آداب السفر وأحكامه
LADUBBAN TAFIYA DA HUKUNCE-HUKUNCENTA Dukkanin godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai, tsira da aminci su tabbata ga Annabimmu Muhammad da alayansa da sahabbansa baki ɗaya.
LADUBBAN TAFIYA DA HUKUNCE-HUKUNCENTA Dukkanin godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai, tsira da aminci su tabbata ga Annabimmu Muhammad da alayansa da sahabbansa baki ɗaya.
Bayan haka:
Wannan taƙaitaccan saƙo ne ne akan LADUBBAN TAFIYA DA HUKUNCE HUKUNCENTA, mun yi ƙoƙarin kawo bayanin mafi yawan abinda matafiyi yake da buƙata zuwa gareshi.
Allah kaɗai nake roƙo da Ya sanya wannan aikin domin Shi ne kaɗai, kuma Ya anfani da al’ummar musulmi baki ɗaya.
Kwamitin ilimi na Cibiyar hidimar abinda Musulunci ya ƙunsa a cikin harsuna daban daban.
Na farko: Ladubban tafiya
Yana kamata ga duk wanda zai yi tafiya zuwa aikin Hajji ko waninsa na ibada da ya yi la’akari da waɗannan abubuwan da ke tafe:
1- Ya baiwa Allah - tsarki ya tabbatar maSa - zaɓi a lokacin tafiya, da abin hawa, da abokin tafiya, da hanyar da za’a bi, idan hanyoyin suna da yawa. Sai kuma ya shawarci masana da mutanan kirki akan hakan. Amma a Hajji da Umarah to su alheri ne babu wata shakka akan hakan. Siffar yadda ake bawa Allah zaɓi (Istikharah): Ita ce: ya yi sallah raka’a biyu sannan ya yi addu’ar da aka ruwaito daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -.
Yana wajaba ga mahajjaci da mai Umrah ya nufaci Allah - Maɗaukakin sarki - a hajjinsa da kuma Umrarsa, ya nemi kusanci zuwa gareShi, ya yakiyayi nufatar rabon duniya da alfahari ko tara laƙabubbuka ko riya ko jiyarwa; domin hakan yana zama sababi na lalata aikin da kuma rashin karɓarsa, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: (Ka ce: "Nĩ, mutum ne kawai kamarku, anã yin wahayi zuwa gare ni cewa: Lalle ne, Abin bautawarku, Abin bautawa Guda ne, sabõda haka wanda ya kasance yanã fãtan haɗuwa da Ubangijinsa, to, sai ya yi aiki na ƙwarai. Kuma kada ya haɗa kõwa ga bauta wa Ubangijinsa) [al-Kahf: 110]. Ya kuma ya zo a Hadisi Ƙudusi: «Ni ne Mafi wadatuwa da shirkar masu shirka, duk wanda ya yi wani aiki kuma ya haɗaNi da wani a cikinsa zan bar shi da shikarsa». [1] Muslim ne ya ruwaito, a lamaba ta (2985).
Ya wajaba ga maniyyaci (da Hajji) ko Umrah ya nemi sanin hukunce-hukuncen Hajji da Umrah, da kuma sanin hukunce-hukuncen tafiya kafin ya fara tafiyar; dan kada ya bar wani wajibi ko ya faɗa cikin haram, Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: «Duk wanda Allah Yake nufinsa da alheri zai fahimtar da shi Addini»[12]. (2) Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (3116), da Muslim, a lamba ta (100).
4.Ya wajaba ga maniyyaci da Hajji ko Umarah ya zaɓi dukiya ta halal domin gudanar da Hajjin sa da Umrarsa; domin cewa Allah Mai tsarki ne ba Ya karɓa sai mai tsarki; kuma domin ita dukiya ta haram sababi ce ta rashin amsa addu’a.
5.Tuba daga barin dukkan zunubai da laifuffuka, idan akwai kayan mutane da ya zalince su a wurinsa sai ya mayarwa kowa, daidai ne sun kasance haja ce ko kuɗi ko wanin haka.
6. An so ga ga matafiyi ya rubuta wasiyyarsa, da abinda yake bin mutane, da kuma abinda mutane suke bin sa; Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: «Bai da ce ga mutum musulmi ba yana da wani abin da zai yi wasiyya da shi, ya zauna kwana biyu face sai wasiyyarsa ta kasance a rubuce tare da shi»[3] Sai ya kafa shaida akanta, ya biya basussukan da ake binsa, ya kuma mayar da kayan ajiya ga masu ita, ko kuma ya nemi izinin su wurin ci gaba da zamanta (a wurinsa). [3] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (2738), da Muslim, a lamba ta (1627).
An so ga matafiyi ya yi iya ƙoƙari wurin zaɓin abokin tafiya nagari, kuma ya yi ƙoƙari (abokin) ya kasance cikin ɗaliban ilimin shari'a; domin hakan yana cikin sabubban datar da shi da kuma rashin afkawarsa cikin kuskure a tafiyar tasa da Hajjin sa da kuma Umrarsa; saboda faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: «Mutum yana kan Addinin abokinsa, saboda haka ɗayanku ya duba wanda zai yi abokantaka (da shi)»[4]; da kuma faɗinsa - Annabi tsira da amncin Allah su tabbata su tabbata agare shi -: «Kada ka yi abota da kowa sai mumini, kuma kada wani ya ci abincinka sai mai tsoron Allah»[5]. [4] Abu Dawud ne ya rawaito shi, a lamba (4833). 4] Abu Dawud ne ya ruwaito shi, a lamba (4832), da Tirmizi a lamaba ta (2395).
8. An so ga matafiyi ya yi bankwana da iyalansa, da ‘yan uwansa, da maƙwabtansa da abokansa, Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: «Wanda ya yi nufin tafiya to ya ce wa wanda ya bari (a gida): Ina bada kulawarku ga Allah, wanda ajiyoyin da aka ba Shi ba sa wulaƙanta»[6]. Kuma Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance yana bankwana da sahabbansa idan ɗayansu ya yi nufin yin wata tafiya sai ya ce: «Ina ba Allah kulawar Addininka, da amanarka, da ƙarshen ayyukanka»[7]. Kuma Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana cewa ga duk wanda ya nemi ya yi mishi wasiyya daga cikin matafiya: «Allah Ya yi maka guzurin jin tsoranSa, Ya gafarta maka zunubinka, kuma Ya sauƙaƙa maka alheri a duk inda kake»[8] Wani mutum ya zo wurin Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana son zai yi tafiya, sai ya ce: Ya Manzon Allah! ka yi min wasiyya, sai ya ce: «Ina maka wasiyya da jin tsoron Allah, da yin kabbara a kan kowane tudu", lokacin da ya tafi, sai ya ce: "Ya Allah Ka naɗe masa ƙasa, kuma Ka sawwaƙe masa tafiyar» [9]. [6] Ɗabarani ne ya ruwaito shi, a Lamba ta (823). [7] Ahmad ne ya ruwaito a Musnad, a lamba (4524). [8] Tirmizi ne ya ruwaito, a lamba (3444). [9] Ahmad ne ya ruwaito a Musnad, a lamba (9724).
9. Kada kuma ya tafi da ƙararrawa da garayu da kare a halin tafiya tare da shi; saboda hadisin Abu Hurairah - Allah Ya yarda da shi - cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: «Mala'iku ba sa tafiya da ayarin da a cikinsa akwai kare ko ƙararrawa» [10]. [10] Muslim ne ya ruwaito, a lamaba ta (2113).
10. Idan ya yi nufin yin tafiya da ɗaya daga cikin iyalan sa, idan yana da sama da mace ɗaya to sai ya yi ƙuri’a a tsakanin su, to duk wacce lambarka ta fito sai ya tafi da ita, saboda hadisin Nana Aisha - Allah Ya yarda da ita - ta ce: «Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance idan yana son zai yi tafiya sai ya yi ƙuri’a a tsakanin matansa, duk wacce ƙuri’arta ta fito sai ya tafi tare da ita»[11]. [11] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (2593), da Muslim, a lamba ta (2770).
11. An so ga matafiyi ya tafi ranar alhamis a farkon yini, idan hakan ya sawwaƙa gare shi, saboda aikinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - Ka’abu ɗan Malik - Allah Ya yarda da shi - ya ce: «Kaɗan ne Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance yake fita tafiya ba ranar Alhamis ba»[12]. [12] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (2949).
12. An kuma so ga matafiyi ya yi Addu’ar fita daga gida a lokacin tafiyarsa da wanin hakan, sai ya ce a lokacin fitarsa: «Bismillah, na dogara ga Allah, babu dabara kuma babu ƙarfi sai ga Allah, ya Allah ina neman tsarinKa akan kada in ɓata ko a ɓatar da ni, ko in zame ko a zamar da ni, ko in yi zalinci ko a zalinceni, ko in yi wauta ko a yi min wauta» [13]. [13 Abu Dawud ne ya rawaito shi, a lamba (5094).
13. An so ga mai tafiya da ya yi Addu’ar tafiya, idan ya hau abin hawansa, motarsa ko jirgi ko wanin haka na ababan hawa, sai ya ce: «Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allahu Akbar {Subahanallazi sakhkhara lana haza wama kunna lahu muƙrinina wa'inna ila rabbina lamunƙalibuna} [al-Zukhruf: 14], Allahumma inna nas'aluka fi safarina hazal birra wattaƙwa, wa minal amali ma tardha, Allahumma hawwin alaina safarana haza, waɗwi anna bu'udahu, Allahumma antas Sahibu fis safar, wal khalifa fil ahl, Allahumma inni a'uzu biKa min wa'asayis safar waka'abatil manzar wa su'il munƙalab fil mali wal ahl. Ma’ana: (Allah ne Mafi girma, Allah ne Mafi girma (Tsarki ya tabbata ga wanda Ya hore mana wannan alhali bamu da wani iko gare shi, kuma lallai mu masu komawa ne ga Ubangijinmu) [al-Zukhruf: 14], ya Allah lallai mu muna roƙonKa aikin alheri da tsoron Allah a cikin wannan tafiya ta mu, da kuma aikin da Ka yarda da shi, ya Allah Ka sauƙaƙa mana wannan tafiyar ta mu, kuma Ka ninke mana nisanta, ya Allah Kaine kake tare da mu a cikin tafiya, kuma kai ne mai mayewa a cikin iyalai, ya Allah ni ina neman tsarinKa daga wahalhalun tafiya, da mummunan abin gani, da mummunan juyowa a cikin dukiya da kuma iyalai. (14) Wa’atha’is Safar: Ita ce wahalhalun tafiya, a duba al’ifsah an ma’anis Sihah (4/284). (15) Mummunan yanayi da baƙin ciki. al’ifsah an ma’anis sihah, (4/284). (16) Almunƙlib: Shi ne komawa. al’ifsah an ma’anis sihah (4/284). (17) Ahmad ne ya ruwaito a Musnad, a lamba (6374).
An so ga matafiyi da kada ya yi tafiya shi kaɗai ba tare da abokan tafiya ba; saboda faɗin Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: «Da mutane sun san abinda yake cikin kaɗaitaka irin abinda na sani, da matafiyi bai yi tafiya da daddare shi kaɗai ba»[18]. [18] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (2998).
15. Matafiya su shugabantar da ɗaya daga cikinsu; don ya zama mai haɗa kansu, kuma mafi tattara abinda suka yi ittifaki akai, kuma mafi tabbas wurin samun abinda suke so, (Annabi) tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: «Idan mutum uku suka fita tafiya to su naɗa ɗayansu ya zama shugaba»[19]. [19] Abu Dawud ne ya rawaito shi, a lamba (2608).
16. (Matafiyi) ya yi iya ƙoƙarinsa na abinda Allah Ya ɗora masa na biyayya da kuma nisantar abubuwan da aka haramta, kuma ya ɗabi’antu da ɗabi’u na ƙwarai, sai ya taimakawa wanda yake buƙatar taimako, ya taimaki wanda yake buƙatar taimako da agaji, ya kuma bada ilimi ga mai nemansa da mai buƙatuwa zuwa gare shi, ya zama mai kyauta da dukiyarsa, ya yi anfani da ita wurin biyan buƙatar kansa da ‘yan uwansa da kuma buƙatunsu.
17. Kuma yana kamata ya yi guzuri da yawa na abinci da buƙatun tafiya, domin takan yi wu wasu buƙatu su ta so, al’amura kuma su canza.
18. A dukkan hakan ya kamata ya zama mai sakin fuska, mai daɗin mu’amala, mai kwaɗayin sanya farin ciki ga abokan tafiyarsa, domin ya zama mai sauƙin hali, wanda za’a saba da shi.
19. Ya kamata ya yi haƙuri akan abinda zai faru na wawancin abokan tafiyarsa da yadda za su saɓawa ra’ayin sa, ya tafiyar da su da abu mafi kyau, domin ya kasance abin mutuntawa a cikinsu abin girmamawa a zukatansu.
20. An so idan matafiya suka isa zango sashinsu ya haɗu da sashi, domin sahabban Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - sun kasance idan suka isa zango sai su rarrabu a gindin bishiyoyi da kwari, sai Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: «Lallai cewa rarrabuwarku a cikin wadannan wurare da kwari wannan daga Shaidan ne» [20]. sai suka kasance sashinsu yana haɗuwa da sashi, ta yadda da za'a shinfiɗa mayafi da ya yalwace su. (20).Ahmad ne ya ruwaito a Musnad, a lamba (17736).
An so idan ya isa masauki yana a halin tafiya ko wanin haka na masaukai ya yi addu’a da abinda ya tabbata daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: «Ina neman tsari da kalmomin Allah cikakku daga sharrin abinda Ya halitta». To shi idan ya faɗi hakan babu abinda zai cutar da shi har sai ya bar wannan masaukin. [21] Muslim ne ya ruwaito shi, a lamaba ta (2708).
22. Kuma an so gare shi ya yawaita Kabbara idan zai hau tudu, idan zai gangara kwari kuma sai ya yi Tasbihi, Jabir - Allah Ya yarda da shi - ya ce: "Mun kasance idan zamu hau (tudu) sai mu yi kabbara, idan kuma mun gangara sai mu yi Tasbihi"[22], Kada su ɗaga muryarsu da yin Kabbara, Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -ya ce: «Ya ku mutane! Ku sauƙaƙawa kanku, domin ku ba kwa kiran kurma ko wanda ba ya nan, lalle Shi Yana tare da ku, lalle Shi Mai ji ne kuma Makusanci ne»[23]. [22] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (2994). [23] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (2993).
23. Kuma an so a lokacin tafiyar yayi tafiya da daddare musamman farkon dare, saboda faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: «Na umarce ku da yin tafiya cikin duhun dare, Saboda ƙasa ana naɗeta da daddare»[24]. [24] Abu Dawud ne ya rawaito shi, a lamba (2571).
24. An so gare shi ya yawaita addu’a a halin tafiya, saboda faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: «Addu’o’i uku ababan amsawa ne babu kokwanto a cikin su: Addu’ar wanda aka zalinta, da addu’ar matafiyi, da addu’ar uba akan ɗan sa»[25]. [25] Ahmad ne ya ruwaito a Musnad, a lamba (10771).
***
NA BIYU: TSARKI A HALIN TAFIYA
Yana wajaba matafiyi ya kula da tsarkinsa, ya yi alwala saboda ƙaramin hadasi, ya kuma yi wanka na janaba.
Idan bai sami ruwa ba, ko kuma yana da ruwan kaɗan yana buƙatarsa domin abincinsa da abin shansa, to sai ya yi taimama.
Siffar taimama: Ya bigi ƙasa da hannayansa, sai ya shafi fuskarsa da tafukansa biyu da su.
Tsarki na taimama tsarki ne na ɗan lokaci, saboda haka a duk lokacin da ya sami ruwa to taimamar ta ɓaci, ya wajaba ya yi anfani da shi. Idan ya yi taimama saboda janaba sannan ya sami ruwa, to ya wajaba ya yi wankan janabar, idan ya yi taimama saboda bayan gida sannan ya sami ruwa, to ya wajaba ya yi alwala a maimakon taimamar, ya zo a cikin hadisi: «Bigire mai tsarki shi ne abin alwalar musulmi, ko da bai sami ruwa ba (tsawon) shekara goma. Idan kuma ya sami ruwa to ya ji tsoron Allah ya shafi fatarsa da shi»[26]. [26] Ahmad ne ya ruwaito a Musnad, a lamba (10068).
Shafa Akan huffi biyu, ya tabbata a Alƙur’ani da sunnah da ijma’in Ahlus sunnah.
An sharɗanta wasu sharuɗɗa dan yin shafa a kan huffi biyu da abinda yake da ma’anarsu:
1. Huffun ko Jaurab ɗin su kasance na halal masu tsarki.
2. Ya sanya su bayan ya gama alwala.
3. Huffin su kasance sun rufe wurin (wankewar) farilla.
4. Shafar ta kasance a ƙaramin hadasi, ba ya halatta a yi shafa a janaba ko a abinda yake wajabta wanka.
5. Shafar ta kasance a lokacin da shari’a ta iyakance, shi ne yini da dare ga mazauni, kwanaki uku da dararan su ga matafiyi. Waɗannan lokutan a mafi ingancin magana suna farawa ne daga farkon shafar da ya yi bayan hadasi, kuma yana ƙarewa a awa ashirin da huɗu dangane da mazaunin gida, da kuma awa saba’in da biyu dangane da matafiyi.
Shafar tana ɓaci da ɗayan abubuwa uku:
1. Idan ya yi hadasin da yake wajabta wanka, kamar janaba, to shafar ta ɓaci dole sai ya yi wanka.
2. Idan ya cire su bayan ya yi shafa akan su.
3. Idan lokacin da shari’a ta ƙayyade ya ɓare to shafar ta ɓaci.
***
NA UKU: HUKUNCE-HUKUNCEN ƘASARU A HALIN TAFIYA:
Yin ƙasaru a halin tafiya shi ne ya fi akan cikawa, saidai ko da matafiyi ya cika sallah mai raka’a huɗu, ya cika ta huɗu to sallarsa ta yi, saidai ya saɓawa abinda ya fi.
Matafiyi yana yin ƙasaru ne idan ya fice daga dukkan gidajan garinsa ko birninsa, wannan kuwa shi ne mazahabar jumhurun ɗin malamai.
Idan ya yi tafiya bayan shigar lokacin sallah, to ya samu ya yi mata ƙasaru; domin ya yi tafiyar ne kafin fitar lokacin ta.
Amma haɗa Azahar da La’asar, haka kuma Magariba da Issha to wannan sunna ne ga matafiyi idan akwai buƙatar hakan, idan tafiyar ta tsananta da shi kuma ya ci gaba da ita, to sai ya yi abinda ya fi masa sauƙi na haɗawar Taƙdeem ko kuma Ta’akeer.
Amma idan matafiyi bai kasance yana da buƙatar haɗawa ba to ba zai haɗa ba, misali a ce ya sauka ne a wurin da ba ya da buƙatar ya bar wurin sai bayan shigar lokacin sallah ta biyu, to abinda ya fi kada ya haɗa; domin ba shi da buƙatar hakan, saboda haka ne Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - lokacin da ya zauna a Mina a Hajjin bankwana bai haɗa ba, saboda rashin buƙatuwar hakan.
Amma sallar nafila, to matafiyi zai yi sallar nafila wacce mazaunin gida yake yi, zai yi sallar walaha, da tsayuwar dare da wuturi da wanin su na nafilili banda na kafin Azahar da na bayanta da bayan Magariba da Issha, abinda yake sunnah shi ne kada ya yi su.
Nafila ta inganta akan abin hawa a halin tafiya: Jirgin sama ne, ko mota, ko jirgin ruwa, ko wasunsu na abubuwan jigila, amma ita farilla to dole sai an sauka za’a yi ta saidai idan hakan ya faskara.
Sallar matafiyi a bayan mazaunin gida ingantacciya ce, kuma matafiyi zai cika ne kamar limaminsa, shin ya riski dukkanin raka’oin ne ko wasu ya riska, ko da a ce ya riski liman ɗin ne a lokacin yana Tahiya kafin ya yi sallama to shi zai cika ne, wannan kuma shi ne daidai a maganganu biyu na malamai.
***
NA HUƊU: LADUBBAN DAWOWA DAGA HAJJI DA UMARAH KO KUMA TAFIYA
Ya kamata ya gaggauta dawowa, kada ya tsawaita zama a tafiya ba tare da wata buƙata ba; saboda faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: «Tafiya wata yanki ce ta azaba, tana hanawa ɗayanku abin cin sa da abin shan sa da baccinsa, idan ɗayanku ya biya buƙatarsa to ya gaggauta komawa ga iyalansa»[27]. [27] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (1804), da Muslim, a lamba ta (1927).
To idan ya yi nufin komawa garinsa, to sai ya karanta addu’ar tafiya lokacin hawa abin hawansa, sai kuma ya ƙara wannan Addu’ar: «Muna masu dawowa masu tuba masu bauta ga Ubangijimmu, masu godiya»[28]. (28) Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (1797), da Muslim, a lamba ta (1342).
An so ga matafiyi a lokacin dawowarsa daga tafiyarsa ya faɗi abinda ya tabbata daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, domin shi ya kasance idan ya dawo daga yaƙi ko Hajji ko Umarah, yana yin kabarbari ulu a dukkan tudu sannan ya ce: «La'ilaha illallahu, wahdahu lasharika lahu, lahul mulk, walahul hamd, wahuwa ala kulli shai'in ƙadir, ayibuna, ta'ibuna, abiduna, sajiduna, lirabbina hamiduna, sadaƙal lahu wa'adahu, wa nasara abdahu, wa hazamal ahzaba wahdahu. (Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kaɗai yake ba Shi da abokin tarayya, mulki naSa ne godiya taSa ce, kuma Shi mai iko ne akan dukkan komai. Muna masu dawowa, masu tuba, masu bauta, masu sujjada, masu godiya ga Ubangijinmu, Allah Ya cika alƙawarin Sa, Ya kuma taimaki bawanSa, kuma Ya rusa ƙungiyoyin ƙawance Shi kaɗai[)»29]. [29] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (4116).
An so a gare shi idan ya hango garinsu ya ce: «Muna masu dawowa masu tuba masu bauta ga Ubangijinmu masu godiya»[30], Sai ya dinga maimaita hakan, har sai ya shiga garin nasu; saboda aikin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -. [30] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (1797), da Muslim, a lamba ta (1342).
Kada ya dira ga iyalan shi cikin dare, idan tafiyar ta yi tsawo ba tare da wata buƙata ba, sai dai idan ya sanar da su hakan, kuma ya sanar da su zuwansa da daddare; domin hanin da Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - daga hakan, Jabir ɗan Abdullahi - Allah Ya yarda da su - ya ce: «Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya hana mutum ya dirarwa iyalansa cikin dare»[31]. Yana daga cikin hikimar hakan shine abinda wata ruwayar ta fassara: «Har wacce ba ta da kitso ta yi kitso[32], kuma wacce mijinta bayanan ta kimtsa»[33], A wata riwayar kuma: «Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya hana mutum ya isa ga iyalansa da daddare, don kada ya yi zatan faruwar ha'inci daga gurinsu, ko kuma ya kware musu zani».[34]. [31] Muslim ne ya ruwaito, a lamaba ta (715). [32] (Sha’asah): Wacce ta daɗe bata tsefe kai ba, kuma bata taje shi ba. (Istihdad): Shi ne amfani da ƙarfe. (Almugayyabah): Wacce mijinta ba ya nan. al-Tahrir fi sharhi Sahihi Muslim, al-Asfihani (shafi na: 292). [33] Nasa’i ne ya ruwaito shi a lamba ta (9099). [34] Muslim ne ya ruwaito shi, a lamaba ta (715).
An so ga wanda ya dawo daga tafiya ya fara shiga masallacin da ke maƙwabtaka da shi ya yi sallah raka’a biyu, saboda haka Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya yi.
An so ga mai tafiya idan ya dawo daga tafiya ya yi oyoyo da yara ƙanana na gidan shi da maƙwabtansa, ya kyautata musu (tsaraba) idan suka tare shi, an karbo daga Ɗan Abbas - Allah Ya yarda da su - ya ce: A lokacin da Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya dawo daga Makkah sai wasu ƙananan yara na Bani AbdulMuɗɗalib suka tare shi, sai ya ɗauki ɗaya ya sa a gabansa ɗayan kuma a bayansa. Abdullahi ɗan Ja’afar - Allah ya yarda da shi - ya ce: "Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kasance idan ya dawo daga tafiya sai mu tare shi, sai ya tare mu ni da Hasan ko Husaini, yace: Sai ya ɗora ɗayammu a gabansa ɗayan kuma a bayansa har muka shiga Madina" [35]. [35] Muslim ne ya ruwaito, a lamaba ta (2428).
An so tsaraba, saboda tana faranta zukata, da kawar da gaba, kuma an so a karɓeta, da kuma bada tukwici akanta, an karhanta kin karɓarta ba tare da wani abu na shari’a da ya hana ba, saboda haka ne Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Ku ba juna kyauta, za ku so juna» [36]. Kyauta tana daga cikin sabubban sanya ƙauna tsakanin musulmai. [36] Baihaƙi ne ya ruwaito shi a Sunanul Kubrah, a Lamba (11946).
Idan matafiyi ya dawo garinsu an so rungumar juna, saboda abinda ya tabbata daga sahabban Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, kamar yadda Anas ɗan Malik - Allah Ya yarda da shi - ya faɗa: "Sun kasance idan suka haɗu sai su yi musafaha (miƙa wa juna hannu), idan kuma suka dawo daga tafiya sai su rungumi juna" [37]. [37] Ɗabarani ne ya ruwaito shi a cikin al-Awsaɗ a Lamba (97).
Allah Ya yi daɗin tsira ga Annabinmu Muhammad.