المنهج لمريد العمرة والحج

المنهج لمريد العمرة والحج

كتيب يحتوي على دليل مفصل حول مناسك الحج والعمرة، يشرح بدقة الخطوات والآداب الواجب اتباعها خلال تأدية هذه الشعائر. يبدأ بالتأكيد على أهمية الحج في الإسلام كونه أحد أركان الإسلام الخمسة. ويشدد على ضرورة الإخلاص في النية واتباع سنة النبي محمد صلى الله عليه وسلم في جميع الأفعال والأقوال أثناء تأدية هذه الشعيرة المباركة.

Language: lang_ha
Prepared by: MUHAMMAD BIN SALIH AL-UTHAIMEEN
Version: 2.0
Translations 14
Bengali English Spanish Persian +10
Attachments 7
PDF
Audio
Video
+3

TSARI GA WANDA YA YI NUFIN UMARAH DA HAJJI

RUBUTUN MAI GIRMA BABBAN MALAMI MAI YAWAN SANI

MUHAMMAD BIN SALIH AL-UTHAIMEEN

ALLAH YA YI MASA GAFARA SHI DA MAHAIFANSA DA MUSULMAI BAKI ƊAYA

GABATARWA

Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, muna gode maSa, muna neman taimakonSa, muna neman gafararSa, muna tuba zuwa gare Shi, muna neman tsarin Allah daga sharrukan kawunanmu, da munanan ayyukanmu, wanda Allah Ya shiryar da shi babu mai ɓatar da shi, wanda kuma Ya ɓatar babu mai shiryar da shi. Ina shaida cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Shi kaɗai Yake, ba Shi da abokin tarayya, ina kuma shaida cewa Annabi Muhammad bawanSa ne kuma manzanSa ne - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, da alayensa da sahabbansa, da wanda ya biyosu da kyautatawa zuwa ranar sakamako, da aminci amincewa, bayan haka:

Lallai aikin Hajji yana daga cikin mafifitan ibadu kuma mafi girman ayyukan biyayya; domin shi ɗaya ne daga cikin rukunan Musuluncin da Allah Ya aiko (Annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - da shi, waɗanda addinin bawa ba ya tsayuwa sai da su.

Yayin da ibada ta kasance, neman kusanci zuwa ga Allah ba ya tabbata da ita, kuma bata kasancewa karɓaɓɓiya sai da al'amura biyu:

Na farkonsu: Tsarkake (ibada) saboda Allah - Mai girma da ɗaukaka -; shi ne ya nufi fuskar Allah da gidan lahira da ita, kada kuma ya nufi riya ko jiyarwa da ita.

Na biyu: Bin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - a cikinta, faɗa da aikatawa; kuma bin Annabi - tisra da amincin Allah su tabbata a gare shi - ba ya yi wuwa sai da sanin sunnar Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -. Saboda haka ya kasance babu makawa ga wanda yake nufin tabbatar da bin (Annabi) da ya san sunnarsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -; bari ma dai, ya karɓeta daga ma'abota saninta; ko dai ta hanyar rubutu ko ta hanyar baki da baki. Ya kasance daga wajibin ma'abota ilimi waɗanda suka gaji Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - suka kuma maye gurbinsa a cikin al'ummarsa shi ne su ɗabbaƙa ibadunsu da ɗabi'unsu da mu'amalolinsu akan abin da suka san shi daga sunnar Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, kuma su isar da hakan zuwa ga al'umma kuma su kirasu zuwa gare shi; don gadon Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya tabbata garesu a ilimi da kuma aiki, da isarwa da kuma Da’awah, don kuma su zama daga masu rabauta waɗanda suka yi imani suka aikata aiki na gari, suka yi wa juna wasiyya da bin gaskiya, kuma suka yi wa juna wasiyya da yin haƙuri.

Wannan shi ne taƙaitawa a cikin abinda ke rataye da ayyukan Hajji da Umarah, na tsara a littafin akan abinda na san shi daga nassosin Littafi (Alkur’ani) da Sunnah, ina mai ƙauna daga Allah - Maɗaukakin sarki - ya zama tsarkakakke gare Shi, kuma mai amfani ga bayinSa.

Mawallafi

* * *

LADUBBAN TAFIYA

Yana kamata ga wanda ya fita zuwa ga Hajji ko waninsa na ibadu ya halarto niyyar neman kusanci zuwa ga Allah - Maɗaukakin sarki - a cikin dukkanin halayensa; don maganganunsa da ayyukansa da ciyarwarsa su zama mai kusanto da shi zuwa ga Allah - Maɗaukakin sarki -. «Dukkan ayyuka basa ingantuwa sai da niyyoyi, kuma kowane mutum ana ba shi ladan abinda ya niyyata ne [1]». [1] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin farkon wahayi, babin yaya farkon wahayi zuwa ga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kasance, lamba ta (1). Da Muslim: Littafin shugabanci, babin faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: «Dukkan ayyuka basa ingantuwa sai da niyya», Kuma yaƙi da waninsa daga ayyuka suna shiga cikinsa, lamba ta (1907), daga hadisin Umar bn Al-Khaɗɗab - Allah Ya yarda da shi -.

Yana kamata ya ɗabi'antu da mafifitan ɗabi'u, misali: Karamci da kau da kai da jarumta, da sakin fuska ga abokanan tafiyarsa, da kuma taimakonsu da dukiya da kuma jiki, da shigar da farin ciki garesu. Wannan da ƙara tsayuwarsa ga abinda Allah Ya wajabta a kansa na ibadu da kuma nisantar abubuwan da aka haramta.

Kuma yana kamata ya yawaita guzuri da kayan tafiya, ya tafi da sama da buƙatarsa daga hakan; don tsoro ga abinda zai bijiro na buƙatu.

Kuma yana kamata a lokacin tafiyarsa da ma cikin tafiyarsa ya faɗi abinda ya zo daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, daga hakan:

1- Idan ya ɗora ƙafarsa akan abin hawansa to ya ce: «Bismillah» (Da sunan Allah), idan kuma ya tabbata a kansa, to ya tuna ni'imar Allah ga bayinSa don Ya sawwaƙa ababen hawa daban-daban, sannan ya ce: «Allāhu Akbar, Allāhu Akbar, Allāhu Akbar (Subāhanallazī sakhkhara lanā hāza wamā kunnā lahū muƙrinīna wa'innā ilā rabbinā lamunƙalibūna), Allāhumma innā nas'aluka fī safarinā hāzal birra wattaƙwa, wa minal amali mā tardhā, Allāhumma hawwin alainā safarana hāza, waɗwi annā bu'dahu, Allahumma antas Sāhibu fis safar, wal khalifatu fil ahl, Allāhumma inni a'ūzu biKa min wa'thā'is safar waka'ābatil manzar wa sā'il munƙalab fil māli wal ahl». (Allah ne Mafi girma, Allah ne Mafi girma (Tsarki ya tabbata ga wanda Ya hore mana wannan alhali bamu da wani iko gareshi kuma lallai mu masu komawa ne ga Ubangijinmu), ya Allah lallai mu muna roƙonKa aikin alheri da tsoron Allah a cikin wannan tafiya ta mu, da kuma aikin da Ka yarda da shi, ya Allah Ka sauƙaƙa mana wannan tafiyar ta mu, kuma Ka ninke mana nisanta, ya Allah Kaine aboki a cikin tafiya, kuma mai mayewa a cikin iyalai, ya Allah ni ina neman tsarinKa daga wahalhalun tafiya, da mummunan abin gani, da mummunan juyowa a cikin dukiya da kuma iyalai. [2] Muslim ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin abin da (mutum) zai faɗa idan ya hau (abin hawa) domin tafiya Hajji da waninsa, lamba ta (1342), daga hadisin Ibnu Umar - Allah Ya yarda da su -.

2- Kabbara idan ya hau tudu, da kuma tasbihi idan ya gangaro ƙasa [3]. [3] Bukhari ne ya fitar da shi, Littafin jihadi da siyar, babin tasbihi idan ya gangaro kwari, lamba ta (2993), daga hadisin Jabir - Allah Ya yarda da shi -.

3- Idan ya sauka wani masauki sai ya ce: «A'ūzu bi kalimātil lāhit tāmmāti min sharri mā khalaƙa». (Ina neman tsari da kalmomin Allah cikakku daga sharrin abinda Ya halitta) [4]. Domin lallai wanda ya faɗeta wani abu ba zai cutar da shi ba har ya bar masaukinsa wanda ya faɗeta a cikinsa. [4] Muslim ne ya fitar da shi: Littafin zikiri da addu'a da tuba da istigfari, babi a kan neman tsari daga mummunan hukunci da kuma riskar taɓewa da waninsa, lamba ta (2708) daga hadisin Khaulah bint Hakim - Allah Ya yarda da ita -.

* * *

TAFIYAR MACE

Ba ya halatta ga mace ta yi tafiyar Hajji ko waninsa sai a tare da ita akwai muharrami, duk ɗaya ne tafiyar ta kasance mai tsawo ce ko gajera ce, kuma duk ɗaya ne a tare da ita akwai mata ko babu, kuma duk ɗaya ne budurwa ce ko tsohuwa ce; saboda gamewar faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: «Kada mace ta yi tafiya sai a tare da ita akwai muharrami» [5]. [5] Bkukhari ne ya fitar da shi: Littafin sakamakon farauta, babin Hajjin mata, lamba ta (1862), da Muslim: Littafin Hajji, babin tafiyar mace tare da muharrami zuwa Hajji da waninsa, lamba ta (1341), daga hadisin Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su -.

Hikima a kan hana mace tafiya ba tare da muharrami ba ita ce: Taƙaitawar mace a cikar hankalinta da kare kanta, kuma ita mai sa kwaɗayi ga maza ce, wataƙila a yaudareta ko a rinjayeta, ko ta zama mai rauni a Addini, sai tabi bayan sha'awowinta, kuma ta zama abar kwaɗayi ga masu kwaɗayi. Muharrami kuwa zai tsareta ya kiyaye mutuncinta kuma ya kare ta; saboda haka ne aka sharɗanta (muharrami) ya zama baligi mai hankali; yaron da bai balaga ba, bai isa ba ko wanda ba shi da hankali.

Muharrami shi ne mijin mace, da dukkanin wanda take haramta gare shi haramci na har abada da 'yan'uwantaka ko shayarwa ko suhurtaka, muharramai daga 'yan uwantaka su bakwai ne:

1- Iyaye da kakanni ko da kakannin kakanni ne, duk ɗaya ne sun kasance ta ɓangaren uwa ne, ko ta ɓangaren uba.

2- 'Ya'ya maza da 'ya'yan 'ya'yan su, da kuma 'ya'yan 'ya'ya mata, ko da 'ya'yan 'ya'ya ne.

3- 'Yan uwa, duk ɗaya ne sun kasance 'yan uwa shaƙiƙai ne, ko 'yan uba ko 'yan uwa ta ɓangaren uwa.

4- 'Ya'yan 'yan uwa, duk ɗaya ne sun kasance shaƙiƙai ne, ko 'ya'yan 'yan uwa 'yan uba, ko 'ya'yan 'yan uwa ta ɓangaren uwa.

5- 'Ya'yan 'yan uwa mata, duk ɗaya ne sun kasance 'ya'yan 'yan uwa mata shaƙiƙai ne, ko ta ɓangaren uba, ko ta ɓangaren uwa.

6- Baffannai (‘yan uwan uba), duk ɗaya ne sun kasance shaƙiƙai ne ko ta ɓangaren uba, ko ta ɓangaren uwa.

7- Kawunnai (‘yan uwan uwa), duk ɗaya ne sun kasance shaƙiƙai ne, ko ta ɓangaren uba, ko ta ɓangaren uwa.

Muharramai daga shayarwa daidai suke da muharramai daga 'yan uwantaka; saboda faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - «Abinda yake haramta daga nasaba yana haramta daga shayarwa» [6]. [6] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin shahadat, babin shaida akan dangantaka, lamba ta (2645), da Muslim: Littafin shayarwa, babin haramcin 'yar ɗan uwa daga shayarwa, lamba ta (1447), daga hadisin Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su -

Muharramai daga suhurtaka su ne:

1- 'Ya'yan mijin mata, da 'ya'yan 'ya'yansa maza, da 'ya'yan 'yan'yansa mata, ko da sun yi nisa, duk ɗaya ne sun kasance daga macen da take kafinta ne ko tare da ita ko bayanta.

2- Iyayen mijin mata da kakanninsa, ko da kakannin kakanni ne, duk ɗaya ne ta ɓangaren babansa ne ko ta ɓangaren babarsa ne.

3- Mazajen 'ya'ya mata, da mazajen 'ya'ya matan 'ya'ya maza, da mazajen 'ya'ya matan 'ya'ya mata, ko da sun yi nisa.

Waɗannan ukun haramci yana tabbata a cikinsu da mujarradin ɗaura aure, ko da ya rabu da ita da mutuwa ne ko da saki ko da warware aure, domin cewa haramci yana wanzuwa ga waɗannan.

4- Mazajen iyaye mata, da mazajen kakanni mata, ko da sun yi nisa, sai dai waɗannan ba sa zama muharramai ga 'ya'ya matan mazajensu, ko 'ya'ya matan 'ya'yan matansu, ko 'ya'ya matan 'ya'yan matansu har sai sun tare da matan. Idan tarewa ( saduwa) ta tabbata to mijin ya zama muharrami ga 'ya'yan matansa daga wani mijin kafinsa ko mijin bayansa, da 'ya'ya matan 'ya'yanta da 'ya'ya matan 'ya'yanta mata, ko da ya saketa bayan nan, amma idan ya auri mace sannan ya saketa kafin ya tare (saduwa) da ita, to hakan ba ya zama muharrami ga 'ya'yanta, ko ga 'ya'yan 'ya'yanta, ko ga 'ya'yan matan 'ya'yanta mata.

* * *

SALLAR MATAFIYI

Addinin Musulunci Addinin sauƙi ne da rangwame, babu takura ko wahala a cikinsa, a duk lokacin da aka samu wata wahala Allah zai buɗe ƙofofin sauƙi; Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Shi ne wanda ya zaɓeku kuma bai sanya muku wani ƙunci a cikin Addini ba.} [al- Hajj: 78]. Kuma Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Addini sauƙi ne» [7]. Ma'abota ilimi sun ce: «Wahala tana jawo sauƙi». [7] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin imani, babin Addini sauƙi ne, lamba ta (39), daga hadisin Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi -.

Yayin da tafiya ta zama ana zatan wahala a cikinta galibi sai aka yi wa hukunce-hukuncenta sauƙi; daga hakan:

1- Halaccin yin taimama ga matafiyi idan bai samu ruwa ba, ko a tare da shi akwai ruwan da yake buƙatarsa don ci ko sha, sai dai a duk lokacin da zatansa ya rinjaya cewa zai isa inda ruwa yake kafin fitar lokaci mukhtari, to abinda ya fi ya jinkirta sallah har sai ya isa ga ruwan; don ya yi tsarki da shi.

2- Lallai abin da aka shara'anta a haƙƙin matafiyi shi ne ya yi ƙasarun sallah mai raka'o'i huɗu; sai ya maida ita raka'o'i biyu tun daga lokacin da ya fita daga garinsa har sai ya dawo zuwa gare shi, ko da muddar ta yi tsawo; saboda abin da ya tabbata a cikin (Sahihul Bukhari) daga Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su -: «Cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya zauna a Makka a shekarar buɗe Makka kwana goma sha tara yana sallah raka'o'i biyu» [8]. Kuma Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya zauna a Tabuka kwana ashirin yana ƙasarun sallah [9]. [8] Bukhari ne ya fitar da shi: Babukan yin ƙasarun sallah, babin abin da ya zo a cikin yin ƙasaru kuma har kwana nawa zai zauna har ya samu damar yin ƙasaru, lamba ta (1080), daga hadisin Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su -. [9] Abu Dawud ne ya fitar shi, rassantuwar sallar tafiya, babin idan ya zauna a garin maƙiya to ya yi ƙasaru, lamba ta (1235), daga hadisin Jabir - Allah Ya yarda da shi -.

Sai dai idan matafiyi zai yi sallah a bayan limamin da yake yin sallah raka'o'i huɗu, to shi zai yi sallah raka'o'i huɗu don bi ga limaminsa, duk ɗaya ne shin ya riski liman ne tun daga farkon sallah ko a tsakiyarta. Idan liman ya yi sallama sai ya zo da cikon raka'o'i huɗun; saboda faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: «Kaɗai an sanya limami ne dan a yi koyi da shi, don haka kada ku saɓa masa» [10]. Da kuma gamewar faɗinsa: «Abin da ku ka riska to ku sallata, kuma abin da ya kuɓuce muku to sai ku cika» [11]. An tambayi Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su -: Me yasa matafiyi ne yake yin sallah raka'o'i biyu idan shi kaɗai yake, kuma yake yin huɗu idan ya yi koyi da mazaunin gida? sai ya ce: "Wannan ce sunnah" [12]. [10] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin kiran sallah, babin kaɗai an sanya limami ne don a yi koyi da shi, lamba ta (689), da Muslim: Littafin sallah, babin mamu ya yi koyi da liman, lamba ta (411), daga hadisin Anas - Allah Ya yarda da shi -. [11] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin kiran sallah, babin kada ya yi gaggawa zuwa sallah, ya zo da nutsuwa da kuma tabbata, lamba ta (636), da Muslim: Littafin masallatai da guraren sallah, babin an so zuwa sallah da tabbata da nutsuwa da kuma hani daga zo wa sallah da gaggawa, lamba ta (602), daga hadisin Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi -. [12] Imamu Ahmad ya fitar da shi (1/216).

"Ibnu Umar - Allah Ya yarda da shi - ya kasance idan ya yi sallah tare da su yana yin sallah raka'o'i huɗu, idan kuma ya yi sallah shi kaɗai sai ya yi sallah raka'o'i biyu, yana nufin: A halin tafiya"[13]. [13] Muslim ne ya fitar da shi: Littafin sallar matafiya da ƙasarunta, babin ƙasarun sallah a Mina, lamba ta (694).

3- Lallai abin da aka shara'anta a cikin haƙƙin matafiyi shi ne ya haɗa tsakanin Azahar da La'asar, da kuma tsakanin Magariba da Issha'i idan ya buƙaci haɗawar, misali: Ya zama yana tafiya a cikin tafiyarsa, abin da yafi a wannan lokacin ya yi abinda ya fi sauƙi gare shi na jam'i taƙdim ko jam'i ta'akhir.

Amma idan ya kasance ba ya buƙatar haɗawar, to abinda ya fi kada ya haɗa, idan ya haɗa ɗin to babu laifi, misalinsa: Ya zama ya sauka a wani guri, ba ya nufin tashi daga gare shi sai bayan shigar lokacin sallah ta biyu, to sai ya sallaci kowacce farilla a cikin lokacinta; domin cewa shi ba ya buƙatar haɗawar.

* * *

MIƘATAI (WURAREN ƊAUKAR NIYYAR HAJJI KO UMARAH)

Miƙatai: Sune guraren da Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ayyanasu don wanda ya yi nufin yin Hajji ko Umarah ya yi harama daga garesu, miƙatai guda biyar ne:

Na farko: Zul-Hulaifa: Ana ambatanta da (Abyāru Ali), wasu daga cikin mutane suna kiransa (al-Hasā'u), tsakaninsa da Makka gwargwadan marhala goma ne, kuma shi ne miƙatin mutanen Madina, da wanda ya biyo ta nan daga wasun mutanen Madina.

Na biyu: Juhfa: ita wata tsohuwar alƙarya ce tsakaninta da Makka gwargwadan marhala biyar ne, haƙiƙa ta rushe sai mutane suka zama suna yin harama daga (Rabigh) canjinta, kuma ita ce miƙatin mutanen Sham (Syria) da wanda ya wuce ta wurin wanda ba ya daga cikin ma'abotanta.

Na uku: Yalamlam: Shi wani dutse ne ko wani wuri a Tihama, tsakaninsa da Makkah gwargwadan marhala biyu ne, shi ne miƙatin mutanen Yamen da wanda ya biyo ta wurin cikin waɗanda ba ahalin wurin ba.

Na huɗu: Ƙarnul manāzil: Ana ambatansa da (al-Sail), tsakaninsa da Makkah gwargwadan marhala biyu ne, kuma shi ne miƙatin mutanen Najd da wanda ya biyo ta wurin wanda ba ya cikin mutanan wurin.

Na biyar: Zātu irƙin: Ana ambatansa da (al-Darībah), tsakaninsa da Makkah marhala biyu ne, shi ne miƙatin mutanen Iraƙ da wanda ya biyo ta wurin cikin waɗanda ba ahalin wurin ba.

Wanda ya kasance ya fi kusa da Makkah daga waɗannan miƙatan to miƙatinsa shi ne wurinsa; sai ya yi harama daga wurin, har mutanen Makkah daga Makkah za su yi, wannan idan sun yi harama da Hajji, amma idan harama da Umarah ce to sai su yi harama daga Hilli (wajen harami); saboda faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ga Abdurrahman ibnu Abubakar: «Ka fita da 'yar uwarka - ma'ana Nana Aisha - daga Harami, sai ta yi haramar yin Umarah» [14]. [14] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin faɗin Allah - Maɗaukakin Sarki -: (Hajji wasu watanni ne sanannu wanda ya wajabta Hajji a cikinsu to babu kwarkwasa babu fasiƙanci kuma babu jayayya a cikin Hajj) [al-Baƙara: 197], lamba ta (1560), da Muslim: Littafin Hajji, babin bayanin Nau’ukan harama, kuma cewa ya halatta a yi Ifradin Hajji da Tamattu'i da kuma Ƙirani, da kuma halaccin shigar da Hajji akan Umarah, kuma a duk lokacin da mai Ƙirani ya fita daga ibadarsa, lamba ta (1211), daga hadisin Nana A'isha - Allah Ya yarda da ita -.

Duk wanda hanyarsa ta zama a dama ko a hagu daga waɗannan miƙatan, to cewa shi zai yi harama ne lokacin da ya yi daura da mafi kusancin miƙati gare shi, wanda ya kasance a cikin jirgi, to zai yi harama idan ya yi daura da miƙati daga sama, sai ya yi shiri ya sanya tufafin harama kafin ya yi daura da miƙatin, idan ya yi daura da shi sai ya yi niyyar harami a lokacin. Ba ya halatta ya jinkirta shi. Wani daga cikin mutanen yana kasancewa a cikin jirgi alhali shi yana nufin hajji ko Umarah, sai ya yi daura da miƙatii amma ba zai yi harama daga gare shi ba, kai sai ya jinkirta haramarsa har sai ya sauka filin jirgin sama, to wannan ba ya halatta; domin cewa shi yana daga ƙetare iyakokin Allah - Maɗaukakin sarki -. Eh, da a ce zai wuce ta miƙati alhali shi ba ya nufin Hajji ko Umarah, daga ba ya sai ya yi niyyar Hajji ko Umarah, cewa shi zai yi harama ne daga inda ya yi niyyarsa, kuma babu komai a kansa.

Wanda ya wuce ta waɗannan miƙatan alhali ba ya nufin yin Hajji ko Umarah, kawai yana nufin Makkah ne; don ziyartar wani ɗan uwa, ko kasuwanci, ko neman ilimi, ko magani, ko wanin hakan daga buƙatu to harama ba ta wajaba a kansa; saboda hadisin Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su -: cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya iyakance miƙatai, sannan ya ce: «Su sun tabbata garesu, da wanda ya zo ta wurinsu wanda ba ahalin gurin ba, ga wanda ya yi nufin yin Hajji ko Umarah » [15]. Sai ya rataya hukunci ga wanda ya yi nufin yin Hajji ko Umarah, abin da aka fahimta cewa wanda bai yi nufin yin Hajji da Umarah ba to harama ba ta wajaba a kansa daga garesu, kuma nufin Hajji ko Umarah ba wajibi ba ne akan wanda ya bada farali, kuma Hajji ba ya wajaba a rayuwa sai sau ɗaya; saboda faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: «Hajji sau ɗaya ne, wanda ya ƙara to nafila ne» [16]. Sai dai abin da yafi shi ne kada ya haramtawa kansa taɗawwu'in ibada; don ya samu lada; saboda sauƙin harama a cikin wannan lokacin, yabo da baiwa sun tabbata ga Allah. [15] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin wurin niyyar Hajji da Umarah ga mutanen Makkah, lamba ta (1524), da Muslim: Littafin Hajji, babin miƙatan Hajji da Umarah, lamba ta (1181), daga hadisin Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su -. [16] Muslim ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin farillar Hajji sau ɗaya ne a rayuwa, lamba ta (1337), da Ahmad (1/290), kuma lafazin nasa ne, daga hadisin Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi -.

* * *

NAU'IKAN AYYUKAN (HAJJI)

Nau'ikan ayyukan (Hajji) uku ne: Tamattu'i, Ifradi da Ƙirani.

Tamattu'i: Shi ne ya yi niyyar Umarah ita kaɗai a cikin watannin Hajji, idan ya isa Makkah sai ya yi ɗawafi ya yi sa'ayin Umarah, ya yi ƙwal-ƙwal ko ya yi saisaye, idan ranar Tarwiyah ta zo: Ita ce rana ta takwas ga Zul-Hijja sai ya yi harama da Hajji shi kaɗai, kuma ya zo da dukkanin ayyukansa.

Ifradi: Shi ne ya yi harama da Hajji shi kaɗai, idan ya isa Makkah sai ya yi Ɗawaful ƙudum (ɗawafin isowa) sannan ya yi sa'ayi ga Hajji, ba zai yi aski ƙwal-ƙwal ba kuma ba zai yi saisaye ba, ba kuma zai warware haramarsa ba, bari dai zai wanzu yana mai harama har sai ya warware haramarsa bayan ya jefi Jamratul Aƙabah (babban Shaiɗan) a ranar idi. Idan ya jinkirta sa'ayin Hajji har zuwa bayan ɗawafin hajji to babu laifi.

Ƙirani: Shi ne ya yi harama da Umarah da Hajji baki ɗaya, ko ya yi harama da Umarah a farko sannan ya shigar da Hajji a kanta kafin fara ɗawafinta. Aikin mai Ƙirani kamar aikin mai Ifradi ne daidai wa daida, sai dai cewa mai yin Ƙirani a kansa akwai hadaya, mai Ifradi kuma babu hadaya a kansa.

Mafificin waɗannan nau'ikan ayyukan uku shi ne Tamattu'i, domin wanda Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya umarci sahabbansa da shi kuma ya kwaɗaitar da su a kansa, kai da a ce mutum zai yi harama yana mai Ƙirani ko yana mai Ifradi, to cewa shi yana ƙarfafuwa a kansa ya juyar da haramarsa zuwa Umarah; don ya zama mai yin Tamattu'i ko da bayan ya yi ɗawafi ne ya yi sa'ayi; domin cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - lokacin da ya yi ɗawafi ya yi sa'ayi a shekarar Hajjin ban kwana alhali a tare da shi akwai sahabbansa sai ya umarci dukkan wanda babu hadaya a tare da shi ya mayar da haramarsa ta koma Umarah kuma ya yi saisaiye ya warware haramarsa, kuma ya ce: «Da a ce na koro hadaya, da na aikata irin abinda na umarce ku da shi» [17]. [17] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin Tamattu'i da Ƙirani da Ifradi a Hajji, lamba ta (1568), da Muslim: Littafin Hajji, babin Nau’ukan Harama, lamba ta (1216), daga hadisin Jabir - Allah Ya yarda da shi -.

Wannan kenan, mutum zai iya yin harama da Umarah alhali yana mai Tamattu'i da ita zuwa Hajji, sannan ba shi da tabbacin cika Umarah kafin tsayuwar Arfa, to a wannan yanayin zai shigar da Hajji akan Umarah sai ya zama mai Ƙirani, zamu kawo maka misalai biyu:

Misali na farko: Mace ce ta yi haramar Umarah tana mai tamattu'i da ita zuwa Hajji, sai ta yi al’ada ko ta yi jinin biƙi (haihuwa) kafin ta yi ɗawafi, ba ta yi tsarki ba har sai da lokacin tsayuwar Arfa ya zo, to ita a wannan halin za ta yi niyyar shigar da Hajji akan Umarah sai ta zama mai Ƙirani, sai ta zarce a cikin haramarta ta aikata abin da mahajjaci yake aikatawa sai dai cewa ita ba za ta yi ɗawafi a ɗaki ba kuma ba za ta yi sa'ayi tsakanin Safa da Marwa ba har sai ta yi tsarki ta yi wanka.

Misali na biyu: Mutum ne ya yi haramar Umarah yana mai tamattu'i da ita zuwa Hajji, sai wani abu mai hanawa ya hana shi shiga Makkah kafin ranar Arfa, to cewa shi zai yi niyyar shigar da Hajji akan Umarah sai ya zama mai Ƙirani, sai ya zarce a cikin haramarsa, kuma ya aikata abinda mahajjaci yake aikatawa.

* * *

MAI HARAMAR DA HADAYA TA LAZIMCE SHI

Mai haramar da hadaya ta lazimce shi shi ne mai Tamattu'i da mai Ƙirani; amma mai Ifradi to babu abin da ya lazimce shi.

Mai Tamattu'i: Shi ne wanda zai yi harama da Umarah a cikin watannin Hajji, wato: Bayan shigar Shawwal, sai kuma ya kammala a cikin watannin na Umarah, sannan ya yi haramar Hajji a cikin wannan shekarar. Idan ya yi haramar Umarah kafin shigar watan Shawwal to shi ba mai Tamattu'i ba ne, saboda haka babu hadaya a kansa daidai ne ya kasance ya azumci Ramadan ne a Makka ko a'a, to azumin Ramadan a Makkah ba shi da wani gurbi, kaɗai abin lura da ƙulla haramar Umarah ne kawai, a duk lokacin da ya zama kafin shigar watan Shawwal ne to babu hadaya a kansa, idan ya kasance bayan shigar watan Shawwal ne to shi mai Tamattu'i ne, hadaya ta wajaba idan sharuɗɗan wajabci suka cika. Amma abin da wasu daga gamagarin mutane suke ƙudircewa cewa abin lura da azumtar Ramadan ne, kuma cewa wanda ya yi azumi a Makkah to babu hadaya a kansa, wanda kuma bai yi azumi ba a Makkah ba to akwai hadaya a kansa, to wannan ƙudiri ne mara inganci.

Amma mai Ƙirani: Shi ne wanda yake yin haramar Umarah da Hajji baki ɗaya, ko ya yi haramar Umarah sannan ya shigar da Hajji a kanta kafin fara ɗawafinta.

Hadaya bata wajaba akan mai Tamattu'i da mai Ƙirani sai da sharaɗin cewa basu zama daga cikin mazauna masallaci mai alfarma ba, idan sun kasance daga mazauna masallaci mai alfarma ne (wato su ‘yan Makkah ne ) to babu hadaya a kansu. Mazauna masallaci mai alfarma: Su ne mutanen harami, da waɗanda suka kasance kusa da shi ta inda tsakaninsu da harami tafiyar bata zama za'a ɗauketa a matsayin tafiya ba, kamar mutanen Shara'i'i da makantansu, to cewa su babu hadaya a kansu. Amma waɗanda suke a nesa da harami ta inda tsakaninsu da harami akwai tafiyar da za'a iya ɗaukarta a matsayin tafiya, kamar mutanen Jidda to cewa hadaya ta lazimcesu. Wanda ya kasance daga cikin mutanen Makkah, sannan ya yi tafiya zuwa wani guri don neman ilimi ko waninsa, kuma ya dawo gareta yana mai Tamatt'i to babu hadaya a kansa; domin cewa abin lura da wurin zamansa ne kuma gurin zamansa shi ne Makkah, sai dai idan ya tashi zuwa wani wurin da ba Makka ba don zama, to cewa shi idan ya dawo zuwa gareta to hadaya ta lazimce shi; domin cewa shi a wannan lokacin bai zama daga mahalarta masallaci mai alfarma ba.

Ita Hadaya ta wajibi akan mai Tamattu'i da mai Ƙirani ita ce akuya da ta isa a yi layya da ita, ko ɗaya bisa bakwai na taguwa, ko ɗaya bisa bakwai na saniya, idan bai samu ba to zai yi azimin kwana uku a cikin (kwanukan) hajji, da kuma bakwai idan ya dawo zuwa iyalansa, kuma yana halatta ya azumci kwanuka ukun a cikin kwanukan Tashriƙ; sune rana ta goma sha ɗaya, da sha biyu, da kuma sha uku ga Zul-Hijja, kuma yana halatta ya azimcesu kafin hakan bayan ya yi haramar Umarah, sai dai ba zai azumce su ba a ranar idi ko a ranar Arfa; domin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya yi hani daga azimin ranakun idi biyu [18], kuma ya yi hani daga azimin ranar Arfa a Arfa [19], kuma yana halatta ya azumci waɗannan ranaku ukun a jere ko a rarrabe, sai dai kada ya jinkirta su daga ranakun Tashriƙ, amma ragowar bakwan zai azimce su ne idan ya dawo zuwa ga iyalansa; idan ya so ya azimce su a jere, idan kuma ya so a rarrabe. [18] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin Azumi, Babin Azumin ranar Idin ƙaramar sallah, lamba ta (1990), da Muslim: Littafin Azumi, Babin hanin yin azumi ranar Idin ƙaramar sallah da ranar idin babbar sallah, lamba ta (1137), daga hadisin Umar. [19] Abu Dawud: Littafin azumi, Babin azumin ranar Arfa a Arfa, lamba ta (2440), da Ibnu Majah: Littafin azumi, babin azumin ranar Arfa, lamba ta (1732), daga hadisin Abu Hurairah.

Ranakun yankan hadaya huɗu ne: Ranar idi, da ranaku uku bayanta, wanda ya yi yanka kafin waɗannan ranakun, to akuyarsa akuya ce ta nama ba ta isar wa ga yin hadaya; domin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - bai yanka hadayarsa ba kafin ranar idi. Hadaya tana daga ayyukan ibadu na Hajji, kuma haƙiƙa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Ku riƙi ayyukan ibadunku (na Hajji da Umarah) daga gare ni [20]». A wani hadisin daga gare shi, ya ce: «Dukkan ranakun Tashriƙ, (ranakun) yanka ne» [21]. Ranakun Tashriƙ sune ranaku uku bayan idi. [20] Muslim ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin mustahabbancin jifan Jamratul Aƙabah a ranar layya akan abin hawa, da bayanin faɗinsa – tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi: «Ku riƙi ayyukan ibadunku (na Hajji da Umra)» lamba ta (1297), daga hadisin Jabir, - Allah Ya yarda da shi -. [21] Ahmad ne ya fitar da shi (4/82), daga hadisin Jubayr ibn Muɗ’im - Allah Ya yarda da shi -.

Yanka yana halatta a waɗannan ranakun a cikin dare ko rana, saidai da rana shi yafi falala. Haka nan, yana halatta a Mina da Makka, sai dai a Mina shi ya fi falala, saidai idan yankan ya kasance zai fi amfanarwa ne ga talakawa a Makkah, ta yadda amfani da shi a Mina zai zama kaɗan ne, to zai bi abin da ya fi masalaha da amfanarwa. Saboda haka, da ya jinkirta yin hadayarsa har zuwa rana ta goma sha uku kuma ya yanka ta a Makkah, to babu laifi.

Ka sani cewa wajibcin yin hadaya akan mai iko, ko yin azumi ga wanda bai samu abun yin hadaya ba, bai zamo bashi akan bawa ba ko wahalarwa ga jikinsa ba tare da wata fa'idah ba. Kaɗai yana daga cika ayyukan ibadun Hajji ne da kammalawarsa, kuma yana daga rahmar Allah da kyautayinsa yayin da Ya shar'anta ga bayi abin da yake akwai cikar ibadarsu a cikinsa, kuma da kusantuwarsu zuwa ga Ubangijinsu, da ƙarin ladansu, da kuma ɗaukakar darajojinsu.

Ciyarwa a cikinsa abar mayewa ce (da lada), kuma aiki a cikinsa abin godewa ne, da yawa daga cikin mutane ba sa lura da wannan fa'idar, kuma ba sa neman wannan ladan, sai ka samesu suna gujewa wajabcin hadaya, suna ƙoƙari don sarayar da ita ta kowace hanya, har wasu daga cikinsu suna yin Ifradi a Hajji saboda kada hadaya ta wajaba a kansa, sai su haramtawa kansu ladan Tamattu'i da kuma ladan hadaya, wannan wata rafkana ce da ya kamata a faɗakar da ita.

SIFAR UMARAH

Idan (mutum) ya yi nufin yin harama da Umara, to abin da aka shar'anta masa shi ya tsirata daga tufafinsa, ya yi wanka kamar yadda yake wankan tsarki, ya shafa turare da mafi daɗin abinda zai samu daga man oud ko waninsa a kansa da gemunsa, kuma wanzuwar hakan (ƙamshin) ba zai cutar da shi ba bayan yin harama; saboda abinda ke cikin Bukhari da Muslim daga hadisin Nana Aisha - Allah Ya yarda da ita - ta ce: «‌Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kasance idan ya yi nufin yin harama, sai ya shafa turare da mafi daɗin abin da zai samu, sannan ana ganin walwalin almiski a kansa da gemunsa bayan haka» [22]. [22] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin tufafi, babin shafa turare a ka da gemu, lamba ta (5923), da Muslim: Littafin Hajji, babin shafa turare ga mai yin harama a yayin yin harama, lamba ta (1190), daga hadisin Nana Aisha - Allah Ya yarda da ita -.

Yin wanka a yayin yin harama sunnah ne a haƙƙin namiji da mace, har mai yin jinin biƙi da na al'ada; saboda Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya umarci Asma'u 'yar Umaisin a yayin da take jinin biƙi (haihuwa) da ta yi wanka a yayin yin haramarta kuma ta yi ɗamara da tufafi ta yi harama [23]. [23] Muslim ne ya fitar dashi: Littafin Hajji, babin Hajjin Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, lamba ta (1218), daga hadisin Jabir - Allah Ya yarda da shi -.

Sannan bayan yin wanka da shafa turare, zai sanya tufafin yin harama, sannan ya yi sallah ta farilla - banda mai jinin al'ada da na biƙi -, idan lokacin yin sallar farilla ne, idan ba haka ba kuwa, ya yi sallah raka'o'i biyu yana mai yin niyyar sunnar alwala da su, idan ya gama sallar, sai ya yi harama kuma ya ce: «LabbayKa Umratan, labbayKa allāhumma labbayK, labbayKa lā sharīka laKa labbayK, innal-hamda wan-ni‘mata laKa wal-mulk, lā sharīKa lak». Ma’ana: (AmsawarKa ya Allah ga Umra, AmsawarKa ya Allah AmsawarKa, amsawarKa, ba Ka da abokin tarayya amsawarKa, lallai godiya da ni'ima naKa ne, mulki ma (naKa ne) ba Ka da abokin tarayya) [24]. Namiji zai ɗaga sautinsa da wannan, mace kuma zata dinga faɗa gwargwadon abin da na gefenta ta zai ji. [24] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin Talbiyah, lamba ta (1549), da Muslim: Littafin Hajji, babin Talbiyah da sifarta, lamba ta (1184), daga Ibnu Umar - Allah Ya yarda da su -.

Idan mai nufin yin harama ya ji tsorin wani abu da zai hana shi cika ibadunsa (na aikin Hajji ko Umra), to ya kamata ya sharɗanta a yayin yin harama; sai ya ce lokacin ƙullawarsa: «Idan wani mai tsarewa ya tsare ni, to wurin warwarewa ta inda duk Ka tsare ni»[25]. Wato: Idan wani mai hanawa ya hana ni cika ayyukan ibaduna na, na daga rashin lafiya ko jinkiri ko waninsu, to lallai ni ina warwarewa daga haramata; Domin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya umarci Dhuba'ah 'yar Zubair - Allah Ya yarda da ita - yayin da ta yi nufin yin harama alhali tana rashin lafiya da ta sharɗanta [26], kuma ya ce: «Lallai ke kina da abin da kika togance akan Ubangijinki» [27]. To duk sanda ya sharɗanta kuma abin da zai hana shi cika ayyukan ibadunsa ya same shi, to lallai shi zai warare kuma babu komai a kansa. [25] Nasa’i ne ya fitar da shi: Littafin ayyukan ibadun Hajji, ya zai ce idan ya sharɗanta, lamba ta (2766) daga hadisin Ibn Abbas - Allah Ya yarda da su -. [26] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin aure, babin isuwa a Addini, lamba ta (5089), da Muslim: Littafin Hajji, babin halaccin mai harama ya sharɗanta warwarewa bayan rashin lafiya ko waninsa, lamba ta (1207), daga hadisin Nana Aisha - Allah Ya yarda da ita -. [27] Nasa’i ne ya fitar da shi: Littafin ayyukan ibadun Hajji, ya zai ce idan ya sharɗanta, lamba ta (2766) daga hadisin Ibn Abbas - Allah Ya yarda da su -.

Amma wanda ba ya tsoron wani mai hanawa da zai hana shi cika ayyukan ibadunsa, to lallai ba ya kamata gare shi ya sharɗanta; domin cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - bai sharɗanta ba, kuma bai umarci wani da ya sharɗanta ba, kawai ya umarci Dhuba'ah bint Zubair - Allah Ya yarda da ita - saboda rashin lafiyar da take da ita.

Yana kamata ga wanda ya yi harama ya yawaita yin Talbiya, musamman ma a yayin canjawar halaye da lokuta, misali: Ya hau tudu, ko ya sauka kwari, ko idan dare ya fiskanto ko rana, kuma ya roƙi Allah yardarSa da aljanna bayanta, ya nemi tsari da rahamarSa daga wuta.

Talbiyyah abar shar'antawa ce, a Umarah tun daga harama har zuwa ya fara ɗawafi, a Hajji kuma tun daga harama har zuwa ya fara jifan Jamratul Aƙabah (babban Shaiɗan) a ranar idi.

Yana cancanta idan ya kusanto Makkah ya yi wanka don shigarta; saboda Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya yi wanka yayin shigarsa [28]. Idan ya shiga masallacin Harami ya gabatar da ƙafarsa ta dama, kuma ya ce: «Bismillāhi was salātu was salāmu alā rasūlillāhi, Allāhummag firlī zunūbi, waf tahlī abwāba rahmatiKa, a'uzu bil lāhil azim, wa bi wajhihil karim, wa bi sulɗānihil ƙadim minash shaiɗānir rajīm». Ma’ana: (Da sunan Allah kuma tsira da Aminci su tabbata ga Manzon Allah, Ya Allah Ka yi mun gafarar zunubaina kuma Ka buɗe min ƙofofin rahmarKa, ina neman tsari da Allah Mai girma da kuma fuskarSa Mai karamci da ikonSa dadaɗɗe daga Shaiɗan jefaffe) [29]. Sannan ya gabato zuwa ga al-Hajarul Aswad; domin ya fara ɗawafi, sai ya shafi dutsen da hannunsa na dama kuma ya sumbace shi, idan sumbatarsa ba zata sauƙaƙa gare shi ba, ya sumbaci hannunsa idan ya shafe shi da shi, idan shafar dutsan da hannunsa ba zai sauƙaƙa gare shi ba, to zai fuskanci dutsen ya yi nuni gare shi da hannunsa kuma ba zai sumbace shi (hannun) ba, abin da yafi kada ya yi turmutsutsi; sai ya cutar da mutane shima ya cutu da su; saboda abin da aka rawaito daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - cewa ya ce ga Umarah: «Kai Umarah, lallai kai mutum ne ƙaƙƙarfa, kada ka yi turmutsutsi a dutse (al-Hajarul Aswad) sai ka cutar da rarrauna, idan ka samu wata kafa to ka shafe shi, inba haka ba to ka fuskance shi sai ka yi Hailala kuma ka yi Kabbara» [30]. [28] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin Ihlali ana fuskantar alƙibla, lamba ta (1553), daga hadisin Ibnu Umar - Allah Ya yarda da su -. [29] Abu Dawud ne ya fitar da shi: Littafin sallah, babin abin da mutum zai faɗe shi a lokacin shiga masallaci, lamba ta (466), daga hadisin Ibnu Amr - Allah Ya yarda da su -. [30] Ahmad ne ya fitar da shi (1/28), kuma babban malaminmu wato mawallafin - Allah Ya yi masa rahama - ya yi masa ta'aliƙi a cikin wata bita daban da ya yiwa littafin da faɗinsa: «Wannan hadisi ne mai rauni».

Kuma a yayin shafar al-Hajarul Aswad sai ya ce: «Bismillāh wallāhu Akbar, Allāhumma imānan biKa, wa tasdiƙan bikitabi Ka, wa wafā'an bi ahdiKa, wattibā'an li sunnati nabiyyiKa Muhammad - sallallāhu alaihi wa sallam -». Ma’ana: (Da sunan Allah, Allah ne Mafi girma, ya Allah don imani da Kai, da gasgatawa ga littafinKa, da cika alƙawarinKa, da bin sunnar AnnabinKa Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -) [31]. [31] Ibnu Hajar ya faɗa a cikin al-Talkhisul Habeer (2/472): ban same shi a haka ba, haƙiƙa mai littafin al-Muhazzab ya ambace shi daga hadisin Jabir, kuma haƙiƙa al-Munziri ya yi musu Mudyadda, da Nawawi, kuma Ibnu Asakir ya fitar da shi ta hanyar Ibnu Nājiyah da sanadinsa mai rauni.

Sannan ya nufi dama, kuma ya sanya ɗaki a hagunsa, idan ya isa al-Ruknul Yamani sai ya shafa shi ba tare da sumbata ba, idan hakan bai sawwaƙa ba to kada ya yi tirmutsutsu a kansa, kuma a tsakaninsa da al-Hajarul Aswad sai ya ce: {Rabbanã ãtina fid duniyã hasanatan wafil ãkhirati hasanatan waƙinã azãban nãr. Ma’ana: (Yã Ubangijinmu! Ka bã mu mai kyau a cikin dũniya da mai kyau a cikin Lãhira, kuma Ka tsare mana azãbar wuta)}. [al-Baƙara: 201]. «Ya Allah lallai ni ina roƙonKa rangwame da lafiya a duniya da lahira» [32], A duk lokacin da ya wuce ta al-Hajarul Aswad sai ya yi kabbara, kuma a ragowar ɗawafinsa zai faɗi abin da ya so na zikiri, da addu'a, da karatun Alƙur'ani, «Kawai an sanya ɗawafi a ɗaki, da Safa da Marwa, da jifan Jamrori ne, don tsayar da zikirin Allah» [33]. [32] Ibnu Majah ne ya rawaito shi, a lamba ta (2957). [33] Abu Dawud ne ya fitar da shi: Littafin ayyukan Haiiji, babi a cikin sassarfa, lamba ta (1888), da Tirmizi: Babukan Hajji, babin abin da yazo ta yaya za'a jefi Jamrori, lamba ta (902), daga hadisin Nana A'isha - Allah Ya yarda da ita -.

A cikin wannan ɗawafin, ina nufin: Ɗawafin farkon gabatowar, yana kamata ga namiji ya yi abubuwa biyu:

Na farkonsu: Idɗibā'i, yana farawa ne tun daga farkon ɗawafi har zuwa ƙarshensa, kuma siffar Idɗibā'i: Ita ce ya sanya tsakiyar mayafinsa a cikin hammatarsa ta dama kuma gefansa akan kafaɗarsa ta hagu, idan ya gama ɗawafi sai ya dawo da mayafinsa zuwa yadda yake kafin ɗawafi; domin Idɗiba'i bigirensa shi ne ɗawafi kawai.

Na biyu: Sassarfa a kewaye ukun farko kawai, sassarfa ita ce: Gaggawar tafiya tare da kusanto da taku. Amma ragowar kewaye huɗun to babu sassarfa a cikinsu, kawai zai yi tafiya ne kamar yadda ya saba.

Idan ya cika ɗawafi bakwai, sai ya zo Maƙamu Ibrahim sai ya karanta: {Kuma ku riƙi Maƙamu Ibrahim wurin yin sallah...} [al-Baƙara: 125]. Sannan ya yi sallah raka'o'i biyu a bayansa; zai karanta a ta farko bayan Fatiha: {Ƙul yã ayyuhal kafirun 1}. Ma’ana: (Ka ce: "Ya kũ kãfirai!). [al-Kafirun:1] A (raka'a) ta biyu kuma: {Ƙul huwallahu ahad 1}. Ma’ana: (Ka ce: "Shi ne Allah Makaɗaĩci). [al-Ikhlas: 1]. Bayan Fatiha.

Idan ya gama sallar mai raka'o'i biyu, ya dawo zuwa Hajarul Aswad sai ya shafe shi in hakan ya sauƙaƙa gare shi.

Sannan ya fita zuwa wurin yin Sa'ayi, idan ya kusa da Safa sai ya karanta: {Lalle ne Safã da Marwa suna daga wurãren ibãdar Allah...} [al-Baƙara: 158]. Sannan ya hau kan Safa har sai ya hangi Ka'abah, sai ya fuskanceta kuma ya daga hannuwansa, sai ya godewa Allah ya roƙi abin da yake son roƙa. Ya kasance daga addu'o'in Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - a nan: «Lā ilāha illal lāhu wahdahu lā sharika lahu, lahul mulku wa wa lahul hamdu, wa huwa alā kulli shai'in ƙadir, lā ilāha illalāhu wahdahu, anjaza wa'dahu,, wa nasara abdahu, wa hazamal ahzāba wahdahū». Ma’ana: (Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah Shi kaɗai, ba shi da abokin tarayya. Mulki nasa ne kuma gõdiya ta tabbata a gare shi, kuma Shĩ, a kan kõme, Mai ĩko ne. Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah Shi kaɗai. Ya cika alƙawarinSa, kuma Ya taimaki bawanSa, kuma Ya karya ƙungiyoyi Shi kaɗai. Zai maimaita wannan sau uku, ya yi addu'a a tsakanin wannan. [34] Muslim ne ya fitar dashi: Littafin Hajji, babin Hajjin Annabi, lamba ta (1218), daga hadisin Jabir - Allah Ya yarda da shi -.

Sannan ya sauka daga Safa zuwa Marwa yana mai tafiya, idan ya isa koriyar alama, ya yi gaggawa mai tsanani gwargwadon yadda ya sami iko kuma ba zai cutar ba. Haƙiƙa an rawaito daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: «Cewa ya kasance yana yin gaggawa har ana ganin gwiwowinsa saboda tsananin gaggawa, kwarjallensa yana kewaya da (gefan ƙafafuwansa)», a wani lafazin: «Kuma lallai kwarjallensa yana cirata akan ƙafafuwansa saboda tsananin gaggawa» [35]. Idan ya isa koriyar alama ta biyu, ya yi tafiya irin yadda ya saba har ya isa zuwa Marwa, sai ya hau kan dutsan, kuma ya fuskanci Alƙibla ya ɗaga hannuwansa, ya faɗi abinda ya faɗa akan dutsan Safa, sannan ya sauka daga Marwa zuwa Safa, sai ya yi tafiya a wurin da ya yi tafiya, kuma ya yi sassarfa a wurin da ya yi sassarfa. Idan ya isa Safa, ya aikata irin yadda ya aikata a karon farko, haka nan a Marwa har ya cika kewaye bakwai. Zuwansa daga Safa zuwa Marwa kewaye ɗaya ne, komawarsa daga Marwa zuwa Safa wani kewayen ne daban, zai roki duk irin abinda yake so na zikiri da addu'a da karatun Alƙur'ani a Sa'ayinsa. [35] Imam Ahmad ne ya fitar da shi (6/421) daga hadisin Habibah bint Abu Tajrata - Allah Ya yarda da ita -.

Idan ya gama Sa'ayinsa kewaye bakwai, ya aske kansa (ƙwalƙwal) idan namiji ne, idan mace ce to zata rage gwargwadon ɗan yatsa daga dukkan sililin gashi.

Yana wajaba ƙwalƙwal ɗin ya game dukkan kai, haka nan saisayen ma ya game dukkan ɓangarorin kai da shi. Yin ƙwalƙwal shi ya fi falala daga yin saisaye, saboda Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya yi addua ga masu ƙwalƙwal sau uku, su kuma masu saisaiye sau ɗaya [36]. Saidai in lokacin aikin Hajji ya ƙarato ta yadda ba zai isa gashi ya fito ba, to abinda ya fi shi ne saisaye; saboda kai ya ragu ga yin ƙwalƙwal a aikin Hajji, saboda Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya umarci sahabbansa a Hajjin ban kwana da su yi saisaye a Umarah [37], saboda isowarsu ta kasance a asubahin rana ta huɗu ne ga Zul Hijjah. [36] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin yin ƙwalƙwal da saisaye yayin warware harama, lamba ta (1727), da Muslim: Littafin Hajji, babin fifikon yin ƙwalƙwal akan saisaye da halaccin yin saisaye, lamta ta (1301), daga hadisin Ibn Umar - Allah Ya yarda da su -. [37] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin Tamattu'i da Ƙirani, lamba ta (1568), da Muslim: Littafin Hajji, babin bayanin fuskokin yin harama, lamba ta (1216), daga hadisin Jabir - Allah Ya yarda da shi -.

Da waɗannan ayyukan Umarah ta cika, don haka Umarah tana kasancewa da yin: Harama, ɗawafi, Sa'ayi da Saki ƙwalƙwal ko saisaye. Sannan bayan wannan zai warware daga gareta cikakkiyar warwarewa, (wato ya kammala Umararsa) kuma ya aikata duk abinda masu warware harama suke yi na daga tufafi, turare, saduwa da mata da wanin wannan.

* * *

SIFAR AIKIN HAJJI

Idan ranar Tarwiya tazo, ita ce rana ta takwas ga watan Zul Hijjah, sai ya yi haramar Hajji da hantsi, daga wurinsa da ya yi nufin yin aikin Hajji daga gare shi (Ma’ana daga masauki sa ko gidansa) ya aikata irin abin da ya aikata a yin haramarsa da Umarah a yayin yin haramarsa da Hajji, na wanka da shafa turare da yin sallah. Sai ya yi niyyar yin harama da Hajji ya yi Talbiya. Sifar yin Talbiya a Hajji kamar siffar yin Talbiya ce a Umarah, saidai a nan zai ce: Labbaikal lāhumma Hajjan (amsawarKa Ya Allah ga Hajji), maimakon faɗinsa: Labbaikal lāhumma Umratan (amsawarKa Ya Allah ga Umarah, a lokacin da zai yi Umarah). Idan yana jin tsoron wani abu da zai hana shi cika aikin Hajjinsa, sai sharɗanta, sai ya ce: «Idan wani abu mai tsarewa ya tsareni, to wurin warware haramata inda Ka tsareni» [38]. Idan kuma ba ya jin tsoro to ba zai sharɗanta ba. [38] Nasa’i ne ya fitar da shi: Littafin ayyukan ibadun Hajji, ya zai ce idan zai sharɗanta, lamba ta (2766) daga hadisin Ibn Abbas - Allah Ya yarda da su -.

Sannan ya fita zuwa Mina, sai ya yi sallar Azahar da La'asar da Magariba da Isha'i da Asubah a nan, zai yi ƙasaru ba tare da ya haɗe sallolin ba; saboda Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kasance yana yin ƙasaru a Mina kuma ba ya haɗewa [39]. Ƙasaru - kamar yadda aka sani - shi ne sanya sallah mai raka'o'i huɗu ta zama raka'o'i biyu. Mutanen Makka da wasunsu za su yi ƙasaru a Mina da Arafah da Muzdalifah; saboda Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kasance yana yin sallah da mutane a Hajjin ban kwana kuma a tare da shi akwai mutanen Makkah kuma bai umarce su da su cika ba, da ya zama wajibi a kansu da ya umarce su da su cika, kamar yadda ya umarce su da hakan a shekarar Fathu (buɗe Makkah). [39] Muslim ne ya fitar dashi: Littafin Hajji, babin Hajjin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, lamba ta (1218), daga hadisin Jabir - Allah Ya yarda da shi -.

Idan rana ta ɓullo a ranar Arafah, zai tafi daga Mina zuwa Arafah, sai ya yada zango a Namira, har zuwa karkacewar rana - idan hakan ya sawwaƙa gare shi - inba haka ba to babu ƙuntatawa; domin tsayawa a Namira sunnah ce.

Idan rana ta karkace (wato lokacin Azzahar ya shigo), ya yi sallar Azzahar da La'asar raka'o'i biyu, zai haɗe su a tsarin Jam'u Taƙdim (ya haɗe sallar Azzahar da La'asar a lokacin Azzahar), kamar yadda Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya aikata; saboda lokacin tsayawa da yin addu'a ya tsawaita.

Sannan ya duƙufa bayan idar da sallar ga yin zikiri da addu'a, da ƙanƙan da kai zuwa ga Allah - Mai girma da ɗaukaka -, ya yi addu'a da abin da ya so, yana mai ɗaga hannayensa yana fuskantar Alƙibla, koda kuwa dutsen yana bayansa; saboda sunnah ita ce fuskantar Alƙibla ba dutsen ba, kuma haƙiƙa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya tsaya a wurin dutsen, kuma ya ce: [40] Muslim ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin abinda ya zo cewa Arafah dukkanta wurin tsayuwa ce, lamba ta (1218), daga hadisin Jabir - Allah Ya yarda da shi -. «‌Na tsaya a nan, kuma Arafah dukkanta wurin tsayuwa ce» [40].

«Ku nisanci Baɗnu Uranah» [41]. [41] Ibn Majah ne fitar da shi; Littafin ayyukan ibadu (na Hajji da Umra), babin wurin tsayuwa a Arafah, lamba ta (3012), daga hadisin Jabir - Allah Ya yarda da shi -.

Mafi yawan addu'ar Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - a wannan wurin tsayuwa mai girma ta kasance: «Lā ilāha illallāhu wahdahu lā sharika lahu, lahul mulku wa lahul hamdu, wa huwa alā kulli shai'in ƙadīr.» Ma’ana: (Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Shi kaɗai yake ba Shi da abokin tarayya, mulki naSa ne kuma godiya taSa ce, kuma Shi mai ikon ne akan komai) [42]. [42] Bukhari ne ya fitar da shi: Babukan Umarah, babin abin da zai ce idan zai dawo daga Hajji ko Umarah ko yaƙi, lamba ta (1797), da Muslim: Littafin Hajji, Babin abin da zai ce idan ya dawo daga tafiyar Hajji ko waninsa, lamba ta (1344), daga hadisin Ibn Umar - Allah Ya yarda da su -.

Idan ya ƙosa yana so ya huta ɗan wani lokaci ta hanyar hira tare da abokanansa da zantuttuka masu amfani ko karanta abin da ya sawwaƙa na litattafai masu fa'ida, musamman ma dai a cikin abin da yake da alaƙa da girman Allah da gwaggwaɓar kyautayinSa; don ya ƙarfafa bangaren ƙauna a wannan ranar to hakan yana da kyau, sannan ya koma ga ƙanƙan da kai ga Allah da kuma roƙonSa, kuma ya yi kwaɗayi a ribatar ƙarshen yinin da addu'a, domin mafificiyar addu'a ita ce addu'ar ranar Arafah.

Idan rana ta faɗi, sai ya tafi zuwa Muzdalifah. Idan ya je can, sai ya yi sallar Magariba da Isha'i a haɗe, saidai idan ya kai Muzdalifah kafin Isha'i, to zai yi sallar Magariba a kan lokacinta, sannan ya jira har lokacin Isha'i ya shiga, sai ya sallaceta a lokacinta. Wannan shi ne abinda nake gani a wannan mas'alar.

Zancen sahabbai - Allah Ya yi musu rahma - a lokutan sallah yana nuni akan hakan: Gabatar da ita - suna nufin Magariba - shi ya fi, sai fa a daren Muzdalifa ga wanda ya yi nufinta alhali yana mai harama, in bai zo mata ba a lokacin faɗuwar rana. Idan ya zo mata (Muzdalifa) a lokacin faɗuwar rana, zai yi sallar Magriba a lokacinta kuma ba zai jinkirtata ba. Ya faɗa a cikin al-Sharh al-Iƙna': Idan lokacinsa ya tabbata da ita (sallar Magariba) to ba zai jinkirtata ba, bari dai zai sallaceta ne a lokacinta; saboda ba shi da wani uzuri. Sun faɗa akan hadewar: Zai jinkirta a Muzdalifa, sannan suka bada dalili akan hakan da cewa lokacin Magariba ana shagalta ne da tafiya zuwa Muzdalifa a cikinsa. Malikiyya suka ce: Idan ya tsaya a tare da liman kuma ya tafi tare da shi, zai haɗe (sallolin) a Muzdalifah, idan kuwa bai tsaya tare da liman ba kuma ya tafi tare da shi, bari dai ya tsaya shi kaɗai ne ko ya jinkirta ga tafiyar limamin, ya yi sallar Magariba da Isha'i a lokacinta. Ya faɗa a cikin (Jawahirul Iklil) (Shafi na 181, Juz'i na 1). Ibn Hazmin - Allah Ya yi masa rahama - ya tsananta, sai ya ce: Sallar Magariba ba ta isuwa a wannan daren face a Muzdalifah, kuma babu makawa bayan ɓoyuwar shafaƙi, kuma babu makawa [43]. Ya ƙare. [43] Al-Muhalla (3/165).

A cikin (Sahihul Bukhari) daga ibn Mas'ud - Allah Ya yarda da shi -: «‌Cewa shi ya zo Muzdalifah a lokacin kiran sallar Isha'i ko kusa da hakan, sai ya umarci wani mutum, sai ya yi kiran sallah ya kuma yi iƙamah, sannan ya yi sallar Magariba, kuma ya yi sallah raka'o'i biyu a bayanta, sannan ya sa a kawo abincin darensa ya ci, sannan ya umarci wani mutum ya yi kiran sallah ya kuma yi iƙamah, sannan ya yi sallar Isha'i raka'o'i biyu». A wata ruwayar: «Sai ya yi salloli biyu, kowace sallah ita kaɗai da kiran sallah da iƙamah, kuma ya ci abincin dare a tsakaninsu» [44]. [44] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin wanda ya yi kiran sallah da iƙamah ga kowace ɗaya daga cikinsu, lamba ta (1675), daga hadisin Abdullahi bin Mas'ud - Allah Ya yarda da shi -.

Saidai in ya buƙaci haɗewar; ko saboda wahala ko ƙarancin ruwa ko waninsu to babu laifi da haɗewar, koda kuwa lokacin Isha'in bai shiga ba. Idan yana tsoron ba zai isa zuwa Muzdalifah ba sai bayan tsakiyar dare, to lallai shi zai yi sallah koda kuwa kafin ya kai zuwa Muzdalifah ne, kuma ba ya halatta ya jinkirta sallah zuwa bayan tsakiyar dare.

Sai ya kwana a Muzdalifah, idan alfijir ya bayyana, ya yi sallar Asubah da wuri da kiran sallah da iƙamah, sannan ya nufi Mash'aril Haram, sai ya yi hailala da kabbara, ya yi addu'a da abinda ya so har (gari) ya waye sosai. Idan tafiya Mash'aril Haram (Masallacin Muzdalifa) bata sawwaƙa a gare shi ba ya yi addu'a a nan wurin na sa; saboda faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: «Na tsaya a nan, kuma Jam'u (Muzdalifah) dukkanta wurin tsayuwa ne»[45]. A halin yin zikirin da addu'a zai kasance yana mai fuskantar Alƙibla yana ɗaga hannayensa. [45] Muslim ne ya fitar dashi: Littafin Hajji, babin Hajjin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, lamba ta (1218), daga hadisin Jabir - Allah Ya yarda da shi -.

Idan (gari) ya waye sosai, sai ya tafi zuwa Mina kafin bullowar rana, ya yi gaggawa a Wadi Muhassar, idan ya isa Mina ya jefi Jamratul Aƙabah (babban shaiɗan), shi ne na ƙarshe daga gefen Makkah, da tsakwankwani bakwai a jere; ɗaya bayan ɗaya, kowane ɗaya kusan gwargwadon girman ƙwallon dabino, yana yin kabbara a tare da kowace tsakuwa, idan ya gama ya yanka hadayarsa, sannan ya aske kansa ƙwalƙwal idan namiji ne, amma mace saisaye (ta rage gashinta gwargwadon girman ɗan yatsa) shi ne haƙƙinta ba ƙwalƙwal ba, sannan ya gangara zuwa Makkah, sai ya yi ɗawafi da Sa'ayi na Hajji.

Sunna ita ce ya shafa turare idan ya yi nufin gangarawa zuwa Makkah don yin ɗawafi bayan jifa da aski ƙwal-ƙwal; saboda faɗin Nana A'isha - Allah Ya yarda da ita -: "Na kasance ina shafawa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata gare shi - turare don haramarsa kafin ya yi harama, haka kuma don fita daga haramarsa kafin ya yi Dawafi a Ɗaki"[46]. [46] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin shafa turare a lokacin harama da abin da zai ɗaura idan ya yi nufin yin harama, ya taje kai ya shafa mai, a lamba ta (1539), da Muslim: Littafin Hajji, babin shafa turare ga mai harama a lokacin yin harama, a lamba ta (1189), daga hadisin A'isha - Allah Ya yarda da ita -.

Sannan bayan ɗawafi da sa'ayi zai koma Mina, sai ya kwana a can daren goma sha ɗaya da goma sha biyu, zai jefi Jamarori uku idan rana ta yi zawali a ranaku biyun, abin da ya fi ya tafi jifan a ƙasa, idan ya hau abin hawa to babu laifi, sai ya jefi Jamra ta farko wacce ita ce mafi nisan jamrori uku daga Makka, ita ce wacce take bin masallacin Khaif, da tsakwankwani bakwai a jere suna bin juna, ɗaya bayan ɗaya, yana mai yin kabbara tare da kowace tsakuwa, sannan ya yi gaba kaɗan sai ya yi addu'a mai tsawo da abin da yake so, idan tsawon tsayuwar da addu'ar sun wahalar da shi, sai ya roƙi abin da ya sawwaƙa gare shi, ko da kaɗan ne don ya dace da sunnah.

Sannan ya jefi Jamratul Wusɗah (na tsakiya) da tsakwankwani bakwai a jere, yana mai yin kabbara a tare da kowace tsakuwa. Sannan ya matsa ɓangaran hagu, sai ya tsaya yana mai fuskantar Alƙibla yana mai ɗaga hannayensa yana yin addu'a mai tsawo in hakan ya sawwaƙa gare shi, idan ba haka ba, to ya tsaya gwargwadon abin da ya sawwaƙa. Bai kamata ya bar tsayuwar addu'ar ba saboda sunnah ce, kuma da yawan mutane suna barinta; ko dai don jahilci ko wulaƙantarwa, kuma duk sanda aka bar sunnah, to aikatata da yaɗa ta tsakanin mutane ya fi ƙarfi; don kada a barta ta mutu.

Sannan ya jefi Jamratul Aƙabah (babban shaiɗan) da tsakwankwani bakwai a jere, yana mai yin kabbara a tare da kowace tsakuwa, sannan ya juya kuma kada ya yi addu'a bayansa.

Idan ya gama jifan Jamrorin a rana ta sha biyu, idan ya so ya gaggauta sai ya Mina, idan ya so ya jinkirta, sai ya kwana a nan a daren goma sha uku ya jefi Jamrorin uku bayan rana ta yi zawali kamar yadda ya gabata, yin jinkirta shi ya fi, kuma ba ya wajaba har sai rana ta faɗi a rana ta goma sha biyu alhali yana Mina, to jinkirtawa tana wajaba akansa har sai ya jefi Jamrorin uku bayan rana ta yi zawali. Sai dai, da rana za ta faɗi alhali yana Mina a rana ta goma sha biyu ba da zaɓinsa ba, misali: ya kasance ya tafi ya hau (abin hawa), sai dai ya makara saboda cunkoson ababen hawa da makamancinsa, to lallai yin jinkirin ba ya hawa kansa; saboda jinkrtawarsa zuwa faɗuwar rana ba akan zabinsa bane.

Idan ya yi nufin fita daga Makkah zuwa garinsa (komawa gida), ba zai fita ba har sai ya yi ɗawafin bankwana; saboda faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: «‌Kada wani ya tafi har sai ƙarshen lamarinsa ya zama da ɗaki (Ka'aba) ne» [47]. A wata riwayar: «‌An umarci mutane da ƙarshen lamarinsu ya zama da ɗaki (Ka'aba) ne, sai dai an sauƙaƙawa mai al’ada » [48]. Mai jinin al'ada da mai biƙi babu (yin ɗawafin) bankwana a kansu, kuma ba ya kamata su tsaya a bakin ƙofar masallacin Harami don yin bankwana; saboda rashin zuwan hakan daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -. [47] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin ɗawafin bankwana, lamba ta (1755), da Muslim: Littafin Hajji, babin wajibcin ɗawafin bankwana da faduwarsa ga mai al’ada, lamba ta (1327), daga hadisin ibn Abbas - Allah Ya yarda da su -. [48] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin ɗawafin bankwana, lamba ta (1755), da Muslim: Littafin Hajji, babin wajibcin ɗawafin bankwana da faduwarsa ga mai al’ada, lamba ta (1328), daga hadisin ibn Abbas - Allah Ya yarda da su -.

Zai sanya ɗawafin bankwana ya zama shi ne ƙarshen lamarinsa da ɗaki (Ka'aba) idan ya tashi yin tafiya, idan ya zauna bayan ɗawafin bankwana don jiran ayari, ko ɗora kayansa, ko siyan wata haja a hanyarsa, to babu laifi a kansa, kuma ba zai sake yin ɗawafin ba sai idan ya yi niyyar jinkirta tafiyarsa. Misali: ya yi niyyar tafiya da safe, sai ya yi ɗawafin bankwana, sannan ya jinkirta tafiya zuwa ƙarshen yini (da yamma) misali, to lallai maimaita yin ɗawafin yana tabbata; don ƙarshen lamarinsa ya zama da ɗaki (Ka'aba) ne.

* * *

Ziyartar Masallacin Annabi.

Idan mai aikin Hajji ya so ya ziyarci masallacin Annabi kafin aikin Hajji ko bayansa, to ya yi niyyar ziyartar masallaci Annabi ba ziyartar kabari ba, domin ɗaure sirdi (yin tafiya) da nufin ibada ba ya kasancewa don ziyartar kaburbura, kaɗai yana kasancewa ne ga masallatai uku: Masallacin Harami, masallacin Annabi da masallacin al-Aƙsa, kamar yadda yake a tabbataccen hadisi daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: «Ba'a ɗaura sirdi, sai zuwa masallatai uku: Masallaci mai alfarma, da wannan masallacin nawa, da msallacin al-Aƙsa [49]». [49] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin falalar sallah a masallacin Makkah da Madina, babin falalar sallah a masallacin Makkah da Madina, lamba ta (1189), da Muslim: Littafin Hajji, babin ba'a ɗaura sirdi face zuwa masallatai uku, lamba ta (1397), daga hadisin Abu Hurairah - Allah Ya yarda da shi -.

Idan ya isa masallacin Annabi, ya gabatar da ƙafarsa ta dama don shiga, kuma ya ce: «Bismillāhi was salātu was salāmu alā rasūlillāhi, Allāhummag firlī zunūbi, waf tahlī abwāba rahmatiKa, a'ūzu bil lāhil azīm, wa bi wajhihil karīm, wa bi sulɗānihil ƙadīm minash shaiɗānir rajīm». Ma’ana: (Da sunan Allah, kuma tsira da Aminci su tabbata ga Manzon Allah, Ya Allah Ka yi mun gafarar zunubaina kuma Ka buɗe min ƙofofin rahmarKa, ina neman tsari da Allah Mai girma da kuma fuskarSa Mai karamci da ikonSa dadaɗɗe daga Shaiɗan jefaffe) [50]. Sannan ya yi sallah (gwargwadon) yadda ya so. [50] Abu Dawud ne ya fitar da shi: Littafin sallah, babin abin da mutum zai faɗa a yayin shiga masallaci, lamba ta (466), daga hadisin Ibn Amr - Allah Ya yarda da su -.

Abinda ya fi shi ne sallar ta zama a Raudah, ita ce abin da ke tsakanin mimbarin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - da ɗakinsa da kabarinsa ke ciki; domin abin da ke tsakaninsu dausayi ne daga dausayan aljannah [51]. Idan ya yi sallar, kuma ya yi nufin ziyartar kabarin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - to sai ya tsaya a gabansa cikin ladabi da kawaici, sai ya ce: «Assalāmu alaika ayyuhan nabiyyu wa rahmatullāhi wa barakātuhu, Allāhumma salli alā Muhammadin wa alā āli Muhammadin kamā sallaita alā Ibrahim wa alā āli Ibrahim, innaKa hamīdun majīd, Allāhumma bārik alā Muhammadin wa alā āli Muhammadin kamā bārakta alā Ibrahim wa alā āli Ibrahim, innaKa hamīdun majid [52]. Ashhadu annaka rasūlullahi haƙƙan, wa annaka ƙad ballagtar risālah, wa addaital amānah, wa nasahtal ummah, wa jāhadta fi haƙƙil lāhi haƙƙa jihadihi, fa jazākal lāhu an ummatika afdala mā jazā nabiyyan an ummatihi». Ma’ana: (Aminci ya tabbata a gareka ya kai wannan Annabi, da rahama da albarkar Allah, Ya Allah Ka yi salati ga Muhammadu da alayen Muhammad, kamar yadda Ka yi salati ga Ibrahim da alayen Ibrahim, lallai Kai Abin godiya ne, Mai girma. Ya Allah Ka yi albarka ga Muhammadu da alayen Muhammadu, kamar yadda Ka yi albarka ga Ibrahim da alayen Ibrahim, lallai Kai abin godiya ne, Mai girma. [52] Ina shaidawa lallai kai Manzon Allah ne tabbas, kuma lallai ka isar da saƙo, kuma ka bayar da amanah, kuma ka yi wa al'umma nasiha, kuma ka yi jihadi a tafarkin Allah haƙiƙanin jihadinsa, don haka Allah Ya saka maka a madadin al'ummarka da mafi kyawun sakamako da Ya bai wa Annabi a madadin al'ummarsa). [51] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin falalar sallah a Masallacin Makkah da Madina, babin falalar abinda ke tsakanin kabari da mimbari (na Annabi), lamba ta (1196), da Muslim: Littafin Hajji, babin abin da ke tsakanin kabari da mimbari (na Annabi) dausayi ne daga dausayan aljannah, lamba ta (1391), daga hadisin Abu Hurairah - Allah Ya yarda da shi -. [52] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (6350), da Muslim, a lamba ta (406).

Sannan ya matsa ɓangaran dama kaɗan, sai ya yi sallama ga Abubakar al-Siddiƙ ya nema masa yarda, sannan ya ƙara matsawa ɓangaran dama kaɗan, sai ya yi sallama ga Umar bin al-Khaɗɗab ya nema masa yarda, idan ya yi addu'a gare shi da Abubakar - Allah Ya yarda da su - da addu'ar da ta dace to hakan ya yi kyau.

Ba ya halatta ga wani ya nemi kusanci zuwa ga Allah ta hanyar shafa ɗakin Annabi ko ɗawafi a wurin, kuma kada ya fuskance shi a halin addu'a, bari dai ya fuskanci Alƙibla; domin neman kusanci zuwa ga Allah ba ya kasancewa sai da abin da Allah da ManzonSa suka shara'anta, kuma ibadu an ginasu ne akan bi, ba'a kan ƙirƙira ba.

Mace ba zata ziyarci ƙabarin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ba ko ƙabarin waninsa; saboda Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya la'anci mata masu ziyartar ƙaburbura da masu mayar da makabartu masallatai da sanya wa (makabartu) fitilu a cikinsu [53]. Sai dai za ta yi sallah ta yi sallama ga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - alhali tana wajenta, sai hakan ya kai ga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - a duk inda take. Ya zo a cikin hadisi daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - cewa ya ce: «Ku yi salati gare ni domin salatinku yana zuwa min a duk inda kuke» [54]. Kuma - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Allah Yana da wasu Mala'iku waɗanda suke yawo a bayan ƙasa, suna isar min da sallama daga al'ummata» [55].. [53] Abu Dawud ne ya fitar da shi: Littafin jana’iza, babi a kan ziyartar mata ƙaburubra, lamba ta (3236); da Tirmizi: Littafin sallah, babin abin da ya zo dangane da karhancin a riƙi masallaci a kan ƙabari, lamba ta (320); da Nasa’i: Littafin Jana’iza, babin kaurarawa akan sanya fitilu a ƙaburbura, lamba ta (2043), daga hadisin Ibn Abbas - Allah Ya yarda da su -. [54] Abu Dawud ne ya fitar da shi: Littafin ayyukan ibadu, babin ziyartar kaburbura, lamba ta (2042), daga hadisin Abu Hurairah - Allah Ya yarda da shi -. [55] Nasa'i ne ya fitar da shi: Littafin rafkanuwa, babin yin sallama ga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, lamba ta (1282), daga hadisin ibn Mas'ud - Allah Ya yarda da shi -.

Yana kamata ga namiji kaɗai ya ziyarci Baƙi'ah, ita ce maƙabartar Madinah, sai ya ce: «Assalāmu alā ahlid diyār minal mu'minīn, wa innā in shā Allāhu bikum lāhiƙūn, yar hamil lāhul mustaƙdimīna minnā wa minkum wal mustakhirīn, wa nas'alul lāha lanā wa lakumul āfiyah». Ma’ana: (Amincin Allah ya tabbata ga mutanen wannan gida daga muminai, kuma lallai in shā Allahu zamu haɗu da ku. Allah Ya jiƙan magabata a cikinmu da majinkirta, kuma muna roƙon Allah lafiya ga mu da ku [56]. «Allāhumma lā tahrimnā ajrahum wa lā taftinnā ba'dahum, wag firl lanā wa lahum». Ma’ana: (Ya Allah kada Ka haramta mana ladansu kuma kada Ka fitinemu a bayansu, kuma Ka yi mana gafarta da su [57]. [56] Muslim ne ya fitar da shi; Littafin jana'iza, babin abin da ake faɗa yayin shiga maƙabarta da addu'a ga 'yan ciki, lamba ta (974, 975), daga hadisin Nana Aisha - Allah Ya yarda da ita -, da Buraidah - Allah Ya yarda da shi -. [57] Ibn Majah ne ya fitar da shi: Littafin abinda ya zo a jana'iza, babin abin da ya zo cikin abin da ake faɗa idan an shiga maƙabarta, lamba ta (1546), daga hadisin Nana Aisha - Allah Ya yarda da ita -.

Idan ya so ya je «Uhud», ya tuna da abin da ya gudana ga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - da sahabbansa a wannan yaƙi na wahala da ibtila'i da jarrabta da shahada. Sannan ya yi sallama ga shahidan wajen, misali: Hamza ɗan Abdul Muɗallib - Allah Ya yarda da shi - baffan Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - to babu laifi da wannan, domin wannan yana iya zama a cikin tafiya a doron ƙasa da aka yi umarni da shi, kuma Allah Shi ne masani.

* * *

FA'I'DOJI

Waɗannan wasu fa'i'doji ne da suke da alaƙa da ayyukan ibadu da ake buƙatuwa zuwa ga bayanansu da saninsu:

Fa'ida ta farko: A ladubban Hajji da Umarah:

Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Hajji watanni ne sanannu. To, wanda ya yi niyyar hajji a cikinsu to bãbu jimã'i kuma bãbu fãsiƙanci, kuma bãbu jãyayya a cikin hajji. Kuma abin da kuka aikata daga alhẽri, Allah Ya san shi. Kuma ku yi guzuri. To, mafi alhẽrin guzuri yin taƙawa. Kuma ku bi Ni da taƙawa, ya ma'abuta hankula. 197} [al-Baƙara: 197]. Kuma Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Kaɗai an sanya ɗawafi a ɗaki (ka'aba), da Safa da Marwa, da jifan Jamrori ne, don tsayar da zikirin Allah» [58]. [58] Abu Dawud ne ya fitar da shi: Littafin ayyukan ibadu (na Hajji da Umarah), babi a cikin sassarfa, lamba ta (1888), da Tirmizi: Babukan Hajji, babin abin da yazo ta yaya za'a jefi Jamrori, lamba ta (902), daga hadisin A'isha - Allah Ya yarda da ita -.

Don haka, yana kamata ga bawa ya tsayar (tabbatar) da ayyukan ibadun Hajji akan tafarkin girmamawa da Ijlali da soyayya da ƙanƙan da kai ga Allah Ubangijin talikai, sai ya gabatar da su cikin natsuwa da kawaici da bin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -.

Yana kamata ya shagaltar da waɗannan wuraren ibadu masu girma da yin zikiri da Kabbara, da Tasbihi da Tahmidi da Istigfari; saboda shi yana cikin ibada ne tun daga lokacin da ya fara yin harama har zuwa warwarewa. Hajji ba fage ne na shagala da wasa ba, da mutum zai dinga jin daɗi da shi irin yadda yaga dama ba tare da iyakancewa ba, kamar yadda ake gani daga wasu mutanen; suna tare da kayan shagala da kaɗe-kaɗe na abin da zai hana su ambaton Allah ya jefa su cikin saɓo. Kana kuma ganin wasu mutanen suna kutsawa cikin wasa da dariya da izgili da halittu, da wanin wannan na daga ayyukan ƙi, kamar ma an shar'anta aikin Hajjin ne don hutu da wasa.

Kuma yana wajaba ga mai aikin Hajji da waninsa ya kiyaye abin da Allah Ya wajabta a kansa na daga sallar jam'i a lokacinta, da umarni da kyakkyawa da kuma hani daga mummuna.

Kuma yana kamata ya kwaɗaitu akan amfanar musulmai da kyautatawa garesu ta hanyar shiryarwa da taimako a yayin buƙata, ya tausayawa raunanansu, musamman ma a wuraren jin ƙai, kamar wuraren turmutsutsi da makamantansu, domin jin ƙan mutane yana janyo jin aƙan mahalicci. «Kadai Allah Yana jin ƙan masu jin ƙai ne daga bayinSa» [59]. [59] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin jana’iza, babin faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: «Ana azabtar da mamaci da kukan iyalansa a kansa» idan kukan ya kasance daga sunnarsa, lamba ta (1284), da Muslim: Littafin Jana'iza, babin Kuka akan mamaci, lamba ta (923), daga hadisin Usama bin Zaid - Allah Ya yarda da su -.

Ya nisanci kwarkwasa da fasiƙanci da saɓo, da jayayya ba don taimakon gaskiya ba, amma yin jayayya don taimakon gaskiya to wajibi ne a wurinsa. Ya guji yin zalunci akan halittu da cutar da su; sai ya nisanci yin giba da annamimanci da zagi da aibatawa da duka da kalllon mata da ba maharramansa ba, domin wannan haramun ne a harami da wajen harami, sai haramcinsa ya ƙarfafu a halin yin harama.

Ya guji abinda mutane da yawa suke fararwa da shi na zancen da bai dace da wuraren ibadu ba, kamar yadda wasu suke fada idan sun jefi Jamrori: Mun jefi shaiɗan! wataƙil ma ya zagi wajen ibadar ko ya dake shi da takalmi ko makamancinsa na abin da yake kore ƙanƙan da kai a ibada, ya kuma ci karo da abin da aka nufata da yin jifan Jamrorin, shi ne tsayar da ambaton Allah - Mai girma da ɗaukaka -.

Fa'ida ta biyu; A abubuwan da aka hana saboda yin harama:

Abubuwan da aka hana saboda yin harama: Sune abubuwan da aka hana mai yin harama da aikin Hajji ko Umarah (ya aikata su) saboda yin harama, sun kasu kashi uku:

Kason da suka haramta akan maza da mata, da kason da suka haramta akan maza kaɗai banda mata, da kason da suka haramta akan mata banda maza.

Amma waɗanda suka haramta akan maza da mata, akwai daga cikinsu:

1- Yin jima'i a farji: Shi ne mafi girman abin da aka hana, idan ya afku a Hajji kafin warware harama ta farko, al'amurra guda uku suna kansa:

Na farko: Aikin Hajjin ya baci, sai dai zai ci gaba da shi har ya cika shi.

Na biyu: Wajibcin rama shi a shekara mai zuwa, koda kuwa ya kasance na nafila ne.

Na uku: Soke taguwarsa a Hajjin ramuwar.

2- Kallo da runguma saboda sha'awa.

3- Sanya al-ƙuffazain, sune (safunan) hannaye.

4- Cire gashin kai saboda yin aski ko waninsa, haka nan cire shi daga ragowar jiki a abin da yafi shahara: Sai dai da gashi zai sauka a idonsa da yake cutuwa da shi, kuma ba zai iya kawar da cutar ba sai idan ya cire shi, to ya cire shi kuma babu komai a kansa. Ya halatta mai harama ya sosa kansa da hannunsa, idan gashi ya faɗo ba da ganganci ba to babu komai a kansa.

5- Yanke farcen hannu ko ƙafa: Sai dai idan farcen nasa ya karye kuma yana cutar da shi, to babu laifi ya cire wanda yake cutuwa da shi ɗin kaɗai, kuma babu komai a kansa.

6- Amfani da turare bayan yin harama a kaya ko a jiki ko waninsu; Amma turaren da zai shafa kafin yin harama to wanzuwarsa bayan yin harama ba ya cutar da shi; saboda abin da aka hana a yin harama shi ne a fara sanya turaren ba dawwamarsa ba. Ba ya halatta ga wanda ya yi harama ya sha shayin da akwai za'farani a ciki; saboda za'farani yana daga cikin turare, sai dai idan tabbas ɗanɗanonsa da ƙamshinsa sun tafi saboda an dafa, kuma ba abin da ya ragu face launi kaɗai, to babu laifi.

7- Kashe abin farauta: Shi ne dabbar sarari ta daji da aka halatta, misali: Bareyi, da zomaye, da tantabaru, da fari, amma farautar na kogi to ya halatta, don haka ya halatta ga wanda ya yi harama ya yi su din kifayen kogi, haka nan dabbobin gida sun halatta, kamar kaji.

Idan fara ta kai hari a hanyarsa kuma babu wata hanyar in ba wannan ba, sai ya taka wani abu daga gareta ba da nufi ba to babu komai a kansa; saboda bai yi niyyar kashe ta ba, kuma ba zai iya zagayewa daga gareta ba.

Amma sare bishiya ba haramun bane ga mai harama; saboda babu tasirin yin harama a cikinsa, kaɗai yana haramta ne akan wanda yake cikin milamilan harami, daidai ne ya kasance mai harama ne ko mara harama, saboda haka sare bishiya yana halatta a Arafah, kuma ba ya halatta a Mina da Muzdalifah; saboda Arafah ta fita da milamilan (harami), su kuma Mina da Muzdalifah suna cikin milamilan (haramin).

Da ya sami (cire) wata bishiya alhali yana tafiya ba tare da ya nufata ba, babu komai a kansa, kuma yanke matattun bishiyoyi ba haramun ba ne.

Amma abubuwan da suka haramta akan maza banda mata, guda biyu ne:

1- Sanya ɗinkakken tufafi: Shi ne ya sanya tufafi da makamancinsu a irin sifar da ya saba sakawa, kamar riga (da singileti) da wando da makamantansu, ba ya halatta namiji ya sanya waɗannan abubuwa a irin yadda ya saba. Amma idan ya sanya su ba a irin yadda ya saba ba babu laifi, misali: Ya sanya riga a matsayin mayafi, ko ya rufa da abaya yana mai sanya samanta ya zama ƙasanta to duk babu laifi, babu laifi da sanya mayafi mai faci ko kwarjalle mai faci ko wanda aka haɗe.

Sanya belet, agogon hannu, gilashin ido da haɗe mayafinsa da fil ko makamancinsa duk sun halatta; saboda hani bai zo akan waɗannan abubuwan ba daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, kuma basa cikin ma'anar abinda da aka nassanto akan haninsa, bari dai, haƙiƙa an tambayi Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - game da abin da mai harama zai sanya, sai ya ce: «Kada ya sanya riga, ko rawanai, ko wanduna, ko huluna ko huffuna» [60]. Amsarsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - da abin da (mai harama) ba zai sanya ba daga abin da zai sanya, dalili ne akan cewa duk abin da ba ya cikin waɗannan da aka ambata mai harama zai iya sanyawa. Haka nan, ya halatta ga mai harama ya sanya huffuna guda biyu idan bai sami silifas ba; saboda buƙatuwarsa zuwa kiyaye ƙafafunsa, to kamar gilashin ido shima; saboda buƙatuwarsa zuwa kiyaye idanuwansa, malaman fiƙhu sun halatta sanya zobe ga namiji mai harama a abin da yafi shahara a mazhaba. [60] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin abin da mai harama ba zai sanya ba na tufafi, lamba ta (1543), da Muslim: Littafin Hajji, babin abin da ya halatta ga mai harama da aikin Hajji ko Umarah da abin da bai halatta ba, da bayanin haramcin turare gare shi, lamba ta (1177), daga hadisin ibn Umar - Allah Ya yarda da su -.

Yana halatta mai harama ya sanya wando idan bai sami kwarjalle ba ko kuɗinsa, kuma ya sanya huffuna idan bai sami silifas ba ko kuɗinsu; saboda hadisin ibn Abbas - Allah Ya yarda da su -: Cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce alhali yana huɗuba a Arafah: «Wanda bai sami silifas ba to ya sanya huffuna, wanda bai sami kwarjalle ba to ya sanya wando» [61]. [61] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin sakamakon yin farauta, babin sanya huffuna ga mai harama idan bai sami silifas ba, lamba ta (1841), da Muslim: Littafin Hajji, babin abin da ya halatta ga mai harama da Hajji da Umarah, da abin da bai halatta ga mai harama ba, da bayanin haramcin shafa turare gare shi, lamba ta (1178), daga hadisin Ibn Abbas - Allah Ya yarda da su baki ɗaya -.

2- Rufe kansa da maɗamfarin abu: Kamar rawani, da gutra (rawani me kewayayyen abu da larabawa suke sanyawa), da ɗāƙiyya (hula ce da take rufe kai), da mai kama da su, amma wanda ba ya ɗanfare da kai, kamar shema, da lema, da rufin mota to babu laifi da shi, domin abin da aka hana shi ne rufe kai banda shan inuwa, ya zo cikin Hadisin Ummul Husainul Ahmasiyya ta ce: «‌Munyi aikin Hajji tare da manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabata a gare shi - Hajjin bankwana, sai na gan shi yayin da ya jefi Jamratul Aƙabah ya juya alhali yana kan abar hawarsa, kuma a tare da shi akwai Bilal da Usama, ɗayansu yana jan abar hawarsa da shi, ɗayan kuma yana mai ɗaga tufafinsa a kan manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - yana masa inuwa saboda rana». A wata riwayar: «Yana kare shi daga zafi, har ya jefi Jamratul Aƙabah». Ahmad ne ya rawaito shi da Muslim [62]. Wannan ya kasance ne a ranar idi kafin warware harama; saboda shi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kasance yana jifan Jamrori ba'a ranar idi ba, a ƙasa ba'a abin hawa ba [63]. [62] Ahmad ne ya fitar da shi (6/402), da Muslim: Littafin Hajji, babin mustahabbancin jifan Jamratul Aƙabah ranar layya a abin hawa, da bayanin faɗinsa – tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: «Domin ku riƙi ayyukan ibadunku», lamba ta (1298), daga hadisin Ummul Husain - Allah Ya yarda da ita -. [63] Abu Dawud ne ya fitar da shi: Littafin ayyukan ibadu, babi a cikin jifan Jamrori, lamba ta (1969), daga hadisin ibn Umar - Allah Ya yarda da su baki ɗaya -.

Yana halatta ga mai harama ya ɗauki kaya a kansa idan bai yi nufin rufe kansa ba, haka nan ya halatta gare shi ya shiga cikin ruwa, ko da kuwa ya rufe kansa da ruwan.

Amma wanda ke haramta ga mata kawai banda maza; shi ne niƙabi, shi ne ta suturce fuskarta da wani abu kuma ta buɗe abin da zata dinga gani da idanuwanta, akwai daga malamai wanda ya ce: Baya halatta ta rufe fuskarta ko da niƙabi ko waninsa, sai idan maza suna wucewa ta kusa da ita; to ya zama dole ta rufe fuskarta, kuma babu fitar da fansa (fidiya) a kanta, daidai ne abin rufewar ya shafe ta ko a'a.

Wanda ya aikata abubuwan da aka hana da suka gabata, yana da halaye uku:

Hali na farko: Ya aikata abubuwan da aka hana ba tare da wani uzuri ba ko buƙata, to wannan mai laifi ne kuma akwai fitar da fansa (fidiya) a kansa.

Hali na biyu: Ya aikata abubuwan da aka hana saboda wata buƙatuwa zuwa hakan, misali: Ya buƙaci sanya riga saboda kare sanyi da yake tsoron cutuwa da shi, to ya halatta ya aikata hakan kuma akwai fansa (fidiya) a kansa, kamar yadda ya gudana ga Ka'ab bin Ujrah - Allah Ya yarda da shi - yayin da aka ɗauke shi zuwa ga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - alhali kwarkwata tana ɗiga a fuskarsa daga kansa, sai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya yi masa rangwame da ya aske kansa ya fitar da fansa (fidiya) [64]. [64] Bukhari ne ya fitar da shi: Babikan wanda aka tsare, babin ciyarwa rabin sa'i a fansa, lamba ta (1816), da Muslim: Littafin Hajji, babin halaccin aske kai ga mai harama idan akwai cuta a tare da shi, da wajibcin fitar da fansa saboda aske shi, da bayanin gwargwadonta, lamba ta (1201), daga hadisin Ka'ab bin Ujrah - Allah Ya yarda da shi -.

Hali na uku: Ya aikata abubuwan da aka hana alhali yana abin yi wa uzuri; ko don jahilci ko mantuwa, ko bacci ya yi ko tilasta masa aka yi, to babu laifi a kansa kuma babu fansa (fidiya) saboda faɗinSa - Maɗaukakin Sarki -: {Kuma bābu laifi a kanku game da abin da ku ka yi kuskure da shi, kuma amma (akwai laifi) ga abin da zukātanku suka ganganta...} [al-Ahzab: 5]. Kuma - Allah Maɗaukakin Sarki - Ya ce: {...Yã Ubangijinmu! Kada Ka kãmã mu, idan mun yi mantuwa, ko kuma mun yi kuskure...} [al-Baƙara: 286]. Sai Allah - Madaukakin Sarki - Ya ce: «‌Haƙiƙa Na aikata» [65]. [65] Muslim na ya fitar da shi: Littafin Imani, Babin bayanin faɗinSa - Maɗaukakin Sarki -:, lamba ta (126), daga hadisin Ibn Abbas - Allah Ya yarda da su baki ɗaya -.

A wani hadisin daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: «Lallai Allah Ya yafewa al'ummata kuskure da mantuwa, da kuma abin da aka tilasta musu akansa» [66]. [66] Ibn Majah ne ya fitar da shi: Littafin saki, babin sakin wanda aka tilastawa da wanda ya yi mantuwa, lamba ta (2043), daga hadsin Abu Zarrin Al-Gifari - Allah Ya yarda da shi -.

Waɗannan nassoshi ne gamammu a cikin abubuwan da aka hana saboda yin harama da waninsu da suke fa'idantar da kawar da laifi ga wanda aka yi wa uzuri da jahilci da mantuwa da tilastawa, kuma - Allah Maɗaukakin Sarki - Ya faɗa musamman game da yin farauta wanda yana daya daga abubuwan da aka hana saboda yin harama: {Yaku waɗamsa suka yi imani kada ku kashe abin farauta alhali ku kuna cikin harama, wanda ya kashe shi daga cikinku da gangan to akwai sakayya (a kansa) kwatankwacin abinda ya kashe daga dabbobin ni'ima...} [al-Mā'ida: 95]. Sai Ya ƙayyade wajibcin sakamako da kasancewar wanda ya yi kisan da gangan ya yi, kuma ganganci sifa ce da ta dace da uƙubah da lamuni, sai la'akari da shi da rataya hukunci da shi ya wajaba, idan kuwa bai kasance mai ganganci ba to babu sakamako a kansa kuma babu wani laifi.

Saidai duk sanda uzurin ya gushe, wanda bai sani ba ya sani, mai mantuwa kuma ya tuna, mai bacci ya tashi, tilastawa kuma ta gushe, to lallai ya zama wajibi barin wannan abubuwan da aka hana a nan take, idan ya ci gaba da abin bayan gushewar uzurin to ya yi laifi kuma akwai fitar da fansa (fidiya) a kansa. Misalin wannan: Namiji ya rufe kansa alhali yana bacci, to muddin dai yana bacci babu komai a kansa, idan ya farka to yaye rufin kan nasa ya wajaba a gare shi nan take, idan ya ci gaba da rufe kan nasa tare da saninsa da wajibcin yaye rufin nasa , to akwai fitar da fansa (fidiya) a kansa.

Gwargwadon fansar a abubuwan da aka hana da muka ambata sune kamar haka ne:

1- Game da cire gashi da farce, turare, sumbata don sha'awa, yin inzali saboda maimaita kallo, yin jima'i bayan warware harama ta farko, yin jima'i a Umarah, sanya safar hannu, namiji ya sanya ɗinkakken tufafi, rufe kansa, da mace ta sanya niƙabi, akwai fitar da fansa a waɗannan abubuwan, a kowanne ɗaya daga cikinsu; ko dai yanka ƙaramar dabba, ko ciyar da miskinai shida, ko azumin kwana uku, zai zaɓi abin da yake so daga cikin waɗannan al'amurra uku; saboda faɗinSa - Allah Maɗaukakin Sarki -game da aske gashi: {Wanda ya kasance mara lafiya daga cikinku ko yana da wata cuta a kansa...} Aya [al-Bakarah: 196]. Ka ƙiyasta sauran a kansa. Idan ya zaɓi yanka ƙaramar dabba, to zai yanka namiji ko macen tunkiya ko akuya daga wadda zata isa yanka, ko abin da yake tsayawa a muƙaminta (ƙimarta) na ɗaya bisa bakwai na taguwa ko ɗaya bisa bakwai na saniya, zai raba duka naman ga talakawa, kuma ba zai ci komai daga gare shi ba. Idan kuma ya zaɓi ciyar da miskinai, to zai baiwa kowane miskini rabin sa'i na abin da ake ci na daga dabino ko alkama ko waninsu. Idan ya zaɓi azumi, to zai yi azumin kwana uku; in ya so a jere, in kuma ya so a rarrabe.

2- A sakamakon abin farauta, idan abin farautar yana da kwatankwaci to an ba shi zaɓi tsakanin abubuwa uku; kodai yanka kwatankwacin da rarraba dukkanin namansa ga talakawan Makka, ko kuma ya duba nawane zai yi daidai da wannan kwatankwacin, sai ya fitar da abinci daidai da ƙimarsa, zai rarrabawa miskinai; kowane miskini yana da rabin kwano (rabin sa’i), ko kuma ya yi azimin yini ɗaya a madadin ciyar da kowane miskini.

Idan kuma abin farautar ba shi da kwatankwaci to an ba shi zaɓi tsakanin abubuwa biyu; Kodai ya duba nawane ƙimar abin farautar da aka kashe, sai ya fitar da abinci daidai ƙimarsa ya rarraba shi ga talakawa; kowane talaka yana da rabin kwano (rabin sa’i, mudun Nabiyy biyu kenan), ko kuma ya azimci rana ɗaya a madadin ciyar da kowane miskinin, (saboda idan miskinan sun kai hamsin, sai ya yi azumi hamsin).

Misalin wanda yake da kwatankwaci daga dabbobin ni'ima: Kurciya, kuma misalinta ƙaramar dabba, sai mu ce ga wanda ya kashe kurciya: kana da zaɓi, in ka so ka yanka ƙaramar dabba, in kuma ka so ka duba nawa ne ƙimar ƙaramar dabbar, sai ka fitar da abin da yake daidan ta na abinci ga talakawan harami; rabin sa'i ga kowane ɗaya, idan kuma ka so ka yi azumin rana ɗaya a madadin ciyar da kowane miskini.

Misalin abin farautar da ba shi da kwatankwaci: fara, sai mu ce ga wanda ya kashe fara da gangan: In ka so ka duba nawa ne kimar farar, sai ka fitar da abinda yake daidanta na abinci ga miskinan harami; rabin sa'i ga kowane miskini, idan kuma ka so ka yi azumin rana ɗaya a madadin ciyar da kowane miskini.

3- Game da yin jima'i a Hajji kafin warware haramar farko, taguwa.

Fa'ida ta uku: A Kan haramar ƙaramin yaro:

Ƙaramin yaron da bai balaga ba, Hajji bai wajaba a kansa ba, sai dai da ya yi aikin Hajji yana da ladan Hajjin kuma zai maimaita idan ya balaga. Yana kamata ga wanda yake juɓuntar lamarinsa daga uba ko uwa ko waninsu ya yi masa harama, ladan aikin ibadar yana kasancewa ga yaron, waliyinsa ma yana da ladan hakan; saboda abin da ya zo cikin (Sahihul Bukhari) daga hadisin ibn Abbas - Allah Ya yarda da su -: Cewa wata mace ta ɗaga wani ƙaramin yaro zuwa ga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, sai ta ce: Ya manzon Allah, shin akwai Hajji a kan wannan? Ya ce: «Eh, kuma kina da lada [67]». [67] Muslim ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin ingancin Hajjin ƙaramin yaro, lamba ta (1336), daga hadisin ibn Abbas - Allah Ya yarda da su -.

Idan kuma yaron ya kasance mumayyizi ne, shi ne wanda yake iya fahimtar abin da ake faɗa masa, to zai yi niyyar yin harama da kansa, sai waliyyinsa ya ce da shi: Yi niyyar harama da kaza, ya umarce shi da ya aikata abin da zai iya na ayyukan Hajji, misali: tsayuwar Arafah, da kwanan Mina da Muzdalifa. Amma abin da ba zai iya aikata shi ba kamar jifan Jamrori, to waliyyinsa zai yi masa ko waninsa da izininsa, sai kuma ɗawafi da sa'ayi, idan ba zai iya aikata su ba za'a ɗauke shi, a ce masa: yi niyyar ɗawafi, yi niyyar sa'ayi. A wannan hali ya halatta ga mai ɗaukarsa ya yi niyyar yin ɗawafi da sa'ayi ga kansa shima, yaron ga kansa, sai dawafi da sa'ayi ya tabbata ga dukkansu; saboda dukkansu sun yi niyya, kuma haƙiƙa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Dukkan ayyuka basa ingantuwa sai da niyyoyi, kuma kowane mutum ana ba shi ladan abinda ya niyyata ne [68]». [68] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin fara wahayi, babin yaya fara wahayi zuwa ga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kasance, lamba ta (1). Da Muslim: Littafin shugabanci, babin faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: «Dukkan ayyuka basa ingantuwa sai da niyya», kuma yaƙi da waninsa daga ayyuka suna shiga cikinsa, lamba ta (1907), daga hadisin Umar Ibn Al-Khaɗɗab - Allah Ya yarda da shi -.

Idan kuma yaron ya kasance ba mumayyizi bane, to waliyyinsa zai masa niyyar harama, ya yi masa jifa, zai je da shi wuraren ayyukan Hajji da Arafah da Muzdalifah da Mina, zai yi ɗawafi da sa'ayi da shi, ba ya inganta a wannan halin ya yi niyyar yin ɗawafi da sa'ayi ga kansa alhali yana yin ɗawafi da sa'ayi da yaron; saboda shi yaron a nan niyya da aiki basu tabbata daga gare shi ba, niyyar kawai daga wanda ya ɗauke shi ne, aiki guda ɗaya ba ya inganta da niyyoyi biyu ga mutnane biyu, saɓanin idan yaron ya zama mumayyizi ne; domin niyya ta tabbata daga gare shi, ayyuka kuwa suna ingantuwa ne da niyyoyi, wannan shi ne abin da ya bayyana gare ni. A kansa, sai waliyyin ya yi ɗawafi da sa'ayi ga kansa da farko, sannan ya yi ɗawafi da sa'ayi da yaron, ko ya miƙa shi zuwa wani amintacce da zai yi ɗawafi da sa'ayi da shi.

Hukunce-hukuncen haramar ƙaramin yaro kamar hukunce-hukuncen haramar babba ne; saboda Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya tabbatar da yana da Hajji, idan Hajji ya tabbata, hukunce-hukuncensa da wajibabbunsa sun tabbata. Saboda haka, idan yaron ya zama namiji ne, zai nisanci abin da namiji babba zai nisanta, idan kuma mace ce, zata nisanci abin da babbar mace zata nisanta, sai dai gangancin yaro yana a matsayin kuskuren babba ne, idan ya aikata wani abu daga abubuwan da aka hana saboda yin harama, to babu fitar da fansa a kansa ko a kan waliyyinsa.

Fa'ida ta huɗu: A cikin sanya wani ya yi wa mutum aikin Hajji:

Idan Hajji ya wajaba akan mutum, idan yana da ikon yin aikin Hajjin da kansa, to ya wajaba ya yi aikin Hajjin, idan kuma ba zai iya yin aikin Hajjin da kansa ba, idan yana fatan gazawar tasa zata gushe, kamar rashin lafiyar da yake fatan warkewarta, to zai jinkirta aikin Hajjin har ya sami iko, idan ya rasu kafin hakan, to sai a yi masa aikin Hajjin daga abin da ya bari, kuma babu laifi a kansa.

Idan kuma wanda aikin Hajjin ya wajaba a kansa ya kasance ya gaza yi, gazawar da ba ya sa ran gushewarta, kamar tsufa da rashin lafiyar da aka yanke ƙauna daga gareta, da wanda ba shi da ikon hawa abin hawa, to zai wakilta wanda zai masa aikin Hajjin; saboda abin da ya zo cikin (Bukhari da Muslim) daga hadisin ibn Abbas - Allah Ya yarda da su -: Cewa wata mace daga Khat'amah ta ce: Ya manzon Allah, lallai farillar Allah akan bayinsa a aikin Hajji ta riski baba na yana tsoho tukuf, ba ya iya zama a kan abar hawa, shin na yi masa Hajji? Ya ce; «Eh» [69]. Wannan ya kasance a Hajjin bankwana ne. [69] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin Hajji babin wajibcin Hajji da falalarsa, lamba ta (1513), da Muslim: Littafin Hajji, babin Hajji a madadin wanda ya gaza saboda nakasa, ko tsufa da makamantansu, ko saboda mutuwa, lamba ta (1334), daga hadisin Ibn Abbas - Allah Ya yarda da su duka -.

Ya halatta namiji ya wakilci mace, mace ta wakilci namiji.

Idan Hajji ya tabbata akan wakilin kuma bai yi wa kansa aikin Hajjin ba, to ba zai yi wa waninsa ba, kawai dai zai fara yi wa kansa ne tukunna; saboda hadisin ibn Abbas - Allah Ya yarda da su -: Cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ji wani mutum yana cewa: AmsawarKa ga Shuburumah, ya ce: «wanene Shubrumah?», ya ce: ɗan uwana ne, ko makusanci na ne. Ya ce: «ka yi wa kanka aikin Hajji ne?», ya ce: a'a, ya ce: «Ka yi wa kanka aikin Hajji sannan ka yi wa Shubrumah aikin Hajji». Abu Dawud ne ya rawaito shi da ibn Majah [70]. [70] Abu Dawud ne ya fitar da shi: Littafin ayyukan ibadun Hajji, babin mutum ya yiwa waninsa aikin Hajji, lamba ta (1811), da ibn Majah: Littafin ayyukan ibadun Hajji, babin yi wa mamaci aikin Hajji, lamba ta (2903), daga hadisin ibn Abbas - Allah Ya yarda da su -.

Abin da yafi, wakilin ya bayyana ambaton wanda yake wakilta, sai ya ce: AmsawarKa ga wane, idan mace ce ya ce: AmsawarKa ga mahaifiyar wane, ko ga 'yar wane.

Idan ya yi niyya daga zuciyarsa kuma bai ambaci suna ba, to babu laifi, idan ya mance sunan wanda ya wakilta shi, ya yi niyya da zuciyarsa ga wanda ya wakilta shi koda bai halarto da sunansa ba, Allah - Maɗaukakin Sarki - ya san shi kuma ba zai ɓuya gare shi ba.

Ya wajaba ga wakilin ya ji tsoron Allah - Maɗaukakin Sarki - ya kwaɗaitu akan kammala ayyukan ibadar; saboda shi abin damƙawa amana ne akan wannan, sai ya kwaɗaitu akan aikata abin da ya wajaba ya bar abin da ya haramta, ya kammala abubuwan da yake da iko na ayyukan da suke kammala ibadar da sunnoninta.

Fa'ida ta biyar: A kan canza tufafin harama:

Ya halatta mai haramar aikin Hajji ko Umarah; namiji ne ko mace ya canja tufafin harama da ya yi harama da su ya sanya wasu idan tufafin na biyun sun halatta mai harama ya sanya, kamar yadda ya ke halatta ga mai harama ya sanya silifas bayan yin harama, ko da kuwa lokacin da ya ƙulla haramar ba shi da takalmi.

Fa'ida ta shida; A wurin raka'o'i biyu na ɗawafi:

Sunnah ga wanda ya gama ɗawafi ita ce, ya yi sallah raka'o'i biyu a bayan Maƙamu Ibrahim. Idan wurin da ke kusa da Maƙamin mayalwaci ne to a nan, ida ba haka ba to ya yi sallar ko da a can nesa ne. Zai sanya Maƙamin tsakaninsa da tsakanin Ka'abah, sai ya tabbata a gare shi cewa ya yi sallah a bayan Maƙamin kuma ya bi hanyar Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, kamar yadda ya zo a hadisin Jabir - Allah Ya yarda da shi - a cikin sifar Hajjin Annabi: "Cewa shi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya sanya Maƙamin tsakaninsa da tsakanin ɗakin Ka'abah" [71]. [71] Muslim ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin Hajjin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, lamba ta (1218), daga hadisin Jabir - Allah Ya yarda da shi -.

Fa'ida ta bakwai: A kan jerantawa a yin sa'ayi da tsakaninsa da yin ɗawafi:

Abin da ya fi, sa'ayi ya biyo ɗawafi, idan ya jinkirta shi da yawa babu laifi, misali: Ya yi ɗawafi a farkon yini (da safe) sai ya yi sa'ayi a ƙarshen yuni (da yamma), ko ya yi ɗawafi da daddare sai ya yi sa'ayi bayan nan da tsakar rana. Ya halatta ga wanda ya gaji a sa'ayi ya zauna ya huta, sannan ya kammala sa'ayinsa a ƙasa ko a kan keke ko makamancinsa.

Idan an tada sallah alhali yana yin sa'ayi ya yi sallah, idan ya sallame sai ya cika sa'ayinsa daga wurin da ya tsaya kafin ya tada sallar.

Haka nan, da an tada sallah alhali yana ɗawafi ko an kawo jana'iza, to zai yi sallah, idan ya gama, ya cika ɗawafinsa daga wurin da ya tsaya kafin sallar, kuma babu buƙatar maimaita kewayen da ya yanke a zancen da yafi rinjaye gu na; saboda idan yankewar saboda sallah ce to an masa afuwa, don haka babu dalilin ɓacin zagayan farko.

Fa'ida ta takwas: A kokwanto akan adadin ɗawafi ko sa'ayi:

Idan mai yin ɗawafi ya yi kokwanto a adadin ɗawafin, idan dama mai yawan kokwanto ne, misali: wanda yake waswasi, to ba zai lura da wannan kokwanton ba, idan kuma ba mai yawan kokwanto ba ne, idan kokwanton nasa bayan ya gama ɗawafin ne, to ba zai kula da wannan kokwanton ba dai, sai dai idan ya samu yaƙini cewa ya rage, sai ya cika abin da ya tauye ɗin. Idan kuma kokwanton a tsakiyar ɗawafin ne, misali: ya yi kokwanto; shin kewayen da yake a ciki na uku ne ko na huɗu misali? Idan ɗaya daga al'amurran biyu ya rinjaya gunsa, sai ya yi aiki da wanda ya fi rinjayen a wajensa, idan kuma babu wani abu da ya rinjaya gunsa, sai ya yi aiki da yaƙini, shi ne mafi ƙaranci.

A misalin da aka ambata, idan kewaye uku suka rinjaya gunsa, ya sanya su zama uku ya zo da guda huɗu, idan kuma huɗu ne suka rinjaya gunsa, ya sanya su zama huɗu ya zo da guda uku, idan kuma babu wani abu da ya rinjaya gunsa, ya sanya su zama uku; saboda su ne yaƙini (tabbas), sai ya zo da guda huɗu.

Hukuncin kokwanto a adadin sa'ayi kamar hukuncin kokwanto ne a adadin ɗawafi a dukkan abin da ya gabata.

Fa'ida ta tara: A tsayuwa a Arafah:

Ya gabata cewa abin da ya fi ga mahajjaci ya yi harama da Hajjji a rana ta takwas ga Zul Hijjah, sannan ya fita zuwa Mina, sai ya zauna a nan a ragowar yininsa, ya kwana a dare na tara, sannan ya tafi zuwa Arafah da hantsi. Wannan akan tsarin da ya fi kenan, da ya fita zuwa Arafah ba tare da ya fara zuwa Mina ba, to lallai ya bar abin da ya fi falala, sai dai babu laifi a kansa.

Ya wajaba ga mai tsayuwa a Arafah ya tabbatar da iyakokinta, saboda wasu mahajjatan suna tsayuwa ne a wajen iyakokinta; ko dai don jahilci ko kwaikwayon wasu, kuma waɗanda suka tsaya a wajan iyakokin Arafah basu da Hajji; saboda ba su tsaya a Arafah ba, kuma haƙiƙa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Hajji shi ne Arafah» [72]. A duk inda ya tsaya a Arafah ya ishe shi; saboda faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: «‌Na tsaya a nan, kuma Arafah dukkanta wurin tsayuwa ce» [73]. [72] Abu Dawud ne ya fitar da shi: Littafin ayyukan ibadu, babin wanda bai riski Arafah ba, lamba ta (1949), da Tirmizi: Babikan Hajji, babin abin da ya zo dangane da wanda ya riski liman a Jam'u to lallai ya riski aikin Hajji, lamba ta (889), da Nasa’i: Littafin ayyukan ibadun Hajji, babin wajibcin tsayuwa a Arafah, lamba ta (3016), da Ibnu Majah: Littafin ayyukan ibadu, babin wanda ya halarci Arafah kafin ɓullowar alfijir a daren Jam'u, lamba ta (3015), daga hadisin Abdurrahman Ibn Ya'mar - Allah Ya yarda da shi -. [73] Muslim ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin abin da ya zo cewa Arafah dukkanta wurin tsayuwa ce, lamba ta (1218), daga hadisin Jabir - Allah Ya yarda da shi -.

Ba ya halatta ga wanda ya tsaya a Arafah ya bar iyakokinta har sai rana ta faɗi a ranar Arafah; saboda Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya tsaya har zuwa faɗuwar rana, kuma ya ce: «Ku riƙi ayyukan ibadunku (na Hajji da Umarah) daga gare ni [74]». [20] Muslim ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin mustahabbancin jifan Jamratul Aƙabah a ranar layya (idi) akan abin hawa, da bayanin faɗinsa – tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi: «Domin ku riƙi ayyukan ibadunku (na Hajji da Umarah)» lamba ta (1297), daga hadisin Jabir, - Allah Ya yarda da shi -.

Lokacin tsayuwa a Arafah yana kaiwa har zuwa ɓullowar alfijir ɗin ranar idi. Wanda alfijir ya ɓullo masa a ranar idi kuma bai tsaya a Arafah ba to lallai Hajji ya kuɓuce masa, idan ya sharɗanta a yayin fara yin harama: «Idan wani mai tsarewa ya tsare ni, to wurin warwarewa ta inda duk Ka tsare ni» [75]. Ya warware daga haramarsa kuma babu komai a kansa, idan bai sharɗanta ba kuma tsayuwa ta kuɓuce masa, to zai warware haramar (Hajji) sai ya maida ita Umarah, sai ya tafi zuwa Ka'aba ya yi ɗawafi da sa'ayi ya yi aski. Idan akwai abin hadaya a tare da shi ya yanka, idan shekara ta biyu ta zo, ya rama Hajjin da ya kuɓuce masa ya fitar da hadaya. Idan bai sami hadaya ba ya yi azumin kwana goma; guda uku a Hajji, guda bakwai idan ya koma wajen iyalinsa. [75] Nasa’i ne ya fitar da shi: Littafin ayyukan ibadun Hajji, ya zai ce idan zai sharɗanta, lamba ta (2766) daga hadisin Ibn Abbas - Allah Ya yarda da su -.

Fa'ida ta goma: A barin Muzdalifah:

Ba ya halatta ga mai ƙarfi ya bar Muzdalifa har sai ya yi sallar asuba a ranar idi; saboda Annabi - tsira da amoncin Allah su tabbata a gare shi - ya kwana a nan a daren idi kuma bai bar nan ba har sai da ya yi sallar asuba, kuma ya ce: «Ku riƙi ayyukan ibadunku (na Hajji da Umarah) daga gare ni [76]». [76] Muslim ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin mustahabbancin jifan Jamratul Aƙabah a ranar layya akan abin hawa, da bayanin faɗinsa – tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi: «Ku riƙi ayyukan ibadunku (na Hajji da Umarah)» lamba ta (1297), daga hadisin Jabir, - Allah Ya yarda da shi -.

A cikin (Sahihu Muslim) daga Nana Aisha - Allah Ya yarda da ita - ta ce: Saudatu ta nemi izinin manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - a daren Muzdalifah da ta bar (Muzdalifah) gabaninsa, kuma kafin cunkoson mutane, ta kasance mace ce mai ƙiba, sai ya yi mata izini, sai ta fita kafin barinsa, mu kuma ya riƙe mu har sai da muka yi Asubahi, sai muka tafi da shi [71]. [77] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin wanda ya gabatar da raunanan iyalansa da dare, sai su tsaya a Muzdalifah, su yi addu'a, sai ya wuce idan wata ya ɓuya, lamba ta (1680), da Muslim; Littafin Hajji, babin mustahabbancin gabatar da tura raunanan mata da wasunsu daga Muzdalifah zuwa Mina a ƙarshen dare kafin cunkoson mutane, da mustahabbancin zama ga wasunsu har su yi sallar Asubahi a Muzdalifah, lamba ta (1290), daga hadisin Nana Aisha - Allah Ya yarda da ita -.

A wata riwayar: "Na so a ce na nemi izinin manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - kamar yadda Saudatu ta nemi izininsa, sai na yi sallar Asubahi a Mina, na jefi Jamrah kafin mutane su zo" [78]. [78] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin wanda ya gabatar da raunanan iyalansa da dare, sai su tsaya a Muzdalifah, su yi addu'a, sai ya wuce idan wata ya ɓuya, lamba ta (1681), da Muslim; Littafin Hajji, babin mustahabbancin gabatar da tura raunanan mata da wasunsu daga Muzdalifah zuwa Mina a ƙarshen dare kafin cunkoson mutane, da mustahabbancin zama ga wasunsu har su yi sallar Asubahi a Muzdalifah, lamba ta (1290), daga hadisin Nana Aisha - Allah Ya yarda da ita -.

Amma mai rauni wanda cunkoson mutane a Jamra zai wahalar da shi, to shi yana da damar ya tafi kafin alfijir idan wata ya faku, sai ya jefi jamra kafin mutane su fara jifan. Ya zo a cikin (Sahihu Muslim) daga Asma'u: "Cewa ta kasance tana lura da bacewar wata kuma tana tambayar baranta (bawan da ta 'yanta): Shin wata ya bace ne? idan ya ce: Eh, sai ta ce: Tafi da ni. Ya ce: Sai su tafi har sai ta jefi babbar Jamrah, sannan ta sallaci Asuba a gidanta, sai na ce mata: Yake wannan, haƙiƙa mun yi wanka. Ta ce: A'a, ya kai ɗana, lallai cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi izinin tafiya ne"[79]. [79] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin wanda ya gabatar da raunanan iyalansa da dare, sai su tsaya a Muzdalifah, su yi addu'a, sai ya wuce idan wata ya bace, lamba ta (1679), da Muslim; Littafin Hajji, babin mustahabbancin gabatar da tura raunanan mata da wasunsu daga Muzdalifah zuwa Mina a ƙarshen dare kafin cunkoson mutane, da mustahabbancin zama ga wasunsu har su yi sallar Asubahi a Muzdalifah, lamba ta (1291), daga hadisin Nana Asma'u bint Abubakar - Allah Ya yarda da su -.

Wanda ya kasance cikin waɗannan raunanan waɗanda tafiya daga Muzdalifa kafin Asubahi ta halatta garesu to cewa ya halatta ya tafi tare da su kafin alfijir; domin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya aika Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su - a cikin raunanan iyalansa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - daga Muzdalifah da daddare. Idan ya kasance mai rauni ne sai ya jefi Jamra tare da su idan ya isa Mina; domin shi ba zai iya cunkoso ba, amma idan ya kasance yana iya cunkoso da mutane to ya jinkirta jifan har sai rana ta ɓullo; saboda hadisin Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya aikemu mu yaran Banu Abdul Muɗɗalib akan wasu jakunanmu daga Jam'u (Muzdalifah), sai ya fara yana dukan cinyoyinmu kaɗan yana cewa: «Yaku 'ya'yana kada ku yi jifa, har sai rana ta ɓullo». Ma'abota Sunan biyar ne suka rawaito shi kuma Tirmizi da Ibnu Hibban sun inganta shi [80]. [80] Abu Dawud ne ya fitar da shi: Littafin ayyukan ibadu (na Hajji da Umarah), babin gaggautowa daga Jam'u (Muzdalifah), lamba ta (1940), da Tirmizi: Littafin Hajji, babin abin da ya zo a cikin gabatar da raunana daga Jam'u (Muzdalifa) da daddare, lamba ta (893), da Nasa'i: Littafin ayyukan ibadun Hajj, babin hani daga jifan Jamratul Aƙabah kafin ɓullowar rana, lamba ta (3064), da Ibnu Majah: Littafin ayyyukan ibadu (na Hajji da Umarah), babin wanda ya zo daga Muzdalifa zuwa Mina don jifan Jamrori, lamba ta (3025), da Ibnu Hibban a cikin ingantaccen littafinsa (3869), daga hadisin Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su -.

Tabbataccen abu shi ne: Cewa tafiya daga Muzdalifah da jifan Jamratul Aƙabah a ranar Idi suna kasancewa ne a kan tsarin dake tafe:

Na farko: Wanda ya kasance mai ƙarfi ne kuma babu mai rauni a tare da shi, to ba zai bar Muzdalifah ba har sai ya yi sallar asuba, kuma ba zai jefi Jamrah ba har sai rana ta ɓullo; saboda hakan shi ne aikin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - da ya aikata, kuma ya kasance yana cewa: «Ku riƙi ayyukan ibadunku (na Hajji da Umarah) daga gareni [81]». Bai yi rangwame ga kowa ba daga masu ƙarfi a barin Muzdalifah kafin asuba, ko a jifan Jamra kafin ɓullowar rana. [81] Muslim ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin mustahabbancin jifan Jamratul Aƙabah a ranar layya akan abin hawa, da bayanin faɗinsa – tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi: «Ku riƙi ayyukan ibadunku (na Hajji da Umarah)» lamba ta (1297), daga hadisin Jabir, - Allah Ya yarda da shi -.

Na biyu: Wanda yake da ƙarfi kuma a tare da shi akwai iyalai raunana, to in ya so zai tafi tare da su a ƙarshen dare, mai raunin kuma zai jefi Jamra idan ya isa Mina, amma mai ƙarfi ba zai yi jifa ba har sai rana ta ɓullo, domin ba shi da wani uzuri [82]. [82] Mai girma babban malaminmu mawallafin - Allah Ya yi masa rahma - ya faɗa a cikin Fatāwal Hajji (Juz'i na 2 shafi na 272 da abin da ke bayansa): «Cewa ya halatta ga mai ƙarfin da akwai raunana a tare da shi ya tafi ya jefi Jamratul Aƙabah a tare da su kafin (ɓullowar) alfijir, domin abin da ba ya tabbatuwa shi kaɗai yana tabbata saboda bi».

Na uku: Mai rauni, yana halatta ya bar Muzdalifah a ƙarshen dare idan wata ya ɓuya, ya jefi Jamra ida ya isa Mina.

Wanda bai isa Muzdallifah ba har sai da alfijir ya ɓullo a daren idi, kuma ya riski sallah a cikinsa kuma ya tsaya a Arafah kafin alfijir, to Hajjinsa ingantacce ne; saboda hadisin Urwa bin Mudarris, a cikinsa cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «‌Wanda ya sami sallarmu wannan - yana nufin asuba -, kuma ya tsaya tare da mu har mu tafi, kuma lallai ya tsaya a Arafah kafin wannan da daddare ko da rana, to lallai ya cika Hajjinsa kuma ya gusar da ƙazantarsa». Marawaita biyar ne suka rawaito shi, kuma Tirmizi da Hakimu sun inganta shi [83]. [83] Abu Dawud ne ya fitar da shi: Littafin ayyukan ibadu (na Hajji da Umarah), babin wanda bai riski Arafah ba, lamba ta (1950), da Tirmizi: Littafin Hajji, babin abin da ya zo dangane da wanda ya riski liman a Jam’u (Muzdalifa), to haƙiƙa ya riski aikin Hajji, lamba ta (891), da Nasa’i: Littafin ayyukan ibadun Hajji, babin wanda bai riski sallar Asubahi tare da liman ba a Muzdalifah, lamba ta (3041), da Ibn Majah: Littafin ayyukan ibadu (na Hajji da Umarah), babin wanda ya zo Arafah kafin alfijir, lamba ta (3016), da Hakimu (1/634), daga hadisin Urwah bin Mudarris - Allah Ya yarda da shi -.

Zahirin wannan hadisin shi ne babu jini (yanka) a kansa; hakan kuwa saboda ya riski wani yanki daga lokacin tsayuwa a Muzdalifah kuma ya ambaci Allah - Maɗaukakin Sarki - a Mash'aril Haram saboda abin da ya yi na sallar alfijir, sai aikin Hajjinsa ya zama cikakke, da akwai jini (yanka) a kansa da Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya bayyana shi, kuma Allah shi ne masani.

Fa'ida ta goma sha ɗaya: Akan abin da ke da alaƙa da yin jifa:

1- Dangane da tsakuwar da zai yi jifa da ita, ta kasance tsakanin girman wake da gyadar turawa, ba mai girma ba sosai ko ƙanƙanta. Ana tsintar tsakuwar daga Mina ko Muzdalifah ko wani wurin, kowace rana da ranarsa, kuma bai tabbata daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ba cewa ya tsinci tsakuwar daga Muzdalifah, ko ya tsinci tsakuwar duka ranakun ya tara su, kuma bai umarci kowa da wannan ba daga sahabbansa cikin abin da na sani.

2- Ba ya wajaba tsakuwar ta jifan ta damki jikin ginshiƙin dake tsaye, kawai dai abin da yake wajibi ta tabbata a daidai ramin da ke tara tsakwankwanin, da zata dakki ginshiƙin kuma ba ta faɗa cikin kwarin ba, to ya wajaba ya yi wani jifan maimakon wannan, da ta sauka a kwarin kuma ta tabbata a ciki, ta isa ko da kuwa bata sami ginshiƙin ba.

3- Da zai manta wata tsakuwa daga ɗaya daga Jamrorin, ta yadda bai yi jifa ba face da tsakwankwani shida kuma bai tuna ba har ya isa wurin shemarsa, to zai dawo ya yi jifan da ya manta kuma babu laifi a kansa. Idan rana ta faɗi kafin ya tuna to zai jinkirtata har zuwa rana ta biyu, idan rana ta karkato zai yi jifa da tsakuwar da ya mantata kafin yin komai, sannan ya jefi Jamrori na wannan ranar da ake ciki.

Fa'ida ta goma sha biyu: A kan warwarar harama ta farko da ta biyu:

Idan ya jefi Jamratul Aƙabah a ranar idi, ya kuma aske kansa ƙwalƙwal ko saisaye, to ya yi warwarar harama ta farko kenan, kuma dukkanin abubuwan da aka hana saboda yin harama sun halatta gare shi, na shafa turare, sanya tufafi, cire gashi da farata, da wanin wannan face mata (wato ba’a halatta masa mata ba), domin ba ya halatta gare shi ya rungumi matarsa ko ya kallaceta don sha'awa har sai ya yi ɗawafi a Ka’abah ya kuma yi sa'ayi tsakanin Safa da Marwa. Idan ya yi ɗawafi da sa'ayi to ya yi warwarar harama ta biyu, kuma dukkan abubuwan da aka hana saboda yin harama sun halatta gare shi har mata, sai dai muddin yana cikin mila-milai (na Harami), to yin farauta ba ya halatta a gare shi, haka nan yanke bishiya da koriyar ciyawa, saboda Haramin ba saboda harama ba; saboda harama ta warwaru daga gare shi.

Fa'ida ta goma sha uku: A kan wakiltawa a jifan Jamrori:

Ba ya halatta ga wanda yake da ikon yin jifa da kansa ya wakilta wani ya yi masa, daidai ne Hajjin sa na farilla ne ko na nafila; saboda wanda ya fara aikin Hajji na nafila to ya wajaba a gare shi ya cika shi. Amma wanda jifa da kansa zai yi masa wuya, kamar mara lafiya da tsoho da mace mai ciki da makamatansu, to ya halatta ya wakilta wanda zai yi masa jifan, daidai ne Hajjin nasa na farilla ne ko na nafila, ko ya tsinci tsakuwa ya baiwa wakilin nasa ko wakilin nasa ya tsinta da kansa, to duk wannan ya halatta.

Wakilin zai fara da yin jifan ga kansa tukunna sannan ga wanda ya wakilta ɗin; saboda gamewar zancesa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: «‌Ka fara da kanka tukunna» [84]. Da faɗiinsa: «Ka yi wa kanka aikin Hajji, sannan ka yi wa Shubrumah aikin Hajji» [85]. [85] Abu Dawud ne ya fitar da shi: Littafin ayyukan ibadu (na Hajji da Umra), babin mutum ya yi wa waninsa aikin Hajji, lamba ta (1811), da ibn Majah: Littafin ayyukan ibadu (na Hajji da Umarah), babin yi wa mamaci aikin Hajji, lamba ta (2903), daga hadisin ibn Abbas - Allah Ya yarda da su -. [84] Muslim ne ya fitar da shi: Littafin Zakkah, babin fara ciyar da kai sannan iyalansa, lamba ta (977).

Yana kuma halatta ya yi wa kansa jifa sannnan ya yi wa wanda yake wakilta a tsayuwa ɗaya, sai ya jefi Jamra na farko da tsakwankwani bakwai ga kansa sannan da tsakwankwani bakwai ga wanda yake wakilta, haka nan na biyu da na uku kamar yadda zahirin hadisin da aka rawaito daga Jabir yake fa'idantarwa, ya ce: "Mun yi Hajji tare da Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, sai muka yi Talbiya ga yara muka kuma yi jifa gare su". Ahmad da ibn Majah ne suka rawaito [86]. Zahirinsa shi ne suna aikata hakan a tsayuwa guda ne; tunda da sun kasance sai sun gama guda ukun ga kawunansu sannan su dawo daga farkonsu ga (yi wa) yaran jifan da an ruwaito hakan, kuma Allah shi ne masani. [86] Ahmad ne ya fitar da shi 22/269 (14370) [bugun Risala], da ibn Majah: Littafin ayyukan ibadu (na Hajji da Umarah), babin yin jifa ga yara, lamba ta (3038), daga hadisin Jabir - Allah Ya yarda da shi -.

Fa'ida ta goma sha hudu: A cikin ayyukan ibadun ranar idi:

Mahajjaci zai yi ayyukan Hajji guda huɗu a jere a ranar idi, kamar haka:

Na farko: Jifan Jamratul Aƙabah.

Na biyu: Yanka hadaya in akwai yin hadaya gare shi.

Na uku: Yin ƙwalƙwal ko saisaye.

Na hudu: Yin ɗawafi da ɗakin Ka'aba

Amma sa'ayi, idan mai yin Tamattu'i ne ya yi sa'ayi ga Hajji, idan kuma mai yin Ƙirani ne ko Ifradi, idan dama ya yi sa'ayi bayan ɗawafin Ƙudumi to sa'ayin farko ya ishe shi, idan bai yi ba to ya yi sa'ayi bayan wannan ɗawafin, ina nufin: ɗawafin Hajji.

Abin da aka shar'anta ya jera su akan wannan tsarin, idan ya gabatar da wani sashi akan wani; kamar ya yi yanka kafin yin jifa, ko ya yi aski kafin yanka, ko ya yi ɗawafi kafin aski, idan bai sani ba ko mantawa ya yi to babu laifi a kansa, idan kuma da gangan ne to abin da yake mashhuri a mazhabar Imam Ahmad shi ne babu laifi a kansa dai; saboda abin da Bukhari ya rawaito daga ibn Abbas - Allah Ya yarda da su -: Cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - an tambaye shi game da wanda ya yi aski kafin ya yi yanka da makamancinsa, sai ya ce «Babu laifi» [87]. [87] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin yin yanka kafin aski, lamba ta (1722), da Muslim: Littafin Hajji, babin wanda ya yi aski kafin sokewa, ko ya soke kafin jifa, lamba ta (1703), daga hadisin ibn Abbas - Allah Ya yarda da su -.

Daga gare shi kuma, ya ce: Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kasance ana tambayarsa a ranar babbar sallah a Mina, sai yake cewa: «Babu laifi». Sai wani mutum ya tambaye shi, sai ya ce: Na yi aski kafin na yi yanka. Ya ce: «Ka yi yanka kuma babu laifi». Kuma ya ce: Na yi jifa bayan na yi maraice. Ya ce: «Babu laifi» [88]. [88] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin idan ya yi jifa bayan ya yi maraice, ko ya yi aski kafin ya yi yanka, yana mai mantuwa ko rashin sani, lamba ta (1735), da Muslim: Littafin Hajji, babin wanda ya yi aski kafin sokewa, ko ya soke kafin jifa, lamba ta (1703), daga hadisin ibn Abbas - Allah Ya yarda da su -.

Daga gare shi kuma: Cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -,an ce da shi game da yanka da aski da jifa da gabatarwa da jinkirtawa, sai ya ce: «Babu laifi» [89]. [89] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin idan ya yi jifa bayan ya yi maraice, ko ya yi aski kafin ya yi yanka lamba ta (1734), da Muslim: Littafin Hajji, babin wanda ya yi aski kafin sokewa, ko ya soke kafin jifa, lamba ta (1307), daga hadisin ibn Abbas - Allah Ya yarda da su -.

Kuma an tambaye shi game da wanda ya yi ziyara - wato ya yi ɗawafi ɗawafin ziyara (wato Dawafin Hajji) - kafin ya yi jifa ko ya yi yanka kafin ya yi jifa, sai ya ce; «Babu laifi». Bukhari ne ya rawaito shi [90]. [90] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin yin yanka kafin aski, lamba ta (1722), da Muslim: Littafin Hajji, babin wanda ya yi aski kafin sokewa, ko ya soke kafin jifa, lamba ta (1703), daga hadisin ibn Abbas - Allah Ya yarda da su -.

A hadisin Abdullahi bin Amr, ya ce: Ba'a tambayi Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - wani abu ba a wannan ranar da aka gabatar ko aka jinkirtar face ya ce: «Ka aikata kuma babu wani laifi» [91]. [91] Bukhari ne ya fitar da shi: Littafin ilimi, babin yin fatawa alhali yana tsaye akan dabba da waninta, lamba ta (83), da Muslim: Littafin Hajji, babin wanda ya yi aski kafin sokewa ko ya soke kafin jifa, lamba ta (1306), daga hadisin ibn Amr - Allah Ya yarda da su -.

Idan kuma ya jinkirta yankan har zuwa ya kai ga Makkah to babu laifi, sai dai kada ya jinkirta shi ya wuce kwanukan Tashriƙ (yanyanar nama). Idan ya jinkirta ɗawafi ko sa'ayi daga ranar idi to babu laifi, sai dai kada ya jinkirta su daga watan Zul Hijjah sai da uzuri, misali: Jinin biƙi ya samu mace kafin ta yi ɗawafi, sai ta jinkirta ɗawafin har sai ta yi tsarki, ko da kuwa bayan watan Zul Hijjah ne, to babu laifi a kanta kuma babu fitar da fansa (fidiya).

Fa'ida ta goma sha biyar: A kan lokacin yin jifa da jerantawa tsakanin Jamrori:

Ya gabata gare ka cewa lokacin yin jifa a ranar idi ga mai iko shi ne bayan ɓullowar rana, ga wanda kuma cunkoson mutane ya matsa masa, to daga ƙarshen daren idi. Amma lokacin yin jifa a kwanukan Tashriƙ daga lokacin da rana ta yi zawali (ta karkace daga tsakiyar sama). Don haka babu yin jifa kafin zawali; saboda Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - bai yi jifa a kwanukan Tashriƙ ba sai bayan zawali, kuma ya ce: «Ku riƙi ayyukan ibadunku (na Hajji da Umarah ) daga gareni [92]». [92] Muslim ne ya fitar da shi: Littafin Hajji, babin mustahabbancin jifan Jamratul Aƙabah a ranar babbar sallah akan abin hawa, da bayanin faɗinsa – tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi: «Ku riƙi ayyukan ibadunku (na Hajji da Umarah )» lamba ta (1297), daga hadisin Jabir, - Allah Ya yarda da shi -.

Lokacin yin jifan yana zarcewa a ranar idi da abin da ke bayanta har zuwa faɗuwar rana, don haka kada ya yi jfa da daddare. Sashen malamai suna ganin cewa idan jifa ya kuɓuce da rana to zai iya yin jifa da daddare, face daren goma sha huɗu, saboda ƙarewar kwanunkan Mina da faɗuwar rana a rana ta goma sha uku, zance na farko shi ne mafi tsantseni, kuma a kan hakan, idan jifan wata rana ya kuɓuce masa to zai yi jifan a ranar da ta biyo mata idan rana ta yi zawali, zai fara da jifan ranar da ta kuɓuce masa, idan ya kammala shi, sai ya yi jifan wannan ranar da yake a cikinta [93]. [93] Mai girma babban malaminmu mawallafin - Allah Ya yi masa rahma - ya faɗa a cikin (Fatāwal Hajj): «Abin da yafi ga mahajjaci ya jefi Jamrori da tsakar rana, idan yana tsoron cunkoso, to babu laifi ya jefe su da daddare, hakan saboda Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya tsayar da lokacin fara yin jifa kuma bai tsayar da lokacin gama shi ba, sai hakan ya nuna cewa lamarin a wannan a faɗaɗe yake».

Jerantawa a tsakanin Jamrorin uku wajibi ne, sai ya fara jefan Jamra ta farko wadda take bin masallacin Khaif, sannan ta tsakiya, sannan Jamratul Aƙabah. Da zai fara jifan Jamratul Aƙabah, sannan ta tsakiya ko ya fara da na tsakiya, idan da gangan ne kuma yana sane, to maimaita ta tsakiyar ya wajaba a kansa, sannan Jamratul Aƙabah, idan kuma bai sani ba ko ya manta ne to ya isar masa, kuma babu komai a kansa.

Fa'ida ta goma sha shida: A cikin kwana a Mina:

Kwana a Mina a dare na goma sha ɗaya da dare na goma sha biyu wajibi ne. Abin da yake wajibi anan shi ne kwana a mafi yawan daren, daidai ne daga farkon daren ne ko daga ƙarshensa. Da a ce ya kai Makkah a farkon daren sannan ya dawo kafin daren ya raba , ko ya kai Makkah daga Mina bayan daren ya raba, to babu laifi a kansa; saboda haƙiƙa ya zo da wajibi.

Yana wajaba ya tabbatar da iyakokin Mina don kada ya kwana a wajenta, iyakarta daga gabas ita ce Wadi Muhassar, daga yamma kuma Jamratul Aƙabah, Wadi da Jamrah basa daga cikin Mina. Amma duwatsun da ke kewaye da Mina, to fuskokinsu daga abin da ke bin Mina yana daga cikinta, don haka kwana ya halatta a can. Maniyyaci ya kiyaye daga kwana a Wadi Muhassir ko daga bayan Jamratul Aƙabah; saboda wannan ya fita daga iyakokin Mina, wanda ya kwana a nan to kwanan bai isar masa ba [94]. [94] Mai girma babban malaminmu mawallafin ya faɗa a cikin [Fatāwal Hajj (Juz'i na 2/Shafi na 436 da abin da ke biyo masa)]: «Wannan idan ya sami wuri a Mina ne, amma idan bai samu ba to babu laifi ya kwana a wajen iyakokin Mina ta kowanne bangare nata, kuma masaukinsa ya zama a haɗe da masaukan mahajjata don su kasance al'umma ɗaya a haɗe, kamar yadda muke faɗa game da ace masallaci ya cika da masu yin sallah, to za su yi sallar su a sahu-sahu a haɗe ko da kuwa sun kasance a wajen masallaci, kuma babu laifi a kansu a cikin yin hakan».

Fa'ida ta goma sha bakwai: A kan ɗawafin bankwana:

Ya gabata cewa ɗawafin bankwana wajibi ne akan dukkkan mahajjaci da mai yin Umarah yayin fita daga Makka, face mai jinin al'ada da jinin biƙi, sai dai in sun yi tsarki kafin su rabu da gine-ginen Makkah, to lallai ya lazimcesu. Idan kuma ya yi (ɗawafin) bankwana sannan ya fice daga Makka kuma ya tsaya yini ɗaya ko sama da hakan, maimaita ɗawafin bai wajaba a kan shi ba, ko da kuwa tsayuwar tasa ta kasance a wani wuri ne kusa da Makka.

Allah Shi ne masani. Tsira da amincin Allah su tabbata ga Annabinmu Muhammad da alayensa da sahabbansa baki ɗaya.

Littafi ya kammalu da alƙalamin mawallafinsa: Muhammad As-Salih Al-Uthaimeen, a 7 ga Sha'ban, shekara ta 1387 bayan hijira. Godiya ta tabbata ga Allah wanda da ni'imarSa ce ayyuka na gari suke cika. An gama gyara shi a hantsin ranar Alhamis, bayan kwanaki sha uku na Ramadan sun wuce, shekara ta 1387 bayan hijira. Allah Ya yi salati ga (annabi) Muhammad da alayensa da sahabbansa baki ɗaya.