alhẽri gare su, kuma idan sun jũya bãya, Allah zaiazabtã su da azãba mai raɗaɗi a cikin dũniya da Lãhira, kuma bã su da wani masõyi kõ wani mataimaki a cikin kasa} [al-Taubah: 73-74].
Kuma muna sanin cewa munafunci ƙarami ba ya fitarwa daga Musulunci, ba ya ɓata aiki, kuma ba ya dawwamar da mai shi a cikin wuta, kuma munafunci Nau’uka ne, tsira da a mincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Abubuwa huɗu wanda ya kasance a cikinsu ya zama munafuki tsantsa, duk wanda yake yana da wani hali daga cikinsu to ya kasance yana da wani abu daga munafunci har sai ya bar shi : Idan aka amince masa sai ya yi ha'inci, idan ya yi zance sai ya yi ƙarya, idan ya yi alƙawari sai ya yi yaudara, kuma idan aka yi faɗa da shi sai ya yi fajirci". (Bukhari ne ya fitar da shi (34), da Muslim (58), da Abu Dawud (4688), da Tirmizi (2632) da Nasa'i (5020).)
Daga Abu Musa - Allah Ya yarda dashi - daga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Muminin da yake karanta Alkur’ani, kuma yake aiki da shi, kamar gawasa ce ɗanɗanata mai daɗi ne kuma ƙanshinta mai daɗi ne. Kuma muminin da baya karanta Alkur’ani , kuma yana aiki da shi kamar dabino ne ɗanɗanonsa mai daɗi ne amma ba shi da ƙanshi, misalin munafukin da yake karanta Alkur’ani, kamar raihana ce ƙanshinta mai daɗi ne kuma ɗanɗananta mai ɗaci ne, kuma misalin munafukin da ba ya karanta AlKur'ani kamar maɗaciya ce ɗanɗanonta mai ɗaci ne - ko mummunan ne - kuma ƙanshinta mai ɗaci ne". (Bukhari ne ya fitar da shi (5059), da Muslim (797), da Tirmizi (2865), da Nasa'i (5038), da Ibnu Majah (214).)
BABIN BIDI'A
Muna sanin cewa daga bidi'o'i akwai wadda take kishiyantar asalin imani, daga cikinsu akwai wadda take kishiyantar cikar imani, bidi'o'i na shirka da kafirci suna kishiyantar asalin imani, amma bidi'o'in da suke koma bayan shirka da kafirci to suna kishiyntar cikar imani.
Muna imani cewa Allah Ya cika mana addini, kuma Ya cika mana ni'ima, Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya ce: {Kuma yaune Na cika muku Addininku, kuma Na cika muku ni’imtata a gareku, kuma Na yarje muku Musulunci a matsayin Addini} [al-Ma'ida: 3]. Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Duk wanda ya farar da wani abu a cikin wannan Addinin namu wanda baya ciki, to shi abin mayar masa ne". (Bukharin ne ya fitar da shi (2697), da Muslim (1718), da Abu Dawud (4606), da Ibnu Majah (14).)
Kuma muna sanin cewa daga abinda yake kishiyantar cikar imani bidi'o'i a cikin addini, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Na haneku da fararrun abubuwa; saboda kowane fararren abu bidi'a ne; kuma kowace bidi'a ɓata ce". (Abu Dawud ne ya fitar da shi (4607), da Tirmizi (2676), da Ibnu Majah (42), da Ahmad (17144), da Ibnu Abi Asim a cikin al-Sunnah (26), da Ibnu Waddah a cikin al-Bida'u (54).)
Daga Abu huraira - Allah Ya yarda dashi - cewa manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Wanda ya yi kira zuwa ga shiriya yana da lada kwatankwacin ladaddakin wadanda suka bi shi, ba za’a tauye komai daga ladansu ba, wanda ya yi kira zuwa ga ɓata yana da zunubi kwatankwacin zunuban waɗanda suka bi shi, ba za’a tauye komai daga zunubansu ba". (Muslim ne ya fitar dashi (2674), da Abu Dawud (4609), da Tirmizi (2674), da Ibnu Majah (206).
Kuma Bukhari - Allah Ya yi masa rahama - ya yi babi a cikin "Sahih ɗinsa", sai ya ce: "Babin zunubin wanda ya yi kira zuwa ga ɓata; ko ya sunnanta wata mummunar Sunnah" kuma a cikinsa ya zo da faɗin annabi - tsira da a mincin Allah su tabbata agare shi -: "Babu wani rai da za'a kashe dan zalinci, sai ya kasance akan ɗan Adam na farko akwai alhaki na wannan ran - wataƙila Sufyan ya ce: daga jininta - domin shi ne farkon wanda ya sunnanta kisa tun karon farko". (Bukhari ne ya fitar da shi (7321), da Muslim (1677), da Tirmizi (2673), da Nasa'i (3985), da Ibnu Majah (2616).)
Daga Abu Said -Allah Ya yarda da shi - cewa annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Lallai zaku bi sunnonin waɗanda ke gabaninku taki da taki, zira'i da zira'i, har da sun shiga ramin damo sai kun shige shi", muka ce: Ya manzon Allah, Yahudawa da Nasara? ya ce: "To suwa"?!. (Bukhari ne ya fitar da shi (3456), da Muslim (2669).)
Muna sanin cewa Allah Ya yi hani daga rarrabuwa da saɓani, sai Allah sha'aninSa ya ɗaukaka kuma sunayenSa sun tsarkaka Ya ce: {Kuma kada ku kasance kamar waɗanda suka rarrabu kuma suka sãɓã wa jũna, bãyan hujjõji bayyanannu sun je musu kuma waɗannan sunã da azãba mai girma} [Aal- Imran: 105], Kuma Allah Mabuwayi Ya ce: {To waɗanda suke saɓa umarninsa su kiyayi kansu kada musiba ko fitina ta sauka a kansu ko kuma azaba mai raɗaɗi ta same su} [al-Nnur: 63].
Muna sanin cewa daga bidi'o'i (akwai) girmama ƙaburbura da gini akansu - wannan zai iya zama sababi zuwa shirka. Daga bidi'o'i kuma yin hotunan salihai dan ƙaunar koyi da su bayan mutuwarsu, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi: "...Ku Saurara kuma cewa waɗanda suka gabace ku sun kasance suna riƙar ƙaburburan annabawansu da mutanen kirkinsu masallatai, ku saurara kada ku riƙi ƙaburbura masallatai, lallai ni na hanaku yin hakan". (Muslim ne ya fitar da shi (532).)
Daga Nana A'isha - Allah Ya yarda da ita -: Cewa Ummu Habibah da Ummu Salamah sun ambaci wata coci da suka gani a Habasha a cikinta akwai hotuna, sai suka ambatawa annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai ya ce: "Lallai waɗannan idan a cikinsu akwai mutum na gari sai ya mutu, sai su gina masallaci akan ƙabarinsa, sai su zana waɗancan hotunan, to waɗannan sune mafi sharrin halitta a wurin Allah ranar lahira". (Bukhari ne ya fitar dashi (427), da Muslim (528), da Nasa'i (704).)
Kuma annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi umarni da shafe mutum-mutumai, da daidaita ƙaburbura, Daga Abul Hiyaj al-Asadi ya ce: "Aliyu ɗan Abu Ɗalib - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Bana aikeka akan abinda manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya aikeni akansa ba ?Kada ka bar wani mutum-mutumi sai ka shafe shi, ko wani ƙabari sai ka daidaita shi". (Muslim ya fitar da shi (969), da Abu Dawud (3218), da Nasa'i (1049), da Nasa'i (2031).)
Kuma muna sanin cewa daga bidi'o'i ababen ƙi: Tarukan bidi'o'i da tarayya da kafirai a bukukuwansu. Daga Anas ɗan Malik - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya iso Madina, alhali su suna da yini biyu da suke wasa a cikinsu, sai ya ce: "Waɗanne kwanuka biyu ne waɗannan?" suka ce: Mun kasance muna wasa a cikinsu a lokacin Jahiliyya, sai manzon Allah - tsira da a mincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Lallai Allah haƙiƙa Ya canja muku mafi alheri daga su: Ranar babbar sallah, da ranar ƙaramar sallah". (Abu Dawud ne ya fitar da shi (1134), da Nasa'i (1556), da Isma'il ɗan Ja'afar a cikin hadisin Ali ɗan Haijr (62), da Ahmad (12827), da Abdu ɗan Humaid (1392).)
Kuma Allah yabonSa ya ɗaukaka ya ce: {Ga kõwace al'umma Mun sanya wurin yanka, su ne masu yin baiko gare Shi, sabõda haka, kada su yi maka jãyayya a cikin al'amarin (hadaya). Kuma ka yi kira zuwa ga Ubangijinka lalle kai kana a kan shiriya madaidaiciya} [al-Hajj: 67]. Daga Ɗan Abbas - Allah Ya yarda da su -, a cikin faɗinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Ga kowace al'umma mun sanya gurin yanka su ne masu baiko gare shi}: "ya ce: Idi". (Tafsirul Dabari (18/679), da Ibnu Abi Hatim a cikin al-Tafsir (14718).) kuma annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Lallai akwai idi ga kowacce al’umma, wannan shi ne idin mu". (Bukharin ne ya fitar da shi (952), da Muslim (892), da Abu Dawud (1593), da Ibnu Majah (1898).)
Kuma muna sanin cewa daga bidi'o'i ababen ƙi: Neman albarka daga abinda Allah Bai sanya shi sababi na albarka ba, wannan yakan kasance sababi zuwa ga shirka. Daga Abu Waƙid al-Laisi - Allah Ya yarda da shi -: Cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - lokacin da ya fita zuwa Hunain ya wuce wata bishiya ta mushrikai ana ce mata: Ma'abociyar rataya, suna rataye makamansu akanta, sai suka ce: Ya Manzon Allah, ka sanya mana ma'abociyar rataya kamar yadda suke da ma'abociyar rataya, sai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Tsarki ya tabbata ga Allah! wannan kamar yadda mutanen (annabi) Musa sukace ne: {Ka sanya mana wani ubangiji kamar yadda suke da iyayen giji} [Al-Aaraf: 138]. Na rantse da wanda raina yake a hannunsa zaku bi hanyar wadanda ke gabaninku". (Tirmizi ne ya fitar da shi (2180), da Ma'amar a cikin al-Jami'u (20763), da Abdurrazaƙ a cikin al-tafsir (931), da Ibnu Abi Shaibah (38530).)
BABIN MANYAN ZUNUBAI
Muna sanin cewa zunubai daga cikinsu akwai manya da ƙananu, Allah mai girma da ɗaukaka Ya ce: {Sune masu nisantar manyan zunubai da alfashu sai dai ƙananu} [al-Najm: 32], kuma Allah Mai girma da ɗaukaka Ya ce: {Idan kuka nĩsanci manyan abubuwan da ake hana ku aikatãwa, to, zã Mu kankare mũnanan ayyukanku daga gare ku, kuma Mu shigar da ku mashiga ta karimci} [al-Nisa'a: 31].
Daga Abdullahi ɗan Mas'ud - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Wani mutum ya ce: Ya manzon Allah, wane zunubi ne mafi girma awurin Allah? ya ce: "Ka kira kishiya ga Allah alhali shi Ya halicceka", ya ce: Sannan me? ya ce: "Ka kashe ɗanka dan tsoron ya ci abinci tare da kai" ya ce: sannan me? ya ce: "Ka yi zina da matar maƙocinka" sai Allah Ya saukar da gasgata ta: {Sune waɗanda ba sa kiran wani Allan daban tare da Allah, kuma ba sa kashe ran da Allah Ya haramta sai da agskiya kuma ba sa zina}. (Bukhari ne ya fitar da shi (6001), da Muslim (86).)
Kuma muna sanin cewa imani yana ƙaruwa yana raguwa, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Kuma idan aka saukar da wata sũra, to, daga gare su akwai waɗanda suke cẽwa: "Wãne a cikinku wannan sũra ta ƙãra masa ĩmãni?" To amma waɗanda suka yi ĩmãni, kuma sũ, sunã yin bushãra (da ita)} [al-Taubah: 124]. Ayyukan biyayya suna ƙara imani kuma suna tabbatar da shi, zunubai kuwa suna rage imani kuma suna raunana shi, saɓo - waɗanda basu kai kafirci da shirka ba - suna kishiyantar cikar imani, mai aikata babban laifi ba'a zare masa imani kai taye, kuma ba ya cancantar siffantuwa da imani kai tsaye; domin shi ya zo da abinda yake rage imaninsa, saboda haka ne annabi - tsira da a mincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Mai zina ba zai yi zina ba a lokacin da yake yin zinar alhali shi yana mumini, kuma ba zai sha giya ba a lokacin da yake shan giyar alhali shi yana mumini, ba zai yi sata ba lokacin da yake yin satar alhali shi yana mumini, ba zai fizge abin fizgewa ba, mutane suna ɗaga idanunsu gare shi a cikinta, lokacin da yake fizgewa ba alhali shi yana mumini". (Bukhari ne ya fitar da shi (2475), da Muslim (57).) kuma annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Wanda ya ga wani mummunan abu daga cikinku, to ya canza shi da hannunsa, idan ba zai iya ba to (ya canza shi) da harshe, idan ba zai iya ba to (ya canza shi) da zuciyarsa, wannan shi ne mafi raunin imani". (Muslim ne ya fitar da shi (49).) Tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya faɗa yana mai bada labari game da abinda zai kasance a ranar lahira: "...Sai Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: Ku tafi wanda kuka samu a cikin zuciyarsa akwai kwatankwacin awon dinari na imani to ku fitar da shi...". (Bukhari ne ya fitar da shi (7493), da Muslim (183).) Sai waɗannan Hadisan suka yi nuni akan cewa zunubai suna raunana imani.
Mai babban laifi abin yi wa alƙawari ne da uƙuba akan babban laifinsa muddin dai bai tubaba, ko an tsayar masa da haddi - idan babban laifin irin wanda haddi yake hawa akansa ne, ko Allah Ya gafarta masa da ɗaya daga sabubban gafara, Allah su suna da yawa, sha'aninSa ya ɗaukaka Ya ce: {Allah bai Yin gafara in aka haɗa Shi da wani cikin bauta amma yana gafarta laifin da yake koma da bayan haka ga wanda Ya so} [al-Nisa'a: 48].
KUNDIN SAHABBAI DA SHUGABANCI
BABIN SAHABBAI DA IYALAN GIDAN (ANNABI) ALLAH YA YARDA DA SU
Muna imani cewa Allah - Maɗaukaki - Ya zaɓi sahabban annabinSa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, kuma Ya sanya su zaɓaɓɓun halittarSa bayan annabawa - aminci ya tabbata agare su -, kuma Ya ambaci siffofinsu, ya yi yabo akansu a cikin Attaura da Linjila, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Muhammadu Manron Allah ne. Kuma waɗannan da ke tãre da shi mãsu tsanani ne a kan kãfirai, mãsu rahama ne a tsakãninsu, kanã ganin su sunã mãsu rukũ'i mãsu sujada, sunã nẽman falala daga Ubangijinsu, da yardarSa. Alãmarsu tanã a cikin fuskõkinsu, daga kufan sujuda. Wannan shĩ ne siffarsu a cikin Attaura. Kuma siffarsu, a cikin Injĩla ita ce kamar tsiron shũka wanda ya fitar da rẽshensa, sa'an nan ya ƙarfafa shi, ya yi kauri, sa'an nan ya daidaita a kan ƙafãfunsa, yanã bãyar da sha'awa ga mãsu shũkar' dõmin (Allah) Ya fusãtar da kãfirai game da su. Kuma Allah Ya yi wa'adi ga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, daga cikinsu, da gãfara da ijãra mai girma} [al-Fath: 29], kuma Allah Ya ambaci yardarSa garesu, sai Mabuwayi Ya ce: {Kuma mãsu tsẽrẽwa na farko daga Muhãjirina da Ansar da waɗanda suka bi su da kyautatãwa, Allah Ya yarda daga gare su su kuma sun yarda daga gare Shi, kuma Ya yi mãsu tattalin gidãjen Aljanna; ¡õramu sunã gudãna a ƙarƙashinsu, suna madawwamã a cikinsu har abada. Wancan ne babban rabo mai girma} [al-Taubah: 100].
Kuma annabi - tsira da a mincin Allah su tabbata agare shi - ya bayyana cewa sahabbai masu girma sune mafifitan kowanne zamani kai tsaye, Daga Abdullahi ya ce: An tambayi annabi - tsira da a incin Allah su tabbata agare shi -: Waɗanne mutane ne mafi alheri? ya ce: "Zamanina, sannan waɗanda ke biye da su, sannan waɗanda ke biye da su". (Bukhari ne ya fitar da shi (6658), da Muslim (2533), da Tirmizi (3859), da Ibnu Majah (2362).)
Kuma muna imani cewa Muhajirai sun fi mutanan Madina - Allah Ya yarda da su -; saboda haka Allah Ya gabatar da su a ambato a cikin babban littafinSa kamar yadda yake a cikin ayar "Taubah" wacce ta gabata, kuma Allah - Maɗaukaki - Ya yi yabo ga Muhajirun, sai Ya ce: {(Ku yi mãmãki) Ga matalauta mãsu hijira waɗanda aka fitar daga gidãjẽnsu da dũkiyõyinsu, sunã nẽman falala daga Allah da kuma yarda, kuma sunã taimakon Allah da ManzonSa! Waɗannan sũ ne mãsu gaskiya} [al-Hashr: 8].
Kuma tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Ya faɗa a cikin sha'anin mutanen Madina: {Da waɗanda suka zaunar da gidãjensu (ga Musulunci) kuma (suka zãɓi) ĩmãni, a gabãnin zuwansu, sunã son wanda ya yi hijira zuwa gare su, kuma bã su tunãnin wata bukãta a cikin ƙirãzansu daga abin da aka bai wa muhãjirĩna, kuma sunã fĩfĩta waɗansu a kan kãwunansu, kuma ko dã sunã da wata larũra. Wanda ya sãɓã wa rõwar ransa, to, waɗannan sũ ne mãsu babban rabo} [al-Hashr: 9].
Muna imani cewa mafificin wannan al'ummar bayan annabinta - tsira da a mincin Allah su tabbata agare shi -: Abubakar, sannan Umar, sannan Usman, sannan Aliyu- Allah Ya yarda da su - jerunsu a falala kamar jerinsu ne a cikin Halifanci.
Kuma muna yin shaida ga goman nan waɗanda aka yi wa albishir da aljanna, kamar yadda annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya shaida musu da ita, inda manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Abubakar yana aljanna, Umar ma yana aljanna, Usman ma yana aljanna, Aliyu ma yana aljanna, Ɗalha ma yana aljanna, Zubair ma yana aljanna, Abdurrahaman ɗan Awf ma yana aljanna, Sa'ad ma yana aljanna, Sa'id ma yana aljanna, Abu Ubaida ɗan al-Jarrah ma yana aljanna". (Tirmizi ne ya fitar da shi (3747), da Ahmad a cikin al-Musnad (1675), da kuma a cikin Fada'ilus Sahaba (278), da Ibnu Abi Asim a cikin al-Ahad Wal Masani (232).)
Kuma muna imani cewa mutanen Badr - Allah Ya yarda da su - suna da darajar da babu ita ga wasunsu, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya faɗa kamar yadda yake a cikin hadisi: "... Me ya sanar da kai, ko Allah Ya kasance ya yi tsinkaya ga mutanen Badr, sai Ya ce: Ku aikata abinda kuke so, haƙiƙa Na gafarta muku". (Bukhari ne ya fitar da shi (3007), da Muslim (2494), da Abu Dawud (2650), da Tirmizi (3305).)
Daga Mu'az ɗan Rufa'ah ɗan Rafi'in al-Zuraƙi daga babansa - Allah Ya yarda da shi - babansa ya kasance daga waɗanda suka halarci yaƙin Badar - ya ce: (Mala'ika) Jibril ya zo wajen annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai ya ce: "Me kuke ɗaukar waɗanda suka yi yaƙin Badar a cikinku? ya ce: Daga mafifitan musulmai - ko wata kalma kwatankwacinta - ya ce: Haka nan wanda ya halarci Badar daga mala'iku". (Bukhari ne ya fitar da shi (3992).)
Kuma muna shaida da abinda manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi shaida da shi ga mutanen Bai’atir Ridwan; inda tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Babu wani ɗaya daga waɗanda suka yi caffa ƙarƙashin bishiya da zai shiga wuta". (Abu Dawud ne ya ftar da shi (4653), da Tirmizi (3860), da Abu Jahm a cikin Juzu'in sa (1), da Ahmad (14778), da Nasa'i a cikin al-Kubra (11444).) Kuma su sun rabauta da yin caffarsu wacce har Allah Ya faɗa a cikinta: {Lallai waɗanda suke maka caffa kaɗai suna yi wa Allah caffa ne hannun Allah birbishin hannunsu} [al-Fath: 10]. Kuma muna sanin cewa Allah haƙiƙa Ya saukar da yardarSa garesu, kamar yadda tsarki ya tabbatar maSa Ya faɗa a cikin babban littafinSa: {Lalle ne haƙĩƙa, Allah Ya yarda da muminai a lõkacin da suke yi maka mubãya, a’a ƙarƙashin itãciyar nan dõmin Yã san abin da ke cikin zukãtansu sai Yã saukar da natsuwa a kansu, kuma Ya sãka musu da wani cin nasara makusanci} [al-Fath: 18].
Muna imani cewa Allah - Maɗaukaki - Ya keɓanci iyalan gidansa - tsira da a mincin Allah su tabbata agare shi - da falaloli da haƙƙoƙi, to son su yana wajaba, da jiɓintarsu, da kiyaye haƙƙinsu. Daga cikin haƙƙoƙinsu cewa Allah Ya sanya musu haƙƙi a cikin khumusi, da fai'i, kuma annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi umarni da yi musu salati tare da salati ga manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, sai ya ce mana: "Ku ce: Allahumma Salli Ala Muhammad, Wa’ala Aali Muhammad, kama Sallaita Ala Ibrahim, Wa ala Aali Ibrahim, Innaka Hamidun Majid. Allahumma Barik Ala Muhammad, Wa’ala Aaali Muhammad, Kama Barakta Ala Ibrahim, Wa’ala Aali Ibrahim, Innaka Hamidun Majid".
Daga falalarsu abinda Allah Maɗaukakin sarki Ya amabata a cikin faɗinSa - yabonSa ya ɗaukaka -: {Yã mãtan Annabĩ! Ba ku zama kamar kõwa ba daga mãtã, idan kun yi taƙawa, sabõda haka, kada ku sassautar da magana, har wanda ke da cũta a cikin zuciyarsa ya yi ɗammani, kuma ku faɗi magana ta alheri * Kuma ku tabbata a cikin gidãjenku, kuma kada ku yi fitar gãye-gãye irin fitar gãye-gãye ta jãhiliyyar farko. Kuma ku tsaĩ da salla, kuma ku bãyar da zakka, ku yi ɗã, ã ga Allah da ManzonSa. Allah na nufin Ya tafiyar da ƙazamta kawai daga gare ku, yã mutãnen Babban Gida! Kuma Ya tsarkake ku, tsarkakẽwa} [al-Ahzab: 32-33]. Kuma Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Annabi (shi ne) mafi cancantar mutane daga kawunansu kuma matansa iyayensu ne} [al-Ahzab: 6].
Daga A'isha - Allah Ya yarda da ita - ta ce: Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya fita da jijjifi akansa akwai mayafi wanda ke da hoton sirdi na baƙin gashi, sai Hassan ɗan Ali ya zo sai ya shigar da shi, sannan Hussaini ya zo sai ya shiga tare da shi, sannan Faɗima ta zo sai ya shigar da ita, sannan Aliyu ya zo sai ya shigar da shi, sannan ya ce: "Kaɗai Allah Yana nufin Ya tafiyar muku da datti yaku iyalan gidan (Annabi) kuma Ya tsarkakeku tsarkakewa". (Muslim ne ya fitar da shi (2424).)
Daga Wasila ɗan al-Asƙa'u - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Na ji manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana cewa: "Lallai Allah Ya zaɓi Kinanata daga 'ya'yan (Annabi) Isma'il, kuma Ya zaɓi Kuraishawa daga Kinanata, kuma Ya zaɓi Banu Hashim daga Kuraishawa, kuma Ya zaɓeni daga Banu hashim". (Muslim ne ya fitar da shi (2276).)
Daga Zaid ɗan Arƙam - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya tashi a cikinmu yana mai huɗuba a wani ruwa da ake ce masa Khumma tsakanin Makka da Madina, sai ya godewa Allah ya yi yabo gare shi , ya yi wa'azi, ya tinatar, sannan ya ce: "Bayan haka ku saurara yaku mutane, kaɗai ni mutum ne ya kusa manzon Ubangijina ya zo mini sai in amsa, ni na bar nauyaya biyu a cikinku na farkonsu; Littafin Allah, a cikinsa akwai shiriya da haske to ku yi riƙo da littafin Allah ku riƙe shi". Sai ya zaburar akan littafin Allah ya kwaɗaitar a cikinsa, sannan ya ce: "Da iyalan gidana, ina tunatar da ku Allah a iyalan gidana, ina tunatar da ku Allah a iyalan gidana, ina tunatar da ku Allah a iyalan gidana". (Muslim ne ya ruwaito shi (2408).)
Haƙiƙa sahabban annbi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sun san haƙƙoƙi da falalar makusantan sa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, har cewa Abubakar - Allah Ya yarda da shi - ya ce wa Aliyu - Allah Ya yarda da shi -: "Na rantse da wanda raina yake a hannunSa dangin manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sune mafi soyuwa a gareni da in sadarwa akan 'yan uwana". (Bukhari ne ya fitar da shi (3508), da Muslim (1759).)
Kuma annabi - tsira da a mincin Allah su tabbata agare shi - ya yi hani daga zagin sahabbai - Allah Ya yarda da su -, sai ya ce: "Kada ku zagi sahabbaina, da a ce ɗayanku zai ciyar da zinare kwatankwacin dutsen Uhudu ba zai kai cikin mudun ɗayansu ba, ko rabinsa". (Bukharin ne ya fitar da shi (3673), da Muslim (2541), da Abu Dawud (4658), da Tirmizi (3861).) Kuma annabi mai girma - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bayyana cewa son mutanen Madina alama ce ta imani, ƙinsu kuma alama ce ta munafunci, sai tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: "Alamar imani son mutanen Madina, alamar munafunci ƙin mutanen Madina". (Bukhari ne ya fitar dashi (17), da Muslim (74), da Nasa'i (5019).)
Said ɗan Zaid ɗan Amr ɗan Nufail - Allah Ya yarda da shi - ya ce: "Halartar wani mutum daga cikinsu tare da manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - fuskarsa ta yi ƙura a cikinsa, shi ne mafi alheri daga aikin ɗayanku rayuwarsa, koda an raya shi (tsawon) raywar (Annabi) Nuhu". (Abu Dawud ne ya fitar da shi (4650).)
BABIN WAJABCIN BIYAYYA GA SHUGABANNI.
Muna sanin cewa ji da bi wajine ga majiɓinta al'amuran musulmai; saboda faɗinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Yaku waɗanda suka yi imani ! Ku bi Allah kuma ku bi manzo da majiɓinta al'amura daga cikinku} [al-Nisa'a: 59], da kuma faɗinsa - annabi tsira da amncin Allah su tabbata su tabbata agare shi -: "Ji da bi wajibi ne muddin dai ba'a yi umarni da saɓo ba, idan aka yi umarni da saɓo to babu ji kuma babu bi". (Bukhari ne ya fitar da shi (2955), da Muslim (1839).)
A cikin "Ingantattun littattafan hadisan nan biyu " Daga Ubada ɗan Samit - Allah Ya yarda da shi - ya ce: "Mun yi wa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - mubaya'a a kan ji da biyayya a halin rintsi da sauƙi, da farin ciki da baƙin ciki, da kuma nuna fifiko a kammu. Kuma kada mu yi wa ma'abota al'amari jayayya, kuma mu faɗi gaskiya a duk inda muke, ka da mu ji tsoron zargin mai zargi a al'amarin Allah". (Bukhari ne ya fitar da shi (7055), da Muslim (1709).)
Abu Zur'ata - Allah Ya yi masa rahama - ya ce: "...Muna tsaida wajibcin yaƙi da hajji tare da shugabannin Musulmai a kowane zamani, kuma bama ganin tawaye akan shugabanni ko yaƙi a cikin fitina, kuma muna ji muna bi ga wanda Allah - Mai girma da ɗaukaka - Ya jiɓinta masa al'amarinmu, kuma kada mu zare wani hannu daga biyayya, kuma muna bin sunna da jama'a". (Sharhi Usulul I'itiƙadi Ahlus Sunnah Wal jama'ah na Imam al-Lakal'i (1/175).)
Biyayya ga majiɓinta al'amari kawai tana wajaba ne a aikin alheri, kuma tana haramta a cikin saɓo, saboda faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabata agare shi - kamar yadda yake a cikin Hadisin Ɗan Umar - Allah Ya yarda da shi - wanda ya gabata: "...Muddin dai ba'a yi umarni da saɓo ba, idan aka yi umarni da saɓo to babu ji kuma babu bi". da kuma faɗinsa - annabi tsira da amncin Allah su tabbata su tabbata agare shi -: "Babu biyayya a cikin saɓo, kawai biyayya (tana kasancewa ne) a cikin aikin alheri". (Bukhari ne ya fitar da shi (7257), da Muslim (1840).)
Imam Abu Ibrahim al-Muzani ya ce: "Biyayya ga majiɓinta al'amura a cikin abinda ya kasance abin yarda a wajen Allah - Mai girma da ɗaukaka -, da nisantar abinda ya kasance abin fushi a wajen Allah, da barin tawaye a lokacin ta'addancinsu da zalincinsu, da tuba zuwa ga Allah - Mai girma da ɗaukaka - don su ji tausayin talakawansu". (Sharhus Sunnah na al-Muzani (Shafi na: 84).)
Kammalawa
Godiya ta tabbata ga Allah wanda da ni'imarSa ce ayyukan alheri suke cika, muna salati muna sallama ga abin aikowa dan rahama ga talikai, kuma muna godewa Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka - akan abinda Ya yi baiwa da shi akanmu na cika wannan littafi mai girma mai albarka, kuma muna faɗa kamar yadda 'yan aljanna suke cewa: {Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai} [Yunus: 10]. Kuma kamar yadda Ubangijinmu - sha'aninSa ya ɗaukaka - Ya umarce mu: {Ka ce: "Godiya ta tabbata ga Alah, kuma aminci ya tabbata bisa ga bãyinSa, waɗanda Ya zãɓa." Shin Allah ne Mafi alhẽri koabin da suke yin shirki da Shi?} [al-Naml: 59].
Muna roƙonSa Ya sanya wannan aikin abin tsarkakewa ga zatinSa mai girma, mai dacewa ga shiriyar shugaban manzanni - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, mai anfanar da bayinSa, mai ceto garemu ranar haɗuwa da Shi.
Muna sanin cewa mu duk yadda muka yi ƙoƙari ba zamu karade wannan babban maudu’in ba; domin bayani ne game da Allah da mala'ikunSa da littattafanSa da manzanninSa da ranar lahira da hukunci da ƙaddara, sai dai mu, muna cika littafin da faɗin Allah - sha'aninSa ya ɗaukaka kuma sarautarSa ta ɗaukaka -; {Kuma ba su ƙaddara Allah a kan haƙĩƙanin ĩkon yinsa ba: kasã duka damƙarSa ce, a Rãnar kiyãma, kuma sammai abũbuwan naɗewa ne ga dãmanSa. Tsarki ya tabbata a gare Shi, kuma Ya ɗaukaka daga barin abin da suke shirka da shi} [al-Zumar: 67].