المختصر المفيد للمؤذن والإمام والخطيب وأحكام المساجد

المختصر المفيد للمؤذن والإمام والخطيب وأحكام المساجد

كتاب "المختصر المفيد للمؤذن والإمام والخطيب وأحكام المساجد" يتناول مسؤوليات المؤذن والإمام والخطيب وأحكام الأذان والإقامة وصلاة الجمعة وأحكام المساجد. يوضح الكتاب تعريف الأذان والإقامة وحكمهما وفضلهما، كما يبين الصفات المطلوبة في المؤذن والشروط اللازمة لصحة الأذان والإقامة. بالإضافة إلى ذلك يستعرض الكتاب أحكام الإمامة، ومشروعيتها وفضلها، وشروط وصفات الإمام، مع التركيز على أهمية العلم والخلق في من يتولى هذه الوظيفة الشرعية.

Language: lang_ha
Prepared by: Kwamitin ilimi na Cibiyar hidimar bayanan Addinin Musulunci a cikin harsuna daban daban.
Version: 2.1
Translations 30
Afrikanns Assamese Azerbaijani Bengali +26
Attachments 7
PDF
Audio
Video
+3

TAKAITACCEN BAYANI MAI AMFANI GA LADANAI DA LIMAMAI DA MASU HUDUBA DA KUMA HUKUNCE-HUKUNCEN MASALLACI

Kwamitin ilimi na Cibiyar hidimar bayanan Addinin Musulunci a cikin harsuna daban daban.

Hakika godiya ta tabbata ga Allah, muna gode maSa, muna neman taimakonSa, muna neman gafararSa, kuma muna neman tsarin Allah daga sharrukan kawunanmu da munanan ayyukanmu, wanda Allah Ya shiryar to babu mai ɓatar da shi, wanda kuma Ya ɓatar babu mai shiryar da shi. Kuma ina shaida cewa babu wani abin bautawa da gaskiya sai Allah Shi kaɗai, baShi da abokin tarayya, kuma ina shaida cewa Annabi Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa ne, Allah Yayi tsira a gare shi, da alayensa, da sahabbansa, da waɗanda suka biyo su da kyautatawa, Ya yi aminci amincewa.

Bayan haka: Lalle ne da yake mutane suna cikin buƙata ta dindindin ga abin da zai gyara musu al'amuransu, sai Shari'a ta zo da abin da zai tabbatar da wannan. Daga cikin haka akwai abin da ya shafi kiran sallah da iƙama ga sallah, da yi wa mutane limanci a cikinta, da huɗubar Juma'a, da hukunce-hukuncen masallatai, Saboda haka ne nauyin ladanin masallaci da liman da mai hudubar Juma'a ya kasance nauyi ne mai girma. Kuma a dalilin haka ne muka himmatu wajen shirya wani littafi mai suna:  (المختصر المفيد للمؤذن والإمام والخطيب وأحكام المساجد) da kuma fassara shi zuwa harsuna da dama.

Bincike na farko: Hukunce-hukuncen kiran sallah da iƙama

Kiran sallah alama ce ta Musulunci da mabiyan sa, wanda ake yin sa a kowacce rana da dare sau biyar, kuma lalle Malamai sun ba da himma a cikin littattafansu ga al'amarinsa, da sunnoninsa, da hukunce-hukuncensa, da mustahabbansa, da ma abubuwan da ke warware shi. Wannan kuwa bai zama ba face saboda muhimmancin wannan ibada da darajarta [1]. (1) A duba: Fathul Mun'im Sharhin Sahih Muslim (2/ 460).

Na farko: Ma'anar kiran sallah da iƙama

Kiran sallah a shari'ance: Shi ne sanar da shigar lokacin sallah, da lafuzzan sanannu keɓantattu waɗanda aka shar'anta [2]. [2] Ka duba: "al-Mughni na Ibnu Ƙudama": (1/292), da "Mukhtar as-Sihah": (shafi 16)- madda أ ذ ن, da "al-Azan wal-Iƙama na al-Ƙahtani": (shafi 5).

Iƙama a Shari'ance: Ita ce sanar da faraa sallah, da wani ambato kebantacce wanda aka shar'anta [3]. [3] A duba: Kasshaf al-Ƙina (1/230).

NA BIYU: Hukuncin kiran sallah da iƙama

Kiran sallah da iƙama sun tabbata da Alƙur'ani da Sunnah da Ijma'i:

Amma a Alkur’ani; Allah Madaukakin Sarki ya ce: Kuma idan kuka yi kira zuwa sallah, sai su riƙe ta bisa izgili da wãsa. Wannan dõmin lalle ne su, mutãne ne (waɗanda) bã su hankalta. [al-Ma'ida: 58].

Amma a Sunnah: to lalle hadisai masu yawa sun yi nuni akan shar'antuwarsu, daga cikinsu:

Daga Ibnu Umar Allah ya yarda da su ya ce: Musulmai sun kasance a lokacin da suka iso Madina, suna taruwa su kintaci lokacin Sallah ba tare da an yi kira ta ba. Sai suka tattauna wata rana a kan haka, sai wasunsu suka ce: Ku riki kararrawa kamar kararrawar Nasara. Wasu kuma suka ce: A'a, sai dai kaho kamar kahon Yahudawa. Sai Umar ya ce: Shin ba za ku tura wani mutum ya yi kira Sallah ba? Sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: «Ya Bilai, tashi ka kira sallah» [4]. [4] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (604), da Muslim, a lamba ta (377).

Amma Ijma'i; Al'umma ta haɗu akan shar'antuwarsu salloli biyar:

Imam Ibn Kudamah Al-Makdisi ya ce: "Al'umma ta yi ijma'i akan cewa an shar'anta kiran sallah domin salloli biyar"[5]. [5] al-Mugni: (1/ 293).

Kiran sallah da iƙama suna daga cikin farillan kifaya a haƙƙin maza a halin zaman gida da kuma tafiya a salloli biyar ba waninsu ba; saboda hadisin Malik ɗan Al-Huwairith - Allah Ya yarda da shi - cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce musu: «Idan sallah ta zo, to ɗayanku ya yi muku kiran sallah, kuma babbanku ya yi muku limanci» [6]. [6] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (628), da Muslim, a lamba ta (674).

Saboda suna daga alamomin addinin musulunci na zahiri, barinsu ba ya halatta.

Amma mata, ba a shar'anta musu kiran sallah da tada ikama ba, ko mace ta yi sallah ita kaɗai, ko kuma ta limanci mata [7]. [7] Sharhin al-Umda na Ibnu Taimiyya - Littafin sallah (shafi: 101).

Matashiya ta Uku: Falalar Kiran Sallah da Iƙama

An samo nassoshi masu yawa a kan falalar kiran sallah da ladanai, daga cikinsu akwai falaloli masu zuwa:

Mai kiran sallah yana daga cikin masu kira zuwa ga Allah, kuma yana daga cikin mutane mafi kyawun magana, Allah Madaukakin Sarki ya ce: Kuma wãne ne mafi kyau ga magana daga wanda ya yi kira zuwa ga Allah, kuma ya aikata aiki na ƙwarai kuma ya ce: 'Lalle nĩinã daga mãsu sallamãwar al'amari zuwa ga Allah?' [Surat Fussilat: 33].

Ladanai su ne mafiya tsawon wuya a ranar Alƙiyama; domin daga Muawiyah - Allah ya yarda da shi - ya ce: Na ji Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi - yana cewa: "Ladanai sune mafiya tsawon wuyaye a ranar alƙiyama." [8]. [8] Muslim ne ya ruwaito shi, a lamba ta (387).

Kiran Sallah da Ikama suna kore Shaiɗan; an karɓo daga Abu Huraira - Allah ya yarda da shi - cewa Annabi ﷺ ya ce: «Idan aka kira Sallah sai shaidan ya juya aguje yana tusa, don kar ya ji kiran Sallar, idan aka gama kiran Sallar sai ya dawo, har idan aka tada Sallah -wato aka yi ikama- sai ya sake juyawa aguje, idan aka gama ikamar sai ya sake dawowa, har sai ya shiga tsakani -wato ya sanya waswasi- tsakanin mutum da zuciyarsa, yana ce masa: Ka tuna kaza, kuma ka tuna kaza, ga abin da bai kasance yana tunawa ba a da, har sai mutum ya dimauce bai san raka'a nawa ya yi sallah ba» [9]. [9] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (1222), da Muslim a lamba ta (389).

Kowane abu da ya ji kiran sallar mai kiran sallah zai yi masa shaida; An rawaito daga Abdullah bn Abd al-Rahman al-Ansari, cewa Abu Sa'id al-Khudri -Allah ya yarda da shi- ya ce masa: "Lallai ni ina ganin ka kana son tumaki da ƙauye, to idan ka kasance a cikin tumakanka, ko ƙauyanka, sai ka yi kiran sallah, ka ɗaga muryarka da kiran, domin shi:" "Ba wani aljani ko wani mutum ko wani abu da zai ji muryar mai kiran sallah sai ya yi shaida gareshi ranar Alƙiyama." Abu sa'id ya ce: Na ji shi daga manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi - [10]. [10] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (609).

Lallai da a ce mutane sun san falalar kiran sallah sani na haƙiƙa, da sun yi ƙuri'a a kansa, wato: da sun yi ƙuri'a a tsakaninsu kan wanene a cikinsu zai yi kiran sallah; An karɓo daga Abu Hurairah - Allah ya yarda da shi - cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Da mutane sun san abin da ke cikin kiran sallah (wato: Ladan) da sahun farko, sannan ba za su samu ba sai sun yi ƙuri'a a kan sa; to, da sun yi ƙuri'ar» [11]. [11] Bukhari ne ya ruwaito shi a lamba ta (615), da Muslim a lamba ta (437).

An ruwaito daga Bara'u bn Azib -Allah ya yarda da shi-, cewa Annabin Allah ﷺ ya ce: "Lallai ana gafarta wa mai kiran Sallah iya inda muryarsa ta kai, kuma duk wani ɗanye da busasshe da ya ji shi zai yi masa shaida, kuma yana da lada kwatankwacin ladan wanda ya yi sallah tare da shi; domin mai nuni zuwa ga alheri kamar mai aikata shi ne." «Tabbas Allah da mala'ikunsa suna salati ga sahu na gaba, kuma ana gafarta wa ladani iya inda muryarsa ta kai, kuma duk wani ɗanye da busasshe da ya ji shi yana gaskata shi, kuma yana da kwatankwacin ladan waɗanda suka yi sallah tare da shi» [12]. [12] Ahmad ne ya ruwaito shi, a lamba ta (18506), da Nasa'i, a lamba ta (646). Almunziri ya ce a cikin Attargib Wattarhib (1/176): Isnadinsa Hasanun Jayyid ne. Kuma Ibnu Mulaqqin ya ce a cikin AlBadrul Munir (3/385): Wannan Isnad Jayyid ne.

Lallai kiran sallah na daga cikin mafi girman alamomin Musulunci, kuma shi ne abin da ke banbance tsakanin kasar kafirci da kasar Musulunci; domin kuwa Bukhari ya kawo wani babi a cikin littafinsa na Sahih mai taken: "Babin Kare Jinane ta Hanyar Kiran Sallah" sannan ya kawo hadisin Anas bin Malik, Allah Ya yarda da shi: ""Lallai Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kasance idan zai yaƙi wasu mutane tare da mu, ba ya kai hari da mu har sai gari ya waye ya duba, idan ya ji kiran sallah sai ya kame daga gare su, idan kuma bai ji kiran sallah ba sai ya kai musu hari"[13]." [13] Bukhari ne ya ruwaito shi a lamba ta (610), da Muslim a lamba ta (382).

Imam alKhaɗɗabi ya ce: "A cikinsa akwai bayani cewa lallai kiran sallah alama ce ta addinin Musulunci, kuma shi wajibi ne wanda barinsa ba ya halatta, kuma ko da mutanen wani gari sun haɗu a kan barin kiran sallah kuma suka ƙi, to sarki zai yaƙe su a kansa"[14]. [14] A'lam al-Hadith Sharh Sahih al-Bukhari: (1/ 460).

Buƙata ta huɗu: Sharuɗɗan ingancin kiran sallah da iƙama

1- Musulunci: ba su inganta (ikama da kiran sallah) daga kafiri; domin su ibadu ne guda biyu, kuma bauta bata inganta daga kafiri.

2- Hankali: Ba su inganta ba daga mahaukaci da mashayi da ƙaramin yaro wanda ba ya iya bambanta abubuwa ba, kamar sauran ibadu.

3- Niyya: Ba su inganta ba tare da ita ba; domin su ibadu ne, kuma Ibada ba ta inganta sai da niyya; saboda faɗin Manzon Allah ﷺ: «Dukkan ayyuka basa ingantuwa sai da niyyoyi, kuma kowane mutum ana ba shi ladan abinda ya niyyata ne» [15]. [15] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (1), da Muslim, a lamba ta (1907), daga Umar dan Khaddab - Allah Ya yarda da shi -.

4- Zama Namiji: Ladancin mace ba ya inganta, haka kuma ikmarta.

5- Kiran sallar ya zama a lokacin sallah: bai inganta ba kafin shigar lokacinta; saboda hadisin Malik ɗan Al-Huwairith, Allah Ya yarda da shi, cewa Annabi (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ya ce: "...idan sallah ta zo, to sai ɗayanku ya yi muku kiran sallah, kuma mafi girmanku ya yi muku limanci" [16], sai ya rataya al'amarin kiran sallah a kan halartar sallah, kuma halartarta ba ta kasancewa sai bayan shigar lokacinta, kuma iƙama ta kasance yayin nufin tashi zuwa ga sallah. [16] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (628), da Muslim, a lamba ta (674).

6- Kiran sallar ya zama a jere, haka nan ma iƙama: Abin da ake nufi da jeri shi ne: Ladan ya zo da lafazan kiran sallah da iƙama daidai da nassoshin shari'a waɗanda suka zo da bayanin sifar kiran sallah da iƙama, ba tare da gabatarwa ko jinkirta wata kalma ko jimla a kan wata ba; domin kiran sallah ibada ce da ta tabbata a kan wannan jeri, saboda haka wajibi ne a aikata ta kamar yadda ta zo; saboda faɗinsa ﷺ: "«Duk wanda ya farar da wani abu a cikin wannan Addinin namu wanda baya ciki, to shi abin mayar masa ne»" [17]. [17] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (2697), da Muslim, a lamba ta (1718), daga hadisin Nana A'isha - Allah Ya yarda da ita -.

7- Kiran sallar ya zama - haka nan ma Ikama - mai bibiyar juna ne: Abin da ake nufi da Bibiya kuwa: shi ne bibiyar juna tsakanin lafuzan kiran sallah ba tare da rabewa da magana ko aiki ba, kuma kada a raba tsakaninsu da rabewa mai tsawo.

8- Kiran sallar ya zama, da kuma Ikamar, da harshen larabci, da lafuzan da Sunnah ta zo da su, ba tare da kuskuren lafazi wanda ke karkatar da ma'ana ba.

9- Ɗaga murya a kiran sallah; domin idan Ladan ya kankar da muryarsa ta yadda ba ya jiyarwa sai kansa kawai, to ba za a samu manufar shar’anta kiran sallah ba; domin faɗinsa ﷺ: «To sai ɗayanku ya yi muku kiran salla» [18]، Wannan yana nuni zuwa ga ɗaga murya domin ya jiyar da wasu; sai a samu jiyarwa da ake nufi ta sanarwa. Idan ya yi kiran Sallah don kansa ko ga wanda ke tare da shi, to ba a shar'anta ɗaga murya da shi ba, amma zai ɗaga sautinsa gwargwadon yadda zai jiyar da kansa ko wanda ke tare da shi ya ji shi. Amma idan ya ɗaga muryarsa fiye da haka zai fi falala; saboda hadisin Abu Sa’id AlKhudri Allah ya yarda da shi, daga Annabi ﷺ: "..to, idan ka kasance a cikin tumakanka ko ƙauyenka, sai ka yi kiran sallah kuma ka ɗaga muryarka da kiran; saboda babu wani aljani, ko wani mutum, ko wani abu da zai ji muryar mai kiran sallah, sai ya yi masa shaida a ranar Alƙiyama." [19]. [18] Fitar da shi ya gabata. [19] An riga an fitar da shi.

Maudu'i na Biyar: Daga cikin siffofin da ake buƙata ga Mai kiran sallah

1- Ya zama sananne da adalci da riko da addini; saboda faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: «Liman lãmuni ne, kuma Mai kiran sallah amintacce ne, Ya Allah, Ka shiryar da Limamai, kuma Ka gafarta wa Masu kiran sallah» [20] Kuma Ladani amintacce ne a kan lokacin sallah da azumi. Amana kuwa, babu mai sauke ta sai adali. Saboda haka, kada Ladanin ya zama fasiƙi, ko mai bayyana saɓo a fili, ko wanda ya zubar da mutuncinsa. [20] Abu Dawud ne ya rawaito shi, a lamba (517), da Tirmizi a lamba (207).

2- Ya zama baligi ne; domin kiran sallar baligi ya fi cika, kuma ya halatta kiran sallar yaro mai hankali matukar yana kiran sallah a cikin lokaci, duk lokacin da ya yi kiran sallah to an wadatu da kiran sallar sa; domin da shi ne ake samun sanarwar shigar lokaci.

3- Ya zama masani ne game da lokuta; domin ya bincike su, sannan ya yi kiran sallah a farkonsu; domin kuwa idan bai kasance masani game da su ba, to ba a tsira daga ya yi kuskure ko ya kauce ba.

4- Ya zama mai karfin murya; domin hadisin Abdullahi dan Zaid, Allah ya yarda da shi, game da mafarkin kiran sallah, wanda a ciki Annabi ﷺ ya ce masa: «Haƙiƙa wannan mafarki ne na gaskiya, don haka ka tsaya tare da Bilal domin shi ya fi ka daɗin murya da kuma nisa, ka jefa masa abin da aka faɗa maka, kuma bari ya yi kira da shi» [21], ma'ana: «Kuma ya fika daga murya» Wato: ya fi ka ɗagawa da ƙarfin murya, kuma wannan dalili ne a kan son a riƙi Ladan mai murya mai ƙarfi da bayyana; saboda irin wannan murya ta fi isarwa wajen sanar da kiran sallah [22]. [21] Tirmizi ne ya ruwaito shi (189), kuma ya ce: "Hadisi ne kyakykyawa ingantacce." [22] A duba: Tuhfatul Ahwadhi (1/481).

5- Ya zama mai kyakkyawan sauti; saboda faɗin sa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - a cikin hadisin Abdullahi ɗan Zaid - Allah Ya yarda da shi - wanda ya gabata: «Lallai shi ya fi ka daɗin murya da nisanta» Wato: Mafi kyawun sauti da daɗinsa.

6- Ya kasance mai tsarki daga ƙaramin hadasi da kuma babban; saboda Kiran sallar da iƙama zikiri ne ga Allah Maɗaukakin sarki, kuma an so mai zikiri ya kasance mai tsarki.

7- Ya kira sallah a tsaye; domin faɗin annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: «Yã kai Bilal, ka tsahi, ka yi kira ga sallah» [23], Ibn al-Munzir ya ce: «(Malamai) Sun haɗu akan cewa, yana daga cikin Sunnah, ladani ya yi kiran sallah a tsaye»[24]. [23] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (604), da Muslim, a lamba ta (377), daga Ibnu Umar - Allah Ya yarda da su -. [24] al-Ijma' na Ibn al-Mundhir: (shafi na: 38).

8- Ya yi kiran sallah yana fuskantar alƙibla; saboda abin da ya zo a wata ruwaya ta hadisin Abdullahi ɗan Zaid - Allah Ya yarda da shi - game da mafarkin kiran sallar, ya ce: "Sai ya fuskanci alƙibla, ya ce: "Allah ne Mafi girma, Allah ne Mafi girma. . ."[25]،" Ibnu Al-Munzir ya ce: «Kuma (malamai) sun yi ijma'i a kan cewa yana daga cikin Sunnah a fuskanci Alƙibla wajen kiran sallah»[26]. [25] Abu Dawud ne ya rawaito shi, a lamba (507). [26] al-Ijma' na Ibn al-Mundhir (Shafi na: 38).

9- Ya sanya yatsunsa a cikin kunnuwansa; saboda aikin Bilal - Allah Ya yarda da shi - a kiran sallarsa a gaban Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, daga Abu Juhaifa - Allah Ya yarda da shi - ya ce: "Na ga Bilal yana yin kiran (Sallah), yana juyawa yana bin bakinsa a nan, dama nan, tare da yatsansa a cikin kunnuwansa, kuma Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, a cikin wani dome ja..."[27]. [27] Tirmizi ya ruwaito shi: (197), kuma ya ce: Hadisi ne mai kyau ingantacce, kuma asalinsa yana cikin Sahihul Bukhari (634) da lafazin: Daga Aun dan Abu Juhaifa, daga babansa, cewa ya ga Bilal yana kiran sallah, sai na fara bin bakinsa ta nan da ta nan yayin kiran sallar.

Imam Tirmizi - Allah ya yi masa rahama - ya ce bayan ya ruwaito wannan Hadisin: "Kuma aiki ya tabbata a kansa a wajen ma'abota ilimi: suna so ladani ya sanya yatsunsa a cikin kunnuwansa a lokacin kiran sallah."

An tambayi Ibnu Shubrumah me yasa aka umarci ladani ya sanya 'yan yatsunsa a cikin kunnuwansa? Ya ce: "Domin karfin murya..."[28]. [28] al-Awsaɗ (4/11).

Annawawi Allah ya masa rahama ya ce: "Sunnah ce ya sanya 'yan yatsunsa a cikin kofofin kunnuwansa, kuma wannan abu ne da aka yi ittifaki a kansa, kuma Al-Mahamili ya ruwaito shi a cikin Al-Majmu'u daga mafi yawan ma'abota ilimi, Malamanmu suka ce: Kuma akwai wata fa'ida a cikin hakan, ita ce cewa watakila wani mutum ba zai ji muryarsa ba saboda kurmantaka, ko nisa, ko wanin haka, sai ya gane ta hanyar 'yan yatsunsa cewa kiran sallah yake yi" [29]." [29] Sharhu al-Muhadhdhab (3/113).

10- Ya waiwaya zuwa dama idan ya ce: Ku zo ga sallah, a dukkan nin biyun, da kuma zuwa hagu idan ya ce: “Ku zo zuwa ga babba rabo,” a dukkan sau biyun, tare da tabbatar da ƙafafunsa; saboda hadisin Abu Juhaifa -Allah ya yarda da shi- a cikin kiran sallar Bilal -Allah ya yarda da shi- a gaban Annabi -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi- ya ce: «Sai na kama bin bakinsa, ta nan da ta nan, yana cewa zuwa dama da hagu: Ku zo ga sallah, ku zo ga babban rabo»[30]; Kuma saboda ya fi jiyar da kiran sallah ga wanda ya yi nisa daga masallaci. [30] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (634), da Muslim, a lamba ta (503), kuma lafazin na Muslim ne.

11- Ya yi tartili a kiran sallah, wato ya bi a hankali a cikinsa, ba tare da yalwatawa ba, ba kuma madda mai wuce gona da iri ba; domin kiran sallah sanarwa ne ga waɗanda ba sa nan a masallaci, don haka yin sa a hankali ya fi isar da sako, kuma ya gaggauta yin ikama, wato ya yi sauri a cikinta; domin ita sanarwa ce ga waɗanda suka halarta, don haka gaggawa ta dace a cikinta[31]. [31] A duba: al-Mughni na Ibnu Ƙudama (1/ 295).

12- Ya gabatar da kiran sallah kamar yadda aka shar'anta shi da murya mai laushi da sauƙi, ba tare da ƙwallafa ko karkatar da lafazi ba, ba kuma ya mayar da shi kamar waƙa ba, haka nan ba zai yi masa madda da za ta fitar da shi daga manufarsa ba. Sai dai ladanin ya gabatar da shi da muryarsa, yana mai kiyaye sharuɗɗansa da ladubbansa na shari'a.

MATASHIYA TA SHIDA: SIFFAR KIRAN SALLAH DA IƘAMA

Kiran sallah da iƙama na da siffofi da Nassoshin Annabta suka zo da su, daga cikin abin da ya zo a siffar kiran sallah da iƙama akwai hadisin Abdullahi dan Zaid (Allah ya yarda da shi), kuma lafazin kiran sallah a cikinsa shi ne:

Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allahu Akbar.  Ma’ana:(Allah ne Mafi girma, Allah ne Mafi girma, Allah ne Mafi girma, Allah ne Mafi girma).

Ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah. Ina shaidawa cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah.

Ina shaidawa lalle (Annabi) Muhammadu Manzon Allah ne, Ina shaidawa lalle (Annabi) Muhammadu Manzon Allah ne.

Hayya alas salah, hayya alas salah. Ma’ana: (Ku yi gaggawa zuwa ga sallah, ku yi gaggawa zuwa ga sallah).

Hayya alal falāh, hayya alal falāh.  Ma’ana: (Ku taho zuwa ga tsira, Ku taho zuwa ga tsira).

Allahu Akbar, Allahu Akbar.  (Allah ne Mafi girma, Allah ne Mafi girma).

Babu wani abin bautawa da gaskiya Sai Allah

Kuma lafazin Iƙama:

Allahu Akbar, Allahu Akbar. (Allah ne Mafi girma, Allah ne Mafi girma).

Ina shaida cewa lallai babu wani abin bautawa da ya cancanci a bauta masa da gaskiya sai Allah.

Ina shaidawa lalle (Annabi) Muhammadu Manzon Allah ne.

Ku yi gaggawa zuwa ga sallah, ku taho zuwa ga tsira.

Haƙiƙa sallah ta tsayu, haƙiƙa sallah ta tsayu.

Allahu Akbar, Allahu Akbar. (Allah ne Mafi girma, Allah ne Mafi girma).

Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah.[32] [32] Abu Dawud ne ya ruwaito shi a lamba (499), da Tirmizi a takaice a lamba (189), kuma ya ce: Hadisin Abdullahi bn Zaid, hadisi ne Hasan Sahih.

To wannan ita ce siffar kiran sallah da ikama wacce Bilal - Allah Ya yarda da shi - ya dawwama a kanta tare da Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - a gida da tafiya, har lokacin da ya rasu - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -.

Kuma ya ce a kiran sallar Asuba bayan Hayya 'alal Falah: Assalatu khairun minan naum. Ma’ana: (Sallah ta fi bacci alheri), sau biyu; saboda hadisin da Abu Mahzura, Allah ya yarda da shi, ya ruwaito cewa lallai Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya ce masa: «Idan kuwa sallar Asuba ce, sai ka ce: Sallah ita ce mafi alheri daga bacci, Sallah ita ce mafi alheri daga bacci» [33]. [33] Abu Dawud ne ya rawaito shi, a lamba (500), An-Nawawi ya ce a cikin Khulasatul Ahkam (1/ 286): Hadisi ne Hasan.

Kuma akwai wata siffa ta daban ta kiran sallah, ita ce Tarji’i, wato maimaitawa; sai ya kankar da muryarsa a wajen shahada biyu, sannan ya sake maimaita su da ɗaga murya. A wajen Ikama kuwa, sai ya ninka ta. Wannan siffar ta zo a cikin hadisin Abu Mahzura - Allah ya yarda da shi -, inda ya ce: Manzon Allah ﷺ ya karantar da ni kiran sallah shi da kansa, sai ya ce: «Ka ce: Allah ne mafi girma Allah ne mafi girma, Allah ne mafi girma Allah ne mafi girma, Ina shaidawa cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Ina shaidawa cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Ina shaidawa cewa (Annabi) Muhammad Manzon Allah ne, Ina shaidawa cewa (Annabi) Muhammad Manzon Allah ne - sau biyu-biyu - ya ce: Sannan ka koma, ka ɗaga muryarka:  Ina shaidawa cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Ina shaidawa cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Ina shaidawa cewa (Annabi) Muhammad Manzon Allah ne, Ina shaidawa cewa (Annabi) Muhammad Manzon Allah ne, Ku yi gaggawa zuwa sallah, Ku yi gaggawa zuwa sallah, Ku yi gaggawa zuwa tsira, Ku yi gaggawa zuwa tsira, Allah ne mafi girma Allah ne mafi girma, babu abin bautawa da gaskiya sai Allah».

«Ita kuma Ikama ita ce: Allah ne Mafi girma, Allah ne Mafi girma, Allah ne Mafi girma, Allah ne Mafi girma, Ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Ina shaidawa cewa Annabi Muhammadu manzon Allah ne, Ina shaidawa cewa Annabi Muhammadu manzon Allah ne, Ku yi gaggawa zuwa ga sallah, Ku yi gaggawa zuwa ga sallah, Ku yi gaggawa zuwa ga tsira, Ku yi gaggawa zuwa ga tsira, Hakika an tada sallah, Hakika an tada sallah, Allah ne Mafi girma, Allah ne Mafi girma, babu abin bautawa da gaskiya sai Allah» [34]. [34] Abu Dawud ne ya ruwaito shi, a lamba (502, 503).

Wannan yana daga cikin sabani na nau'o'i, da duk wacce siffa ladani ya dauka daga cikin wadannan siffofi tabbatattu, to ya kyautata. Shaikhul Islam Ibn Taimiyyah - Allah ya yi masa rahama - ya ce bayan ya ambaci wasu daga cikin siffofin kiran sallah tabbatattu: Kuma idan ya kasance haka, to abin da yake daidai shi ne mazhabar Ahlul Hadith da waɗanda suka dace da su, wanda shi ne halatta dukkan abin da ya tabbata game da haka daga Annabi tsira da amincin Allah su kara tabbata a gare shi, ba sa ƙin wani abu daga cikin wannan; domin bambancin siffofin Kiran Salla da Iƙama, kamar na karatuttuka da Tashahhudai ne da makamantansu. Kuma bai halatta ga kowa ba ya ƙi abin da Manzan Allah tsira da amincin Allah su kara tabbata a gare shi ya sunnanta wa al'ummarsa. [35]. [35] Majmu al-Fatawah (66/ 22).

Matashiya Ta Bakwai: Abin da mai jin kiran salla yake fada, da kuma addu'ar da ake yi a bayansa.

Ana so ga wanda ya ji kiran sallah ya fadi irin abinda mai kiran sallah yake fada, saboda hadisin Abu Sa'id al-Khudri - Allah ya yarda da shi - cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Idan kun ji kiran sallah, to ku fadi irin abinda ladani yake fada" [36]. Sai dai a Hai'ala biyu - wato faɗin mai kiran sallah: Ku yi gaggawa zuwa sallah, ku yi gaggawa zuwa tsira - ana so ga wanda ya ji kiran sallah ya faɗa a bayan kowacce daya daga cikinsu: Babu wata Dabara ko karfi sai na Allah saboda hadisin Umar ɗan Khaɗɗab - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira daa mincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Idan mai kiran sallah ya ce: Allahu Akbar Allahu Akbar, sai ɗayanku ya ce: Allahu Akbar Allahu Akbar, sannan ya ce: Ash'hadu alla ilaha illallahu, kuma shima ya ce: Ash'hadu alla ilaha illallahu, sannan ya ce: Ash'hadu anna Muhammadan rasulullah, kuma shima ya ce: Ash'hadu anna Muhammadan rasulullah, sannan ya ce: Hayya alas sallah, sai yace: La haula wala ƙuwwata illa billah, sannan kuma ya ce: Hayya alal falah, sai ya ce: La haula wala ƙuwwata illa billah, sannan ya ce: Allahu Akbar Allahu Akbar, kuma shima ya ce: Allahu Akbar Allahu Akbar, sannan ya ce: La'ilaha illallah, kuma shima yace: La'ilaha illa Allah, daga zuciyarsa, zai shiga Aljanna» [37]. [36] Bukhari ne ya ruwaito shi a lamba ta (611), da Muslim a lamba ta (383). [37] Muslim ne ya ruwaito, a lamaba ta (385).

Kuma ya fadi: (Ina shaidawa cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Shi kadai Yake ba Shi da abokin tarayya, kuma (Annabi) Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa ne, na yarda da Allah a matsayin Ubangiji, da (Annabi) Muhammadu a matsayin Manzo, da kuma Musulunci a matsayin addini) bayan shaida biyu.

Daga Sa'ad ɗan Abu Waƙas - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Duk wanda ya ce lokacin da ya ji mai kiran sallah: Ina shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah Shi kaɗai, ba Shi da abokin tarayya, kuma Annabi Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa ne, na yadda da Allah Shi ne Ubangiji, da Muhammad shi ne Manzo, da Musulunci shi ne Addini.” za’a gafarta masa zunubinsa»[38]. [38] Muslim ne ya ruwaito shi, a lamba ta (386).

Kuma idan mai kiran sallah ya ce a sallar Asuba: "Assalatu khairun minan naum," to shi ma mai sauraro zai faɗi irinsa; saboda faɗin Annabi ﷺ: "Idan kun ji kiran sallah, to ku fadi irin abinda ladani yake fada". [39]. An haɗu a kansa [39].

Sannan ya yi salati ga annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, sannan ya fadi abinda ya zo a hadisi daga gare shi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Duk wanda ya ce a yayin da ya ji kiran sallah: (Ya Allah, Ma’abocin wannan cikakken kira da sallah da za'a tayar, Ka bai wa [Annabi] Muhammad al-Wasila da al-Fadila, kuma Ka tashe shi a matsayi abin yabo wanda Ka yi masa alƙawarin sa), ceto na zai halatta a gare shi ranar alƙiyama." [40], kuma ma'ana: Kira Cikakke Wato: kiran sallah, cikakke ne kammalalle; saboda ya ƙunshi girmama Allah da kadaita shi, da shaidawa da Manzanci, da kuma kira zuwa ga alheri. «Kuma Sallar da za a tsayar» Wato: wadda za a tsayar kuma a aikata. Al-Wasila Matsayi ne a cikin Aljanna. FALALA Martaba maɗaukakiya wadda ya kaɗaita da ita. matsayi abin godewa Matsayi abun godewa: kowane matsayi ne da mutane suke gode masa a cikinsa, kuma daga ciki akwai babban ceto ga dukkan halittu, wanda ake yin ceto a cikinsa ga mutanen filin Alkiyama har sai an yi hukunci a tsakaninsu. [40] Bukhari ne ya rawaito shi a lamba ta (614), daga hadisin Jabir - Allah Ya yarda da shi -.

Daga Abdullahi ɗan Amr ɗan Aas - Allah Ya yarda da su - cewa ya ji Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - yana cewa: «Idan kun ji ladani; to, ku faɗi irin abin da yake faɗa, sannan ku yi min salati, domin duk wanda ya yi min salati ɗaya Allah zai yi masa salati goma da shi, sannan ku roƙi Allah Wasila gareni, domin cewa ita wani matsayi ne a aljanna, ba ya kamata sai ga wani bawa daga bayin Allah, ina ƙaunar in zama ni ne shi, duk wanda ya roƙi Allah Wasila gareni, to, cetona zai tabbata gare shi» [41]. [41] Muslim ne ya ruwaito, a lamaba ta (384).

Kuma daga cikin bidi'o'in da aka farar a cikin kiran sallah, Mai kiran sallah ya daga muryarsa da salati da aminci ga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - bayan gama kiran sallah, Kuma haka nan kawo Zikirin da ya zo bayan gama kiran Sallah, wanda shi ne: (Ya Allah Ma’abocin wannan cikakken kira . . .) a cikin murya daya, Da ɗaga hannaye yayin addu'a da shi, Da kuma ƙarin da mai amsawa ladani yake yi na kalmar (Haqqan) ko (Abadan) a ƙarshen jumla, sai ya ce: (Haqqan lā ilāha illallāh) ko kuma (Abadan lā ilāha illallāh); saboda rashin dalili a kan wannan gaba ɗaya.

Babi na Takwas: Hukuncin fita daga masallaci bayan kiran sallah.

Yana haramta ga mutum ya fita daga masallaci bayan kiran sallah har sai ya yi sallah, sai dai idan yana da uzuri, ko kuma yana da niyyar dawowa, to babu laifi a gare shi; daga Abi Sha'atha ya ce: "Muna zaune a cikin masallaci tare da Abu Hurairah, sai malamin ya kira, sai wani mutum daga masallacin ya taka, sai Abu Hurairah ya bi shi da idanunsa har ya fita daga masallacin, sai Abu Hurairah ya ce: amma wannan, hakika ya sabawa Baban Alkasim tsira da amincin Allah su tabbata agare shi "[42]. [42] Muslim ne ya ruwaito shi, a lamaba ta (655).

Tirmizi ya ce bayan ya ruwaito shi wannan Hadisi a cikin Sunan nasa: "A kan wannan ne aiki ya tabbata a wurin ma'abota ilimi daga cikin sahabban Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - da waɗanda suka zo bayansu: cewa kada wani ya fita daga masallaci bayan kiran sallah, sai da wani uzuri: kamar ya kasance ba shi da alwala, ko kuma wani al'amari da babu makawa"[43]. [43] Sunan Tirmizi: (1/ 397), lamba (204).

Matashiya T Tara: Tazarar lokaci tsakanin kiran sallah da iƙama?

Ya zo a cikin Sunnah abin da ke nuna cewa an sami isasshen lokaci tsakanin kiran sallah da iƙama; daga Abdullah bin Mughaffal - yardar Allah ta tabbata a gare shi - ya ce: Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "A kwai sallah tsakanin dukkan kiran sallah biyu, akwai sallah tsakanin dukkan kiran sallah biyu" sannan ana uku ya ce: "Ga wanda ya so". [44]. Kuma abin nufi da kiran sallah biyu: Kiran sallah da iƙama, sai ladan ya sanya wani lokaci tsakanin kiran sallarsa da iƙamarsa, domin mahalarta su samu damar yin raka'a biyu kafin sallah, kuma domin mutanen masallaci su zo su riski sallar. [44] Bukhari ne ya rawaito shi a lamba ta (627), da Muslim a lamba ta (838).

Imam Ahmad ya ce: "Yana da kyau ga ladan idan ya yi kiran sallah kada ya gaggauta da iƙama, sai ya jira har jama'ar masallaci su zo, kuma wanda ke takure -wato wanda ke son yin bahaya- ya biya bukatarsa, ya sanya tazara tsakanin kiran sallarsa da iƙamarsa"[45]. [45] Sharhin Umdatul Fiqh na Ibn Taimiyyah, Littafin sallah: (shafi na 135).

MATASHIYA TA GOMA : NAUYIN DA YAKE AKAN LADAN DA LADUBBANSA

Ya kamata ga mai kiran sallah ya nemi yardar Allah Ta'ala da kiran sallarsa; saboda hadisin Usman dan Abi al-As - Allah Ya yarda da shi - ya ce: «Lalle ne daga cikin karshen wasiyyar da Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya yi min, shi ne in dauki Ladanin da ba ya karbar lada saboda kiran sallarsa»[46]. [46] Tirmizi ne ya ruwaito shi (209), kuma ya ce: Hadisi ne kyakkyawa.

Tirmizi - Allah ya yi masa rahama - ya ce bayan ya ruwaito wannan Hadisi: Kuma aiki a kan wannan a wurin malamai, sun karhanta ladani ya karɓi lada a kan kiran sallah, kuma sun fi so ya nemi lada (a wurin Allah) a kiran sallarsa.

Amma ba wa ladani daga baitul malin musulmai babu laifi a ciki. Domin an kafa baitul mali ne don maslahar musulmai, kuma kiran sallah da ikama na daga cikin maslahar musulmai [47]. [47] Ka duba: Kiran Sallah da Ikama na Kahtani (19).

Kuma yana wajaba a kan sa ya sani cewa shi ke da alhakin kiran sallah na salloli biyar a lokutan su; saboda faɗin sa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: Liman mai lamuni ne, kuma Ladan mai riƙon amana ne. [48] Wato: Cewa shi amintacce ne a kan lokutan sallah, saboda haka ya wajaba a kansa ya je masallaci a cikin tsarki tun kafin lokacin kiran sallah da isasshen lokaci, kuma kada ya rasa yin kiran sallah sai da wani uzuri, a wannan hali wajibi ne a kansa ya wakilta wanda zai maye gurbinsa wajen yin kiran sallar. [48] Abu Dawud ne ya ruwaito shi (517), da Tirmizi (207), daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi -.

Abubuwan da suka kamata ga Ladanin:

(1) Ya kula da tsaftar masallaci da tsare shi, kuma ya kasance mai haɗin kai da ma'aikatan masallaci da jama'ar masallaci a kan haka; domin kuwa Allah ya yabi masu raya gidajenSa, ya ce: Abin sani kawai, mai rãya masallãtan Allah, shĩ ne wanda ya yi ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira, kuma ya tsayar da salla kuma ya bãyar da zakka, kuma bai ji tsõron kõwa ba fãce Allah. To, akwai tsammãnin waɗannan su kasance daga shiryayyu. [al-Taubah: 18] Daidai ne ya zama rayarwar tasu gare shi ta hanyar gina Masallatai ne da kiyaye su da tsaftace su, ko kuma ta hanyar tsayar da Sallah da ambaton Allah a cikin su, to, dukkan ma'anonin nan guda biyu su ake nufi da Rayawa[49]. [49] A duba: Fathul Bari na Ibnu Hajar, 1/541.

(2) Ya koyi akida sahihiya da hukunce-hukuncen kiran sallah da tsarki da sallah, kuma ya haddace daga littafin Allah adadin da ya wadatar, kuma ya kasance wanda ya cancanta don ya maye gurbin liman idan ba ya nan sai ya gabatar da sallah.

(3) Ya yi umarni da kyakkyawa kuma ya yi hani da mummuna, ya yi kira zuwa ga Allah Maɗaukaki da hikima da wa'azi mai kyau, kuma ya yi wa mutane sassauci, ya yi haƙuri akan cutarwarsu, kuma ya ba da haɗin kai a kan haka tare da Limamin masallaci.

(4) A kebance masallaci ga ilimi da ibada, da abin da yake amfanar masallata, kuma a nisanci dukkanin abin da zai cutar da su a cikin addininsu da duniyarsu.

(5) Ya kulla zumunta da taimakekeniya tare da jama'ar masallaci da ma'abutansa, ya tambayi labarinsu idan bai gansu ba, ya ziyarci marasa lafiyarsu, ya sallaci mamatansu kuma ya raka su zuwa makabartu, kuma ya tsaya tare da su a cikin masifu da manyan al'amura.

BABI NA BIYU: Hukunce-hukuncen limanci

Matshiya Ta Farko: Ma'anar limanci

Limanci a sallah: shi ne wani mutum ya gabata daga cikin masu sallah; domin su yi koyi da shi a sallarsu. Shi kuma Liman a sallah: shi ne wanda mutane suke koyi da shi a sallarsu [50]. [50] A duba: Hashiyatur Raudil Murabba' (2/296), da al-Imamatu fis Salati na al-Kahtani (sh. 6).

Matashiya Ta Biyu: Shar'antuwar Shugabanci da falalarsa

Limancin Sallah na daga cikin mafi alkhairin ayyuka wanda mafi alkhairin mutane masu kyawawan siffofi na ilimi da karatu da adalci da sauransu ke jagoranta kamar yadda zai zo, kuma sallar jama'a ba ta tabbata sai da shi, kuma sallar jama'a tana daga cikin manya-manyan alamomin Musulunci[51]. [51] A duba: Al-Mausu'ah al-Fiqhiyyah al-Kuwaitiyyah (6/ 201).

Kuma yana daga cikin Falalar limanci:

1- Limanci falalarsa sananniya ce, Annabi -tsira da amincin Allah su tabba a gare shi- ya jibince shi da kansa, haka nan ma Halifofinsa masu shiryarwa, kuma bai gushe ba mafifitan Musulmai a ilmance da aikace suke jibintarsa[52]. [52] A duba: al-Imamatu fi as-Salati na al-Qahtani: (9).

2- Limanci a sallah wani shugabanci ne na shari'a mai falala, wadda ma'abota falala ke kula da shi; bisa ga faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: «Wanda ya fi mutane sanin Littafin Allah shi ke musu limanci ...» [53], Kuma an sani cewa mafi iya karatu shi ya fi; don haka haɗa ta da shi yana nuna fifikonta [54]. [53] Muslim ne ya ruwaito shi daga hadisin Abu Mas'ud Al’Ansari - Allah Ya yarda da shi - a lamba ta (673). [54] A duba: Sharhin Al-Mumti'a akan Zaad al-Mustaqni (2/41).

3- Addu'ar Annabi-tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ga Limamai ta shiriya; an karɓo daga Abu Huraira, Allah ya yarda da shi, ya ce: Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya ce: «Liman lamini ne, Ladan kuma amini ne, Ya Allah, Ka shiryar da limamai, kuma Ka gafarta wa ladanai» [55]. [55] Abu Dawud ne ya ruwaito shi, a lamba (517), da Tirmizi a lamba (207).

ma'anar: «Limami lãmuni ne» Wato: mai ɗaukar nauyin ingancin sallar mamu ne; saboda alaƙar sallarsu da sallarsa. Ma'anar: "Ya Ubangiji ka shiryar da Limamai" Wato: Ka shiryar da su zuwa ga hanyar daidai, dõmin su zo da sallar a bisa mafi cikar hãli [56]. [56] A duba: Sharhin Abi Dawud na Ainy, (2/468), da Faidul Kadir na Manawy, (3/182).

Matashiya Ta Uku: Wanene ya fi cancantar zama liman

Manzo Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya bayyana wanda ya fi cancanta kuma ya fi dacewa da limanci, Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Zai limanci jama'a, wanda ya fi su karatu na littafin Allah, idan sun yi dai-dai a karatu, sai wanda ya fi su sanin Sunnah, idan sun yi daidai a Sunnah, sai wanda ya riga su Hijira, idan sun yi daidai a Hijira, sai wanda ya riga su Musulunta - a wata riwayar: girmansu a shekaru - kuma kada wani mutum ya limanci wani a wurin ikonsa." [57]. To, mutanen da suka fi cancanta kuma suka fi hakki da limanci sune kamar haka: [57] Muslim ne ya ruwaito shi a lamba ta (673).

Wanda ya fi su haddar Alƙur'ani, da wanda ya fi su kyawun karatu, wato wanda ya gwanance wajen karatun Alƙur'ani kuma yake yinsa a hanya mafi kamala, Masanin Fikihun Sallah. Idan kuma aka samu wanda ya fi karatu da wanda bai kai shi ba amma ya fi shi Fikihu, to za a gabatar da Makarancin da ya fi Fikihu a kan wanda ya fi karatu alhali ba masanin Fikihu ba ne, domin buƙata zuwa ga Fikihu a Sallah da hukunce-hukuncen ta ta fi tsanani akan buƙatar kyautata karatu.

2- Sannan wanda ya fi Ilimin Sunna; idan aka samu limamai biyu da suka daidaita a karatu, amma ɗayansu ya fi ɗayan fikihu da ilimin Sunna, sai a gabatar da wanda ya fi fikihu, saboda faɗinsa ﷺ: «Idan kuma suka kasance daidai a Karatu, to wanda ya fi su sanin Sunnah.»

3- Sannan wanda ya fi dadewa kuma ya fi gabata da yin hijira daga ƙasashen kafirci zuwa ƙasashen Musulunci, wannan idan sun kasance daidai a wajen karatu da ilimin Sunnah; saboda faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: «Sannan idan sun kasance daidai a cikin Sunnah, to wanda ya fi su riga hijira»

4- Sannan wanda ya fi dadewa a musulunci, idan suka kasance daidai a cikin ƙaura (hijira); saboda faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a cikin Hadisin da ya gabata: «Idan sun kasance daidai a Hijira, to wanda ya fi su dadewa a Musulunci» Wato: Musulunci.

5- Sannan wanda ya fi girma a shekaru, idan suka yi daidai a dukkan al'amuran da suka gabata; saboda faɗar sa tsira da amincin Allah su kara tabbata a gare shi a ɗaya daga cikin ruwayoyin Hadisin da ya gabata: «To, mafi girmansu a shekaru» Kuma a hadisin Malik ɗan Huwairith - Allah Ya yarda da shi - ya ce: «To sai ɗayanku ya yi muku kiran sallah, kuma mafi girmanku ya jagorance ku» [58]. [58] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (628), da Muslim a lamba ta (674).

Kuma gabatarwar da Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yi a wannan hadisin ga babba a shekaru; saboda sun kasance masu kusanci a ilimi.

To idan suka yi daidai a cikin dukkan abin da ya gabata kuma suka yi jayayya, kowannensu yana son Limanci, sai a yi kuri'a a tsakaninsu, to wanda kuri'a ta fito masa shi za a gabatar; saboda sun yi daidai a wajen cancanta, kuma ya gagara a hada su, sai a yi musu kuri'a a tsakaninsu kamar sauran haƙƙoƙi.

Kuma mai gida ya fi cancanta da imamanci fiye da bakonsa, haka kuma shugaba – wato shi ne babban liman – ya fi cancanta da imamanci fiye da waninsa, idan har kowannensu ya cancanci imamanci; saboda faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: «Kada wani mutum ya kuskura ya yi wa wani mutum limanci a cikin iyalinsa, ko a inda yake shugabanta»

Haka nan limamin masallaci ratibi; shi ya fi waninsa cancanta - sai dai sarki - ko da kuwa waninsa ya fi shi karatu da ilimi; saboda gamewar hadisin da ya gabata.

Ibnu Umar - Allah Ya yarda da su - ya kasance yana da wani bawansa da ke sallah a wani masallaci, sai ya halarta, sai bawansa ya gabatar da shi, sai Ibnu Umar ya ce masa: «Kai ne ka fi cancanta da limanci a cikin masallacinka» [59]. Shafi'i ya ruwaito shi a cikin (Al-Um) (1/185), da Abdurrazak a cikin (Al-Musannaf) (2/399), da Baihaqi (3/126) (5531). Kuma Nawawi ya ce a cikin (Al-Khulasa) (2/701): Isnadinsa hasan ne ko sahih. Kuma Albany ya kyautata isnadinsa a cikin (Irwa'u Al-galil) (2/302).

Kuma domin cewa a cikin gabatar da waninsa a kansa akwai tsallake shi, da kuma karya masa zuciya.

An yi saɓani a kan limancin yaro mai hankali ga wasunsa, wasu daga cikin ma'abota ilimi sun halatta shi, saboda hadisin Amru ɗan Salama - Allah Ya yarda da shi - «Ya limanci mutanensa a zamanin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - kuma yana ɗan shekara shida ko bakwai»[60]. [60] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (4302).

Kuma ya inganta ga mai sallar nafila ya yi wa mai sallar farilla limanci; domin hadisin Mu'az ɗan Jabal - Allah Ya yarda da shi - «Cewa shi (Mu’azu dan Jabal) ya kasance yana sallar Isha'i tare da Annabi - tsira da aminicin Allah su tabbata a gare shi -, sannan ya dawo wajen mutanensa, sai ya yi musu wannan sallar»[61]. [61] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (701), da Muslim, a lamba ta (465).

Matashiya Ta huɗu: Wanda limancinsa yake haramta:

Limanci yana haramta a cikin halaye masu zuwa:

1- Limancin mace ga namiji, saboda gamewar faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: «Duk mutanen da suka jiɓinta wa mace al'amuransu ba zasu rabauta ba» [62], Kuma limanci wani nau'i ne na shugabanci, kuma saboda asali shi ne kasancewarta a karshen sahu, kamar yadda ya zo a cikin Sunnah; Daga Abu Hurairah, Allah ya yarda da shi, ya ce: Manzon Allah -SAW - ya ce: "Mafi alherin sahun maza shi ne na farkon su, kuma mafi sharrin su shi ne na ƙarshen su, mafi alherin sahun mata shi ne na ƙarshen su, kuma mafi sharrin su shi ne na farkon su". [63]، Hakan kuwa don tsare mutuncinta ne da suturta ta, to da a ce an gabatar da ita don limanci, da hakan ya saba wa wannan asali na shari'a. Kuma hakika malamai sun yi ijma'i a kan wannan al'amari, Imam Ibn Hazm, Allah ya yi masa rahama, yana cewa: Kuma sun yi ittifãƙi a kan cewa mace ba ta yi wa maza limanci, alhãli kuwa sun san cewa ita mace ce; idan kuwa suka aikata haka, to sallarsu ta ɓãci da ijma'i. [64]. [62] Bukhari ne ya ruwaito shi daga hadisin Abu Bakra - Allah Ya yarda da shi - a lamba ta (4425). [63] Muslim ne ya ruwaito, a lamaba ta (440). [64] Maratib al-Ijma': (s. 27).

2- Limancin wanda ba shi da tsarki da wanda ke da najasa, alhali ya san da haka, idan mamu ba su san da haka ba har sai da aka idar da sallah, to sallarsu ta inganta, saboda abin da ya zo daga Umar dan Khaddab - Allah ya yarda da shi - «Cewa shi ya yi sallah da mutane alhali yana da janaba, sai ya sake, kuma bai umarce su ba da su sake» [65]. [65] Dara ƙuɗni ne ya ruwaito shi a Sunaninsa, a lamba ta (1371).

Kuma Abdurrahman ɗan Mahdi - Allah Ya yi masa rahama - ya ce: "Wannan shi ne abin da aka haɗu a kansa: Mai janaba zai sake, su kuwa ba za su sake ba, ban san wani saɓani a cikinsa ba"[66]." [66] Sunan ad-Daraqutni: (2/ 188).

3- Limancin wanda bai haddace Fatiha ba, ko bai iya karatunta ba, ko kuma yana haɗa haruffan da ba'a haɗawa a cikinta, kamar wanda yake haɗa Ha'u da Ra'u a cikin faɗinSa Maɗaukaki: Godiya ta tabbata ga Allah, Ubangijin halittu; [al-Fatiha: 2] Domin yana haɗa harafi da wanda ba kamarsa ba, kuma ba kusa da shi ba, ko yana canza harafi da wani, kamar mai canza Ra'i da Ya'i, ko kuma ya yi kuskuren karatu da yake canza ma'ana, to wannan limancinsa ba ya inganta sai da irinsa; saboda gazawarsa ga rukunin sallah, ko kuma ya tauye shi.

4-Limancin dan bidi'a wanda ake kafirta shi saboda bidi'arsa; saboda fadin Allah Madaukaki: Shin, wanda ya zama mũmini yanã kamar wanda ya zama fãsiƙi? Bã zã su yi daidai ba. [al-Sajda: 18], Fasiki a nan shi ne kafiri, kamar yadda yake bayyana daga cikin jerin Ayoyin.

5- Yana haramta a yi limanci a masallacin da yake da limami wanda aka naɗa, don haka ba ya inganta limancin waninsa a gabansa, saidai da izininsa, ko kuma idan ya yi jinkiri da ƙuncin lokaci[67]. [67] A duba: Al-As'ila wal-Ajwiba Al-Fiqhiyya lis-Salman: (163/1).

Matashiya Ta biyar: Waɗanda limancinsu makruhi ne

An karhanta limancin Wadannan:

1- Al-Lahhan: Shi ne mai yawan kuskuren karatu da ba ya canza ma'ana, ko ya kasance a Fatiha ne ko a waninta, kamar idan ya karanta: (Alhamda lillahi) da fataha a kan harfin Dal, to sallarsa ta inganta, kuma an ƙi limancinsa; saboda faɗin Annabi ﷺ: «Yana limantar mutane wanda ya fisu sanin Littafin Allah» [68]. [68] Fitar da shi ya gabata.

Idan kuma kuskure ya canza ma'ana a wanin Fatiha saboda mantuwa ko jahilci ko wata larura a harshensa, to limancinsa ya inganta tare da karhanci; saboda da a ce ya bar karatun wanin Fatiha da limancinsa ya inganta, to haka ma idan ya yi kuskure a cikinta. Idan kuma ya yi shi da gangan to ta ɓaci; saboda shi mai wasa ne a sallarsa.

2- Wanda ke maimaita wasu haruffa, kamar wanda ke maimaita Fa'u, ko Ta'u, ko wasunsu, wannan kuwa domin karin harafi ne a Karatu.

3- Fasiki da Mai Bidi'a wanda ba a kafirta shi ba da bidi'arsa[69]. [69] A duba: Kasshaf al-Ƙina: (1/ 475) da abin da ya biyo bayansa.

4- Limancin wanda mafi yawan jama'arsa ke ƙinsa a kan gaskiya; Daga Abu Umamah - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: «Mutane uku sallarsu ba ta wuce kunnuwansu: Gudajjan bawa har sai ya dawo, da matar da ta kwana mijinta yana fushi da ita, da limamin da mutanensa suke ƙinsa» [70]. [70] Tirmizi ne ya ruwaito shi a lamba ta (360), kuma ya ce: wannan Hadisi ne Hasan Garibi ta wannan fuskar.

Imam Tirmizi ya ce: "Kuma wasu daga cikin malamai sun ƙyamaci mutum ya limanci jama'a alhali suna ƙinsa, idan Liman ba azzalumi ba ne to zunubi na kan wanda ya ƙi shi ne kawai, kuma Ahmad da Ishak sun ce a kan wannan: Idan mutum ɗaya ko biyu ko uku suka ƙi shi, to babu laifi ya yi sallah da su, har sai mafi yawan jama'ar sun ƙi shi"[71]. [71] Sunan Tirmizi: (2/ 192).

To idan sun ƙi shi ne saboda yana himmatuwa wajen bin Sunnah a cikin sallah, sai ya karanta musu surorin da aka sunnanta, kuma ya yi sallah da su cikin natsuwa, to limancinsa a cikinsu ba abin ƙi ba ne; domin sun ƙi shi ne ba bisa hakki ba, don haka ba a la'akari da kiyayyarsu. Yana kamata gare shi idan suna ƙin sa ba bisa hakki ba ya yi musu wa'azi, ya tunatar da su, kuma ya janyo hankalinsu; kuma ya yi sallah da su gwargwadon abin da ya zo a Sunnah, idan kuma Allah Ya san gaskiyar niyyarsa ta haɗa kansu, Allah zai sauƙaƙa masa hakan. [72] A duba: Sharhin Al-Mumti'a ala Zad Al-Mustaqni' (4/ 253).

Sashe na Shida: Inda limami zai tsaya a tare da Mamu.

Abinda yake sunna shi ne liman ya wuce gaban mamu, su kuma masu su tsaya a bayan liman idan sun kasance biyu ko fiye da haka; saboda Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance idan ya tashi sallah yakan wuce gaba, kuma sahabbansa sukan tsaya a bayansa, da kuma abinda ya tabbata. Cewa Jabir da Jabbar -Allah ya yarda da su- dayansu ya tsaya a damansa SAW yana sallah, dayan kuma a hagunsa, sai ya riko hannayensu har ya tsayar da su a bayansa» [73]. [73] Muslim ne ya ruwaito shi a cikin wani dogon hadisi daga Jabir - Allah Ya yarda da shi - a lamba ta (3010).

Kuma namiji guda daya zai tsaya a hannun daman liman, yana daidai da shi (kafada da kafada) saboda faɗin Ibn Abbas - Allah Ya yarda da su -: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya tashi yana sallah, sai na tsaya a hagunsa, sai ya ruko kunnena ya juyar dani a damansa. [74] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (6316), da Muslim, a lamba ta (763).

Kuma mata su kasance a bayan sahun maza; saboda hadisin Anas - Allah Ya yarda da shi -: «Na yi sahu ni da maraya a bayan Annabi -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi-, kuma wata tsohuwa tana bayanmu» [75]. [75] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (380), da Muslim, a lamba ta (658).

Ya kamata liman ya tsaya daidai tsakiyar sahu, Allamah Ibnu Baz -Allah ya yi masa rahama- ya ce: "«Sunna ita ce Liman ya kasance a tsakiya a cikin masallatai, wannan ita ce sunna ta aikace wadda Musulmai suka gudana a kanta» [76]." [76] Sheikh Sa'id Al-Qahtani - Allah Ya yi masa rahama - ne ya kawota daga gare shi a littafin "Al-Imamatu fis-Salah" (shafi na 55).

Kuma ya ce - Allah Ya yi masa rahama -: Ana fara sahu ne daga tsakiya, daga wajen da ke biye da Liman, kuma ɓangaren dama na kowane sahu ya fi na hagu falala, kuma wajibi ne kada a fara wani sahu har sai wanda ke gabansa ya cika.

Matashiya Ta Bakwai: Rigayar Liman

Ya wajaba a kan mamu ya shiga ayyukan sallah bayan limaminsa, kuma ya yi koyi da shi ya kuma bi shi a ayyukansa, kuma daga cikin sha'anin mai bi (mamu) shi ne kada ya riga wanda yake bi, kuma kada ya gwama da shi, sai dai ya lura da yanayinsa sannan ya zo da irin aikinsa a bayansa, kuma abinda hakan ke nufi shi ne kada ya saɓa masa a kowane hali; wannan kuwa saboda abin da ya tabbata daga Abu Huraira, Allah ya yarda da shi, daga Annabi ﷺ cewa lallai ya ce: «Kuma ai an sanya Limami ne don a yi koyi da shi, to kuma kada ku saba Masa, idan ya yi ruku'u, to ku yi ruku'u, kuma idan ya ce: Allah ya ji mai gode masa, to ku ce: Ubangijinmu godiya ta tabbata a gareka, kuma idan ya yi Sujada to ku yi Sujjada, kuma idan ya yi Sallah a zaune, to ku yi sallah a zaune baki dayanku, kuma ku tsayar da sahu a cikin Sallah; domin lalle tsayar da sahu na daga kyawun Sallah» [77]. [77] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (722), da Muslim, a lamba ta (417).

Kuma an haramta riganyar Liman a dukkan rukunnai; Daga Anas ɗan Malik - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya yi mana Sallah wata rana, bayan ya idar da Sallah, sai ya juyo ya fuskance mu da fuskarsa, ya ce: «Yaku mutane, lallai ni ne limaminku, kada ku riga ni yin ruku'u, ko yin sujjada, ko yin tsayuwa, ko yin sallama; domin lallai ina ganinku a gabana da kuma a bayana» Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi - ya ce: "Shin dayanku ba ya jin tsoron idan ya dago kansa kafin liman, Allah Ya maida kansa kan jaki ko Allah Ya maida surarsa surar jaki" [79]. [78] Muslim ne ya ruwaito shi a lamba ta (426). [79] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (691), da Muslim, a lamba ta (427).

Duk wanda ya yi kabbarar harama kafin limaminsa, to sallarsa ba ta kullu ba; saboda sharadinta shi ne ya yi ta bayan limaminsa, kuma hakika ta kubuce masa.

Matashiya Ta Takwas: Hukunce-Hukunce Daban daban game da limanci da sallar jam’i

Wasu hukunce-hukunce da suka shafi limanci da sallar jam’i, ban da waɗanda suka gabata:

1- An so a gabatar da ma'abota hankali da falala baligai a bayan liman kusa da shi; saboda faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: «Su biyo ni daga cikinku, wadanda suka balaga da ma'abota da hankali, sannan waɗanda suke biye musu, sannan waɗanda suke biye musu» [80]. [80] Muslim ne ya ruwaito shi daga hadisin Abdullahi bn Mas'ud - Allah Ya yarda da shi - a lamba ta (432).

2- Kwaɗayi a kan sahun farko: Ana so ga mamu su yo gaba zuwa sawun farko su yi kwadayin sa, kuma su kiyayi yin jinkiri daga gare shi; Daga Abu Sa’id Al-Khudri - Allah Ya yarda da shi -, cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ga a cikin sahabbansa wani jinkiri, don haka ya ce musu:

«Ku gabato, ku yi koyi da ni kuma waɗanda ke bayanku su yi koyi da ku, mutane ba za su gushe ba suna ja baya har sai Allah Ya jinkirtar da su» [81]، Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Da mutane sun san abin da ke cikin kiran sallah da sahun farko, sannan ba za su samu ba sai sun yi ƙuri'a a kan sa; to, da sun yi ƙuri'ar» [82], Kuma ma'ana: «da sun yi ƙuri'a a kansa» Wato: da sun jefa ƙuri'a a tsakaninsu a kan wanene zai tsaya a sahun farko. [81] Muslim ne ya ruwaito shi, a lamaba ta (438). [82] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (615), da Muslim, a lamba ta (437).

Amma mata, an so su tsaya a sahun baya, daga Abu Hurairah, Allah ya yarda da shi, ya ce: Manzon Allah -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Mafi alherin sahun maza shi ne na farkon su, kuma mafi sharrin su shi ne na ƙarshen su, mafi alherin sahun mata shi ne na ƙarshen su, kuma mafi sharrin su shi ne na farkon su" [83]. Kuma wannan an ɗora shi ne a kan idan suna sallah a bayan maza ba tare da wani shamaki ba, amma idan suna sallah a wani wurin sallah da aka suturta daga maza, to sai su cika sahu na farko sannan na farko [84]. [83] Muslim ne ya ruwaito, a lamaba ta (440). [84] A duba: Majmu'u fatawa Bin Baaz (196/ 12).

3- Ya kamata ga liman ya kauce wa gaggawa wajen Karatun Fatiha, ya kuma bi a hankali, domin mamu ya samu damar karanta ta[85]. [85] A duba: Al-Minzar, a bayyana kurakurai da dama da suka yadu, na Salih Al Shaikh, shafi (53).

4- Sallar mutum shi kaɗai a bayan sahu ba ta inganta ba; an karɓo daga Wabiṣa ɗan Ma'abad - Allah ya yarda da shi - cewa wani mutum ya yi sallah a bayan sahu shi kaɗai, sai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya umurce shi da ya maimaita salla[86]. [86] Tirmizi ne ya ruwaito shi (230), kuma ya ce: Hadisin Wabisa hadisi ne kyakkyawa.

MATASHIYA TA TARA: Sunnonin da ya kamata Liman ya tsayar da su.

Ya kamata ga Liman ya kasance mai koyi da sunnar Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a cikin limanci, kuma daga cikin waɗannan sunnoni:

1- Ya sauƙaƙa a sallarsa, kuma ya kiyaye yanayin mutane, wato liman ya bi a hankali a cikin sallarsa, bai halatta liman ya yi gaggawa a sallah ba ta yadda masu ibada ba za su samu damar zuwa da rukunan sallah da wajibanta ba, kuma ya bi a hankali a karatunsa ta yadda waɗanda ke bayansa daga cikin masallata za su samu damar cika sallarsu, Daga Abu Mas'ud Al-Ansari - Allah Ya yarda da shi - wani mutum ya ce: Na rantse da Allah, ya Manzon Allah, lallai ina jinkiri a sallar safiya -wato sallar Asuba- saboda tsawaitawar da wane yake yi mana. Don haka ban ga Manzon Allah ﷺ ba a wata huduba da ya fi tsananin fushi kamar a wannan rana, sannan ya ce: «Lallai daga cikinku akwai masu korar mutane, don haka duk wanda daga cikinku ya yi sallah da mutane, to ya sassauta; domin daga cikinsu akwai mai rauni, da tsoho, da mai bukata». [87]. [87] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (90).

2- Ya yi umarnin daidaita sahu da tattoshe kafofi kafin a shiga sallah; saboda aikinsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - da kuma umarninsa ga masu yin sallah da yin haka. Daga Nu'umanu ɗan Bashir - Allah ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi- ya kasance yana daidaita sahu, har kace yana jera tukwane ne, har sai idan ya ga lallai mun fahimce shi, sannan ya fito wata rana sai ya tsaya, sai da ya kusa ya yi kabbara, sai ya ga wani mutum kirjinsa ya fito daga cikin sahun, sai ya ce: "Ya bayin Allah, ko dai ku daidaita sahunku, ko kuma Allah ya saba tsakanin fuskokinku." [88]. [88] Bukhari ne ya ruwaito shi (717), da Muslim (436), kuma lafazin na Muslim ne.

Imamu Annawawi Allah ya masa rahama ya ce: "Al-Qidahu, da kasra a Ƙafun, su ne sandunan kibau yayin da ake sassaƙa su kuma ake gyara su, ma'anarsa: Ana tsanantawa wajen daidaita su har su zama kamar ana miƙar da kibau da su; saboda tsananin miƙewarsu da daidaituwarsu"[89]. [89] Sharhin Al-nawawi na Muslim: (4/ 157).

3- Ya umarce su da cika sawun farko, sannan wanda ke biye da shi, idan kuma aka samu tawaya, to ta zama a cikin sahun ƙarshe; saboda faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: «Shin bakwayi sahu ba kamar yadda mala'iku suke yin sawu a wajen Ubangijinsu ba!?» Sai muka ce: Ya Manzon Allah, yaya mala'iku suke yin sawu a gaban Ubangjinsu!? Ya ce: «Suna cika sahu na farko ne, kuma suna matsawa a cikin sahu» [90]. [90] Muslim ne ya ruwaito shi daga hadisin Jabir bn Samura - Allah Ya yarda da shi - a lamba ta (430).

4- Ya yi koyi da Annabi ﷺ a karatunsa a cikin Sallah, domin mafi yawan karatunsa ﷺ ya kasance yana karantawa a sallar Asuba cikin dogayen Mufassal, a Magariba kuma cikin gajerun Mufassal, sannan a sallar Isha da Azahar da La'asar cikin tsakatsakin Mufassal. Daga Sulaiman bn Yasar, daga Abu Huraira - Allah ya yarda da shi - ya ce: «Ban yi sallah a bayan wani ba wanda sallarsa ta fi kama da ta Manzon Allah ﷺ ba, sama da wane, Sulaiman ya ce: Ya kasance yana tsawaita raka’o’i biyu na farko na Azahar, kuma yana sassauta sauran biyun, kuma yana sassauta La’asar, kuma yana karatu a Magariba da gajerun surori na Mufassal, kuma yana karatu a Isha’i da matsakaitan surori na Mufassal, kuma yana karatu a Asuba da dogayen surori na Mufassal.» [91]. [91] Nasa’i ne ya ruwaito shi, a lamba ta (982), Al-Hafiz ya ce a cikin Bulughul Maram a lamba ta (286): Isnadinsa sahihin ne.

Dogayen Mufassal: Daga Suratul Hujurat zuwa Suratul Buruj, amma matsakaitan kuwa: daga Suratul Buruj zuwa Suratul Bayyinah, amma gajerun kuwa: daga Suratul Bayyinah har zuwa ƙarshen Alƙur'ani[92]. [92] A duba: Mirqat al-Mafatih (2/ 700).

Matashiya Ta Goma: Ginshikan Liman

Ana lissafa Limamin masallaci shi ne ginshikinsa da karfinsa, ta hanyarsa ne masallaci ke isar da sakonsa na yada Da’awah da wayar da kan al'umma, da kuma haskaka wa mutane al'amuran addininsu. Idan Limami ya kasance masani, mai hankali, mai kaifin basira, kuma masanin al'adun mutane da halayensu, to tasirinsa zai zama mai kyau da amfani ga jama'ar masallaci, da kuma mazauna unguwar da masallacin yake, yana koya musu da shiryar da su kuma yana jagorantar su zuwa ga dukkan alheri da daraja.

Kuma haka abin ya kasance ga limamai waɗanda suka cika sharuɗɗan limanci; a farkon Musulunci Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - shi ne Limami, sannan halifofinsa shiryayyu, sannan sarakuna da jagorori da malamai da fitattun mutane. Wannan kuwa yana nuni da cewa ya wajaba wanda zai riƙi wannan aiki ya kasance a matsayi madaukaki ta fuskar addini da ɗabi'a da ilimi da kuma hali.

A nan ne ! Muhimmancin wannan aiki yake bayyana a rayuwar mutane; saboda ƙarfin limamai yana bayyana a kan al'ummominsu, haka kuma rauninsu tasirinsa yana bayyana a cikin waɗannan al'ummomin; domin masallaci shi ne ke koyar da al'umma haɗa magana da aiki, idan har liman ya kasance mai ƙarancin ilimi ko hankali, ko mummunan hali da ɗabi'a, to lallai zai yi illa ne ba zai amfanar ba, kuma idan har yana daga cikin aikin liman ya shiryar da masu sallah zuwa ga alheri da kyautatawa da salihanci, to zai yi wahala ga limami jahili ya cimma wannan babban aiki mai girma.

Wani lokaci liman na iya zama ya cika sharuddan wannan aiki ta fuskar ilimi da kwarewa, saidai wasu ayyuka daban su shagaltar da shi daga aikinsa wanda hakan ke shafar yadda yake gudanar da shi, sai ya rika zuwa a makare akan lokutan tada sallah, kuma ba ya samun isasshen lokaci na yin muraja’ar surori ko ayoyin da yake karantawa a sallah; a dalilin haka sai a gan shi yana sallah da wasu takamaiman surori ko ayoyi da ba ya wuce su.

Kuma wani lokacin son rai ko jahilci ko rigingimu ko tsattsauran ra'ayi abin zargi na iya rinjayarsa, sai ya fita daga tsakaitawa da shiryarwa ta tarbiyya da kira da hikima da wa'azi mai kyau.

Kuma lallai masallaci yana da babban tasiri a cikin wannan addini; domin shi hasumiyar shiriya ne wanda bawa yake haɗuwa da Ubangijinsa a ciki, kuma imaninsa yana ƙaruwa, kuma yana haɗuwa da 'yan'uwansa domin kowa ya taimake juna wajen yaɗa kyawawan ɗabi'u da yaƙar munanan ayyuka, kuma Masallacin ba zai iya yin hakan ba, sai fa idan Allah Ya datar da shi da limamin da ya cika siffofin ilimi da na ɗabi'u waɗanda ake buƙata ga duk wanda zai riƙe wannan babban matsayi, kuma ya aiwatar da ayyukan wannan aiki mai girma.

Muhimman Ginshikai na Ilimi da ya kamata a samu a wajen Liman:

1 - Tsarkake aiki domin Allah; domin ya zama aka karfafa wanda aka kuma taimaka, wanda aka ba nasara, karɓaɓɓe, kuma abin so a wajen Allah da kuma wajen mutane.

2 - Nisantar riya da alfahari; domin al'amura da manufofinsu suke, kuma ayyuka sai da niyya, kuma lalle ne ga kowane mutum akwai abin da ya yi niyya. Wanda ya yi ado da abin da ba nasa ba, Allah zai tozarta shi.

3- Ya zama mahaddacin Alkur’ani mai girma, ko kuma ya haddace gwargwadon abinda ya sawwaka, kuma ya dawwama a kan bitar abin da ya haddace, kuma ya kasance da wuridin yau da kullum na karatun Alkur'ani.

4 - Ya haddace adadi na Hadisan Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi), daga Riyadus Salihin, ko Arba'una an-Nawawiyya, ko daga Bulughul Maram, ko waninsu daga ingantattun littattafan Hadisi.

5- Ya koyi sanin AƘIDA INGANTACCIYA, aƙidar magabata shiryayyu.

6 - Ya koyi Fikihu a hukunce-hukuncen addini, musamman ma fikihun ibada, da abinda ya shafi Tsarki, da Sallah, da Zakkah, da Azumi, da kuma fikihun mu'amaloli; don ya san ka'idojin neman arziki da kashe shi, ya kuma gargaɗi mutane daga zamba da yaudara da cin dukiyar mutane a kan ba-zata, ya kuma gargaɗe su haka nan daga wuce gona da iri da almubazzaranci, da kuma rowa da maƙo, ta yadda ayyukansu na dukiya za su kasance bisa ga Alkur'ani da Sunnah.

7- Ya ƙware a harshen larabci domin ya san ma'anonin abin da Allah Ya saukar a kan Manzonsa ﷺ, domin lalle Alkur'ani da harshen larabawa ya sauka.

8 - ya karanta Tarihin Annabta, da kyawawan ɗabi'un Annabi Muhammad -tsira da amincin Allah su tabbata agare shi- da tarihin magabata na gari; domin a cikinsu akwai abin koyi na gari, da kyakkyawan misali, da taskar ilimi mai amfani, da kuma ilimin addinin Musulunci mai zurfi.

9- Ya san malaman kasarsa da sauran malaman masu zurfi cikin ilimi, waɗanda aka san su da ingantacciyar Akida da Ilimi da hankali, kuma ya koma zuwa garesu a cikin dukkan abin da yake buƙata na mas'alolin Addini da warware matsalolin al'ummarsa.

10- Ya san ƙungiyoyin Musulunci da akidunsu, da tsare-tsaren tunani da manufofinsu, da mazhabobi masu rushe addini da manufofinsu, har ya samu damar yin nazari akan su a bisa hasken littafin Allah Ta'ala da Sunnar Manzonsa ﷺ da kuma abin da tabbatattun malaman Musulunci suka rubuta, ya kuma warware ƙaryarsu, kuma ya yi gargaɗi daga batansu.

11- Ya san kafofin yaɗa labarai daban-daban, ya kuma san amfaninsu da illolinsu, da yadda zai amfana da su wajen yin kira zuwa ga Allah, kuma ya kiyaye daga haɗurran da ke cikinsu ga kansa da al'ummarsa.

Kuma idan waɗannan ginshiƙai suka tabbata ga limamin masallaci, to hakan zai haifar da istiƙama da daidaito, da izinin Allah Ta'ala.

Kuma mafi muhimmancin ginshiƙai na Halayya:

1- Ya kamata ga Limamin Massallaci ya zama mai kira kuma malami ga jama'ar massallacinsa da ma'abutansa da masu zuwa Masallacin cikin mutanen unguwa da waninsu, don hakan wajibi ne, Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya zama abin koyinsa; domin shi ne abin koyi nagari, da abin kwaikwayo kyakkyawa, kuma mafi ɗaukakar misali ga al'umma da shugabanni, Allah Maɗaukaki Ya ce: Lalle, abin kõyi mai kyau ya kasance gare ku daga Manzon Allah, ga wanda ya kasance yanã fãtan rahamar Allah da Rãnar Lãhira, kuma ya ambaci Allah da yawa. [al-Ahzab: 21].

Kuma ya nisantar da kansa da ma'abota masallacinsa daga maganar duniya da siyasa, kuma ya sanya masallaci ya zama kebantacce ga ilimi da ibada.

2- Ya zama mai tsafta, tsararre a kansa, kuma ya kula haka nan da tsaftar masallaci, da jera kayayyakinsa da tsara su, da kiyaye kayan amfaninsa, kuma ya nisanci barna a cikin haka, kuma ya guji yi wa masallaci ado.

3- Ya zama mai kyawun shiriya da kamanni, mai riƙo da Sunnar Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, na sakin gemu da rage gashin baki, tare da nisantar jan tufa, kuma ya lazimci kamala da natsuwa, kuma ya zama mai bin sawun magabatan kwarai da suka gabata, Allah Ya yi musu rahama.

4- Ya kasance mai sauƙi, mai haƙuri, mai tausayi; domin lallai sauƙi ba ya kasancewa a cikin komai face ya ƙawata shi, kuma ba a cire shi daga komai ba face ya aibanta shi, kamar yadda ya zo a hadisi; an ruwaito daga Nana Aisha -Allah ya yarda da ita- daga Annabi -tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi- ya ce: Lalle sassauci ba ya kasance wa a komai sai ya ƙara masa kyau, kuma ba a cire shi a komai sai ya aibanta shi. [93]. [93] Muslim ne ya ruwaito shi a lamba ta (2594).

Idan wani daga cikin masallata ya yi kuskure, to bai kamata Liman ya tsawata masa ba, sai dai ya yi masa nasiha da sauƙi; kuma ya sanar da shi da kyakkyawa; Daga Mu'awiyah Bin Hakam AsSulami - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Wata rana ina sallah tare da manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, sai wani mutum daga cikin mutane ya yi atishawa, sai na ce: Allah Ya yi maka rahama, sai mutane suka kalleni da idanuwansu, sai na ce: Ya yi wabin mahaifiyarsa, me ya sameku ne kuke kallona? sai suka buga hannayensu akan cinyoyinsu, lokacin da na ga suna ƙoƙarin sani in yi shiru sai na yi shirun, lokacin da manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya idar da sallah, fansarsa babana da babata, ban taɓa ganin malami ba kafinsa ko abayansa mafi iya koyarwa sama da shi, na rantse da Allah bai yi min tsawa ba -wato: bai yi min fin karfi ba kuma bai tsawatar min ba- bai dake ni ba, bai zageni ba. Ya ce: "Lalle wannan sallar babu wani abu da yake inganta a cikinta na zancen mutane, kadai ita ce tasbihi da kabbara da karatun AlKur'ani". [94]. [94] Muslim ne ya ruwaito shi a lamba ta (537).

5- Ya kasance mai laushi da taushin zuciya; domin ya tara mutane a kewayensa su amfana da sauƙinsa, da taimakonsa da iliminsa, kuma ya tsaya tare da su a cikin masifunsu da buƙatunsu, kuma yana kamata ya shawarce su a kan abin da ya shafi ayyukan masallaci.

Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kasance a matsayi mafi ɗaukaka a kan wannan duka, kamar yadda Allah - Maɗaukakin sarki - Ya faɗa game da shi: Sabõda wata rahama ce daga Allah ka yi sanyin hali a gare su. Kuma dã kã kasance mai hushi mai kaurin zuciya, dã sun wãtse daga gẽfenka. Sai ka yãfe musu laifinsu, kuma ka nẽma musu gãfara, kuma ka yi shãwara da su a cikin al'amarin. Sa'an nan kuma idan ka yi niyyar zartarwa, to, ka dõgara ga Allah, lalle ne, Allah Yana son mãsu tawakkali. [Aal- Imran: 159].

6- Ya zama mai haƙuri da yakini, da gaskiya a cikin abinda yake faɗa, domin ya cancanci darajar limanci a cikin masallacinsa da tsakanin jama'arsa; lallai haƙuri da yakini suna kai bawa zuwa ga matsayin limanci a cikin addini, Allah maɗaukakin sarki ya ce: Kuma Mun sanya shugabanni daga cikinsu, sunã shiryarwa da umurnin Mu, a lõkacin da suka yi haƙuri, kuma sun kasance sunã yin yaƙĩni da ãyõyin Mu. [al-Sajda: 24].

7- Ya wajaba ya zama mai gaskiya a cikin abinda yake faɗa, ko ya kasance hakan a cikin huɗubar Juma'a, ko a darasin koyarwa da wa'azi, ko a cikin maganarsa da mutane; domin ya zama daga cikin masu gaskiya, da shiryayyu, da masu rabauta; domin hakika an samo a Hadisi daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - cewa ya ce: "Na hore ku da gaskiya, saboda gaskiya tana shiryarwa zuwa ga aikin alheri, kuma lallai aikin alheri yana shiryarwa zuwa ga Aljanna, kuma mutum ba zai gushe ba yana yin gaskiya, kuma yana kirdadon gaskiya har sai an rubuta shi a wajen Allah mai yawan gaskiya ne, kuma na haneku da ƙarya, saboda ƙarya tana shiryarwa ne zuwa ga fajirci, kuma fajirci yana shiryarwa ne zuwa ga wuta, kuma mutum ba zai gushe ba yana yin ƙarya kuma yana kirdadon ƙarya har sai an rubuta shi a wajen Allah mai yawan ƙarya." [95]. [95] Bukhari ne ya ruwaito shi (6094), da Muslim (2607), daga hadisin Abdullahi ɗan Mas’ud - Allah Ya yarda da shi -.

Kuma ƙarya sharri ce kuma bala'i, kuma mafi girman ƙarya ita ce ƙarya ga Allah - Maɗaukakin sarki - da kuma faɗa a kanSa ba tare da ilimi ba, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: Ka ce: "Abin sani kawai, Ubangijina Yã hana abũbuwanalfãsha; abin da ya bayyana daga gare su da abin da ya ɓõyu, da zunubi da rarraba jama'a, bã da wani hakki ba, kuma da ku yi shirki da Allah ga abin da bai saukar da wani dalĩli ba gare shi, kuma da ku faɗi abin da ba ku sani ba, ga Allah. [al-A'araf: 33].

To wannan aya mai girma ta tattara mafi girman zunubai, ta fara daga mafi ƙanƙanta zuwa ga mafi girma, wanda shi ne faɗa ga Allah ba tare da ilimi ba a cikin sunayenSa da siffofinSa da kuma shari'arSa.

Kuma karya ga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - na daga cikin mafi girman karya kuma mafi munin zunubbai, kuma yana daga cikin manyan zunubbai wanda aka yi wa ma'abocinsa wa'idin wuta; Daga Mughira ɗan Shu'bah - Allah ya yarda da shi - ya ce: Na ji Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - yana cewa: «Lallai yi mini karya ba kamar yi wa wani karya ba ne, Wanda ya yi mini karya da gangan, to ya tanadi masaukinsa a wuta» [96]. [96] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (1291), da Muslim a lamba ta (4).

Kuma ya nisanci karya koda kuwa ta kasance da kyakkyawan Niyya ce don manufar kwadaitarwa a kan alkhairi da kuma tsoratarwa daga sharri, kamar yadda wasu masu Wa'azi suke aikatawa; domin shi Muni ne babu alkhairi a cikinsa kuma babu shiriya, kuma mai faɗarsa mai ɗaukar zunubi ne, ba mai samun lada ba ne, kuma mai laifi ne ba mai cin riba ba.

8- Ya kasance mai amana wajen nakalto magana, kuma ya tabbatar da ingancin labarai, kada ya yi gaggawa wajen karɓar jita-jita, kada kuma ya dogara sai da magana amintacciya, kuma haƙiƙa Allah Maɗaukaki ya umurce mu da hakan a cikin faɗinSa: Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Idan fãsiƙi Yã zo muku da wani babban lãbãri, to, ku nẽmi bayãni, dõmin kada ku cũci waɗansu mutãne a cikin jãhilci, sabõda haka ku wãyi gari a kan abin da kuka aikata kunã mãsu nadãma. [al-Hujurat: 6].

9- Ya dage wajen suturta mutane, kuma ya ɓoye asirinsu, domin wanda ya suturta wani musulmi Allah Zai suturta shi a duniya da lahira, kuma duk wanda ya bibiyi al'aurar musulmai, Allah Zai bibiyi al'aurarsa har sai Ya tone shi ko da a cikin tsakiyar gidansa ne; an karɓo daga Abdullahi ɗan Umar, Allah Ya yarda da su, cewa lallai Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Wanda ya suturta wani musulmi Allah Zai suturta shi ranar Alƙiyama" [97]. Daga Abu Burzata Al-Aslami - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Ya ku jama'ar da ya yi imani da harshen sa kuma imani bai shiga zuciyarsa ba, kada ku yi wa musulmai gulma, kuma kada ku bibiyi al'aurorinsu; saboda duk wanda ya bibiyi al'aurorinsu, to Allah Zai bibiyi al'aurarsa, kuma duk wanda Allah Ya bibiyi al'aurarsa, sai Ya kunyatashi a cikin gidansa» [98]. [97] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (2442), da Muslim, a lamba ta (2580). [98] Abu Dawud ne ya rawaito shi, a lamba (4880), kuma game da waɗannan ginshiƙai a duba littafin Imamul Masjid Muqawwamatuhu al-Ilmiyya wal-Khulqiyya na Sheikh Sa'ud bin Muhammad al-Bashar.

Babi Na Uku: Sallar Juma'a da Hudubar ta

Matashiya Ta FARKO: Sallar Juma'a

Mas'ala ta farko: Ma'anar sallar Juma'a da lokacinta:

Na farko: Ma'anar sallar Juma'a:

Juma'a: Wata rana ce daga cikin ranakun mako, wadda ake yin wata Sallah ta musamman a cikinta, wato Sallar Juma'a [99]. [99] A duba: Mu'ujamu Lugatil Fukaha' na Muhammad Rawas Qal'aji da wasu (166).

Kuma shiriyar da Allah Ya yi wa wannan al'umma zuwa ga ranar Juma'a falala ce mai girma; daga Abu Hurairah - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Mune na ƙarshe, masu rigaya ranar Alkiyama, sai dai cewa su an ba su Littafi gabaninmu, mu kuma an ba mu shi a bayansu, kuma wannan ita ce ranarsu wadda aka farlanta a kansu sai suka yi saɓani a cikinta, sai Allah Ya shiryar da mu zuwa gare ta. Don haka su mabiyanmu ne a cikinta; Yahudawa gobe, da Nasara jibi» [100]. [100] Bukhari ne ya ruwaito shi a lamba ta (876), da Muslim a lamba ta (855).

Kuma Ranar Juma'a ita ce mafi alherin yini da rana ta fito a cikinsa; an karɓo daga Abu Huraira - Allah ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Mafi alherin yini da rana ta futo a cikin shi, shi ne yinin ranar Jumu'a: a cikinta ne aka Halicci Annabi Adam, kuma a cikinta aka shigar da shi Aljanna, Kuma a cikinsa aka futar da shi daga cikinta" [101]. [101] Muslim ne ya ruwaito shi a lamba ta (854).

Kuma Juma'a zuwa Juma'a kaffara ce ga abin da ke tsakaninsu; saboda hadisin Abu Huraira, Allah ya yarda da shi, cewa Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kasance yana cewa: «Salloli biyar, da Jumu'a zuwa Jumu'a, da Ramadan zuwa Ramadan, suna kankare zunuban da ke tsakaninsu, matukar an nisanci Manyan Zunubai» [102]. [102] Muslim ne ya ruwaito shi, a lamaba ta (233).

Sallar Juma'a: Sallah ce mai zaman kanta, tana sabawa sallar Azahar a wajen adadin (raka'o'i), da bayyanar (da karatu), da khuduba, da sharuda ababan lura a gareta, tana kuma dacewa da ita a lokaci.

Na biyu: Lokacin sallar Juma'a:

Lokacin Juma'a shi ne lokacin azahar, daga bayan karyawar rana har sai inuwar abu ta zama daidai da tsawonsa; saboda hadisin Anas bn Malik - Allah ya yarda da shi - cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kasance yana sallar Juma'a a lokacin da rana ta karkata [103]. Wato: ta karkata zuwa yamma, kuma ta gushe daga tsakiyar sama, kuma shi ne lokacin sallar azahar. [103] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (904).

Mas'ala ta biyu: Hukuncin sallar Juma'a, kuma a kan wa ta wajaba?

Na farko: Hukuncin sallar Juma'a:

Sallar Juma'a farilla ce ta aini akan maza; saboda faɗinSa - tsarki ya tabbata a gare Shi -: Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Idan an yi kirã zuwã ga sallah a rãnar Jumu'a, sai ku yi aiki zuwa ga ambaton Allah, kuma ku bar ciniki. Wancan ɗinku ne mafi alhẽri a gare ku idan kun kasance kunã sani. (Al-Jumu'ah ta: 9), Daga Abdullahi ɗan Umar da kuma Abu Huraira - Allah Ya yarda da su - cewa su sun ji manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbat agare shi - yana faɗa akan minbarinsa: «Lallai wasu mutane kodai su hanu daga barinsu -wato: barinsu- Juma'o'i, ko Allah Zai yi yumƙi akan zukatansu, sannan zasu kasance daga marafkana» [104]. [104] Muslim ne ya ruwaito shi a lamba ta (865).

Haƙiƙa Musulmai sun yi ijma'i akan wajabcin sallar Juma'a, Ibnul Munzir Allah Ta'ala ya yi masa rahama ya ce: "Kuma sun yi ijma'i akan cewa sallar Juma'a wajiba ce akan 'ya’ya balligai mazauna gari waɗanda ba su da wani uzuri" [105]. [105] al-Ijma'i: (sh. 40).

Na biyu: A kan wa ta wajaba?

Juma'a tana wajaba akan kowanne musulmi namiji ɗa baligi mai hankali, mai ikon zuwanta, mazauni; don haka bata wajaba akan: bawa da ake mallaka, ko mace, ko yaro, ko mahaukaci, ko majiyyaci, ko matafiyi. Dalilin hakan kuwa shi ne, abin da Tarik ɗan Shihab -Allah ya yarda da shi- ya rawaito, daga Annabi ﷺ ya ce: «Sallar Juma'a hakki ce wajibi akan kowanne musulmi a jam'i, sai dai mutum hudu: bawa da ake mallaka, ko mace, ko yaro, ko mara lafiya» [106]. [106] Abu Dawud ne ya rawaito shi, a lamba (1067).

Shi kuwa matafiyi, Juma'a ba ta hau kansa ba; saboda Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - bai kasance yana yin ta ba a tafiye-tafiyensa. Kuma lalle ranar Arfa ta dace da ranar Juma'a a Hajjinsa, duk da haka ya yi sallar Azahar ne kuma ya hada La'asar tare da ita.

Ibnul Munzir - Allah ya yi masa rahama - ya hakaito Ijma'i a kan haka, sai ya ce: "Kuma sun yi ijma'i akan cewa Juma'a ba ta hau kan yaro ba, kuma ba ta kan mata ba...Kuma sun yi ijma'i akan cewa Juma'a wajiba ce akan 'yantattu, baligai, mazauna gari, waɗanda ba su da wani uzuri"[107]. [107] al-Ijma'i: (Shafi na: 40).

Kuma idan Bawa da ake mallaka, ko Mace, ko Yaro, ko Mara lafiya, ko Matafiyi ya halarce ta, to ta inganta a gare shi, kuma ta isar masa daga sallar Azzahar.

Sallar Juma'a bata wajaba ba akan Badawa (mutanan kauye) waɗanda suke tafiye-tafiye don neman wurin kiwo da ruwa; domin Badawa a zamanin Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi sun kasance a kewayen Madina, kuma Annabi tsira da amincin Allah su tabbata agare shi bai umarce su da Juma'a ba, kuma Imam Ahmad ya ce: Babu Juma'a akan 'yan ƙauye; domin suna tashi. Saboda haka dalilin faɗuwarta akan su yin tashi, don haka duk wanda ya kasance mazauni ne ba ya tashi da zaɓin kansa to yana daga cikin 'yan gari [108]. [108] Majmu al-Fatawah: (166/24).

Kuma Juma'a tana tabbata da mutum uku: ɗaya yana huɗuba, da biyu suna sauraro; saboda faɗin Allah Ta'ala: ...ku yi aiki zuwa ga ambaton Allah... [al-Juma'a: 9] Kuma wannan jam’i ne, mafi ƙarancin jam’i kuma uku ne.

Na uku: Yadda ake sallar Juma'a:

Sallar Juma'a raka'a biyu ce, ana bayyanar da karatu a cikinta; domin Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya kasance yana aikata haka, kuma malaman ilimi sun yi ijma'i a kan hakan. Ibn Hazm Allah ya yi masa rahama ya ce: "Sun yi ijma'i a kan cewa lallai Juma'a -idan aka gudanar da ita a kan sharruɗɗanta- raka'o'i biyu ce da ake bayyana karatu a cikinsu" [109]. [109] Maratib al-Ijma': (sh. 33).

Kuma Sunnah ce a karanta Fatiha da Suratul A'ala a raka'a ta farko, a ta biyu kuma Fatiha da Suratul Ghashiyah; domin an karbo daga Nu'uman dan Bashir, Allah ya yarda da su, yace: Manzon Allah ﷺ ya kasance yana karantawa a Sallar Idi biyu da kuma ta Juma'a: Suratul A'ala, da kuma Suratul Ghashiyah. [110] Muslim ne ya ruwaito shi a lamba ta (878).

Ko kuwa ya karanta a raka'ar farko da Fatiha da suratul Jumu'ah, a ta biyu kuma da Fatiha da suratul Munafiqun; An karbo daga Ibnu Abi Rafi' ya ce: Marwan ya wakilta Abu Huraira a kan Madina, kuma ya fita zuwa Makka, sai Abu Huraira ya yi mana limancin Jumu'a, sai ya karanta bayan suratul Jumu'ah, a raka'a ta karshe: Idan munafukai suka zo maka, ya ce: Sai na riski Abu Huraira a lokacin da ya idar, sai na ce masa: Lalle ka karanta da surori biyu waɗanda Aliyu ɗan Abi Talib ya kasance yana karanta su a Kufa, sai Abu Huraira ya ce: «Lallai na ji Manzon Allah -tsira da amincin Allah- yana karantawa da su a ranar Juma'a» [111]. [111] Muslim ne ya ruwaito shi a lamba ta (877).

Mas’ala Ta huɗu: Da me ake riskar Juma'a?

Ana riskar Juma'a da riskar raka'a ɗaya tare da liman; domin an karɓo daga Abdullahi ɗan Umar, Allah Ya yarda da su, cewa lallai Annabi ﷺ ya ce: «Wanda ya riski raka'a ɗaya daga cikin Jumu'a ko waninta, to, hakiƙa sallarsa ta cika» [112]. [112] Nasa’i ne ya ruwaito shi a lamba ta (557).

Kuma idan ya riski mafi ƙaranci daga raka'a ɗaya sai ya sallace ta azahar [113]. [113] A duba: "al-Mughni na Ibnu Ƙudama" (2/231).

To wanda raka'a ɗaya ta wuce masa a sallar Juma'a, kuma ya riski liman a raka'a ta biyu a yayin ruku'unsa ko kafin shi, to zai rama raka'a ɗaya kawai, saboda hadisin: «Wanda ya riski raka'a ɗaya, to, hakiƙa ya riski sallah» [114]. [114] Abu Dawud ne ya ruwaito shi, a lamba (893).

Mas'ala ta biyar: Abinda aka haramta ko aka hana aikatawa a ranar Juma'a:

1- Zance yana haramta, alhali liman yana huɗuba, saboda abin da ya tabbata daga Abu Huraira Allah ya yarda da shi cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Idan ka ce wa abokinka: Yi shiru, a ranar Juma'a, a lokacin liman yana huɗuba, to, haƙiƙa ka yi zance mara anfani» {115} Wato: ka yi lagawu, shi ne: magana batacciya korarriya, kuma falalar Juma'arka ta baci. [115] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (934), da Muslim, a lamba ta (851).

Annawawi Allah ya masa rahama ya ce: "A cikin Hadisin akwai hani kan kowane nau'in zance a lokacin huɗuba, kuma da wannan aka yi tanbihi akan waninsa; domin idan aka ce: Yi shiru, wanda a asali umarni ne da kyakkyawa, amma aka kira shi wasa, to balle zancen da bai kai shi ba."[116]." [116] Sharhin Muslim: (6/ 138).

Kuma yana shiga cikin hani daga yin zance: gaishe da mai atishawa, da amsa sallama, bai halatta ba alhali liman yana huɗuba. Amma kafin mai huɗuba ya fara huɗubar, da kuma lokacin shiru tsakanin huɗuba biyu, to babu laifi a cikin zance.

Amma maganar mamu da mai huɗuba, babu laifi a ciki, daga Anas ɗan Malik - Allah Ya yarda da shi - ya ce: «Cewa wani mutum ya shiga masallaci a ranar Juma'a ta wata ƙofar da ta kasance daura da gidan hukunci, alhali Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - yana tsaye yana huɗuba, sai ya fuskanci Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - a tsaye, sannan ya ce: Ya Manzon Allah, dukiyoyi sun halaka, hanyoyi sun yanke, ka roƙa mana Allah Ya shayar da mu, sai Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ɗaga hannayensa...» Hadisin [117]. [117] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (967), da Muslim a lamba ta (897).

2- Kuma wasa yana haramta alokacin huɗuba, da taɓa tsakuwa, ko amfani da carbi, ko shagaltuwa da wayar salula, da makamantansu; saboda abinda ya tabbata daga Abu Huraira - Allah ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Wanda ya taɓa tsakuwa to haƙiƙa ya yi lagawu" [118]. Wannan kuwa saboda wasa yana hana fahimta da khushu'i. [118] Muslim ne ya ruwaito shi a lamba ta (857).

3- An haramta tsallaka wuyan mutane a lokacin Huɗuba; saboda hadisin Abdullahi ɗan Busr -Allah ya yarda da shi- ya ce: Wani mutum ya zo yana tattaka wuyan mutane ranar Jumu'a, alhali Annabi -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi- yana huɗuba, sai Annabi -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi- ya ce da shi: «Ka zauna hakika ka cutar» [119]. [119] Abu Dawud ne ya ruwaito shi, a lamba (1118).

Wannan kuwa saboda a cikin ƙetare mutane akwai cutarwa ga masallata, da kuma shagaltar da su daga sauraron huɗuba. Amma liman babu laifi ya ƙetare in ba zai iya kai wa ga wurinsa ba sai da hakan, haka nan kuma wanda larura ta sa ya ƙetare don wata bukata da ba makawa, kamar alwala, ko don ya cike wata kafa a gabansa, ko makamancin haka.

4- Kuma an haramta tada mutum daga wurinsa wanda ya riga ya zauna, da kuma zama a gurbinsa; saboda abinda ya tabbata daga Jabir Dan Abdullah - Allah Ya yarda da su -, daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: «Kada ɗayanku ya tayar da ɗan'uwansa ranar Juma'a, sannan ya je mazauninsa ya zauna a ciki, amma ku fadada» [120]. [120] Muslim ne ya ruwaito, a lamaba ta (2178).

5- Kuma an karhanta raba tsakanin mutum biyu; ta hanyar zama a tsakaninsu ko a tsallake su; domin ya tabbata daga Salman AlFarisi - Allah ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - Salati da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "«Wanda ya yi wanka ranar Juma'a... sannan ya tafi bai raba tsakanin mutum biyu ba, sai ya sallaci abinda aka wajabta masa, sannan idan liman ya fito sai ya yi shiru, za'a gafarta masa abin da ke tsakanin sa da tsakanin wata Juma'ar daban»" [121], Wannan ya nuna cewa wanda ya raba tsakanin mutum biyu ba ya samun wannan gafarar. [121] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (910).

Mas’ala ta shida: Sunnonin Juma'a:

1- An Sunnanta a karanta a Sallar Asubar ranar Juma’a Suratu Sajada da Suratul Insan; saboda dawwamar Annabi ﷺ akan hakan, daga Abu Huraira, Allah ya yarda da shi, ya ce: Annabi tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya kasance yana Karantawa a Sallar Asubar Ranar Jumua : Suratu Sajada, da Suratul Insan"[122]. [122] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (891), da Muslim, a lamba ta (880).

2- Yin wanka a ranar Juma'a, kuma shi sunna ne mai karfi; saboda hadisin Abdullahi dan Umar -Allah ya kara yarda a garesu-, cewa Manzon Allah -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Idan dayanku zai je Juma'a, to ya yi wanka." {123}. Kuma ya kamata a kwadaita akansa da rashin barin sa, musamman ma ga masu mummunan wari. [123] Bukhari ne ya ruwaito shi a lamba ta (877), da Muslim a lamba ta (844).

Kuma lokacin wankan Juma'a yana farawa ne daga fitowar alfijir, kuma wankan janaba yana isarwa daga wankan Juma'a; domin manufar wankan Juma'a ita ce tsaftacewa da gusar da wari daga jiki, kuma hakan yana samuwa ta hanyar wankan janaba, amma an shar'anta a hada niyyar wankan Juma'a a cikin wankan janaba; domin a samu ladan hakan.

3- An sunnanta masa sanya turare da yin tsafta, da cire abin da ya kamata a cire daga jiki; kamar yanke farce, da aske gashin mara, da tsige gashin hamata, da rage gashin baki; saboda hadisin Salmanul Farisi, Allah ya yarda da shi, ya ce: Manzon Allah tsira da aminci su tabbata a gare shi ya ce: "Wanda ya yi wanka ranar juma'a, ya yi tsarki da abinda zai iya na tsarki, sannan ya shafa mai, ko ya shafa turare, sannan ya tafi bai raba tsakanin mutum biyu ba, sai ya sallaci abinda aka wajabta masa, sannan idan liman ya fito sai ya yi shiru, za'a gafarta masa abin da ke tsakanin sa da tsakanin wata Juma'ar daban" [124]. [124] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (910).

Haka nan an karfafa masa amfani da asuwaki a cikin wannan rana; saboda hadisin Abi Sa'id Alkhudri Allah ya kara masa yarda, ya ce: Na shaida akan Manzon Allah - tsira da Amincin Allah su kara tabbata a gare shi - cewa ya ce: "Wanka ranar Juma'a wajibi ne akan kowanne baligi, kuma ya yi asuwaki, ya shafa tirare in ya samu." [125]. [125] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (880).

4- Sunnah ne a gare shi ya sanya mafi kyawun tufafin da ya samu; saboda hadisin Umar dan Khaɗɗab Allah Ya yarda da shi. «Cewa ya ga wani kaya na alhariri a kofar Masallaci, sai ya ce: Ya Manzon Allah, da ka sayi wannan, sai ka sanya ta ranar Juma'a da kuma don baki idan sun zo gare ka...» [126]. [126] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (886), da Muslim a lamba ta (2068).

5- An sunnanta sammakon zuwa masallaci a ranar Juma'a; saboda kwadaitarwar da Annabi mai tsira da aminci su kara tabbata a gare shi ya yi a kan haka; domin a hadisin Abi Hurairata -Allah ya kara yarda a gareshi- cewa Manzon Allah mai tsira da aminci su kara tabbata a gareshi ya ce: "Wanda ya yi wanka a ranar Juma'a irin wankan janaba -(wato: wanka wanda siffarsa take kamar ta wankan janaba)- sannan ya tafi, kamar ya bayar da sadakar rakumi ne -(kuma shi ɗaya ne daga cikin rakuma, namiji ko tamata)- wanda ya tafi a lokaci na biyu, kamar ya bayar da sadakar saniya ne, wanda ya tafi a lokaci na uku kamar ya bayar da sadakar rago ne mai ƙaho, wanda ya tafi a lokaci na huɗu kamar ya bayar da sadakar kaza ne, wanda kuma ya tafi a lokaci na biyar kamar ya bayar da sadakar ƙwai ne. Idan liman ya fito Mala'iku za su halarto suna sauraron zikiri (Huduba)." [127]. [127] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (881), da Muslim a lamba ta (850).

6- Sunnah ce ga wanda ya shiga masallaci ranar Juma'a alhali limami yana huduba, cewa kada ya zauna har sai ya yi sallah raka'a biyu kuma ya saukake su; saboda Annabi ﷺ ya umurci wanda ya shigo a lokacin huduba da yin hakan. Daga Jabir dan Abdullahi -Allah ya kara yarda a garesu su biyun- ya ce: Sulaiku algadafaniy ya zo a ranar Juma'a, alhali Manzon Allah ﷺ yana huduba, sai ya zauna, sai ya ce masa: "Ya Sulaiku, tashi ka yi raka'a biyu, kuma ka takaita a cikinsu" Sannan ya ce: "Idan ɗayanku ya zo a ranar Juma'a, a lokacin liman yana huɗuba, to, ya yi sallah raka'a biyu, kuma ya sauƙaƙa su." [128]. [128] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (930), da Muslim a lamba ta (875).

7- Sunnah ce a karanta Suratul Kahf a ranar Jumu'a; an ruwaito daga Abu Sa'id AlKhudri, Allah ya yarda da shi, cewa Annabi, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya ce: Duk wanda ya karanta suratul Kahfi a ranar Jumu'a za'a haskaka masa haske tsawon zuwa wata Jumu'a [129]. [129] Hakim ne ya ruwaito shi a cikin Al-Mustadrak, a lamba ta (3392), kuma hadisin yana da illar tsayawa akan Abu Sa'id.

8- An sunnanta a yinin Juma’a da darenta yawaita salati ga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -; daga Aus ɗan Aus - Allah ya yarda da shi - ya ce: Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Lallai ranar Juma'a tana daga cikin mafi alherin kwanakinku, don haka ku yawaita salati a gare ni a cikinta; domin lallai ana gabatar da salatinku a gare ni» [130]. [130] Abu Dawud ne ya ruwaito shi, a lamba (1531).

9- An sunnanta a yawaita yin Addu'a a cikin wannan rana, kuma a kirdaji lokacin amsawa; An karbo daga Abu Hurairah (Allah ya yarda da shi) cewa lallai Manzon Allah ﷺ ya ambaci ranar Juma'a, sai ya ce: «A cikinta akwai wani lokaci, babu wani bawa musulmi da zai dace da shi yana tsaye yana Sallah, yana roƙon Allah Ta'ala wani abu, sai Ya bashi shi» [131]. [131] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (935), da Muslim a lamba ta (852).

Kuma ana kwadayin samun amsawa a dukkan lokutan ranar Juma'a, amma mafi kwadayin samunta shi ne daga lokacin da Liman ya zauna a ranar Juma'a don yin huduba har zuwa idar da Sallah, da kuma karshen lokaci na ranar Juma'a ga wanda ya zauna yana jiran sallar Magariba, ko ya kasance a Masallaci ko a gidansa; saboda hadisin Abu Musa AlAsh'ari Allah ya yarda da shi, cewa Annabi ﷺ yace game da lokacin Juma'a: «Ita ce daga lokacin da liman ya zauna har a idar da sallah» [132]. [132] Muslim ne ya ruwaito shi a lamba ta (853).

Mas’ala Ta Bakwai: Nafilar Juma'a:

Sallar Juma'a ba ta da sunna da ake jeranta ta kafin ta, amma an sunnanta ga wanda ya zo Juma'a ya yi sallar abin da ya so, raka'a biyu, ko hudu, ko shida, ko fiye da haka, yana yin sallama bayan kowace raka'a biyu; saboda kwadaitarwar da Annabi -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi- ya yi a kan hakan, kamar yadda ya zo a hadisin Salmanul Farisi -Allah ya yarda da shi- ya ce: Manzon Allah -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi- ya ce: «Wanda ya yi wanka ranar juma'a... sannan ya tafi bai raba tsakanin mutum biyu ba, sai ya sallaci abinda aka wajabta masa, sannan idan liman ya fito sai ya yi shiru, za'a gafarta masa abin da ke tsakanin sa da tsakanin wata Juma'ar daban» [133]. Kuma saboda aikin Sahabbai -Allah Ya yarda da su-, da kuma gamammiyar falalar da ta zo kan nafila wadda ba a kayyade ba. [133] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (910).

Amma Sunnar da ake jerawa bayan Juma'a, sai ya yi sallah raka'a biyu a gidansa, ko raka'a hudu a masallaci; «Hakika Annabi - tsira da a mincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance yana sallah raka'a biyu bayan Juma'a a gidansa» [134]. Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Idan ɗayanku ya sallaci Juma'a, to ya sallaci huɗu a bayanta." [135]. [134] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (937), da Muslim, a lamba ta (729), daga Ibnu Umar - Allah Ya yarda da su -. [135] Muslim ne ya ruwaito shi a lamba ta (881).

Amma Sunnar Juma'a, idan an sallace ta a masallaci, to raka'a hudu ake yi, idan kuma an sallace ta a gida, to raka'a biyu ake yi.

Matashiya Ta Biyu: Hudubar Juma’a

Mas’ala Ta farko: Hudubar Jumu'a:

(Huduba): Ita ce magana wacce ake gabatarwa ga jama'a, gabanin Sallar Jumu'a, ta kunshi godiya ga Allah, da yabo a gare Shi, da salati da aminci ga Annabi ﷺ, da wa'azi da tunatarwa[136]. [136] A duba: Mu'ujam Lugatil Fukaha (shafi na: 197), da Khutbatul Jumu'ah wa Ahkamuhal Fikhiyyah na Al-Hujailan (shafi na: 22).

Mas’ata Ta Biyu: HUKUNCIN HUƊUBA

Huduba sharadi ce a cikin sallar Juma'a, (Juma’a) bata inganta ba sai da ita; saboda faɗinSa Ta'ala: Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Idan an yi kirã zuwã ga salla a rãnar Jumu'a, sai ku yi aiki zuwa ga ambaton Allah... [al-Juma'a: 9] An fassara ambaton Allah da cewa shi ne huɗuba; da a ce bata kasance wajiba ba, to da tafiya zuwa gare ta bai zama wajibi ba, haka nan kuma saboda dawwamarsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi a kanta, da kuma rashin barinta har abada. [137] A duba: Tafsirin Dabari (22/ 642).

Imam Ibnu Kudama AlHambali - Allah ya yi masa Rahama - ya ce: "Adunkule wannan magana ita ce, huɗuba sharaɗi ce a Juma'a, wadda ba ta inganta ba tare da ita ba"[138]." [138] al-Mughni (2/224).

Mas’ala Ta Uku: Sharuɗɗan Huɗuba:

1- Kasancewarsu huɗubobi biyu, saboda ya tabbata daga Hadisin Abdullahi dan umar -Allah ya kara yarda a gare su su biyun- ya ce: «Annabi - tsira da aminci su kara tabbata a gare shi - ya kasance yana yin hudubobi guda biyu yana zama a tsakanin su» [139]. [139] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (928).

2- Ta zama bayan shigar lokacin sallar Juma'a, idan kuwa ta auku ko wani ɓangarenta kafin lokacin, to bata inganta ba.

3- Gabatuwar huɗubobi biyu akan sallah; saboda hadisin Sa'ib ɗan Yazid - Allah Ya yarda da shi - ya ce: «Lallai kiran sallah a ranar Juma'a, farkonsa ya kasance a lokacin da liman ya zauna a kan munbari a zamanin Manzon Allah ﷺ, da Abubakar, da Umar, Allah ya yarda da su» [140] Wannan kuwa a sarari yake akan gabatar da huɗuba biyu akan sallah. [140] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (916).

kuma saboda faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: «Ku yi sallah kamar yadda kuka ga ina yin sallah» [141], Kuma Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - bai yi sallah ba sai bayan Huɗubobi biyu, kuma AlMurdawi ya ce: "An shar'anta gabatar da su -wato: huɗubobin biyu- a kan sallah, ba tare da saɓani ba" [142]." [141] Bukhari ne ya ruwaito shi a lamba ta (631) daga hadisin Malik bn Huwairith - Allah Ya yarda da shi -. [142] al-Insaf (2/389).

4- Hada tsakanin sassan Huɗuba, ya ce Imam Ibnu Ƙudamah Allah ya yi masa rahama: Kuma hadawa sharaɗi ne a cikin ingancin huɗuba, idan ya raba wani sashenta da wani, da magana mai tsawo, ko shiru mai tsawo, ko wani abu wanin haka wanda zai yanke hadawar, to sai ya sake ta daga farko, kuma abin da ake komawa a kai wajen tsawon rabawar da gajartarsa shine al'ada, haka kuma ana sharɗanta hada tsakanin huɗuba da sallah, idan ya buƙaci yin tsarki (alwala) sai ya yi tsarki, kuma ya ɗora akan huɗubar sa, matuƙar rabon bai yi tsawo ba [143]. [143] al-Mughni (2/230).

5- Bayyanar da huɗuba; domin huɗuba wajibi ce, kuma sharadi ne na ingancin Juma'a, kuma bayyanarwa hanya ce ta gudanar da ita da kuma tabbatar da manufar da ake nufi daga gareta, wato wa'azi da tunatarwa, kuma duk abin da wajibi ba ya cika sai da shi, to shi ma wajibi ne.

6- Halartar adadin da ake yin Juma'a da shi; domin huɗuba zikiri ce da ya wajabta a yi kokarin halartar sa, don haka ya lazimta adadin da aka ambata ya saurare ta.

Mas’ala Ta Huɗu: Rukunan huɗuba:

1- Fara ta da godewa Allah Mai girma da daukaka da yabo a gare Shi; saboda hadisin Jabir dan Abdullahi, Allah Ya yarda da su, yace: «Huɗubar Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ranar Juma'a ta kasance, yana gode wa Allah, kuma yana yaba Masa, sannan yana faɗa a bayan haka...» Hadith [144]. [144] Muslim ne ya ruwaito, a lamba ta (867).

2- Ta kumshi Salati ga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, saboda Salati ga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a cikin huɗubobi wani al'amari ne sananne kuma mashahuri a wajen Sahabbai - Allah ya yarda da su - [145]. [145] A duba: Jala'ul Afham na ibn Kayyim, (shafi na 371).

2- Ta kunshi wa'azi da Wasiyya da tsoron Allah Ta'ala; domin hadisin Jabir dan Samurah - Allah Ya yarda da shi - ya ce: «Annabi -tsira da amincin Allah su kara tabbata a gare shi- ya kasance yana da hudubobi guda biyu, yana zama a tsakanin su, yana karanta Alkur’ani, kuma yana tunatar da mutane» [146]; Domin kuwa ita ce manufar Huɗuba. [146] Muslim ne ya ruwaito, a lamba ta (862).

4- Karanta wani abu daga AlKur'ani Mai girma; saboda hadisin Jabir bn Samurah - Allah ya yarda da shi -: "Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kasance yana yin hudubobi guda biyu, yana zama a tsakaninsu, yana karanta Alƙur'ani, kuma yana tunatar da mutane."

Mas'ala Ta Biyar: Sunnonin Huɗuba:

1- Yin huɗuba akan minbari ko wuri mai tudu; «To, haƙiƙa an sassakawa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - minbari, sai ya yi huɗuba a kansa a ranar Juma'a» [147], Kuma hakika ya tabbata daga jama'a daga cikin sahabbai - Allah ya yarda da su - cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance yana yin huɗuba a kan minbari[148], kuma hakika Nawawi - Allah ya yi masa rahama - ya nakalto ijma'i a kan mustahabbancin hakan, sai ya ce: "Malamai sun haɗu a kan cewa mustahabbi ne a gabatar da huɗuba a kan mumbari"[149]،" Kuma domin hakan ya fi isarwa; sannan idan mutane suka ga mai huɗuba, hakan ya fi tasiri a wa'azinsu. [147] Bukhari ne ya fitar da shi daga Jabir - Allah Ya yarda da shi - a lamba ta (2095). [148] A duba: Irwa'ul Ghaleel fi takhrij ahadith Manar as-Sabil: (3/ 75) da bayansa. [149] Al-Majmu'u Sharhu al-Muhadhdhab: (4/527).

2- Tsayuwar mai huɗuba a lokacin huɗuba; saboda faɗinsa Ta'ala: Kuma idan suka ga wani fatauci kõ kuma wani wasan shagala, sai su yi rũgũguwar fita zuwa gare su, kuma su bar ka kanã tsaye... (Al-Jumu'ah, aya ta: 11), Kuma Daga Abdullahi ɗan Umar - Allah Ya yarda da su - ya ce: «Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kasance yana yin huduba a tsaye, sannan ya zauna, sannan ya tashi, kamar yadda kuke aikatawa a yanzu» [150]. [150] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (920), da Muslim, a lamba ta (861).

3- An sunnanta wa mai huɗuba ya fuskanci mamu (masallata); Daga Abdullahi ɗan Umar - Allah Ya yarda da su -, «Lallai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kasance idan ya kusanci minbarinsa ranar Juma'a, sai ya yi sallama ga waɗanda ke zaune a wajensa, kuma idan ya hau kan Minbarin, sai ya fuskanci mutane da fuskarsa sannan ya yi sallama»[151]. [151] Baihaƙi ne ya ruwaito shi a Sunanul Kubrah, a lamba ta (5742).

Al-hafiz Ibnu Rajab ya ce: Fuskantar liman ga mutanen masallaci da kuma juya wa Alƙibla baya, abu ne da aka yi ijma'i a kansa, kuma nassoshi ma suna nuni a kan haka; domin shi yana yi musu jawabi ne don su fahimta daga gare shi, kuma wannan dukkaninsa Sunna ne, to, idan liman ya saɓa mata, to, haƙiƙa ya saɓa wa Sunna, kuma Juma'arsa ta inganta"[152]. (152) Fathul Bari na Ibnu Rajab: (8/ 250).

4- An sunnanta wa mai huɗuba ya yi sallama ga mamu idan ya fuskance su; saboda hadisin Jabir - Allah Ya yarda da shi -, «Cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kasance idan ya hau kan Minbari, ya yi sallama»[153]. [153] Ibnu Majah ne ya ruwaito shi a lamba ta (1109).

5- Sunna ce ya zauna a kan minbari har sai ladan ya gama (kiran sallah); saboda faɗin Abdullahi ɗan Umar, Allah Ya yarda da su: {Annabi tsira da aminci su kara tabbata a gare shi ya kasance yana yin hudubobi guda biyu, ya kasance yana zama idan ya hau kan munbari har sai Ladan ya gama, sannan ya mike sai ya yi huduba, sannan ya zauna bai yin magana, sannan ya mike sai ya yi huduba}[154]. Kuma hadisin Sa'ib ɗan Yazid - Allah Ya yarda da shi - ya shaida wa wannan, cewa ya ce: «Lallai kiran sallar Juma'a, farkonsa ya kasance a lokacin da liman ya zauna a kan munbari a zamanin Manzon Allah ﷺ da Abubakar da Umar (Allah ya yarda da su)» [155]. [154] Abu Dawud ne ya ruwaito shi, a lamba (1092). [155] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (916).

6- Ya ɗaga muryarsa a wajen huɗuba iya ƙarfinsa; domin hadisin Jabir ɗan Abdullahi - Allah ya yarda da su - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kasance idan ya yi huɗuba, idanunsa su yi ja, kuma muryarsa ta ɗaukaka, kuma fushinsa ya tsananta, har ya zama kamar mai yi wa runduna gargadi ne, yana cewa: «Allah Ya sanya muku alkhairi a sãfiya da maraice» [156]، (صَبَّحَكُم) ma'ana:  Runduna ta zo muku da safe. kuma (مسَّاكم) ma'ana: sun zo muku da yamma, kuma duk wanda ya tsoratar da wani, to zai iya faɗin waɗannan lafuzza biyu. [156] Muslim ne ya ruwaito shi a lamba ta (867).

7- Ya zauna tsakanin huɗubobi biyu ɗan kaɗan, saboda hadisin dan umar - Allah ya kara yarda a gare su su biyun-: «Annabi -tsira da amincin Allah su kara tabbata a gare shi - ya kasance yana yin hudubobi guda biyu yana zama a tsakanin su» [157]. [157] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (928).

8- Sunnah ce a gajarta huɗubobi biyu, kuma ta biyu ta kasance mafi gajarta akan ta farko, tare da tsawaita Sallah; saboda hadisin Ammar -Allah ya yarda da shi- cewa Manzon Allah -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi- ya ce: «Hakika tsawon sallar Mutum da gajartar hudubarsa alama ce ta fikihunsa, don haka ku tsawaita Sallah, kuma ku gajarta Huduba» [158]. [158] Muslim ne ya ruwaito, a lamaba ta (869).

9- An sunnanta addu'a ga musulmai da abin da ya ƙunshi gyaran addininsu da duniyarsu, da kuma addu'a ga majiɓinta al'amuran musulmai da gyara da dacewa; Nawawi Allah Ya yi masa rahama ya ce: "Amma addu'a ga limaman Musulmai da majiɓinta al'amuransu ta salaha da taimako akan gaskiya da tsayar da adalci da makamancin haka, da kuma ga rundunonin Musulunci, to mustahabbi ce a bisa ittifaki"[159]." [159] Al-Majmu'u Sharhu al-Muhadhdhab (4/521).

Ba a shar'anta wa liman ya ɗaga hannayensa ba a lokacin addu'a a huɗubar Juma'a ba, saidai a wajen roƙon ruwa (Istisqa'i). Kuma an so ya yi nuni da ɗan yatsansa na manuniya; an karɓo daga Umarah ɗan Ru'aibah - Allah ya yarda da shi - cewa ya ga Bishr ɗan Marwan a kan mimbari yana ɗaga hannayensa, sai ya ce: «Allah Ya munana waɗannan hannaye guda biyu; lallai na ga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - bai yi fiye da ya yi nuni da hannunsa kamar haka ba, kuma ya nuna da ɗan yatsansa na manuniya»[160]. [160] Muslim ne ya ruwaito shi a lamba ta (874).

10- Ya jagoranci sallah wanda ya jagoranci huɗuba; Saboda Annabi - tsira da amincin Allah su kara tabbata a gare shi - ya kasance yana gudanar da su da kansa, haka nan ma khalifofinsa daga bayansa. Idan kuma wani ya yi huɗuba, wani kuma ya jagoranci sallah saboda uzuri, ya halatta[161]. [161] al-Mughni na Ibnu Ƙudama: (2/ 228).

Mas'ala Ta shida: Fassara Hudubar Jumu'a:

Ya halatta ga mai Huduba a garin da mutanan sa ko mafi yawansu ba sa fahimtar Larabci ya yi musu Huduba (fassara) da harshensu, domin su fahimci hudubar kuma abinda ake nema ya samu, su kuma anfanu da abinda yake cikinta na ilimi da wa’azi da fadakarwa, kuma domin bai tabbata daga Annabi-tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi abinda yake nuni akan shardanta Hudubar Juma’a ta kasance da Larabci ba, kawai dai abin sani Ma’aikin Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance yana Huduba ne da Larabci, domin shi ne harshan sa kuma harshan mutanan sa.

Abinda ya fi cancanta ga mai huɗuba (liman) shi ne ya yi huɗuba da harshen Larabci sannan ya fassarata zuwa ga harshen ƙasarsa, don koyi da annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a cikin huɗubobinsa, da kuma don fita daga saɓani a cikin wannan mas'alar.

Kuma za a kiyaye a wajen fassara abin da ya fi maslaha ga masu sauraro, na rarraba ta bayan kowace gaba ta huɗubar, ko kuma a jinkirta fassarar har sai an kammala huɗubar da Larabci kafin sallah.

Haka kuma ya halatta a fassara huɗuba nan take, da watsa wannan fassarar ta hanyar wata tashar watsawa, da kuma amfani da na'urorin sauraro don wannan fassarar daga wajen waɗanda ba sa jin harshen Larabci cikin masu sallah, kuma wannan ba ya zama daga cikin surutun da aka hana, walau daga wajen mai fassara ko kuma mai karɓa; saboda maslahar da ke cikinsa ga baki ɗaya, da kuma tabbatar da manufar huɗubar.

Mas'ala Ta Bakwai: Ginshiƙan Mai Huɗuba:

Mai huɗuba a Masallacin Juma’a shi ne ginshiƙin masallaci da ƙarfinsa. Ta hanyarsa ne masallaci ke isar da saƙonsa wajen yaɗa Da’awah da wayar da kan al'umma da kuma nusar da mutane kan al'amuran addininsu. Idan mai huɗuba ya kasance masani, mai hankali, mai zurfin basira, wanda ya san al'adun mutane da yanayin rayuwarsu, to tasirinsa zai zama mai kyau kuma mai amfani ga jama'ar masallaci, da kuma mazauna unguwar da masallacin yake; zai ilimantar da su, ya shiryar da su, kuma ya ja-gorance su zuwa ga dukkanin alheri da falala.

Haka abin ya kasance ga masu huɗuba waɗanda suka haɗa sharuddan yin huɗuba; a farkon Musulunci, Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - shi ne mai huɗuba, sannan sai halifofinsa shiryayyu, sannan shugabanni da kwamandoji da Malamai da fitattun mutane. Wannan yana nuna cewa ya wajaba ga wanda zai riƙe wannan aiki ya kasance a matsayi madaukaki na addini da ɗabi'a da ilimi da hali.

A nan ne muhimmancin wannan aiki yake bayyana a rayuwar mutane; domin kuwa ƙarfin masu huɗuba yana bayyana a kan al'ummominsu, kuma rauninsu tasirinsa na bayyana a cikin waɗancan al'ummomi; saboda masallaci shi ne yake ilmantar da al'umma haɗa magana da aiki, idan ya kasance mai huɗuba mai raunin ilimi ne ko hankali ko kamala ko mummunan hali da ɗabi'a, to lallai yana cutarwa ne ba ya amfanarwa, kuma idan ya kasance daga cikin aikin mai huɗuba akwai shiryar da masu sallah zuwa ga alheri da kyautatawa da gyara, to yana da matuƙar wahala mai huɗuba jahili ya cimma wannan aiki mai girma.

Kuma ya kan iya kasancewa mai huɗuba ya cika sharruɗan wannan aikin ta fuskar ilimi da kuma iyawarsa ta kashin kansa, sai dai ya shagaltu daga aikinsa da wasu ayyuka daban da suke shafar matakin aikinsa.

Kuma haka nan, yana iya rashin samun isasshen lokaci na shirya huɗubar da ta dace da yanayi, sai ya fito ga mutane - kamar yadda Ibnu Kayyim Al-Jawziyya - Allah Ya yi masa rahama - ya faɗa - da huɗubar da bata samarwa a cikin zuciya imani da Allah, ko tauhidi gare Shi, ko sanayya ta musamman da Shi, ko tunatarwa da kwanakinsa, ko tada rayuka akan sonsa da kuma kwadayin haɗuwa da shi[162]. (162) Zad al'ma'ad, 1/409.

Wani lokaci kuma son rai ko jahilci ko jayayya ko tsaurin ra'ayi abin zargi kan rinjaye shi, sai ya fita daga daidaito da shiryarwa ta tarbiyya da kira da hikima da wa'azi mai kyau.

Kuma lallai masallaci yana da gagarumin tasiri a cikin wannan Addini; domin shi hasken shiriya ne wanda bawa yake saduwa da Ubangijinsa a cikinsa, kuma imaninsa na ƙaruwa, kuma yana haɗuwa da 'yan uwansa domin kowa ya haɗa kai akan yaɗa kyawawan ɗabi'u da yaƙar munanan ɗabi'u, kuma Masallaci ba zai iya yin hakan ba sai idan Allah Ya shirya masa limami wanda ya cika siffofin ilimi da na ɗabi'u da ake buƙata ga duk wanda zai riƙe wannan babban matsayi, kuma ya gudanar da ayyukan wannan aiki mai daraja.

WASU MUHIMMAN GINSHIƘAI NA ILIMI DA YA KAMATA A SAMU GA MAI HUƊUBA:

1 - Tsarkake aiki saboda Allah; don ya zama abin karfafawa, mai nasara, karɓaɓɓe, kuma masoyi a wajen Allah da kuma wajen mutane.

2 - Nisantar riya da alfahari; domin al'amura da manufofinsu ake auna su, kuma ayyuka sai da niyya, kuma lallai kowane mutum zai sami abin da ya yi niyya. Kuma duk wanda ya yi ado da abin da babu a tare da shi, to Allah zai tozarta shi.

3- Ya zama mahaddacin Alkur’ani, ko kuma ya haddace wani kaso daga cikin shi, kuma ya dawwama a kan yin muraja'ar abin da ya haddace, kuma ya sanya wa kansa wuridi na yau da kullum na karatun Alkur'ani.

4- Ya haddace wani adadi na Hadisan Annabi (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ), daga Riyadus Salihin, ko Arba'in an-Nawawiyya, ko Bulugul Maram, ko wasunsu daga cikin littattafan Hadisai da aka dogara da su.

5 - Ya san Aƙida ingantacciya, wato aƙidar magabata nagari.

6 - Ya koyi Fikihu a hukunce-hukuncen Addini, musamman ma fikihun ibada, kuma mafi muhimmancin hakan shi ne abinda ya shafi Tsarki, da Sallah, da Zakkah, da Azumi, haka nan da fikihun mu'amaloli; don ya san ka'idojin nema da kashewa, kuma ya gargadi mutane daga ha'inci da yaudara da kuma cin dukiyar mutane a kan ba-zata, kuma ya gargade su haka nan daga ɓarna da almundahana da rowa da maƙo, domin harkokinsu na dukiya su kasance a ƙarƙashin hasken Alƙur'ani da Sunnah.

7- Ya kware a harshen Larabci domin ya san ma'anonin abin da Allah ya saukar wa Manzonsa ﷺ, domin lalle Alkur’ani da harshen Larabci ya sauka.

8- Ya Karanta Tarihin Annabi, da Siffofin Annabi Muhammadu -tsira da amincin Allah su tabbata agare shi, da kuma tarihin Magabata na kwarai; domin a cikinsu akwai abin koyi na kwarai, da kyakkyawan misali, da taskar ilimi mai amfani, da kuma wayewa ta Musulunci madaukakiya.

9- Sanin malaman ƙasarsa da sauran malamai masu zurfi cikin ilimi, waɗanda aka san su da ingancin akida da ilimi da hankali, da komawa zuwa gare su a cikin dukkan abin da yake buƙata na mas'alolin addini da warware matsalolin al'ummarsa.

10- Ya san kungiyoyin Musulunci da akidojinsu, da mabambantan ra'ayoyi na tunani da manufofinsu, da mazhabobi masu rusa addini da manufofinsu, har ya iya yin muhawara da su a bisa ga littafin Allah Ta'ala da Sunnar Manzonsa ﷺ da abin da kwararrun malaman Musulunci suka rubuta, ya warware jabunsu, kuma ya yi gargadi daga batancinsu.

11- Ya kasance yana maida himma akan halin da Musulmai suke ciki da rauninsu da mamayar maƙiya a kansu, kuma ya sani cewa hakan ya faru ne saboda nisantarsu daga tafarkin Allah madaidaici, da raunin Imani da Allah da kuma miƙa wuya ga shari'arsa, sai ya yi ƙoƙari wajen koyar da su abin da zai amfane su a cikin addininsu da duniyarsu.

12- Ya san kafofin yaɗa labarai daban-daban, ya san amfaninsu da illolinsu, da kuma yadda zai amfana da su wajen kira zuwa ga Allah, ya kuma yi hattara daga haɗurran da ke cikinsu ga kansa da al'ummarsa.

Kuma idan waɗannan ginshiƙan suka tabbata ga limamin Juma'a; to lallai hakan yana haifar da istiqama da daidaito, da izinin Allah - Maɗaukakin sarki -.

Kuma Manyan Jigogin Halayya:

1- Ya kamata ga limamin massallaci ya zama mai kira kuma malami ga jama'ar massallaci da kuma waɗanda suke zuwa massallacinsa daga cikin mutanen unguwa da waninsu, don haka ya wajaba ya zamana cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - shi ne abin koyinsa; domin shi ne abin koyi nagari, kuma kyakkyawan abin koyi, kuma mafi girman misali ga al'umma da shuwagabanni, Allah maɗaukakin sarki ya ce: Lalle, abin kõyi mai kyau ya kasance gare ku daga Manzon Allah, ga wanda ya kasanee yanã fãtan rahamar Allah da Rãnar Lãhira, kuma ya ambaci Allah da yawa. [al-Ahzab: 21].

Kuma ya nisantar da kansa da jama'ar masallacinsa daga zancen duniya da siyasa, kuma ya kebance masallacin don ilimi da ibada.

2- Ya zama mai tsafta, mai tsari akan kansa, kuma haka nan ya kula da tsabtar masallaci, da jera kayayyakinsa da tsara su, da kula da abubuwan amfaninsa, kuma ya nisanci barna a cikin haka, ya kuma guji yi wa masallaci ado.

3- Ya zama mai kyakkyawar shiriya da kamun kai, yana mai bin Sunnar Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - na sakin gemu da rage gashin baki, tare da nisantar sakin tufafi a kasa, kuma ya lazimci kamun kai da nutsuwa, kuma ya zama mai bin tafarkin waɗanda suka gabata daga cikin Magabata Na Kwarai - Allah Ya yi musu rahama -.

4- Ya kasance mai tausasawa, mai haƙuri, mai jinƙai; domin lallai sauƙi ba a samunsa a cikin wani abu face sai ya ƙawata shi, kuma ba a cire shi daga wani abu ba face sai ya munana shi, kamar yadda ya zo a hadisi; an ruwaito daga Nana Aisha -Allah ya yarda da ita- cewa Annabi -tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi- ya ce: Lalle sassauci ba ya kasance wa a komai sai ya ƙara masa kyau, kuma ba a cire shi a komai sai ya aibanta shi. [163]. [163] Muslim ne ya ruwaito shi a lamba ta (2594).

Idan kuskure ya auku daga ɗaya daga cikin masu zuwa masallaci, to bai kamata ga mai huduba ya tsawatar masa ba, saidai ya yi masa nasiha cikin sauƙi; kuma ya sanar da shi ta hanya kyakkyawa; Daga Mu'awiya Bn Al-hakam Al-aslami Allah ya yarda da shi ya ce: Wata rana ina sallah tare da manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, sai wani mutum daga cikin mutane ya yi atishawa, sai na ce: Allah Ya yi maka rahama, sai mutane suka kalleni da idanuwansu, sai na ce: Ya yi wabin mahaifiyarsa, me ya sameku ne kuke kallona?! sai suka buga hannayensu akan cinyoyinsu, lokacin da na ga suna ƙoƙarin sani in yi shiru sai na yi shirun, lokacin da tsira da amincin Allh su tabbata agare shi ya idar da sallah, fansarsa babana da babata, ban taɓa ganin malami ba kafinsa ko abayansa mafi iya koyarwa sama da shi, na rantse da Allah, bai yi min tsawa ba, bai dake ni ba, bai zageni ba. Ya ce: "Lalle wannan sallar babu wani abu da yake inganta a cikinta daga zancen mutane, kadai shi ne tasbihi da kabbara da karatun AlKur'ani". [164]. [164] Muslim ne ya ruwaito shi, a lamba ta (537).

5- Ya kasance mai laushi da taushin zuciya; domin ya tara mutane a kewayensa su amfana da tausayinsa, da taimakonsa da iliminsa, kuma ya tsaya tare da su a cikin masifunsu da bukatunsu. Kuma ya kamata ya shawarce su a kan abin da ya shafi saƙon masallaci.

Kuma Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kasance a mafi ɗaukakan matsayi a cikin wannan duka, kamar yadda Allah - Maɗaukakin sarki - Ya faɗa game da shi: Sabõda wata rahama ce daga Allah ka yi sanyin hali a gare su. Kuma dã kã kasance mai hushi mai kaurin zuciya, dã sun wãtse daga gẽfenka. Sai ka yãfe musu laifinsu, kuma ka nẽma musu gãfara, kuma ka yi shãwara da su a cikin al'amarin. Sa'an nan kuma idan ka yi niyyar zartarwa, to, ka dõgara ga Allah, lalle ne, Allah Yana son mãsu tawakkali. [Aal- Imran: 159].

6- Ya siffantu da haƙuri da yakini; domin ya cancanci matsayi na limanci a cikin masallacinsa da kuma tsakanin jama'arsa; domin hakika haƙuri da yakini suna isar da bawa izuwa ga matsayin limanci a cikin addini, Allah Ta'ala ya ce: Kuma Mun sanya shugabanni daga cikinsu, sunã shiryarwa da umurnin Mu, a lõkacin da suka yi haƙuri, kuma sun kasance sunã yin yaƙĩni da ãyõyin Mu. [al-Sajda: 24].

7- Wajibi ne ya zama mai gaskiya a cikin maganarsa, ko a cikin huɗubar Juma'a, ko a cikin darasin karantarwa da wa'azi, ko a cikin zancensa da mutane; domin ya kasance daga cikin masu gaskiya, shiryayyu, masu rabauta; kamar yadda ya zo a Hadisi daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - cewa ya faɗa: "Na hore ku da gaskiya, saboda gaskiya tana shiryarwa zuwa ga aikin alheri, kuma lallai aikin alheri yana shiryarwa zuwa ga Aljanna, kuma mutum ba zai gushe ba yana yin gaskiya, kuma yana kirdadon gaskiya har sai an rubuta shi a wajen Allah mai yawan gaskiya ne. Kuma na haneku da ƙarya, saboda ƙarya tana ja ne zuwa ga fajirci, kuma fajirci yana ja ne zuwa ga wuta, kuma mutum ba zai gushe ba yana yin ƙarya kuma yana kirdadon ƙarya har sai an rubuta shi a wajen Allah mai yawan ƙarya." [165]. [165] Bukhari ne ya ruwaito shi (6094), da Muslim (2607), daga hadisin Abdullahi ɗan Mas’ud - Allah Ya yarda da shi -.

Ƙarya sharri ce da bala'i, kuma mafi girman ƙarya ita ce yin ƙarya ga Allah - Maɗaukakin sarki - da kuma faɗa a Kansa ba tare da ilimi ba, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: Ka ce: "Abin sani kawai, Ubangijina Yã hana abũbuwanalfãsha; abin da ya bayyana daga gare su da abin da ya ɓõyu, da zunubi da rarraba jama'a, bã da wani hakki ba, kuma da ku yi shirki da Allah ga abin da bai saukar da wani dalĩli ba gare shi, kuma da ku faɗi abin da ba ku sani ba, ga Allah. [al-A'araf: 33].

To wannan aya mai girma ta tattara mafi girman zunubai, ta fara daga mafi ƙasƙanci zuwa mafi girma, shi ne kuwa yin magana ga Allah ba da ilimi ba a cikin sunayenSa da siffofinSa da kuma shari'arSa.

Kuma karya ga Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi, tana daga cikin mafi girman karya kuma mafi munin zunubai, kuma tana daga cikin manyan zunubai wadda aka yi wa mai ita barazanar wuta; an karɓo daga Mughira ɗan Shu’ubah, Allah ya yarda da shi, ya ce: Na ji Annabi, tsira da amincin Allah su tabbata agare shi, yana cewa: «Lallai karya a kaina ba kamar karya a kan wani ba ne, wanda ya yi mini karya da gangan, to ya tanadi masaukinsa a wuta» [166]. [166] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (1291), da Muslim, a lamba ta (4).

Kuma ya nisanci karya ko da kuwa da kyakkyawar niyya ce don kwadaitarwa akan alkhairi da kuma tsoratarwa daga sharri, kamar yadda wasu masu wa’azi suke aikatawa; domin ita mummuna ce, babu alkhairi a cikinta kuma babu shiriya, kuma mai faɗinta mai ɗaukar zunubi ne ba mai lada ba, kuma mai laifi ne ba mai cin riba ba.

8- Ya kasance mai amana a wajen isar da magana, kuma ya tabbatar da ingancin labarai, kada ya yi gaggawa wajen karɓar jita-jita, kuma kada ya dogara sai da magana amintacciya. Kuma haƙiƙa Allah Ta'ala ya umarce mu da hakan a cikin faɗinsa: Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Idan fãsiƙi Yã zo muku da wani babban lãbãri, to, ku nẽmi bayãni, dõmin kada ku cũci waɗansu mutãne a cikin jãhilci, sabõda haka ku wãyi gari a kan abin da kuka aikata kunã mãsu nadãma. [al-Hujurat: 6].

9- Ya yawaita suturta mutane, kuma ya ɓoye asirinsu, domin wanda ya suturta wani musulmi, Allah Zai suturta shi a duniya da lahira, kuma wanda ya bibiyi al'aurar musulmai, Allah zai bibiyi al'aurarsa har sai ya tona shi ko da a tsakiyar gidansa ne; an ruwaito daga Abdullah ɗan Umar, Allah ya yarda da su, cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Wanda ya suturta wani musulmi Allah Zai suturta shi ranar Alƙiyama" [167]. Daga Abu Burzata Al-Aslami - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: «Ya ku jama'ar da ya yi imani da harshensa, kuma imani bai shiga zuciyarsa ba, kada ku yi gulmar musulmai, kuma kada ku bibiyi al'aurorinsu; saboda duk wanda ya bibiyi al'aurorinsu to Allah Zai bibiyi al'aurarsa, kuma duk wanda Allah Ya bibiyi al'aurarsa sai Ya kunyatashi a cikin gidansa» [168]. [167] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (2442), da Muslim, a lamba ta (2580). [168] Abu Dawud ne ya ruwaito shi, a lamba (4880).

Mas'ala ta Takwas: Ladubban Huɗuba da Mai Huɗuba

1- Ya wajaba huɗubar Juma'a ta tsaftata daga mayar da ita abin tallata wani mutum, ko wata kungiya, ko wata cibiya, ko wanin haka, kuma ta kasance tsantsa domin Allah Ta'ala da addininSa, da kuma isar da kiransa da ɗaukaka kalmarSa, Allah Ta'ala ya ce: Kuma lalle ne wurãren sujada na Allah ne, saboda haka kada ku kira kõwa tãre da Allah (da su, a cikinsu). [al-Jinn: 18].

2- Ya kamata mai huɗuba kada ya tsawaita har ya kai ga ya yi wa masu saurare nauyi, kuma ya sa su guji sauraron huɗubar, kada kuma ya gajarta ta har ya kai ga ya tauye maudu'in kuma ya gutsure shi.

3- Ya kamata ga mai huɗuba ya kiyaye halin masu saurare, sai ya yi magana ga mutane gama-gari gwargwadon hankulansu, yana mai gujewa lafuzzan da suke nesa da fahimtarsu. Kuma ya tsakaita magana da gwargwado tsakaitawa, ya kuma ƙawata ta ga waɗanda suka keɓanta. Domin ya kasance mai hikima ga dukkan bangarorin mutane, yana ajiye abubuwa a mazauninsu. Kuma a kowane hali ya nisanci duk wani ƙawanyar magana ta ƙarya.

4- Ya nisanci al'amuran saɓani masu tayar da gaba da ƙiyayya; domin lallai babban aikin mai huɗuba shi ne ilmantar da mutane, da haɗa zukatansu akan gaskiya, da kuma gusar da dalilan rarrabuwar kai a tsakaninsu.

5- Ba ya kallafa wa kansa Saj'i ko zurfafawa, kawai babban nufinsa shi ne isar da ma'anoni masu amfani da lafazi mafi bayyana kuma mafi gajarta.

6- Ya nisanci kwaikwayo abin ƙyama da na tilastawa, da kuma shiga siffar shahararrun masu huɗuba; domin hakan yana haifarwa a cikin zukata rashin nutsuwa da gamsuwa[169]. [169] A duba: Salon Huɗubar Juma'a na Abdullahi dan Daifullahi Ar-Ruhaili: (shafi: 12, 20, 22), da Wasiyya Hamsin da Ɗaya Don Zama Mahuɗubi Mai Nasara na Amir dan Muhammad Al-Madri (shafi: 33, 73, 87).

Mas’ala Ta Tara: Manufar Huɗuba da maƙasudinta:

Ya kamata Hudubar Juma’a ta yi nufin tabbatar da manufofi kamar haka:

1- Bayanin tushen Tauhidi da muhimmancinsa da falalarsa, da kuma gargaɗi akan shirka da dukkan nau'o'insa da siffofinsa da hanyoyinsa.

2- Wa'azi da tunatarwa game da Allah - Maɗaukakin sarki - da hisabinsa da sakamakonsa a Lahira, da ma'anoni na Ubangiji waɗanda zukata ke rayuwa da su, da kira zuwa ga alheri da umarni da kyakkyawa da hani daga abin ƙi.

3- Fahimtar da Musulmai da kuma koyar da su haƙiƙanin addininsu daga littafin Allah Madaukaki da Sunnar ManzonSa ﷺ, tare da kula da ingancin ɗabi'u da ladubba daga tsanantawa da sakaci.

4- Gyara gurɓatattun fahimta game da Musulunci, da yin raddi ga shubuhohi da abubuwan ɓata da maƙiyansa suke tayarwa domin rikitar da hankula, da salo mai gamsarwa da hikima, ya nisanci ihu da zage-zage.

5- Fuskantar muggan tunani masu rushe addini da masu ɓatarwa ta hanyar gabatar da Musulunci ingantacce a matsayin tafarki na asali ga al'umma, wanda Allah ya yarda da shi a gare ta, kuma ita ma ta yarda da shi a matsayin addininta, tare da bayyanar da kebantattun siffofinsa na haɗaka, da daidaito, da zurfi, da kuma fa'idarsa.

6- Danganta huɗuba da rayuwa, da kuma halin da mutane ke ciki, ta hanyar mai da hankali kan magance cututtukan al'umma, da samar da mafita ga matsalolinta, wanda aka ciro daga Shari'ar Musulunci mai girma, tare da ba da muhimmanci ga Akidah da gyara ta, da rukunan Musulunci da Imani, da al'amuran mata da iyalan musulmi da sauran batutuwa da mutane ke da bukata a kansu.

7- Lura da lokuta daban-daban na musamman da suke maimaituwa a shekara, kaman watan Ramadan da Hajji da sauransu, abin dake shagaltar da zukatan masu sauraro, kuma yana ƙara musu sha'awar samun sanin da zai haskaka musu hanya a kan sha'aninsa.

8- Tabbatar da ma'anar 'yan’uwantaka ta musulunci tsakanin musulmai, da yaƙar rikice-rikice da bangaranci na ƙabilanci da na mazhaba da na yanki da sauransu masu rarraba kan musulmai.

Mas'ala ta Goma: Yadda ake shirya Huɗuba:

Yana kamata ga mai huɗuba ya kula da shirya huɗubarsa shiri ingantacce, kuma ya yi la’akari da waɗannan abubuwan da ke tafe:

Galibi Huɗuba ta ƙunshi sassa uku: Gabatarwa, da Jigo, da kuma Kammalawa. Waɗannan sassa ne da ba a bayyana su kai tsaye a yayin rubutawa ko gabatarwa, kuma sassa ne masu saƙewa da juna cikin jituwa, wanda ingancin haɗin kansu ya danganta ne da gwanintar mai huɗuba, da yalwar iliminsa, da kuma gogewarsa, ta yadda sassan Huɗubar suke samun tsari kuma gininta yake ƙarfafa.

Kuma wannan tsari da kamala shi yake sanya ma'anoni su zama a bayyane da manufofi su fito fili, kuma yana tabbatar ma mai magana kyakkyawan saurare daga wajen masu jinsa, da cikar nutsuwa daga wajen abokan zamansa.

Gabatarwa: Ya kamata mai huɗuba ya kula da gabatarwarsa da kuma buɗe jawabinsa, ta yadda zai kawo kalaman buɗe jawabi waɗanda za su nunawa mai sauraro manufar huɗubar, wanda hakan zai jawo hankali kuma ya shirya zukata. Wannan na iya kasancewa ta hanyar kawo ayoyi na Alƙur’ani masu tsawatarwa ko masu kwadaitarwa, ko kuma wasu daga cikin hikimomin Annabta masu ratsa jiki. Shi kuma jawabin buɗewa, shi ne abu na farko da mai huɗuba yake gabatarwa ga jama'arsa, idan har ya burge su da kyakkyawar gabatarwa, za su iya bibiyar sauran huɗubarsa cikin himma da kuzari.

Ya kamata a gabatarwar magana a samu abin da ke nuni ga manufar mai magana, duba da cewa an sani ana buɗe huɗubar Juma’a da yabo ga Allah da jinjina a gare Shi da shaidawa biyu da salati da aminci ga Manzon Allah ﷺ, sai ya kasance a cikin waɗannan lafuzza akwai kyakkyawan zaɓi da ke nuni ga jigon huɗubar da kuma manufarta.

Maudu'i: Wato shi ne mafi girman manufar huɗubar, kuma yana iya dacewa a bayyana shi a farkon huɗubar, kamar ya ce: Ina son in yi muku magana a kan kaza... Idan ya kasance yana daga cikin al'amuran zamani wanda al'umma ke ciki, kuma take sa ran samun cikakken bayani a kansa.

Wani lokacin kuma ba ya kyautatuwa a bayyana shi a sarari, ko dai don yana da sarkakiya, ko kuma yana jawo rabuwar kan mutane. A wannan hali ya kamata mai huɗuba ya shigo da shi a hankali, ya kuma tattauna shi ba kai tsaye ba, domin ya dauki masu saurare a jere bisa tsari mai ma'ana har ya cimma manufarsa cikin tsakaitawa da daidaito, yana mai gujewa tayar da hankali da haddasa rarrabuwar kai. Daga nan sai mai huɗuba ya cimma burinsa na shirya zukata idan sun kasance masu kau da kai ne, ko kuma idan maganar ta kasance ba abin da zukatansu suka saba da shi ba.

Jigon Huɗuba galibi ya ginu ne akan rukunai biyu na asali, wato: Bayyanawa da kuma kafa hujja.

Amma bayyanawa: yana kasancewa da ambaton Ta'arifin maudu'in da ake magana a kansa, da kuma ambaton siffofinsa da kebantattun halayensa da kuma fifikonsa.

Amma kafa hujja: Galibi maudhu'i yana buƙatar abin da zai ƙarfafa shi da dalilai da hujjoji da kuma shaidu, kuma galibi suna kasancewa ne daga Alƙur'ani da Sunnah da maganganun magabata. Da kuma kawo wasu waƙi'o'i da abubuwan da suka faru a matsayin kiyasi da kuma izina. Kuma yana da amfani a wannan babin a yi nuƙuli daga shahararrun limamai da masu hikimarsu, daga cikin waɗanda aka san su da salihanci da shugabanci da mutumtaka da gudun duniya da jarumtaka da kuma tsoron Allah, kamar yadda yanayi ya buƙata kuma ya dace da maƙalar.

Kammaluwar Huɗuba: Bayan mai huɗuba ya gama gabatar da maudu'insa, ya kyautu ya rufe huɗubarsa da rufewa ta daidai, wadda za ta tattara tunaninsa, kuma ta taƙaita maudu'insa, da kalamai mabanbanta, ta hanya taƙaitacciya, saboda tsawaitawa a irin wannan yanayi yana janyo kosawa da wargaza tunani.

Kuma bai kamata ta ƙunshi sababbin ra'ayoyi da sababbin dalilai ba; domin a lokacin ba kammalawa ba ce, a'a wani sashi ne na Huɗuba kuma ci gabanta.

Kuma ya kamata Kammalawar ta kasance mai ƙarfi a wajen salon bayaninta da tasirinta, domin ita ce abu na ƙarshe da ke dukan kunnen mai sauraro, kuma ya tabbata a cikin zuciyarsa. Idan kuma ta zama mai rauni a wajen tsarinta, sanyayya a wajen gabatar da ita, to fa'idar huɗubar ta salwanta.

Kuma Kammalawa na iya kasancewa wasu ayoyi na Alƙur’ani waɗanda ba a ambace su ba a baya, waɗanda suka tattara maudu'in huɗubar wajen kwadaitarwa ko tsoratarwa, ko kuma kafa hujja da tabbatarwa. Haka nan, tana iya kasancewa wani hadisin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi- da ke ba da irin fa'idar da ayoyin Alƙur'ani ke bayarwa. Kuma tana iya kasancewa sake maimaita muhimman abubuwan huɗubar ta wani salo daban, kuma ta hanya guda tattararra, bayyananna, mai tasiri mai ƙarfi.

Kuma akwai wasu mas'aloli guda biyu da ya kamata mai huɗuba ya kula da su, kuma su ne: Riƙon maudu'i guda ɗaya, da kuma sabuntawa da canji.

Kadaita maudhu'i: Akwai bukatar a takaita akan maudhu'i guda daya, a cika bangarorinsa, a ƙawata kalamansa, kuma a zurfafa maganinsa; domin rarrabuwar maudhu'o'i da yawaitar mas'aloli a wuri guda kan rudar da hankula, ya sa wasu su manta da wasu, sannan ya kai ga tsawaitawa mai gundurarwa da sura marar armashi da rashin zurfin tantancewa.

Sabuntawa da Canji: Wato kada huɗubobinsa su zama gaba ɗaya a kan maudu'ai masu maimaituwa waɗanda bai fita daga cikin su, saidai ya bambanta a cikin maudu'ansa; domin su ƙunshi dukkan al'amuran Shari'a daga tauhidi da ibadu da mu'amaloli da ɗabi'u da sauransu.

Kada ya lizimci hanya guda ɗaya a salon jawabinsa, a'a, sai ya riƙa canzawa tsakanin salon tambaya da na tabbatarwa, da bayar da misalai, da neman hikimomi da asirrai, tare da lura da halin da al'umma ke ciki, da binciko buƙatun mutane, da yi musu jagora da haskaka musu hanya, domin ya dace da tasirin waɗannan sauye-sauye a kansu[170]. [170] A duba: Manhaj Fii I'idaadi Khutbatil Jumu'ah na Dakta Salih bin Abdullah bin Humaid: (shafi na: 22) da bayansa.

BABI NA HUƊU: Hukunce Hukuncen Masallatai

Matashiya Ta Farko: Ma'anar Masallaci

Masallaci a shar’ance: shine wurin da ake tsaida salloli biyar na farilla da Juma'a da waninsu, kuma ake yin kiran sallah a cikinsa. Kuma an sa masa suna masallaci; saboda wuri ne na yin sujjada ga Allah madaukakin sarki.

Bambanci tsakanin Masallaci da wurin sallah (Musalla).

Masallaci shine Guri da aka keɓance shi don Salloli wajababbu a bisa dawwama, kuma aka yi masa wakafi don haka, amma Gurin Sallah shi ne abin da aka tanada don sallar da ba ta dindindin ba; kamar guraren sallah na makarantu da ma'aikatu da kamfanoni da hanyoyin tafiya da sauransu, kuma ba'a yi masa wakafi don salloli biyar ba, kuma ba'a sunnanta yin Gaisuwar Masallaci ba wajen shiga Gurin Sallah, an sunnanta ta ne kawai wajen shiga Masallaci.

Matashiya Ta Biyu: GINA MASALLACI DA FALALARSA

Msallatai sune mafifitan gurare a doron kasa kuma mafi darajarsu, ana tsayar da mafifitan ibadu a cikinsu wato Sallah, Allah madaukakin sarki ya ce: A cikin waɗansu gidãje waɗanda Allah Yã yi umurnin a ɗaukaka kuma a ambaci sũnansa a cikinsu, sunã yin tasbĩhi a gare Shi a cikinsu, sãfe da maraice. Waɗansu maza, waɗanda wani fatauci bã ya shagaltar da su, kuma sayarwa bã ta shagaltar da su daga ambaton Allah, da tsai da salla da bãyar da zakka, sunã tsõron wani yini wanda zukãta sunã bibbirkita a cikinsa, da gannai. [al-Nur: 36-37].

Kuma hakika Allah Ta'ala ya jingina wuraren sujada gare shi jinginawa ta girmamawa da karramawa, Allah Ta'ala ya ce: Kuma wãne ne mafi zãlunci daga wanda ya hana masallãtan Allah, dõmin kada a ambaci sunanSa a cikinsu... [al-Baƙara: 114], Kuma - tsarki ya tabbatar maSa - Ya ce: Kuma lalle ne wurãren sujada na Allah ne, saboda haka kada ku kira kõwa tãre da Allah (da su, a cikinsu). [al-Jinn: 18].

Don haka haƙiƙa Shari'a ta kwaɗaitar a kan gina su da raya su ta zahiri da ta ɓoye, daga cikin wannan: Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: Abin sani kawai, mai rãya masallãtan Allah, shĩ ne wanda ya yi ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira, kuma ya tsayar da salla kuma ya bãyar da zakka, kuma bai ji tsõron kõwa ba fãce Allah. To, akwai tsammãnin waɗannan su kasance daga shiryayyu. [al-Taubah: 18].

Daga Usman ɗan Affan - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Wanda ya gina masallaci yana mai neman fuskar Allah da shi, Allah zai gina masa makamancin sa a cikin Aljanna» [171]. [171] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (450), da Muslim, a lamba ta (533).

Daga Jabir ɗan Abdullahi - Allah Ya yarda da su - cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Wanda ya gina masallaci domin Allah kamar sheƙar kazar-daji, ko ma ƙarami, Allah zai gina masa gida a cikin Aljanna» [172]. [172] Ibnu Majah ne ya ruwaito shi, a lamba ta (738), kuma Al-Busiri ya ce a "Az-Zawa'id" (1/94): Wannan isnadi ne Sahih.

Da faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi: «Koda kuwa kamar sheƙar fakara» Ma'ana: Gurin da macen tsuntsu ke gyarawa a ƙasa domin ƙwan ta, an yi nufin nuna matuƙar ƙanƙanta, don kada wani ya raina masallacin da ya gina, ko da kuwa yana da matuƙar ƙanƙanta.

Kuma hakan na iya haɗawa da wanda ya ba da gudummawa wajen gina shi, ko da kuwa da bulo ne ko laka, ko ya yi aiki a ciki da hannunsa, ko ya biya ladan ma’aikata, da makamancin wannan aiki wanda ake danganta wa mai shi cewa ya taimaka wajen gina masallacin da kansa ko da dukiyarsa, yana mai lissafin neman ladan da ke tattare da hakan. Wato Allah ya gina masa irinsa ko wanda ya fi shi faɗi a Aljanna; domin gidan Aljanna ba a kwatanta shi da na duniya ba, kuma babu wata muƙabala a tsakaninsu. Wannan kuwa na daga abin da ke ƙarfafa gwiwar wanda Allah ya wadata shi zuwa ga yin gaggawa cikin ayyukan alheri, da kuma ribantar dama a wannan rayuwa, don ya gabatar wa Lahirarsa abin da zai samu ladansa a nanninke a wurin Ubangijinsa ninki mai yawa[173]. [173] A duba: Fusul wa Masa'il Tata'allaq bil Masajid na Sheikh Ibnu Jibrin, Allah ya yi masa rahama (shafi na: 14).

Matashiya Ta Uku: Raya masallatai da falalar hakan

Raya Masallatai a gamammiyar ma'anarta ta kunshi raya su iri biyu na zahiri da na badini, don haka ya kunshi gina masallatai da kuma gyara su, da sanya musu haske da shimfida su, da yi musu hidima da tsaftace su, da bauta wa Allah a cikinsu, da nada Limamai da Ladanai a cikin su, da bude wuraren zikiri a cikinsu; kamar koyar da Alkur’ani da Fiqhu da Tafsiri da Hadisi da sauran ilimai masu amfani, da kuma bayar da tallafi ga ma'aikata a cikinsu, da yin wakafi a kansu na abin da akwai maslaha a gare su, kamar wakafin gidajen zama ga Liman da Ladan da Malami da daliban ilimi a cikinsu, da samar da wuraren alwala da sauran abubuwan da suke maslaharsu ne.

Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: Abin sani kawai, mai rãya masallãtan Allah, shĩ ne wanda ya yi ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira, kuma ya tsayar da salla kuma ya bãyar da zakka, kuma bai ji tsõron kõwa ba fãce Allah. To, akwai tsammãnin waɗannan su kasance daga shiryayyu. [al-Taubah: 18].

Haƙiƙa wannan aya mai girma ta tabbatar da Imani ga wanda ya raya masallatai da yin sallah a cikinsu, da tsaftace su, da kuma gyara abin da ya lalace daga cikinsu[174]. [174] A duba: al-Mashru'u wal-Mamnu'u fil-Masjid na Muhammad al-Arfaj (shafi na: 9).

Matashiya Ta Hudu: Tsaftace Masallatai da kiyayesu daga ƙazanta

Kasantuwar masallatai wuraren bauta ne da neman kusanci ga Allah Madaukakin Sarki ta hanyar biyayya, an yi umarni da kula da su, da kiyaye su daga ƙazanta da najasa da datti, domin su samu tsabta da kyau da kuma ado.

Shiekh Ibnu Sa'adi Allah ya yi masa rahama ya ce a cikin tafsirin fadin Allah Madaukakin Sarki: A cikin waɗansu gidãje waɗanda Allah Yã yi umurnin a ɗaukaka kuma a ambaci sũnansa a cikinsu, sunã yin tasbĩhi a gare Shi a cikinsu, sãfe da maraice. [al-Nur: 36]. Ya ce: " ...a ɗaukaka kuma a ambaci sũnansa a cikinsu... Waɗannan su ne jimillar hukunce-hukuncen masallatai, kuma yana shiga cikin girmama su: ginasu, da share su da tsaftacesu daga najasa da abin cutarwa, da tsaresu daga mahaukata da yara ƙanana waɗanda ba sa iya kiyaye kansu daga najasa, da kuma kafirai, da kuma a tsare su daga surutu mara anfani a cikinsu, da ɗaga murya ba tare da ambaton Allah ba"[175]. [175] Tafsiru Assiadi (569).

Daga Abu Hurairah -Allah ya yarda da shi-, cewa wata mata baƙa ta kasance tana share Masallaci, sai Manzon Allah -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi- ya nemeta ya rasa, sai ya tambaya game da ita, sai suka ce: Ta rasu, sai ya ce: «Don me ba ku sanar da ni ba?» Ya ce: sai ya zama kamar sun ɗauki al’amarinta da sauƙi, sai ya ce:«ku nuna min kabarinta» sai suka nuna masa, sai ya yi mata sallah, sannan ya ce: «Lallai waɗannan Kaburburan cike suke da duhu a kan ma'abotansu, kuma lallai Allah Mai girma da ɗaukaka Yana haskaka musu su da sallata a kansu» [176]. [176] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (460), da Muslim a lamba ta (956).

Kuma ya tabbata daga Anas -Allah ya yarda da shi- cewa ya ce: Wata rana muna cikin masallaci tare da Manzon Allah -tsira da amincin Allah su tabbata agare shi-, sai ga wani balaraben ƙauye ya zo, sai ya miƙe yana fitsari a cikin masallaci, sai sahabban Manzon Allah -tsira da amincin Allah su tabbata agare shi- suka ce: Tsaya tsaya, sai Manzon Allah -tsira da amincin Allah su tabbata agare shi- ya ce: «Kada ku yanke masa - wato: kada ku yanke masa fitsarinsa - Ku ƙyale shi» Sai suka barshi har sai da ya yi fitsari, sannan Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kira shi sai ya ce masa: Lallai wadannan masallatan basu dace da wani abu daga wannan fitsarin ko kazantar ba, a'a sun kasance ne don ambaton Allah - Mai girma da ɗaukaka -, da sallah, da kuma karatun Alkur'ani. Sai ya umarci wani mutum daga cikin mutanen sai ya zo da guga na ruwa sai ya kwara akai, wato: ya zuba shi akai [177]. [177] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (219) a takaice, da Muslim, a lamba ta (285).

Kuma babu saɓani cewa fitsari da makamancinsa na daga cikin najasa da wajibi ne a kiyaye masallatai daga gare su, tunda tsarkinsu sharadi ne. Don haka, a kiyaye masallatai da shimfiɗunsu da abin da ya haɗa da su na filayensu da saman gine-ginensu da makamantansu daga dukkan najasa, kuma a tsarkake su a duk lokacin da wani abu daga wannan ya auku a cikinsu.

Haka kuma an ruwaito tsarkake su daga kazanta kamar kaki, da majina, da yawu, da jini, da mugunya, da makamantansu, daga Anas bn Malik - Allah ya yarda da shi - cewa Annabi tsira da amincin Allah su tabbata agare shi- ya ga Kaki a Alkibla, don haka yana da wahala gare shi har sai da aka hakan a fuskarsa, don haka sai ya tashi ya goge da hannunsa, sai ya ce: Idan dayanku ya tsaya a cikin sallarsa, to lallai yana ganawa ne da Ubangijinsa, ko kuma Ubangijinsa yana tsakaninsa da Alkibla, don haka kada ɗayanku ya yi tofi ta gabanin alkiblarsa, amma ya tofa ta hagunsa ko ƙarƙashin ƙafafunsa. Sannan ya ɗauki gefen mayafinsa, sai ya tofa a ciki, sannan ya mayar da wani ɓangare a kan wani, sai ya ce: "Ko kuma ya yi haka". [178]. [178] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (405), da Muslim, a lamba ta (551).

Akwai hadisai masu yawa da suke nuni akan hanin tofar da yawu da kaki a cikin Masallaci, a wasunsu kuma akwai hani akan mutum ya tofa a gaban Alkibla ko ta gefen dama, da kuma izinin tofarwa a gefen hagu ko kuma karkashin kafar hagu, sannan ya murje shi da kafa. Kuma babu shakka cewa tofar da yawu da kaki suna daga cikin abubuwan da ake kyama a dabi'a, saboda haka Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi fushi lokacin da ya ga tofar da yawu a alkiblar Masallaci, har fuskarsa ta yi ja, kuma ya gaggauta goge shi sannan ya shafa wurin da turaren khaluk ko zafaran.

Kuma an sani cewa idan masallaci an gina shi da laka, to goge shi abu ne mai sauki, kuma kasar turbaya ce, za a iya binne abin da ya fada a ciki, ko a fitar da turbayarta mai kazanta.

Ganin cewa Masallatai a wadannan lokutan galibi an yi musu dabe kuma an shimfida musu shimfidu masu tsafta, wadanda datti da kazanta ke saurin kamawa, kuma alamar kaki da jini da dafi da makamantansu na bayyana a cikinsu, ya zama wajibi a hana tofa miyau a kasansu kwata-kwata, ko a kan shimfidu ne, ko a bango, ko kuma a kan dabe. Duk wanda tofar miyau ko kaki ya zo masa, to ya fita waje don yin hakan, ko kuma ya tofa a cikin mayani sannan ya fita da shi, ko a gefen rigarsa ya nade sashin a kan sashi kamar yadda aka ambata a Hadisi, domin Masallacin ya dawwama cikin tsafta da kyau.

Kuma daga Nana Aisha Allah ya yarda da ita ta ce Manzon Allah -tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi umarni da a gina masallatai a cikin gidaje, kuma a tsaftace su, a kuma sanya musu turare. Sufyan ya ce: "Ginin masallatai a cikin gidaje yana nufin: a cikin unguwanni"[179]. [179] Tirmizi ne ya ruwaito shi, a lamba ta (594), kuma a duba: "Fasali-fasali da Masa'aloli da suka shafi Masallatai" (shafi na 27).

Matashiya Ta Biyar: Hukuncin gina Masallaci a kan kabari ko shigar da Kabari a cikin Masallaci

Ba ya halatta gina masallaci akan kabarin kowa koma waye shi; domin lallai wannan an yi hani akansa, Shaikhul Islam IbnuTaimiyyah Allah ya yi masa rahama ya ce: Manyan Malamai sun yi ittifaki a kan cewa ba a gina masallaci a kan kabari; domin Annabi -tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi- ya ce: "Lallai waɗanda suka gabace ku sun kasance suna riƙar ƙaburbura masallatai, ku saurara kada ku riƙi ƙaburbura masallatai; lallai ni na hanaku yin hakan."

Kuma lalle bai halatta a binne mamaci a masallaci ba, idan masallacin ya kasance kafin binnewar ne to a canza shi: ko dai a daidaita kabarin, ko kuma a tone shi idan ya kasance sabo ne.

Kuma idan ya kasance an gina masallacin bayan kabari: to ko dai a gusar da masallacin, ko kuma a gusar da siffar kabarin, saboda masallacin da yake kan kabari, ba'a sallar farilla ko ta nafila a cikinsa; domin an yi hani akan hakan[180]. [180] Majmu al-Fatawah (194/22).

Kuma daga cikin dalilai kan haka, banda abin da Shehin Musulunci -Allah ya yi masa rahama- ya ambata: Daga Nana Aisha da Abdullahi dan Abbas, sun ce: A lokacin da mutuwa ta zo ga Annabi ﷺ, sai ya fara dora mayafinsa a kan fuskarsa, idan hakan ya takura masa, sai ya yaye shi daga fuskarsa, sai ya fada, yana cikin wannan hali: «Tsinuwar Allah ta tabbata a kan Yahudawa da Nasara, sun riƙi ƙaburburan Annabawansu masallatai» Yana gargaɗi daga kwatankwacin abinda suka aikata [181]. [181] Bukhari ne ya ruwaito shi a lamba ta (435), da Muslim a lamba ta (531).

Manzon Allah ﷺ ya bayyana a lokacin da yake bugun mutuwa cewa Allah Mai girma da daukaka ya la’anci Yahudu da Nasara saboda sun riki kaburburan annabawansu masallatai, kuma ya bayyana cewa hakan ya kasance al'adar kafiran da suka gabata, domin ya gargadi al’ummarsa daga yin kama da su, kuma domin ya toshe musu kofar shirka da Allah da bautar waninsa.

Daga Nana A'isha Uwar Muminai, cewa Ummu Habibah da Ummu Salamah sun ambaci wata coci da suka gani a Habasha a cikinta akwai hotuna, sai suka ambatawa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sai ya ce: «Lallai waɗannan mutane idan mutumin kirki ya kasance a cikinsu ya mutu, sai su gina masallaci a kan ƙabarinsa, kuma su suranta waɗancan hotunan a cikinsa, to waɗancan su ne mafi sharrin halitta a wajen Allah a ranar alƙiyama» [182]. [182] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (427), da Muslim, a lamba ta (528).

Daga Nana A'isha - Allah Ya yarda da ita - ta ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya faɗa a cikin rashin lafiyarsa wacce bai tashi daga gareta ba: «Allah Ya tsinewa Yahudawa da Nasara, sun riƙi ƙaburburan Annabawansu masallatai» Da badan haka ba da an bayyanar da ƙabarinsa, sai dai cewa an ji tsoron a riƙe shi a matsayin masallaci [183]. [183] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (1390), da Muslim a lamba ta (529).

Matashita Ta Shida: Hukuncin ƙawata Masallatai

Bai kamata a ƙawata masallatai da kuma yin alfahari da su ba, domin kuwa Bukhari ya ruwaito daga Abdullahi bn Abbas - Allah ya yarda da shi - ya ce: "Lallai za ku ƙawata su kamar yadda Yahudawa da Nasara suka ƙawata".

Daga Anas ɗan Malik - Allah Ya yarda da shi - cewa ya ce: «Suna yin fariya da su, sannan ba sa rayasu sai kaɗan».

Kuma an ambata daga Umar - Allah ya yarda da shi - cewa ya yi umarni da gina Masallatai, kuma ya ce: «Ka kange mutane daga ruwan sama, kuma ka kiyayi sanya ado da ja ko rawaya; domin kada ka fitini mutane»[184]. [184] Bukhari ne ya ambaci wadannan Athar din a cikin «Sahihinsa» a rataye, da sigar tabbatarwa (1/ 96- 97).

Kuma hakika nuna isa ya yawaita a wadannan lokutan dangane da Masallatai, kuma mutane sun wuce gona da iri wajen ƙawata su da yawan kashe kuɗi a kansu. Kuma Malamai sun bayar da fatawar halaccin kyautata gininsu idan har an kyautata ginin gidajen zama, domin kada masallatan su zama munana kuma wulaƙantattu idan aka kwatanta su da gidaje. Amma ba tare da barna da wuce gona da iri ba wajen yin ƙawa da kaloli da kuma fenti kala-kala, da kuma banbanta nau'ikan abubuwan da ake kashewa a cikinsu na fale-fale da tayils da shimfiɗu wanda babu buƙatarsa. Alhali an san cewa akwai wasu masallatai da ke buƙatar gyara mafi ƙanƙanta, saboda haka ya kamata a karkatar da dukiyoyin zuwa ga gyaran waɗancan masallatan.

Daga Abdullahi ɗan Umar - Allah Ya yarda da su -, «Cewa lallai masallaci ya kasance a zamanin Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - an gina shi da tubali, rufinsa kuwa azara ce, ginshiƙansa kuma itacen dabino ne. Abubakar bai ƙara komai a ciki ba. Umar kuma ya ƙara a ciki, ya gina shi a kan tsarinsa na zamanin Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - da tubali da azara, kuma ya sake mayar da ginshiƙansa na katako. Sannan Usman ya canza shi, ya yi ƙari mai yawa a ciki; ya gina ganuwarsa da duwatsu masu ado da sumunti, ya sanya ginshiƙansa na duwatsu masu ado, rufinsa kuma ya yi shi da katakon Saji» [185]. [185] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (446).

Babban Malami Abdul-Azeez Bn Baaz Allah ya yi masa Rahama ya ce: Aikin Usman - Allah Ya yarda da shi - yana nuni kan halascin kyautata Masallaci da duwatsu masu zane, da itace masu kyau, da kuma fentin bango, babu laifi a cikin hakan, ko da yake rayuwar magabata ita ta fi dacewa kuma ta fi falala, amma idan mutane suka kyautata gidajensu, kuma suka guji tsofaffin gine-gine, sannan ya zama barin masallacin a kan tsohon yanayinsa na iya sa su guji sallah da taruwa a masallatai, to babu laifi a aikata irin abin da Usman - Allah Ya yarda da shi - ya yi domin janyo hankali zuwa ga masallatai; amma don nuna isa, to a'a. Kuma abin ƙi ne a yi rubutu a cikin masallaci, abin da ya fi shi ne ya kasance babu ado"[186]. [186] An ciro shi daga al-Masajid na al-Qahtani (sh: 71).

Matashiya Ta Bakwai: Hukuncin shigar kafiri masallaci

Haramun ne a kan Musulmai su baiwa wani kafiri damar shiga Masallaci Mai alfarma da dukkanin Haramin da ke kewaye da shi; kuma dalili a kan haka shi ne fadinSa Madaukaki: Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Abin sani kawai, mushirikai najasa ne, sabõda haka kada su kusanci Masallaci Mai Alfarma a bãyan shẽkarar su wannan... [al-Taubah: 28], Amma sauran masallatai, idan shigarsu ya kasance don wata manufa ce ta shari'a, to babu laifi a cikin hakan, kamar tambaya game da Musulunci, ko wani aiki da ya shafi masallacin, ko don maslahar Musulmai, ko don ya saurari wa'azi, ko ya shiga don wani abu halattacce kamar ya sha ruwan da ke cikin masallacin. A irin wadannan yanayi hakan ya halatta, saboda Annabi -tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi- ya taɓa ɗaure Sumama ɗan Usal a wani turken masallaci. An karɓo daga Abu Huraira -Allah ya yarda da shi- ya ce: «Annabi ﷺ ya aika da dawakai zuwa Najd, sai suka zo da wani mutum daga Banu Hanifa ana ce da shi Sumama dan Asal, suka daure shi a Durka daga cikin Durakun masallacin. Sai Annabi ﷺ ya fito zuwa gare shi ya ce: «Me kake da shi, ya Sumama?». Sai ya ce: «Akwai alheri a wurina, ya Muhammadu. Idan ka kashe ni, ka kashe mai jini ne, idan kuma ka yi ni'ima, ka yi wa mai godiya ne. Kuma idan dukiya kake so, to ka roka daga cikinta abin da ka so». Sai ya kyale shi har washegari…» Hadisin[187]. An haɗu a kansa [187].

Kuma tawagar Najran sun shiga masallaci alhali su Nasara (Kisitoci) ne[188], kuma Dimam Dan Sa'alaba ya shiga wurin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - alhali yana cikin masallaci. Daga Anas Dan Malik - Allah ya yarda da shi - ya ce: «Muna zaune tare da Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a cikin masallaci sai wani mutum ya shigo akan wani rakumi, sai ya dirkusar da shi a cikin masallaci sannan ya daure shi, sannan ya ce da su: Waye Muhammad a cikinku? alhali Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana kishingide a tsakaninsu, sai muka ce: Wannan farin mutumin wanda ke kishingide, sai mutumin ya ce da shi: Dan Abdul Mudallib, sai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce da shi: «Hakika na amsa maka», sai mutumin ya cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: Ni mai tambayarka ne mai tsananta maka a tambaya, kada ka ji haushi na a ranka? sai ya ce: «Ka tambayi abinda ya bayyana gareka»... har zuwa inda ya ce: sai mutumin ya ce: Na yi imani da abinda ka zo da shi, kuma ni manzo ne na wadanda ke bayana cikin mutane na, kuma ni ne Dimam dan Sa'alabata dan uwan Banu Sa'ad dan Bakar» [189]. An haɗu a kansa [188]. [189] Bukhari ya ruwaito shi. Kuma a duba: Majmu'u Fatawa wa Maqalat Ibnu Baz, Mujalladi na takwas, Hukuncin shigar kafirai masallatai, da Fatawowin Kwamitin Dindindin 6/276.

Wannan shi ne abin da muka samu damar kawowa game da abin da Ladan da Liman da kuma Mai huɗuba suke buƙata, da kuma hukunce-hukuncen masallatai, kuma muna yi wa Ladan da Liman da kuma Mai huɗuba wasiyya da tsoron Allah Mai girma da ɗaukaka, da kuma ƙwazo wajen neman ilimi da yaɗa shi, da kuma mayar da hankali kan haka.

Wannan kenan, kuma Allah ne Mai datarwa, Allah Ya yi salati da aminci ga Annabinmu Muhammadu da alayensa da sahabbansa baki ɗaya, kuma ƙarshen addu'ar mu shine, 'Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai'.

Wasu daga cikin madogara Masu Amfani ga Ladan da Liman da mai huɗuba

Kiran Sallah da Iƙama, Na Dokta Sa'id bn Ali bn Wahf al-Qahtani, Mawallafi: Maɗaba'ar Safir, Riyad.

Hukunce-hukuncen limanci da bin liman a sallah, Na Dr. Abdul-Muhsin Al-Munif.

Limanci a sallah a mahangar Alkur’ani da Sunnah: Sa'id Bn Ali Bn Wahf Al-Kahdani.

Salon Hudubar Jumu'a, Na Abdullahi ɗan Ḍaifullahi Ar-Ruhaili, Maɗaba'a: Ma'aikatar Harkokin Addinin Musulunci Da Da'awa Da Shiryarwa, Masarautar Saudi Arabiya.

Limanci a Sallah - Ma'anarsa, da falalolinsa, da ire-irensa, da ladubbansa, da hukunce-hukuncensa a cikin hasken Alkur’ani da Sunnah, na Dakta Sa'id bin Ali bin Wahf al-Qahtani, Wanda ya buga: Madaba'ar Safeer, Riyadh.

Hudubobin Jumu'a da Nauyin dake kan Limamai, Tsarawa: Majalisar Da'awa da Shiriya, Ma'aikatar Harkokin Musulunci da Da'awa da Shiriya, Masarautar Kasar Saudiyya.

Hudubar Jumu'a a cikin Alkur’ani da Sunnah, na Abdurrahman bin Muhammad Al-Hamd, Mawallafi: Ma'aikatar Harkokin Addinin Musulunci da Da'awah da Shiryarwa, Masarautar Larabawa ta Saudiya.

Hudubar Juma’a da Hukunce Hukuncen ta Na Fiqihu, Wallafar Abdul'aziz ɗan Muhammad ɗan Abdullah Al-Hujailan, Masu Bugawa: Ma'aikatar Harkokin Addinin Musulunci da Da'awa da Shiryarwa, Cibiyar Bincike-Bincike da Nazari na Musulunci.

Hudubar Jumu'a da Rawar da tasirinta Wajen Tarbiyyantar da Al'umma, Na Abdulganiyyu Ahmad Jabr Muzhir, Masu Bugawa: Ma'aikatar Harkokin Addinin Musulunci Da Da'awa Da Shiryarwa, Masarautar Saudiyya.

Wasiyyoyi Guda Hamsin da Ɗaya Domin Zama Mai Huɗuba Mai Nasara, Na Amir ɗan Muhammad Al-Madari, wanda aka buga a shafin yanar gizo na Ma'aikatar Kula da Al'amurran Musulunci da Da’awah da Shiryarwa, ta Masarautar Ƙasar Saudiyya.

Sallar Jumu'a - Ma'anarta, da Sharuddanta, da Falalolinta, da Kébantattun Siffofinta, da Ladubbanta, da Hukuncinta a Mahangar Alkur’ani da Sunnah, na Dakta Sa'id bn Ali bn Wahf al-Qahtani, Mawallafa: Matba'ar Safeer, Riyadh.

Munbarin Juma'a Amana da kuma Nauyi, Na Abdullahi dan Muhammad dan Humaid, Maɗaba'a: Ma'aikatar Harkokin Musulunci da Da’awah da Shiryarwa, Masarautar Saudiyya.

Manhaji wurin shirya Hudubar Jumu'a, Na Dakta Salih Bn Abdullahi Bn Humaid, Wanda ya buga: Ma'aikatar harkokin addinin musulunci da Da’awah da shiryarwa, Masarautar Saudiyya ta Larabawa.

Saƙonni ga Limamai da Ladanai na Shiekh Abdullahi bn Salih Al-Fauzan, Dar Ibn Al-Jauzi.

Sako zuwa ga Limaman Masallatai da Ladanai da màmùmai, Na Shiekh Abdullahi Bn Jarullah Aljarullah.

Bakandamiyar FIƘHU ta Kuwait, da kuma babin Huduba, da Limanci, da Kiran Sallah, da Masallatai.