التحقيق والإيضاح لكثير من مسائل الحج والعمرة والزيارة على ضوء الكتاب والسنة

التحقيق والإيضاح لكثير من مسائل الحج والعمرة والزيارة على ضوء الكتاب والسنة

TABBATACCAN BAYYANI AKAN YAWANCIN MAS'ALOLIN HAJJI DA UMRA DA KUMA ZIYARA AKAN DORON LITTAFI (ALKUR'ANI)

Language: lang_ha
Prepared by: AbdulAzeez Bn Abdullahi Bn Baaz
Version: 3.1
Translations 42
Amharic Azerbaijani Bengali Bosnian +38
Attachments 7
PDF
Audio
Video
+3

TABBATACCAN BAYYANI AKAN YAWANCIN MAS'ALOLIN HAJJI DA UMRA DA KUMA ZIYARA AKAN DORON LITTAFI (ALKUR'ANI)

Na Babban Malami

AbdulAzeez Bn Abdullahi Bn Baaz

Gabatarwar Mawallafin

Da sunan Allah Mai rahama Mai jin ƙai [1]

Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai, kyakkyawan ƙarshe ya tabbata ga masu tsoron Allah, tsira da aminci su tabbata ga bawanSa kuma manzonSa (Annabi) Muhammad, da alayensa da sahabbansa baki ɗaya.

Bayan haka:

Wannan wani taƙaitaccen saƙo ne a aikin Hajji da bayanin falalarsa, da kuma ladubbansa, da abinda yake kamata ga wanda ya yi nufin yin tafiya dan yin sa, da bayanin masa'aloli masu yawa kuma muhimmai cikin mas'alolin Hajji da Umarah da kuma ziyara ta hanyar bayani da kuma taƙaitawa, haƙiƙa na hasaso abinda Littafin Allah da sunnar manzonSa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, na tattarosu ne dan yin nasiha ga musulmai, da kuma aiki da faɗin Allah - Maɗaukakin sarki -: {Kuma ka tunãtar, dõmin tunãtarwa tanã amfãnin mũminai] ([2]) [al-Zariyat: 55], da faɗinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Kuma ka tuna lokacin da Allah Ya yi alƙawari da waɗanda aka baiwa littafi cewa zaku bayyana shi ga mutane kuma ba zaku ɓoye shi ba} ([3]) [Āli- Imran: 187]. har zuwa ƙarshen ayar, da kuma faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Ku yi taimakekeniya akan aikin alheri da kuma tsoran Allah} ([4]) [al-Ma'ida: 2].

Da kuma abinda ya zo a cikin hadisi ingantacce daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - cewa shi ya ce: «Addini nasiha ne, sau uku, aka ce : Ga wa ! Ya manzon Allah? ya ce: Ga Allah, da littafinSa, da manzonSa, da shugabannin musulmai da gabaɗayansu ([5])» [1] Muslim ne ya ruwaito, a lamba ta (55).

Kuma Ɗabarani ya ruwaito daga Huzaifa, cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: «Wanda bai damu da al'amarin musulmai ba to ba ya tare da su, wanda bai wayi gari kuma bai yi maraice yana mai nasiha ga Allah da manzonSa da littafinSa da shugansa da kuma gabaɗayan musulmai ba to, ba ya daga cikinsu [6]». [2] Ɗabarani ne ya ruwaito shi a cikin al-Awsaɗ, a lamba ta (7469).

Allah nake roƙo Ya amfanar dani da ita, da musulmai, kuma Ya sanya ƙoƙari a cikinta tsarkakakke ne domin samun yardar sa Mai girma, kuma sababi na rabauta gareShi a cikin gidajan aljanna ta ni'ima, lallai cewa Shi Mai yawan ji ne kuma Mai amsawa, kuma Shi ne Mai isar mana madalla da Wakili.

FASALI

A akan dalilan wajabcin aikin Hajji da Umarah da kuma gaggawa zuwa ga aikata su

Idan ansan wannan, I to ku sani - Allah Ya datar da mu da ku ga sanin gaskiya da kuma binta - cewa Allah - Mai girma da ɗaukaka - haƙiƙa Ya wajabatawa bayinSa ziyarar ɗakinSa mai alfarma, kuma Ya sanya shi ɗaya daga cikin rukunan musulunci, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce {Kuma Allah Ya wajabta hajjatar dakinSa ga wanda ya samu ikon tafiya zuwa gare shi, wanda ya Kafirce to lallai Allah Mawadaci ne ga barin talikai} ([7]) [Āli-Imran: 97].

A cikin ingnatattun littattafai biyu daga Ɗan Umar - Allah Ya yarda da su - daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «An gina musulunci akan abubuwa biyar: Shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma (annabi) Muhammad manzon Allah ne, da tsaida sallah, da bada zakka, da azimtar Ramadan, da Hajjin Ɗakin Allah Mai alfarma ([8])». [3] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (8), da Muslim, a lamba ta (16).

Kuma Sa'id ya ruwaito a cikin Sunan na sa, daga Umar ɗan Khaɗɗab - Allah Ya yarda da shi - cewa shi ya ce: «Haƙiƙa na yi niyyar in aiki wasu mazaje zuwa waɗannan biranen, su duba dukkan wanda yake da wadata ([9]) bai yi Hajji ba, su sanya jizya a kansu, su ba musulmaiba ne, su ba musulmai ba ne», [10] [4] Wato: Yalwatar dukiya. [5] Ya danganta shi a cikin Jami'ul Ahadis da lamba (31221) zuwa Sunan na Sa'id bn Mansur, sai dai cewa ni ban same shi a cikin kwafin da aka bada dama ba.

Kuma an ruwaito daga Aliyu - Allah Ya yarda da shi - cewa shi ya ce: «Wanda ya samu iko a kan yin Hajji sai bai yi ba, to babu abin da ke kansa sai dai kawai ya mutu yana Bayahude ko Banasare» [6]. [6] Tirmizi ne ya ruwaito shi, a lamba ta (812).

Yana wajaba akan wanda bai yi Hajji ba alhali yana da ikon yin Hajji, ya yi gaggawa zuwa gare shi; dan abinda aka ruwaito daga Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da shi -, cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce: «Ku yi gaggawa zuwa Hajji - yana nufin: (na ) Farilla- domin cewa ɗayanku bai san abinda zai bijiro masa ba ([12])» Ahmad ne ya ruwaito shi.. [7] Abu Dawud ne ya rawaito shi, a lamba (1732).

Kuma domin cewa yin aikin Hajji wajibi ne a gaggauce, a cikin haƙƙin wanda ya samu ikon tafiya zuwa gare shi; dan zahirin faɗinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: {Kuma Allah Ya wajabta hajjatar dakinSa ga wanda ya samu ikon tafiya zuwa gare shi, wanda ya Kafirce to lallai Allah Mawadaci ne ga barin talikai [13] [Āli-Imran: 97]. da faɗin Annabi - tsira da Aminci su tabbata a gare shi - a cikin huɗubarsa: «Yaku mutane, lallai Allah Ya wajabta muku Hajji, to ku yi Hajji ([14])». [8] Muslim ne ya ruwaito shi, a lamba ta (1337).

Haƙiƙa hadisai sun zo suna nuni alkan wajabcin Umarah, daga cikinsu akwai:

Daga cikinsu akwai: Faɗinsa (Annabi) -tsira da amincin Allah su tabbata agare shi- a amsar da ya amsawa (mala'ika) Jibrilu lokacin da ya tambaye shi game da musulunci, (manzo) - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: «Musulunci shi ne, ka shaida cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma (Annabi) Muhammad manzon Allah ne, ka tsaida sallah, ka bada zakka, ka ziyarci Ɗaki, ka yi Umarah, ka yi wankan janaba, ka cika alwala, ka azimci (watan) Ramadan (15)». Ibnu Khuzaimah ne ya fitar da shi, da Daruƙuɗni, daga hadisin Umar ɗan Khaɗɗab - Allah Ya yarda da shi -, kuma Daruƙuɗni ya ce: Wannan tabbataccen Isnadi ne kuma ingantacce. [9] Ibnu Khuzaimah ne ya rawaito shi, lamba ta (1).

Daga cikinsu akwai: Hadisin Nana A'isha - Allah Ya yarda da ita cewa ita ta ce: «Ya manzon Allah, shin jihadi ya wajaba akan mata? Ya ce: Akwai jihadi a kansu wanda babu yaki a cikinsa: Hajji da Umarah ([16])» Ahmad ne da Ibnu Majah suka fitar da shi da Isnadi ingantacce. [10] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (1520).

Aikin Hajji da Umarah basa wajaba a rayuwa sai sau ɗaya kawai; saboda faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a cikin ingantaccen hadisi: «Hajji sau ɗaya ne, wanda ya ƙara to nafila ne [17]». [11] Nasa’i ne ya ruwaito shi, a lamba ta (2620).

An sunnanta yawaita Hajji da Umarah na nafila; saboda abinda ya tabbata a cikin ingantattun littattafan hadisai biyu, daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - yace: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: «Umarah zuwa Umarah mai kankare abinda ke tsakaninsu ne, kuma kuɓutaccen aikin Hajji ba shi da wani sakamako sai aljanna» [18]. [12] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (1773) da Muslim, a lamba ta (1349).

FASALI

A cikin wajabcin tuba daga saɓo da kuma mayar da kayan zalinci.

Idan musulmi ya yi ƙudirin niyyar tafiya Hajji ko Umarah, an so a gare shi ya yi wa iyalansa da abokanansa wasiyya da tsoron Allah - Mai girma da ɗaukaka - shi ne: Aikata umarnin da ya yi, da nisantar abubuwan da Ya hana.

Kuma yana kamata ya rubuta abinda yake bi da abinda ake binsa na basussuka, ya kafa shaida akan haka, kuma ya wajaba ya gaggauta tuba daga dukkanin zunubai; saboda faɗinSa Allah - Maɗaukakin sarki -: {Kuma ku tuba zuwa ga Allah gaba ɗaya ya ku muminai ko kwa rabauta} [19] [al-Nur: 31].

Haƙiƙanin tuba: Barin zunubai da kuma kyalesu (ciruwa), da yin nadama akan abinda ya shuɗe daga garesu, da niyyar rashin koma musu, idan akwai abubuwan zalinci na mutane a hannunsa na rai ne ko dukiya ko mutunci to ya dawo musu da shi, ko su yafe masa kafin tafiyarsa; dan abinda ya inganta daga gare shi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - cewa shi ya ce: «Wanda ya kasance akwai wani abin da ya zalinci ga ɗan uwansa na dukiya ne, ko mutunci, to a yau ya yi ƙoƙarin warwarewa kafin ranar da babu dinare ko dirhami ta zo, idan yana da wani aiki na gari za'a karɓa daga aikin gwargwadan abinda ya zalinta, idan kuma ba shi da wasu kyawawan ayyuka za'a karɓa daga munanan ayyukan ɗan uwansa sai a ɗora masa ([20])». [13] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (2449).

Yana kamata ya tafi da tsarkakakken guzuri na dukiya ta halal dan Hajjinsa da Umrarsa; dan abinda ya inganta daga gare shi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - cewa shi ya ce: «Lallai Allah - Maɗaukakin sarki - tsarkakakkene ba ya karɓa sai tsarkakakke ([21])», [14] Muslim ne ya ruwaito shi, a lamba ta (1015).

Ɗabarani ya ruwaito Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: «Idan mutum ya tafi aikin Hajji da tsarkakakken guzuri, kuma ya sanya ƙafarsa a cikin sirdin dabbarsa sai ya yi kira: LabbaiKa AlLahumma LabbaiKa (amsawarka ya Allah amsawarka), sai wani mai kira zai kira shi daga sama: Labbaika wa sa'adaiKa, guzurinka na halal ne, abin hawanka na halal ne, kuma Hajjinka kuɓutacce ne, ba mai zunubi ba ne, idan kuma mutum ya fita da mummunan guzuri sai ya sanya ƙafarsa a cikin sirdin dabbarsa sai ya yi kira: LabbaiKa Allahumma LabbaiKa, wani mai kira zai yi kira daga sama: La LabbaiKa wala Sa'adaika, guzurinka na haram ne, ciyarwarka ta haram ce, kuma Hajjinka ba kuɓutacce ba ne ([22])». [15] Ɗabarani ne ya ruwaito shi a al-Kabir, a lamba ta (2989).

Yana kamata ga mahajjaci ya wadatu daga abinda ke hannun mutane, da kamewa daga roƙonsu; saboda faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: «Wanda ya nemi kamewa Allah Zai sa shi ya zama mai kamewa, wanda ya nemi wadatuwa Allah Zai wadata shi ([23])». [16] Bukhari ne ya rawaito shi a lamba ta (1427) da Muslim, a lamba ta (1035).

Da faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi: «Mutum ba zai gushe ba yana roƙon mutane, har sai ya zo ranar alƙiyama alhali babu gutsiren nama a fuskarsa ([24])». [17] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba (1474), da Muslim, a lamba ta (4040).

Yana wajaba ga mahajjaci ya nufi Allah da gidan Lahira da Hajjinsa, da kuma Umrarsa, da neman kusanci zuwa ga Allah da abinda zai yardar da shi na maganganu da ayyuka a waɗannan wurare maɗaukaka, ya kiyaye dukkanin kiyayewa da ya nufi duniya da Hajjinsa da kuma rabon (duniyar), ko riya ko jiyarwa da alfahari da hakan, domin cewa hakan yana daga mafi munin manufofi, kuma sababi ne na ɓacin aiki da rashin karɓarsa, kamar yanda Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Wanda ya kasance yã yi nufin rãyuwar dũniya da ƙawarta, Munã cika musu ayyukansu zuwa gare su a cikinta, kuma a cikinta bã zã a rage su ba} (15) Waɗannan ne waɗanda bã su da kõme a cikin Lãhira fãce wuta, kuma abin da suka sanã'anta a cikinta (dũniya) yã ɓãci, kuma abin da suka kasance sunã aikatãwa ɓãtacce ne} [25] [Hud: 15-16].

Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Wanda ya kasance yanã nufin mai gaggãwa, sai Mu gaggauta masa a cikinta, abin da Muke so ga wanda Muke nufi, sa'an nan kuma Mu sanya masa Jahannama, ya ƙõnu da ita, yanã abin zargi kuma abin tunkuɗewa (18) {Kuma wanda ya nufi Lãhira, kuma ya yi aiki sabõda ita irin aikinta alhãli kuwa yanã mũmĩni, to, waɗannan aikinsu ya kasance abin yabo} ([26]) [al-Isra': 18-19].

Kuma ya inganta daga gare shi - tsira da amincin Allah su tabbata gareshi - cewa shi ya ce: «Allah madaukakin sarki ya fada: Ni ne Mafi wadatuwar masu tarayya daga barin tarayya, wanda ya aikata wani aiki kuma ya haɗani da wani a cikinsa to zan barshi da shikarsa (tarayyarsa) ([27])». [18] Muslim ne ya ruwaito shi, a lamba ta (2985).

Kuma yana kamata gare shi ya abokantaka da zaɓaɓɓu cikin ma'abota biyayya da tsoran Allah da fahimtar Addini a cikin tafiyarsa, ya kiyayi abokantakar wawaye da fasiƙai.

Yana kamata gare shi ya nemi sanin abinda aka shara'anta masa a cikin Hajjinsa da Umrarsa, ya nemi fahimtar hakan, ya yi tambaya kan abinda ya rikice masa; dan ya zama akan ilimi, idan ya hau dabbarsa ko motarsa ko jirgin samansa ko wasunsu cikin ababen hawa, an so ya ambaci Allah - tsarki ya tabbatar maSa - kuma ya gode maSa, sannan ya yi kabbara sau uku sai ya ce: {Tsarki ya tabbata ga wanda ya hore mana wannan, kuma bamu da wani iko akansa (13) {Kuma lalle mũ haƙĩƙa mãsu jũyãwa muke, zuwa ga Ubangijinmu} [28] [al-Zukhruf: 13-14].

«Ya Allah ina roƙonKa aikin alheri da taƙwa a cikin tafiyata wannan, da kuma aikin da zaKa yarda da shi, ya Allah Ka sauƙaƙa mana wannan tafiyar ta mu, ka ninke mana nisanta, ya Allah Kaine aboki (mai kula) a cikin tafiya, kuma khalifa a cikin iyalai, ya Allah ina neman tsarinKa daga wahalar tafiya, da mummunan abin duba, da mummunar majuya a cikin dukiya da iyalai ([29])»; Saboda ingancin haka daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, Muslim ne ya fitar da shi daga Hadisin Ibnu Umar - Allah Ya yarda da su -. [19] Muslim ne ya ruwaito shi, a lamba ta (1342).

Kuma ya yawaita zikiri da istigafri da roƙon Allah - tsarki ya tabbatar maSa - da ƙanƙar dakai gareShi a cikin tafiyarsa da kuma karatun Alƙur'ani da bibiyar ma'anoninsa, kuma ya kiyaye akan salloli a cikin jam’i, ya kiyaye harshensa da yawaita ƙila da ƙala, da kutsawa a cikin abinda bai shafeshi ba, da yawaita kakaci, kuma ya kiyaye harshensa daga ƙarya da giba da annamimanci da yiwa abokanansa izgili da ma wasunsu daga 'yan uwansa musulmai.

Yana kamata gare shi ya aikata alheri ga abokan tafiyarsa, ya kame cutarsa daga garesu, ya umarcesu da aikin alheri, ya hanesu daga abin ƙi da hikima da wa'azi mai kyau gwargwadan iko.

FASALI

A kan abinda mahajjaci zai aikata lokacin isarsa Miƙati

Idan ya isa Miƙati an so gare shi, ya yi wanka ya shafa tirare; saboda abinda aka ruwaito cewa, Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya tsiraita daga ɗinkakken tufafi a lokacin harama, kuma ya yi wanka, kuma saboda abinda ya tabbata a cikin inagntattun Littattafan hadisai biyu, daga Nana A'isha - Allah Ya yarda da ita - ta ce: «Na kasance ina shafawa manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - tirare dan yin haramarsa kafin ya yi harama, haka ga warware haraminsa, kafin ya yi ɗawafi a ɗaki ([30])» Kuma ya umarci Nana A'isha lokacin da ta yi al’ada, alhai ta yi harama da Umarah da ta yi wanka ya yi harama da Hajj, kuma (Annabi) - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya umarci Nana Asma'u 'yar Umais lokacin da ta haihu a Zul Hulaifa da ta yi wanka ta ɗaure kwiɓinta (kunzigo) da tufafi, kuma ta yi harama ([31]), sai hakan ya yi nuni akan cewa mace idan ta isa Miƙati alhali tana al’ada ko jini biƙi, taya yi wanka ta yi harama tare da mutane, kuma ta aikata abinda mahajjaci yake aikata shi banda Ɗawafi a Daki (Ka’abah), kamar yadda Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya umarci Nana Aisha da Nana Asma'u da hakan» [20] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (1539), da Muslim, a lamba ta (1189). [21] Muslim ne ya ruwaito shi, a lamba ta (1218).

An so ga wanda ya yi nufin yin harama, ya bibiyi gashin bakinsa da faratansa da mararsa da hammatarsa, sai ya yanke abinda ake buƙatar yanke shi; dan kada ya buƙaci yanke hakan bayan harama alhali kuma haramun ne a kansa, kuma saboda Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya shara'antawa musulmai bibiyar waɗannan abubuwan kowane lokaci, kamar yadda ya tabbata a cikin ingantattun littattafan hadisai biyu, daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: «Ɗabi'a biyar ne: Kaciya, da yanke gashin mara, da rage gashin baki, da yanke farce, da fige gashin hammata ([32])». [22] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (5891), da Muslim a lamba ta (257).

A cikin Sahihu Muslim, daga Anas - Allah Ya yarda da shi - ya ce: «Ansa mana lokaci a rage gashin baki, da yanke farce, da fige gashin hamamata, da aske gashin mara: Cewa kada mu bar hakan sama da kwana arba'in ([33])». [23] Muslim ne ya ruwaito shi, a lamba ta (258).

Kuma Nasa'i ya fitar da shi da lafazin: «Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya sa mana lokaci», Kuma Ahmad da Abu Dawud da al-Tirmizi sun fitar da shi da lafazin al-Nasa'i, amma kai, ba'a shara'anta yanke wani abu daga gare shi ba a lokacin harama, ba'a haƙƙin maza ba, haka kuma ba'a haƙƙin mata ba. [24] Nasa'i ne ya ruwaito shi, a lamba ta (14).

Amma gemu ya haramta a aske shi ko yanke wani abu daga gare shi a dukkanin lokuta, kai ya wajaba a cika shi; saboda abinda ya tabbata a cikin ingantattun Littattafan hadisai biyu, daga Ibnu Umar - Allah Ya yarda da su - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: «Ku saɓawa mushrikai, ku cika gemu, ku rage gashin baki ([34])», Muslim ya fitar a cikin ingantaccen Littafinsa, daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: «Ku rage gashin baki, ku saki gemma, ku saɓawa majusawa ([35]) ». [25] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (2892), da Muslim, a lamba ta (259). [26] Muslim ne ya ruwaito shi, a lamba ta (260).

Haƙiƙa masifa ta girmama a cikin wannan zamanin , domin mafiyawancin mutane suna saɓawa wannan sunnar sun yaƙi gemu, sun yarda da kamanceceniya da kafirai da mata, musamman ma wanda yake dangantuwa da ilimi da kuma koyarwa, ga Allah muke kuma gare shi zamu koma, muna roƙon Allah Ya shiryar da mu da sauran musulmai ga dacewa da sunna da yin riƙo da ita, da kira zuwa gareta, ko da mafiya yawa sun bijire mata, Allah Ya isar mana madalla da abin dogaro , babu wata dabara babu wani ƙarfi sai ga Allah Maɗaukaki Mai girma.

Sannan namiji ya sanya kwarjalle da mayafi, an so su zama farare masu tsafta, kuma an so ya yi harama da takalma silifa; saboda faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: «Ɗayanku yayi harama a kwarjalle da mayafi da takalma silifa, idan bai samu silifa ba, to ya sanya huffi, kuma ya yankesu har su zama ƙasan idan sawu ({36})», Imam Ahmad ne - Allah Ya yi masa rahama - ya fitar da shi. [27] Muslim ne ya ruwaito shi, a lamba ta (1177).

Amma mace, to yana halatta gareta tayi harama a abinda ta so na baƙi ko kore ko wasunsu, tare da kiyayar kamaceceniya da maza a tufansu, sai dai baya halatta a kanta ta sanya niƙabi ko safar hannu a lokacin haramarta, sai dai ta rufe fuskarta da tafukanta, ba tare da niƙabi ko safar hannu ba; domin cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya hana mace mai harama sa niƙabi da safar hannu, amma wasu daga cikin gamagarin mutane da suke keɓance haramar mace a koren tufa ko baƙi banda wasunsu to hakan bashi da wani asali.

Sannan bayan gama wanka da tsafta, da sanya tufafin harama, zai yi niyyar shiga cikin ibadar da ya yi nufi a zuciyarsa, ta Hajji ce ko Umarah; saboda faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: «Dukkan ayyuka basa ingantuwa sai da niyyoyi, kuma kowane mutum ana bashi ladan abinda ya niyyata ne ([37])». [28] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (1), da Muslim, a lamba ta (1907).

Kuma an shara'anta masa furta abinda ya niyyata, idan niyyarsa itace yin Umra, sai yace: (AmsawarKa Umra) ko (Ya Allah amsawarKa Umra), idan kuma niyyarsa ta kasance ta Hajji ce, sai yace: (AmsawarKa Hajji) ko (Ya Allah amsawarKa Hajji); domin cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya aikata haka. Idan yayi niyyarsu baki ɗaya sai yayi talbiyyaha da hakan, sai yace: (Ya Allah amsawarKa Umra da Hajji), abinda yafi shine furtawar ta zama bayan ya daidaita akan abin hawansa, dabba ce ko mota ko wasunsu; saboda Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - yayi niyya ne bayan ya daidaita akan dabbarsa, ta taso da shi daga miƙati dan tafiya, wannan shine yafi inaganci daga maganganun ma'abota ilimi.

Ba'a sharanta masa furta abinda ya niyyata ba, sai a harama kawai; dan zuwan haka daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -.

Amma sallah da ɗawafi da wasunsu, to yana kamata gare shi, kada ya furta niyyar wani abu daga garesu, ba zai ce ba: Na yi niyyar yin sallah kaza da kaza, ko na yi niyyar yin ɗawafi kaza, kai furta niyya da hakan yana daga cikin bidi'o'i fararru, kuma bayyana hakan ya fi muni kuma ya fi tsananin zunubi, da ace furta niyya abin shara'antawa ne da manzo - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bayyana shi, kuma ya bayyanar da shi ga al'umma da aikinsa, ko da faɗarsa, kuma da magabata na gari sun rigamu zuwa gare shi.

Tunda ba'a cirato hakan daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ba, ko daga sahabbansa - Allah Ya yarda dasu -, to an san cewa shi bidi'a ne, haƙiƙa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Mafi sharrin al'amurra fararrunsu, kuma dukkan bidi'a ɓata ce ([38])». Muslim ne ya fitar da shi a cikin ingantaccen littafinsa. Kuma Mafificin Salati da Aminci a gare shi ya ce: «Duk wanda ya farar da wani sabon abu a cikin wannan Addinin namu, wanda ba ya ciki, to shi abun mayarwa ne ([39])». Bukhari Da Muslim suka tabbatar da ingancinsa, A cikin wani lafazin na Muslim: «Duk wanda ya yi wani aiki wanda babu umarninmu a cikinsa, to shi abun mayarwa ne ([40])». [29] Muslim ne ya ruwaito shi, a lamba ta (867). [30] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (2697), da Muslim, a lamba ta (1718). [31] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (2550), da Muslim, a lamba ta (1718).

FASALI A cikin miƙatai na guri da kuma inda suke.

Miƙatai guda biyar ne:

Na farko: Zul-Hulaifa, shi ne miƙatin mutanen Madina, shi ne inda mutane suke ce masa a yau da: Abyaru Ali.

Na biyu: Juhfa, shi ne miƙatin mutanen Sham, ita wata rushasshiyar alƙarya ce, da take bin Rabigh, mutane a yau suna yin harama ne daga Rabigh, wanda ya yi harama daga Rabigh to haƙiƙa ya yi harama daga miƙati; domin cewa Rabigh tana kusa ita da kaɗan.

Na uku: Karnul manazil, shi ne miƙatin mtanen Najd, shi ne a yau ake kiransa da: AsSail.

Na huɗu: Yalamlam, shi ne miƙatin mutane Yaman.

Na biyar: Zatu irƙin, shi ne miƙatin mutanen Iraƙ.

Waɗannan miƙatan, haƙiƙa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya iyakancesu ga waɗanda muka ambata, da kuma wanda ya wuce ta wurinsu daga waɗanda ba ahalin wurin ba, daga wanda yayi nufin Hajji ko Umra.

Abinda yake wajibi ga wanda ya wuce ta wurinsu shine, yayi harama daga garesu, kuma yana haramta a kansa ya ƙetaresu ba tare da harama ba, idan ya kasance ya nufi Makka da nufin yin Hajji ko Umra, daidai ne wucewarsa garesu ta kasance ta hanyar ƙasa ne ko ta hanyar sama; saboda gamewar faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - lokacin da ya iyakance waɗannan miƙatan: «Su sun tabbata garesu da wanda yazo ta wurinsu, wanda baya daga cikin ahalinsu daga wanda yayi nufin Hajji ko Umra ([41])». [32] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (1524), da Muslim, a lamba ta (1181).

Abinda aka shara'antawa wanda ya fuskanci Makka ta hanyar sama da nufin Hajji ko Umra shine, yayi shiri ga hakan da yin wanka da makamancinsa kafin hawa jirgi, idan ya kusanci miƙati, sai ya ɗaura kwarjallansa da mayafinsa, sannan yayi talbiyyah da Umra idan akwai yalwar lokaci, idan lokacin yayi ƙunci, sai yayi talbiyyah ga Hajji. Idan ya sanya kwarjallansa da mayafinsa kafin hawa ko kafin ya kusanci miƙati, to babu laifi, sai dai bazaiyi niyyar shiga cikin ibada ba, kuma bazaiyi talbiyyah da hakan ba, sai idan ya dauranci miƙati, ko ya kusance shi; domin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - bai yi harama ba sai daga mikati, kuma abinda yake wajibi akan al'umma shine koyi da shi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a cikin hakan kamar waninsa na sha'aninnikan Addini; saboda faɗin Allah - tsarki ya tabbatar maSa -: {Lalle, abin kõyi mai kyau ya kasance gare ku daga Manzon Allah} ([42]) [al-Ahzab: 21]. kuma saboda faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a cikin Hajjin ban kwana: «Ku riƙi ayyukan ibadunku (na Hajji da Umra) daga gareni ([43])». [33] Muslim ne ya ruwaito, a lamba ta (1297).

Amma wanda ya fuskanci Makka bai yi nufin Hajji ko Umarah ba; kamar ɗan kasuwa, da mai saran ita ce, da ɗan saƙo da makamancin hakan, to babu harama a kansa sai dai idan ya yi kwaɗayin haka; saboda faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a cikin hadisin da ya gabata lokacin da ya ambaci miƙatai: «Su sun tabbata garesu da wanda yazo ta wurinsu, wanda baya daga cikin ahalinsu daga wanda yayi nufin Hajji ko Umra ([44])». Abin da aka fahimta daga gare shi shi ne cewa, wanda ya wuce ta miƙatan amma bai yi nufin Hajji ko Umarah ba to babu wata harama a kansa. [34] Fitar da shi ya gabata.

Wannan yana daga rahamar Allah ga bayinSa da kuma sauƙinSa garesu, to godiya da yabo sun tabbata gareShi akan haka, yana ƙarfafa hakan cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - lokacin da ya zo Makka a shekarar buɗe Makka bai yi harama ba, kai ya shigeta ne akansa akwai hular kwano; dan kasancewarsa a wannan lokacin bai yi nufin Hajji ko Umarah ba, kawai ya yi nufin buɗeta ne, da kawar da abinda ke cikinta na shirka.

Amma wanda masaukinsa komabayan miƙatai ne; kamar mazauna Jidda, da Ummu Sulaim, da Bahrah, da Shara'i'i, da Badr, da Masturah da makancinsu, to ba wajibi ne a kansa ya tafi zuwa wani guri na daga miƙatan nan biyar da suka gabata ba, kai masaukinsa shine miƙatinsa, sai yayi harama daga gare shi da abinda yayi nufi na Hajji ko Umra. Idan kuma yana da wani masaukin daban a wajen miƙati, to shi yana da zaɓi, idan yaso yayi harama daga miƙati, idan kuma ya so yayi harama daga masaukinsa, wanda yake kusa da miƙati zuwa Makka; saboda gamewar faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - a cikin hadisin Ibn Abbas - Allah Ya yarda da shi - lokacin da ya ambaci miƙatai, ya ce: «Wanda ya kasance kombayansu, to wurinsa (na harama) ([45]) yana daga alhalin gurin, haka mutanen Makka za suyi harama daga Makka ([46])». Bukhari da Muslim ne suka fitar da shi. [35] Famuhalluhu: Wato: Niyyarsa da talbiyya daga gurin haramarsa ne. [36] Wani yanki ne daga hadisin da ya gabata.

Sai dai wanda ya yi nufin yin Umarah alhali shi yana Harami to wajibi ne akansa ya fita zuwa Hilli (wajan haraji) domin ya yi harama daga gare shi ; domin cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - lokacin da Nana A'isha ta nemi izinin yin Umarah daga gare shi sai ya umarci ɗan uwanta Abdurrahman ya fita da ita zuwa Hilli (wajan haraji) ta yi harama daga wurin, sai hakan ya yi nuni akan cewa mai Umarah ba zai yi haramar Umarah daga cikin Haram ba, kawai zai yi harama ne daga Hilli (wato wajaba Haram).

Wannan hadisin yana keɓance hadisin Ibnu Abbas wanda ya gabata, kuma yana nuni akan cewa, abin da Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yake nufi da faɗinsa: «Har mutanen Makka za suyi haramar Hajji da Umra daga Makka ([47])» Shi ne niyyar Hajji ba Umarah ba, dan da ace ya kasance niyyar Umarah ta halatta a cikin Haram da ya yi wa Nana A'isha - Allah Ya yarda da ita - izini a kan hakan da bai ɗora mata fita zuwa hilli (wajan Haram) ba, wannan al'amari ne bayyananne, kuma shi ne faɗin Jumhur ɗin malamai - Allah Ya yi musu rahama -, kuma ya fi kewayewa ga mumini domin a cikinsa akwai aiki da hadisai biyun gaba ɗaya. Allah ne Mai datarwa. [37] Fitar da shi ya gabata.

Amma abinda wasu daga sashin mutane suke aikatawa na yawaita Umra bayan Hajji daga Tan'im ko Ji'iranah ko wasunsu alhali kuma ya riga ya gabata cewa, yayi Umra kafin Hajji, to babu wani dalili akan halaccinsa, kai dalilai ma suna nuni akan cewa barinsa ma shine ya fi; domin cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - da sahabbansa - Allah Ya yarda da su - ba suyi Umra ba, bayan sun gama Hajji. Nana A'isha ce kaɗai tayi Umra daga Tan'im; saboda kasancewarta ba tayi Umra tare da mutane ba, lokacin shiga Makka saboda haila, sai ta nema daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - cewa tayi Umra a madadin Umrarta wacce tayi harama da ita daga miƙati, sai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya amsa mata hakan, kuma haƙiƙa Umra biyu sun tabbata a gareta: Umrar dake tare da Hajjinta, da kuma wannan Umrar ita kaɗai, to wanda ya kasanace da irin matsalar Nana A'isha, to babu laifi yayi Umra bayan ya gama hajji; dan yin aiki da dalilan gabaɗayansu, da kuma yalwatawa ga musulmai.

Babu kokwanto akan cewa shagaltar alhazai da wata Umrar daban bayan gama Hajji banda Umrar da suka shigo Makka da ita yana takurawa dukkanin mutane, kuma yana haifar da yawaitar cunkoso da haɗarirrika, tare da abinda ke cikinsa na saɓawa shiriyar Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - da kuma sunnarsa. Allah ne Mai datarwa.

FASALI

Akan hukuncin wanda ya isa Miƙati ba a watannin Hajji ba

Ka sani cewa wanda ya isa Miƙati yana da halaye biyu:

Na farkonsu: Ya isa Miƙati ba a watannin Hajji ba, kamar Ramadan da Sha'aban, to sunnah a cikin haƙƙin wannan shi ne ya yi haramar Umra sai ya yi niyyarta a zuciyarsa, kuma ya furtata da harshensa, yana mai cewa: (Allahumma Labbaika Umarah), ko (Ya Allah amsawarKa Umra), sannan ya yi Talbiyyah irin Talbiyyar Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ita ce : «AmsawarKa Ya Allah amsawarKa, amsawarKa, ba Ka da abokin tarayya amsawarKa, lallai godiya da ni'ima naKa ne, mulki ma (na Kane) ba Ka da abokin tarayya ([48])». Kuma ya yawaita wannan Talbiyyar, da kuma ambaton Allah - tsarki ya tabbatar maSa - har sai ya isa Ɗaki (Ka'aba), idan ya isa Ɗaki, sai ya yanke Talbiyyah, yayi ɗawafi kewaye bakwai, yayi sallah a bayan Maƙamu Ibrahim raka'a biyu, sannan ya fita zuwa Safa yayi kewaye tsakakin Safa da Marwa kewaye bakwai, sannan ya aske kansa, ko ya saisaye shi, da haka ne Umrarsa ta cika, kuma kowane abu wanda ya haramta gare shi da harama ya halatta gareshi. [38] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (1549), da Muslim a lamba ta (1184).

Na biyu: Ya isa miƙati a cikin watannin Hajji, sune: Shawwal, da Zul-ƙi'idah, da goman farko na Zul-Hijjah.

To, irin wannan an bashi zaɓi tsakanin abubuwa uku, sune Hajji shi kaɗai, da Umra ita kaɗai, da kuma haɗawa tsakaninsu; domin cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - lokacin da ya isa miƙati a cikin Zul-ƙi'idah a Hajjin bankwana, ya bawa sahabbansa zaɓi tsakanin waɗannan ibadu ukun, sai dai cewa sunnah a cikin haƙƙin wannan idan bashi da hadaya, shine yayi haramar Umra, kuma ya aikata abinda muka ambace shi a cikin haƙƙin wanda ya isa miƙati a watannin da ba na Hajji ba; domin cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya umarci sahabbansa lokacin da suka kusanci Makka, su maida haramarsu ta zama Umra, kuma ya ƙarfafa musu hakan a Makka, sai suka yi dawafi da sa'ayi, sukayi saisaye kuma suka warware haramarsu, dan kamanta umarninsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -. Sai dai wanda a tare da shi akwai hadaya, to lallai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya umarce shi ya wanzu akan haramarsa har sai ya warware haramrsa a ranar babbar sallah, Sunnah kuma akan haƙƙin wanda ya koro hadaya, ita ce ya yi harama da Hajji da Umarah baki ɗaya; domin cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - haƙiƙa ya aikata haka, kuma ya kasance haƙiƙa ya koro hadaya, kuma ya umarci wanda ya koro hadaya cikin sahabbansa alhali ya yi niyyar Umarah da ya yi Talbiyyah da Hajji tare da Umrarsa, kuma kada ya warware haraminsa har sai ya gamasu baki ɗaya a ranar babbar sallah, idan wanda ya koro hadaya ya kasance haƙiƙa ya yi harama da Hajji shi kaɗai to zai wanzu a cikin haramarsa kuma har sai yawarware haraminsa ranar babbar sallah, kamar wanda ya yi ƙirani tsakaninsu.

Sai aka sani da haka: Cewa wanda ya yi harama da Hajji kaɗai, ko Hajji da Umarah kuma a tare da shi babu hadaya to bai kamata a gare shi ba ya wanzu a cikin haramarsa, kai sunnah a cikin haƙƙin sa ita ce, ya maida haramarsa ta koma Umarah, sai ya yi Ɗawafi ya yi Sa'ayi ya yi aski ya warware haraminsa, kamar yadda Annabi - tsira da amincin Allah su tabbara agare shi - ya umarci wanda bai koro hadayarsa daga sahabbansa ba da hakan, sai dai idan wannan ya ji tsoron kufcewar Hajjin; dan kasancewarsa ya zo a makare, to babu laifi ya wanzu a cikin haramarsa. Allah ne Mafi sani.

Idan mai harama yaji tsoron rashin samun damar yin ibadarsa, saboda kasancewrasa mara lafiya, ko yana jin tsoron maƙiyi da makamancinsa, to anso gareshi a lokacin haramarsa ya ce: «Idan wani abu mai tsarewa ya tsareni, to wurin haramata shine inda Ka tsareni»; saboda hadisin Dhiba'ah 'yar Zubair - Allah Ya yarda da ita -, cewa ta ce: Ya Manzon Allah, lallai ni ina nufin yin Hajji alhali bani da lafiya, sai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce mata: «Ki yi Hajji, ki kuma sharɗanta cewa wurin haramarki shine inda (Ya Allah) Ka tsareni ([49])» Bukhari Da Muslim suka rawaito shi. [47] fitar da shi ya gabata.

Kuma fa'idar wannan sharaɗin: Cewa mai harama idan wani abinda zai hanashi cika ibadarsa ya bijiro masa na rashin lafiya ne ko tarewar maƙiyi, to warware haraminsa ya halatta gare shi kuma babu komai a kansa.

FASALI

A Kan hukuncin Hajjin yaro ƙarami, shin yana isar masa daga hajjin Musulunci

Hajjin ƙaramin yaro da ƙaramar yarinya ya inganta; saboda abinda ke cikin Sahihu Muslim daga Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su - cewa wata mace ta ɗagawa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - wani yaro, sai ta ce: Ya Manzon Allah, shin wannan yana da Hajji? sai ya ce: «Eh, kuma kina da lada ([50])». [40] Muslim ne ya ruwaito shi, a lamba ta (1336).

A cikin Sahihul Bukhari, daga Sa'ib ɗan Yazid - Allah Ya yarda da shi - ya ce: «Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - yayi Hajji tare da ni (a Hajjin bankwana), kuma ni ina ɗan shekara bakwai ([51])». Sai dai wannan Hajjin ba ya isar musu daga Hajjin Musulunci. [41] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (1858).

Haka nan bawan da aka mallaka da kuyangar da aka mallaka, Hajji yana inganta daga gare su, kuma ba ya isar musu daga Hajjin Musulunci; saboda abinda ya tabbata daga hadisin Ibnu Abbas - Allah Ya yarada da su -, cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: «Duk yaron da yayi Hajji, sannan ya balaga, to ya wajaba a kansa yayi wani Hajjin daban, kuma dukkanin bawan da yayi Hajji sannan aka 'yantashi, to wajibi ne a kansa yayi wani Hajjin daban ([52])» Ibnu Abi Shaibah ne da Baihaƙi suka fitar da shi da kyakkyawan Isnadi. [42] Ibnu Abi Shaiba ne ya rawaito shi (Juzu'i na 4/444).

Sannan idan yaron ya kasance baikai shekarun mayyazewa ba, sai waliyyinsa yayi masa niyyar harama, sai ya tsiratar da shi daga ɗinkakken tufafi, sai yayi masa talbiyyah, da haka ne yaron zai zama mai harama, kuma zai hanu daga abinda babba mai harama zai hanu daga gare shi. Haka nan yarinyar da bata kai shekarun mayyazewa ba, waliyyinta zai yi mata niyyar harama, kuma zaiyi mata talbiyyah, da haka ne zata zama mai harama, kuma zata hanu daga abinda babbar mace zata hanu daga gareshi, kuma yana kamata su zama masu tsarkin tufafi da jiki a lokacin ɗawafi; domin cewa ɗawafi yana kama da sallah, tsarki kuma sharaɗi ne na ingancin ta.

Idan yaron da yarinyar sun kasance sun kai shekarun mayyazewa, sai suyi harama da izinin waliyyinsu, kuma su aikata abinda babba zai aikata na daga wanka da shafa tirare da makamantansu, waliyyinsu shine mai jiɓintar sha'aninsu, kuma mai tsayuwa da maslahohinsu, daidai ne, ya kasance babansu ne ko babarsu ko wasunsu, kuma waliyyin zai yi musu abinda suka kasa aikata shi, kamar jifa da makamancinsa, kuma aikata wanin wannan na ibadu ya lazimcesu, kamar tsayuwar Arfa, da kwana a Mina da Muzdalifa, da ɗawafi da kuma Sa'ayi. idan suka kasa yin Ɗawafi da Sa'ayi, sai a ɗaukesu a yi Ɗawafin da Sa'ayin da su, kuma abinda ya fi ga wanda ke ɗauke da su shi ne, kada ya sanya Ɗawafin da Sa'ayin na yaran tarayyane takanin nasa da nasu, kawai ya yi musu niyyar Ɗawafin da Sa'ayin (dan su kadai), kuma ya yi Ɗawafinsa kansa a kaɗai, ya yi Sa'ayin a kaɗaice ga kansa; dan tsarewa ga ibada, da kuma aiki da hadisi maɗaukaki: «Kabar abinda ke sanya ka kokwanto, zuwa ga abinda baya sanya ka kokwanto. ([53])». Idan wanda ke ɗauke da su yayi niyyar yin Ɗawafi ga kansa da kuma wanda ya ɗauka, to hakan ya isar masa a cikin mafi ingancin maganganu biyu; domin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - bai umarci wacce ta tambaye shi game da Hajjin yaro cewa tayi masa Ɗawafi shi kaɗai ba, da hakan ya zama wajibi, da Annabi - tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi - ya bayyana hakan. Allah ne Mai datarwa. [43] Tirmizi ne ya ruwaito shi, a lamba ta (2518).

Ana umartar yaro mumayyazi (mai wayo) da yarinya mumayyaza da tsarkaka daga hadasi da kuma najasa, kafin fara Ɗawafi, kamar babba mai harama, kuma yi wa ƙaramin yaro da ƙaramar yarinya harama ba wajibiba ne akan waliyyinsu, nafila ne, idan ya aikata hakan za'a ba shi lada, idan kuma ya bar hakan, to babu laifi a kansa. Allah ne Mafi sani.

FASALI

A cikin bayanin abubuwan da aka hana mai harami aikatawa da kuma abinda aka halatta aikata shi ga mai harama

Ba ya halatta ga mai harama bayan niyyar harama - namiji ne ko mace - ya yanke wani abu daga gashinsa, ko faratansa, ko ya shafa tirare.

Baya halatta ga namiji kaɗai ya sanya ɗinkakken tufafi gabaɗayansa, abin nufi: A kan siffarsa wacce aka yanka kuma aka ɗinka a kanta, kamar riga, ko akan sashinsa; kamar singileti da wanduna, da huffi, da jaurabi, sai dai idan bai samu kwarjalle ba, to ya halatta gare shi ya sanya wando, haka nan wanda bai samu silifa ba, to ya halatta gareshi ya sanya huffi ba tare da ya yankeshi ba; saboda hadisin Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su - tabbatacce a cikin Sahihain (sahihul Bukahri da sahihu Muslim), cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Wanda bai samu takalmi silifa ba, to ya sanya huffi, wanda kuma bai samu kwarjalle ba, to ya sanya wando ([54])». [44] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (1841), da Muslim, a lamba ta (1179).

Amma abinda yazo a cikin hadisin Ibnu Umar - Allah Ya yarda da su - na umarni da yanke huffi idan ya buƙaci sanya shi saboda rasa takalma silifa to (hadisin) an shafe shi; saboda Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - yayi umarni da hakan a cikin Madina, lokacin da aka tambaye shi game da abinda mai harama zai sa na tufafi. Sannan lokacin da yayiwa mutane huɗuba a Arfa yayi izini a sanya huffi lokacin da aka rasa takalma silifa, kuma bai yi umarni da yankesu ba, kuma haƙiƙa wanda baiji amsarsa ba a cikin Madina ya halacci wannan huɗubar, kuma jinkirin bayani ga lokacin buƙata baya halatta, kamar yanda aka sani a ilimin Usulul hadith da kuma Fiƙihu. Sai shafe umarni da yankewar ya tabbata da hakan, da kuma hakan ya zama wajibi,da Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya bayyana shi. Allah ne Mafi sani.

Kuma yana halatta ga mai harama ya sanya huffunan da ƙwaurinsu baikai idan sawu ba; saboda kasancewarsu daga jinsin takalma silifa.

Kuma yana halatta gare shi ya ƙulle kwarjalle da kuma ɗaure shi da zare da makamancinsa; saboda rashin dalilin da ya hukunta hanin.

Kuma yana halatta ga mai harama ya yi wanka ya wanke kansa ya kuma sosa shi idan ya buƙaci hakan da sauƙi, kuma a hankali, idan wani abu ya faɗo daga kansa saboda hakan to babu laifi.

Yana haramta ga mace mai harama, ta sanya tufafi ɗinkakke a fuskarta, kamar burgu (wani abune da matan larabawa suke rufe fuskarsu ad shi a lokacin Hajji) da kuma niƙabi, ko ga hannayenta, kamar safar hannu; saboda faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: «Kada mace ta sanya niƙabi, kuma kada ta sanya safar hannu ([55])» Bukhari ne ya rawaito shi. al-Ƙuffazani: Sune abubuwan da ake ɗinka su ko a saƙa su, daga suf ko auduga ko wasunsu, gwargwadan hannaye. [45] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (1838).

Kuma an halatta mata koma bayan haka, na daga ɗinkakkun tufafi; kamar riga, da wando, da huffi, da jaurabi, da makancin hakan.

Haka nan an halatta mata sakin mayafinta akan fuskarta idan ta buƙaci hakan, ba tare da bandeji ba (daurewa ba), idan mayafin ya taɓa fuskarta to babu komai a kanta; saboda hadisin Nana A'isha - Allah Ya yarda da ita - ta ce: «Mahaya sun kasance suna wuce mu, alhali mu muna tare da manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - muna masu harama, idan suka daurance mu, sai ɗayanmu ta saki mayafinta daga kanta akan fuskarta, idan suka wuce mu, sai mu yaye shi ([56])» Abu Dawud ne ya fitar da shi, da Ibnu Majah, kuma Daruƙuɗni ya fitar da irinsa daga hadisin Ummu Salamah. [46] Abu Dawud ne ya rawaito shi, a lamba (1833).

Haka nan babu laifi ta rufe hannayenta da tufafinta ko waninsa, kuma yana wajaba a kanta ta rufe fuskarta da tafukanta idan ta kasance a gaban maza ajnabai (wadanda ba maharramanta ba) take; domin cewa su al'aura ne; saboda faɗin Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -: {Kuma kada su nũna ƙawarsu fãce ga mazansu ko ubanninsu ko ubannin mazansu} ([57]) [al-Nur: 31]. Bubu kokwanto cewa fuska da tafuka suna daga mafi girman ado.

Kuma fuska a hakan tafi tsanani kuma tafi girma, Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya ce: {Kuma idan zã ku tambaye su waɗansu kãyã, to, ku tambaye su daga bãyan shãmaki. Wannan ya fi muku tsarki ga zukãtanku da zukãtansu} ([58]) [al-Ahzab: 53].

Amma abinda mafi yawancin mata suka saba da shi na sanya bandeji ƙarƙashin mayafi, dan ta ɗago shi daga fuskarta, to ba shi da asali a cikin shari’a a abinda muka sani, da hakan ya zama abin shara'antawa da manzo - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya bayyana shi ga al'ummarsa kuma shiru akan hakan bai halatta gare shi ba.

Kuma yana halatta ga mai harama maza da mata su wanke tufafinsu, waɗanda suka yi harama da su, saboda datti ko waninsa, kuma ya halatta su canja su da wasunsu.

Ba ya halatta ya sanya wani abu daga tufafin da Za'afaran ko Wars ya taɓa su; domin cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi hani daga hakan a cikin hadisin Ibnu Umar - Allah Ya yarda da su -.

Kuma yana wajaba ga mai harama ya bar kwarkwasa, da fasiƙanci, da jayayya; saboda faɗin Allah - Maɗaukakin sarki -: {Hajji watanni ne sanannu. To, wanda ya yi niyyar hajji a cikinsu to bãbu jimã'i kuma bãbu fãsiƙanci, kuma bãbu jãyayya a cikin hajji ([59]) [al-Baƙara: 197].

Kuma ya inganta daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - cewa shi ya ce: «Wanda ya yi Hajji bai yi jima'i ba, kuma bai yi fasiƙanci ba, zai dawo kamar ranar da mahaifiyarsa ta haife shi ([60])». Kwarkwasa: Ana fadin ta akan jima'i, da kuma alfasha na magana da aiki. fasiƙanci kuwa: Saɓo. Jayayya kuwa: Rigima a kan ƙarya, ko a abinda ba shi da wata fa'ida, amma jayayya a abinda yake mafi kayau dan bayyanar da gaskiya da kifar da ƙarya to babu laifi, domin an yi umarni ma da shi; saboda faɗin Allah - Maɗaukakin sarki -: {Ka yi kira zuwa ga hanyar Ubangijinka da hikima da wa'azi mai kyau kuma ka yi jãyayya da su da magana wadda take mafi kyau} ([61] [al-Nahl: 125]. [47] Bukhari ne ya rawaito shi daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi -, a lamba ta (1521), da Muslim, a lamba ta (1350).

Rufe kai da wani abu mai ɗanfarar kai yana haramta ga mai harama namiji; kamar hula da shimag, da rawani ko makamancin haka, haka nan fuskarsa; saboda faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a lamarin wanda ya faɗo daga kan dabbarssa a ranar Arfa ya rasu: «Ku wanke shi da ruwa da magarya, kuma kuyi masa likkafani a tufafinsa biyu, kada ku rufe kansa da fuskarsa, domin cewa shi za'a tasheshi a ranar alƙiyama yana mai Talbiyyah ([62])» An haɗu a kansa, wanann lafazin Muslim ne. [48] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (1521), da Muslim, a lamba ta (1350).

Amma shan inuwarsa da rufin mota, ko lema ko makamancinsu, to babu laifi da shi, kamar shan inuwa da hema ko da bishiya; saboda abinda ya tabbata a cikin Sahih cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - anyi masa inuwa da wani tufafi lokacin da ya jefi Jamratul aƙabah (Babban Shaiɗan), kuma ya inganta daga gare shi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - cewa an kafa masa wata rumfa a Namira, sai ya sauka a ƙarƙashinta har lokacin da rana ta karkace a ranar Arfa.

Kuma yana haramta ga mai harama cikin maza ya kashe abin farauta na saarari (tudu) da taimakekeniya a akan hakan da kore shi daga gurinsa, da ɗaura aure, da jima'i, da neman auren mata, da rungumarsu da sha'awa; saboda hadisin Usman - Allah Ya yarda da shi -, cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: «Mai harama baya aure, kuma baya aurarwa kuma baya neman aure ([63)» Muslim ne ya ruwaito shi. Muslim ne ya ruwaito shi. [49] Muslim ne ya ruwaito, a lamba ta (1409).

Idan mai harama ya sanya ɗinkakken tufafi, ko ya rufe kansa ko ya shafa tirare akan mantuwa ko da jahilci to babu fidiya a kansa, kuma ya gusar da hakan a duk lokacin da ya tuna ko ya sani, haka nan wanda ya aske kansa ko ya yanke wani abu daga gashinsa ko ya yanke farce akan mantuwa ko da jahilci to babu komai a kansa akan ingantacciyar magana.

Kuma yana haramta ga musulmi - mai harama ne ko mara harama, namiji ne ko mace - kashe dabbar farauta ta harami, haka kuma taimakekeniya a kasheta, da makami ne ko nuni ko makamancin haka.

Kuma kore shi daga gurinsa ya haramta, haka yanke bishiyoyin harami ya haramta da tsirransa koraye, da tsintuwarsa, sai dai ga wanda zaiyi cigiya; saboda faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: «Lallai wannan gari - yana nufin Makka - haramun ne da haramcin Allah har zuwa ranar alƙiyama, ba'a yanke ƙayarsa, ba'a kore dabbar farautarsa, ba'a tsintar tsintuwarsa, sai dai ga wanda zaiyi cigiya, kuma ba'a cire ciyawarsa ([64])». An haɗu a kansa. Bukhari Da Muslim suka rawaito shi. [50] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (1834), da Muslim, a lamba ta (1353).

AlMunshid: Shi ne mai yin cigiya, al-Khala kuma: Ita ce ɗanyar ciyawa, kuma Mina da Muzdalifa suna daga cikin Harami, amma Arfa to tana daga cikin hilli (wajen Harami).

FASALI

A cikin abinda mahajjaci yake aikata shi a lokacin shiga Makka, da kuma bayanin abinda yake aikatashi bayan shiga masallaci mai alfarma na Ɗawafi da kuma siffarsa

Idan mai harama ya isa Makka, anso gare shi yayi wanka kafin shigarsa; saboda Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya aikata haka, idan ya isa masallaci mai alfarma, an sunnanta masa ya gabatar da ƙafarsa ta dama, sai ya ce: Da sunan Allah, tsira da aminci su tabbata ga manzon Allah, ina neman tsarin Allah Mai girma da fuskarSa Mai girma da sarautarSa daɗaɗɗiya daga Shaiɗan abin jefewa, Ya Allah Ka buɗe mini ƙofofin rahamarKa, kuma ya faɗi hakan a lokacin shiga ragowar masallatai, kuma babu wani keɓantaccen zikirin da ya tabbata daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ba don shiga masallaci mai alfarma a abinda na sani.

Idan ya isa Ka'aba, sai ya yanke talbiyya kafin ya fara ɗawafi idan ya kasance mai yin tamattu'i ne ko Umra, sannan ya nufaci al-Hajarul aswad (baƙin dutse) kuma ya fuskance shi, sannan ya taɓa shi da damansa, ya sunbace shi idan hakan ya sawwaƙa, kuma kada ya cutar da mutane da tureneniya, a lokacin taɓashi sai ya ce: "Da sunan Allah, Allah ne Mafi girma", ko ya ce: "Allah ne Mafi girma", Idan sunbatar tayi wahala, sai ya taɓashi da hannunsa, ko da sanda, ko makancinsu, sai ya sumbaci abinda ya taɓashi da shi, idan taɓashi yayi wahala, sai yayi nuni zuwa gare shi, sai yace: "Allah ne Mafi girma", kada ya sunbaci abinda ya nuna shi da shi, Ana sharɗantawa ga ingancin ɗawafi cewa: Mai ɗawafin ya zama yana da tsarki daga ƙaramin hadasi da babba; domin cewa ɗawafi kwatankwacin sallah ne, sai dai cewa anyi rangwamin magana a cikinsa, ya kuma sanya Ɗakin a hagunsa a lokacin ɗawafin. Idan a farkon ɗawafin ya ce: «Ya Allah don yin imani da Kai, da gasgata LittafinKa, da cika alƙawarinKa da bin sunnar AnnabinKa Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -» to yana da kyau; domin an ruwaito hakan daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -. Ya kuma yi ɗawafi kewaye bakwai, ya yi sassarfa a dukkanin ukun farko daga ɗawafin farko, shine ɗawafin da zaizo da shi a farkon gabatowarsa Makka, daidai ne ya kasance mai Umra ne, ko mai tamattu'i, ko mai harama da Hajji shi kaɗai, ko mai ƙirani tsakaninsa (Hajji) da Umra. Ya kuma yi tafiya a ragowar huɗun, yana fara kowane kewaye da baƙin dutse kuma yana cikawa da shi.

Sassarfa: ita ce gaggawa a cikin tafiya tare da kusantar taku, kuma an so gare shi ya yi Iɗɗiba'i a dukkanin wannan Ɗawafin banda waninsa. Ibɗiba'i shine: Ya sanya tsakiyar mayafi ƙarƙashin kafaɗarsa ta dama kuma gefunansa akan wuyansa na hagu.

Idan ya yi kokwanto a cikin adadin kewayen, sai yayi gini akan yaƙini, shine mafi ƙaranci. Idan ya yi kokwanto shin ya yi ɗawafi kewaye uku ne ko huɗu? Sai ya maida su uku, haka nan zai aikata a Sa'ayi.

bayan ya gama wannan Ɗawafin, sai ya sanya mayafinsa, sai ya sanya shi akan kafaɗunsa, kuma gefunansa akan ƙirjinsa kafin ya yi sallah raka'a biyun Ɗawafi.

Daga abinda yake kamatuwa yin inkari ga mata da yi musu gargaɗi daga gare shi , shi ne yin Ɗawafinsu cikin ado da tirare nau’i nau’i masu ƙanshi, da rashin suturtuwa alhali su al'aura ce, to yana wajaba akansu, su suturta, daga barin ado a lokacin yin Ɗawafi, da wasunsu daga halayen da mata suke cakuɗuwa da maza; domin cewa su al'aura ce kuma fitina ce, kuma fuskar mace ita ce mafi bayyanar ado dan haka ba ya halatta gareta ta bayyanar da ita sai ga muharramanta; saboda faɗin Allah - Maɗaukakin sarki -: {Kuma kada su nũna ƙawarsu fãce ga mazansu} ([65]) [al-Nur: 31]. Don haka yaye fuska baya halatta a gare su a lokacin sumbatar baƙin dutse, idan ya kasance wani daga maza yana kallonsu. Idan basu samu damar taɓa dutsen da sunbatarsa ba, to baya halatta garesu suyi turmutsutsu da maza, bari dai sai suyi ɗawafi ta bayansu, hakan shine mafi alheri garesu, kuma mafi girman lada daga ɗawafi kusa da Ka'aba a lokacin turmutsutsu da maza. Ba'a shara'anta sassarfa da Ibɗida'i a wanin wannan ɗawafin ba, haka nan ko a cikin Sa'ayi, ko ga mata; domin cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - baiyi sassarfa ko Ibɗada'i ba sai a ɗawafin farko wanda yazo da shi a lokacin da ya gabato Makka, kuma a lokacin ɗawafi ya zama mai tsarki daga hadasi da kuma khabasi, yana mai ƙanƙantar da kai ga Ubangijinsa, yana mai tawali'u gareShi.

An so gare shi ya yawaita ambatan Allah da addu'a a cikin Ɗawafinsa, idan ya karanta wani abu a cikinsa na Alƙur'ani, to yana da kyau, ko kuma wani keɓantaccen zikiri ko wata keɓantacciyar addu'a ba sa wajaba a cikin wannan Ɗawafin ko a waninsa daga ragowar Ɗawafi.

Amma abinda wasu daga cikin mutane suka farar na keɓantar kowane kewaye na ɗawafi ko sa'ayi da wasu keɓantattun zikirai, ko wasu keɓantattun addu'o'i, to ba shi da asali, kai duk abinda ya sawwaƙa na zikiri da addu'a ya isa. Idan ya dauranci Rukunil Yamani, sai ya taɓashi da damansa, sai yace: "Da sunan Allah, kuma Allah ne Mafi girma" kada ya sumbace shi, idan taɓa shi ya yi masa wahala, sai ya bar shi ya cigaba da ɗawafinsa, kada kuma ya yi nuni gare shi kada kuma yayi kabbara a yayin daurantarsa; domin hakan bai tabbata daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ba a cikin abinda muka sani. Anso tsakanin Rukunil Yamani da Hajarul aswad ya ce: {"Yã Ubangijinmu! Ka bã mu mai kyau a cikin dũniya da mai kyau a cikin Lãhira, kuma Ka tsare mana azãbar Wuta!"} ([66]) [al-Baƙara: 201]. A duk lokacin da ya zo kusa da alHajrul Aswad sai ya sumbace shi, kuma ya ce: "Allahu Akbar (Allah ne Mafi girma)", idan sumbatarsa ba ta sawwaƙa gare shi ba, sai ya yi nuni gare shi a duk lokacin da ya zo kusa da shi kuma ya yi kabbara.

Babu laifi da yin Ɗawafi ta bayan Zamzam da Maƙam, musammanma dai lokacin cunkoso, masallaci dukkansa guri ne na Ɗawafi, da zai yi Ɗawafi a gaban masallacin to ya isar masa, sai dai yin Ɗawafinsa kusa da Ka'aba ya fi idan hakan ya sawwaƙa.

Idan ya gama Ɗawafi, sai ya yi sallah raka'a biyu a bayan Maƙam, idan hakan ya sawwaƙa, idan hakan bai sawwaƙa ba, saboda cunkoso da makamancinsa, sai ya sallace su a kowane guri na masallaci, kuma an sunnanta bayan Fatiha ya karanta {Ka ce: "Ya kũ kãfirai! 1} [al-Kafirun:1] A raka'a ta farko da kuma {Ka ce: "Shi ne Allah Makaɗaĩci} ([68]) [al-Ikhlas: 1] A raka'a ta farko da kuma wannan shine yafi, idan ya karanta wasunsu, to babu laifi, sannan ya nufi al-Hajarul Aswad, sai ya sumbace shi da hannunsa na dama, idan hakan ya sawwaƙa; don koyi da Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - a cikin hakan.

Sannan ya fita zuwa Safa ta ƙofarsa, sai ya hau kansa ko ya tsaya a wurinsa, amma hawa dutsen Safa ɗin ya fi idan ya sawwaƙa, kuma a farkon kewaye na farko ya karanta faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Lalle ne Safã da Marwa suna daga wurãren ibãdar Allah} ([69]) [al-Baƙara: 158].

Ana so ya fuskanci Alƙibla akan Safa, ya godewa Allah ya kuma girmamaShi; ya ce: "Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma Allah ne Mafi girma, babu abin bautawa da gaskiya sai Allah Shi kaɗai yake baShi da abokin tarayya, mulki naSa ne, godiya ma tasa ce, Yana rayawa kuma Yana kashewa, Shi Mai iko ne akan dukkan komai, babu abin bautawa da gaskiya sai Allah Shi kaɗai yake, Ya zartar da alƙawarinSa, kuma Ya taimaki bawanSa, Ya tarwatsa rundunar ƙawance Shi kaɗai"». Sannan ya roƙi abinda ya sawwaƙa, yana mai ɗaga hannayensa, kuma yana maimaita wannan zikirin da kuma addu'ar (sau uku), sannan ya sauka, sai ya tafi Marwa har sai ya isa alama ta farko, sai namiji yayi gaggawar tafiya har sai ya kai zuwa alama ta biyu, amma mace ba'a shara'anta mata yin gaggawa tsakanin alamomi biyun ba; domin ita al'aurace, kawai abinda aka shara'anta mata a sa'ayi shine tafiya bakiɗayansa, sannan sai ya tafi ya hau kan Marwa ko ya tsaya a wajensa. Amma hawa kansa yafi, idan hakan ya sawwaƙa, ya faɗa kuma ya aikata akan Marwa, abinda ya faɗa kuma ya aikata akan Safa, banda karanta ayar, itace faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Lalle ne Safã da Marwa* suna daga wurãren ibãdar Allah} ([70]) [al-Baƙara: 158]. Wannan kawai an shara'anta shi ne lokacin hawa Safa a kewaye na farko kawai; dan koyi da Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, sannan ya sauka sai ya yi tafiya a wurin tafiyarsa, kuma ya yi (sassarfa) gaggawa a bigiren gaggawa har sai yakai Safa, ya aikata hakan sau bakwai, tafiyarsa kewaye ne, dawowarsa ma kewaye ne; domin cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya aikata abinda aka ambata, kuma ya ce: «Ku riƙi ayyukan ibadunku (na Hajji da Umra) daga gare ni ([71])». An so ya yawaita zikiri da addu'a da abinda ya sawwaƙa a yayin Sa'ayinsa, kuma ya zama mai tsarki daga babban hadasi (kari) da ƙarami, da a ce zai yi Sa'ayi ba tare da tsarki ba, to hakan ya isar masa, haka nan da a ce mace za ta yi al’ada ko ta yi jinin biƙi bayan Ɗawafi, kuma ta yi Sa'ayi, to hakan ya isar mata; domin cewa tsarki ba sharaɗi ba ne a cikin Sa'ayi, kawai shi mustahabbi ne kamar yadda ya gabata. [51] Fitar da shi ya gabata.

Idan ya gama sa'ayi, sai ya aske kansa ƙwal-ƙwal ko ya saisaye shi, amma ƙwal-ƙwal ga maza yafi, idan yayi saisaye yabar ƙwal-ƙwal ɗin saboda Hajji to yana da kyau, kuma idan gabatowarsa Makka kusa yake da lokacin Hajji, to saisaye a haƙƙinsa yafi, don ya aske ragowar kansa a Hajji; domin cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - lokacin da ya gabato Makka shi da sahabbansa a huɗu ga Zul-Hijja, ya umarci wanda bai koro hadaya ba ya warware harama kuma yayi saisaye, kuma bai umarcesu da yin ƙwal-ƙwal ba, kuma babu makawa a game dukkanin kai a saisayen, saisaye sashinsa baya isuwa, kamar yanda ƙwalƙwale sashinsa baya isuwa. Mace ba'a shara'anta mata komai ba sai rage gashin kai, kuma abinda aka shara'anta mata shine ta yanki gwargwadan Anmula ko ƙasa da haka daga kowane kitso, al-Anmula: Shine kan ɗan yatsa, kuma kada mace ta yanki ƙari akan hakan.

Idan mai harama ya aikata abinda aka ambata, to haƙiƙa Umrarsa ta cika, kuma dukkan abinda ya haramta gare shi da harama to ya halatta gare shi, sai dai idan ya kasance ya koro hadaya daga hillu (wajen harami), to shi zai wanzu akan haramarsa har sai ya gama Hajji da Umra baki ɗaya.

Amma wanda ya yi haramar Hajji shi kaɗai (Ifradi), ko da Hajji da Umra baki ɗaya, to an sunnanta masa ya warware haramarsa zuwa ga Umarah, kuma ya aikata abinda mai Tamattu'i yake aikata wa, sai dai idan ya kasance ya koro hadaya; domin cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya umraci sahabbansa da hakan, kuma ya ce: «Da ban koro hadaya ba, da na warware haramina tare da ku ([72])». [52] Bukhari ne ya ruwaito shi a lamba ta (1568).

Idan mace tayi haila ko biƙi bayan tayi harama da Umra, ba zata yi ɗawafi a ɗaki ba, haka kuma bazata yi sa'ayi tsakanin Safa da Marwa ba, har sai tayi tsarki, idan tayi tsarki sai tayi ɗawafi tayi sa'ayi ta rage (gashin) kanta, kuma da haka ne Umrarta ta cika, idan bata tsarkaka ba kafin ranar tarwiyyah, sai tayi harama da Hajji daga gurinta wanda take zaune a cikinsa, kuma ta fita tare da mutane zuwa Mina, da haka ne zata zama mai ƙirani tsakanin Hajji da Umra, kuma ta aikata abinda mahajjaci yake aikata shi na tsayuwa a Arfa, da Mash'ar, da jifan Jamarat (Shaiɗanu), da kwana a Muzdalifa da Mina, da soke hadaya, da rage kai, idan tayi tsarki sai tayi ɗawafi a Ɗaki, tayi sa'ayi tsakanin Safa da Marwa, ɗawafi ɗaya da sa'ayi ɗaya, kuma hakan ya isar mata daga Hajjinta da Umrarta baki ɗaya; saboda hadisin Nana A'isha cewa ita tayi haila bayan tayi harama da Umra, sai Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce mata: «Ki aikata abinda mahajjaci yake aikatawa, sai dai cewa bazakiyi Ɗawafi a Ɗaki ba, har sai kinyi tsarki ([73])» Bukhari Da Muslim suka rawaito shi. [53] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (305), da Muslim, a lamba ta (1211).

Idan mai al’ada ko mai jinin biƙi ta jefi Jamra (Shaiɗan) ranar babbar sallah ta kuma rage gashin kanta to duk abinda ya haramta gereta da harama ya halatta gare ta , kamar tirare da makamancinsa, sai miji kawai har sai ta cika Hajjinta kamar sauran mata masu tsarki, idan ta yi Ɗawafi ta yi Sa'ayi bayan tsarki to mijinta ya halatta gareta.

FASALI

A cikin hukuncin harama da Hajji ranar takwas ga watan Zul-Hijja da fita zuwa Mina

Idan ranar tarwiyyah tazo, itace ranar takwas ga Zul-Hijja, anso ga waɗanda suka sauka a Makka da wanda yayi niyyar yin Hajji daga mutanenta suyi harama da Hajji daga masaukansu; saboda sahabban Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - sun sauka a Abɗah sunyi haramar Hajji daga nan a ranar tarwiyyah da umarninsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, kuma Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - bai umarcesu su tafi Ɗaki (Ka'aba) suyi harama a gurinsa ba, ko a Mizab, haka nan bai umarcesu da ɗawafin bankwana ba a lokacin fitarsu zuwa Mina, da hakan ya zama abin shara'antawa da ya sanar musu da shi, kuma alheri dukkaninsa yana cikin bin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - da sahabbansa - Allah Ya yarda da su -.

Ana so yayi wanka, yayi tsafta ya shafa tirare a lokacin haramarsa da Hajji, kamar yanda zaiyi hakan a lokacin haramarsa daga Miƙatai. Bayan haramarsu da Hajji, an sunnanta musu su fuskanci Mina kafin zawali ko bayansa daga ranar tarwiyyah. Su yawaita talbiyyah har sai sun jefi Jamratul aƙaba (babban Shaiɗan), su sallaci Azahar da La'asar da Magariba da Issha'i da Asuba a Mina, kuma sunnah shine su sallaci kowace sallah a lokacinta ƙasaru (raka'a bibbiyu) ba tare da haɗawa ba, sai Magariba da Asuba ba'ayi musu ƙasaru.

Babu banbanci tsakanin mutanen Makka da wasunsu; domin cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi wa mutane sallah cikin mutanen Makka da wasunsu a Mina da Arfa da Muzdalifa ƙasaru, kuma bai umarci mutanen Makka da cikawa ba, da ace cikawar ta kasance wajibi ce a kansu da ya bayyana musu.

Sannan bayan huduwar rana a ranar Arfa mahajjaci zai fuskanci Arfa daga Mina, kuma an sunnanta musu su tsaya a Namira har zuwa zawali idan hakan ya sawwaƙa; saboda aikinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -.

Idan rana ta karkace an sunnantawa liman ko na'ibinsa, ya yiwa mutane huɗubar da ta dace da halin (da ake ciki), zai bayyanawa mahajjaci a cikinta abinda aka shara'anta masa a wannan yinin da kuma bayansa, ya umarcesu a cikinta da tsoron Allah, da kaɗaita Shi, da tsarkake ibada gareShi a cikin dukkanin ayyuka, ya gargaɗe su daga abubuwan da Ya haramta, ya yi musu wasicci a cikinta da yin riƙo da Littafin Allah da Sunnar AnnabinSa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, da yin hukunci da su, da kai ƙara zuwa gare su a cikin dukkanin al'amura; don yin koyi da Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - a cikin haka dukkaninsa, kuma bayanta za suyi sallar Azahar da La'asar a tsarin ƙasaru da jam'i (haɗa Azahar da La'asar) a cikin lokacin ta farko da kiran sallah ɗaya da kuma iƙama biyu; saboda aikinsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -. Muslim ne ya rawaito shi daga hadisin Jabir - Allah Ya yarda da shi -.

Sannan mutane su tsaya a Arfa, kuma Arfa dukkanta matsaya ce,. sai fa Baɗnu Uranah, anason fuskantar alƙibla da Jabalur rahma (dutsen rahama) idan hakan ya sawwaƙa. Idan fuskantarsu bai sawwaƙa ba, sai ya fuskanci alƙibla, koda kuwa bai fuskanci dutsen ba. An so ga mahajjaci a wannan matsayar yayi ƙoƙari a ambatan Allah - tsarki ya tabbatar maSa - da roƙonSa da ƙanƙar da kai gareShi, kuma ya ɗaga hannayensa a lokacin addu'a, idan yayi talbiyyah ko ya karanta wani abu daga Alƙur'ani to yana da kyau. An sunnanta ya yawaita faɗin: "Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah Shi kaɗai yake baShi da abokin tarayya, mulki naSa ne godiya ma taSa ce, Shi Ya ke rayawa kuma Ya ke kashewa kuma Shi Mai ikone akan dukkan komai"; saboda abinda aka ruwaito daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - cewa shi ya ce: «Mafi alherin addu'a, addu'ar ranar Arfa, kuma mafificin abinda na ce, ni da Annabawan da ke gabana: Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah Shi kaɗai yake baShi da abokin tarayya, mulki naSa ne godiya ma taSa ce, Yana kashewa kuma Yana rayawa, kuma Shi mai iko ne akan dukkan komai ([74])». Kuma ya inganta daga gare shi - tsira da amincin Allah su tabbata gareshi - cewa shi ya ce: «Mafi soyuwar zance ga Allah huɗu ne: Tsarki ya tabbata ga Allah, godiya ta tabbata ga Allah, babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Allah ne Mafi girma ([75])». [54] Tirmizi ne ya rawaito shi, a lamba ta (3585). [55] Muslim ne ya ruwaito shi, a lamba ta (2137).

To, yana kamata a yawaita wannan zikirin da kuma maimaita shi da khushu'i da halartowar zuciya, kuma yana kamata yawaitawa daga zikirai da kuma addu'o'in da suka zo a cikin shari'a a kowane lokaci, musammanma dai a wannan gurin, kuma a wannan ranar mai girma, ya zaɓi matattaran zikirai da addu'o'i, daga hakan:

* Tsarki ya tabbata ga Allah da godiyarSa, tsarki ya tabbata ga Allah Mai girma, {Babu abin bautawa da gaskiya Sai Kai, tsarki ya tabbata a gareKa, lallai ni na kasance cikin azzalumai}([76]) [al-Anbiya': 87].

* Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma bazamu bautawa kowa ba sai Shi, ni'ima taSa ce falalama taSa ce, kuma Yana da yabo kyakkyawa, babu abin bautawa da gaskiya sai Allah muna masu tsarkake Addini gareShi ko da kafirai sun ƙi.

Babu dabara babu ƙarfi sai da (taimakon) Allah([77]). [56] Muslim ne ya ruwaito shi daga Ibn al-Zubair - Allah Ya yarda da shi - a lamba ta (594).

{"Yã Ubangijinmu! Ka bã mu mai kyau a cikin dũniya da mai kyau a cikin Lãhira, kuma Ka tsare mana azãbar Wuta!"} }([78]). [al-Baƙara: 201].

Ya Allah, Ka gyara min addini na wanda shi ne ƙashin bayan al’amari na, Ka gyara min duniya ta, wacce na ke rayuwa a cikinta, Ka kuma gyara min lahira ta, wacce itace makoma ta, Ka sanya rayuwa ta zamo ƙari ce gare ni a cikin dukkanin alheri, Ka kuma sanya mutuwa ta zamo hutu ce gare ni daga dukkanin sharri([79]). [57] Muslim ne ya rawaito shi daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - a lamba ta (2720).

Ina neman tsarin Allah daga wahalar bala'i, da riskar tsiyata, da mummunar ƙaddara (abinda ka hukuntar), da kuma dariyar maƙiya([80]). [58] Bukhari ne ya fitar da shi daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - a lamba a (6347).

Ya Allah, ina neman tsarinKa daga baƙin ciki da ɓacin rai, kuma ina neman tsarinKa daga gajiyawa da kasala, kuma ina neman tsarinKa daga ragwantaka da rowa, da abinda zai jawo zunubi da abinda zai sa tara, kuma ina neman tsarinKa daga rinjayar bashi da kuma rinjayar mazaje([81]). [59] Da wannan lafazin, Abu Dawud ne ya rawaito shi daga Abu Umama al-Ansari, banda faɗinsa (abin da zai sa zunubi da abin da zai jawo tara) a lamba ta (1554).

Ya Allah, ina neman tsarinKa daga kuturta mai sanya fararen tabunbuna da hauka da kuturta mai sanya daddatsewar yatsu da kuma munanan masassaru([82]). [60] Abu Dawud ne ya rawaito shi daga Anas - Allah Ya yarda da shi - a lamba ta (1554).

* Ya Allah ina roƙonKa rangwami da lafiya a duniya da lahira.

* Ya Allah ina roƙonKa rangwami da lafiya a cikin addinina da duniyata da iyalaina da kuma dukiyata.

Ya Allah, Ka suturta al'aurata, Ka amintar da razanina, Ya Allah, Ka kiyayeni ta gabana da bayana, da damana da haguna, da samana, kuma ina neman tsarinKa kada ayi mini kisan gilla ta ƙarƙashina([83]). [61] Abu Dawud ne ya rawaito shi daga Ibnu Umar - Allah Ya yarda da shi - a lamba ta (5074).

Ya Allah, Ka gafarta mini, yi da gaskena da kakaci na da kuskurena da gangancina, kuma dukkanin hakan daga gareni ne, Ya Allah Ka gafarta mini abinda na gabatar da abinda na jinkirtar, da abinda na ɓoye da abinda na bayyana, da abinda Ka fini saninsa daga gareni, Kaine Mai gabatarwa, kuma Kaine Mai jinkirtarwa, kuma Kaine Mai iko akan dukkan komai([84]). [62] Wani yanki ne daga hadisin da Muslim ya ruwaito shi daga Abu Musa al-Ash'ari - Allah Ya yarda da shi - a lamba ta (2719).

* Ya Allah, ni ina roƙonKa tabbata a cikin al'amari, da ƙudirin niyya akan shiriya, ina roƙonKa godewa ni'imarKa da kyakkyawan bautarKa, ina roƙonKa kuɓutacciyar zuciya, da harshe mai gaskiya, ina roƙonKa daga mafi sanin abinda Ka sani, kuma ina neman tsarinKa daga sharrin abinda Ka sani, kuma ina neman gafararKa ga abinda Kake sani, lallai cewa Kaine Masanin abinda ke fake([85]). [63] Tirmizi ne ya ruwaito daga Shaddad bn Aus - Allah Ya yarda da shi - a lamba ta (3407).

* Ya Allah Ubangijin Annabi Muhammad - tsira da aminci su tabbata a gare shi -, Ka gafarta mini zunubina, Ka tafiyar da fushin zuciyata, Ka tseratar da ni daga fitintinu masu ɓatarwa muddin dai Ka wanzar da ni([86]). [64] Ahmad ne ya ruwaito daga hadisin Ummu Salama - Allah Ya yarda da ita - (6/301).

Ya Allah Ubangijin sammai Ubangijin ƙasa kuma Ubangijin Al'arshi mai girma, Ubangijinmu, kuma Ubangijin kowane abu, Maƙagin ƙwayar hatsi da kwalfar gurtsu, Wanda Ya saukar da Attaura da Linjila da Alfurƙan, ina neman tsarinKa daga sharrin dukkan abinda Kake riƙe da makwankwaɗarsa, ya Allah Kaine na farko, babu wani abu kafinKa, kuma Kaine na ƙarshe babu wani abu a bayanKa, Kaine zahiri babu wani abu a birbishinKa, Kaine baɗini babu wani abu koma bayanKa, Ka biyamana bashi kuma Ka wadatamu daga talauci([87]). [65] Muslim ne ya rawaito shi daga Hadisin Abu Huraira -Allah ya yarda da shi- a lamba ta (2713).

Ya Allah Ka bawa raina taƙawarta, Ka tsarkaketa, Kaine mafi alherin wanda zai tsarkaketa, Kaine Majiɓincinta, kuma shugabanta. Ya Allah, ni ina neman tsarinKa daga gajiyawa da kasala, kuma ina neman tsarinKa daga tsoro da tsufa da rowa, ina neman tsarinKa daga azabar ƙabari([88]). [66] Muslim ne ya rawaito shi daga hadisin Zaid bn Arƙam - Allah Ya yarda da shi - a lamba ta (2722).

Ya Allah gareKa na miƙa wuya, da Kaine nayi imani, gareKa ne na dogara, gareKa ne na koma, saboda Kaine nake husuma, ina neman tsari saboda buwayarKa da Ka ɓatar da ni, babu wani abin bautawa da gaskiya sai Kai, Kaine Rayayye wanda baYa mutuwa, aljanu da mutane suna mutuwa([89]). [67] Muslim ne ya ruwaito shi daga hadisin Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su -, a lamba ta (2717).

Ya Allah ni ina neman tsarinKa daga ilimin da bashi da amfani, da zuciyar da bata tsoron Allah, da ran da bata ƙoshi, da addu'ar da ba'a amsawa([90]). [68] Wannan wani yanki ne na hadisin Zaid bn Arƙam - Allah Ya yarda da shi - wanda fitar da shi ya gabata, a lamba ta (2722).

Ya Allah Ka nisantar da ni munanan ɗabi'u da ayyuka da soye-soyen rayuka da kuma cututtuka([91]). [69] Tirmizi ne ya ruwaito daga Ziyad bn Ilaƙa daga baffansa, a lamba ta (3591).

Ya Allah Ka kimsamin shiriyata, kuma Ka kare ni daga sharrin raina([92]). [70] Tirmizi ne ya rawaito shi daga hadisin Imran bn Husain - Allah Ya yarda da shi -, a lamba ta (3483).

Ya Allah Ka isar mini da halalinKa daga haram ɗinKa, kuma Ka wadatani da falalarKa daga wanda ba Kai ba([93]). [71] Tirmizi ne ya ruwaito daga hadisin Aliyu - Allah Ya yarda da shi -, a lamba ta (3563).

Ya Allah ina roƙonKa shiriya da taƙawa, da kamewa, da wadata([94]). [72] Muslim ne ya ruwaito shi daga hadisin Abdullahi bn Mas'ud - Allah Ya yarda da shi -, a lamba ta (2721).

Ya Allah ni ina roƙonKa shiriya da aiki a bisa daidai([95]). [73] Muslim ne ya ruwaito shi daga hadisin Aliyu - Allah Ya yarda da shi -, a lamba ta (2725).

Ya Allah ina roƙonKa alheri dukkansa, magaggaucinsa da majinkircinsa, abinda na sani daga gareshi da abinda ban sani ba, ina neman tsarinKa daga dukkanin sharri, magaggaucinsa da majinkircinsa, abinda na sani daga gareshi da abinda ban sani ba, ina roƙonKa daga mafi alherin abinda bawanKa kuma AnnabinKa Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya tambayeKa, ina nema tsarinKa daga mafi sharrin abinda bawanKa kuma AnnabinKa Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya nemi tsarinKa daga gareshi, ya Allah ina roƙonKa aljanna da abinda zai kusanto zuwa gareta na magana ko aiki, ina neman tsarinKa daga wuta da abinda zai kusanto zuwa gareta na magana ko aiki, ina roƙonKa Ka sanya dukkan hukuncin da Ka hukunta shi gareni ya zama alheri([96]). [74] Ibn Majah ne ya rawaito shi daga hadisin Nana A'isha - Allah Ya yarda da ita -, a lamba ta (3846).

Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Shi kaɗai Yake, baShi da abokin tarayya, mulki naSa ne, godiya ma taSa ce, Yana rayawa Yana kashewa, alheri yana hannunSa, kuma Shi Mai iko ne akan dukkan komai, tsarki ya tabbata ga Allah, godiya ma ta tabbata ga Allah, babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Allah ne Mafi girma, babu dabara babu ƙarfi sai da (taimakon) Allah Maɗaukaki Mai girma([97]). [75] Bukhari ya ruwaito shi, daga hadisin Ubada bn Samit - Allah Ya yarda da shi -, a lamba ta (1154).

* Ya Allah Kayi salati ga (Annabi) Muhammad da alayen (Annabi) Muhammad, kamar yanda Kayi salati ga (Annabi) Ibrahim da alayen (Annabi) Ibrahim, lallai Kai abin yabo ne Mai girma, Kayi albarka ga (Annabi) Muhammad da alayen (Annabi) Muhammad, kamar yanda Kayi albarka ga (Annabi) Ibrahim da alayen (Annabi) Ibrahim, lallai Kai abin yabo ne Mai girma([98]).. [76] Bukhari ne ya ruwaito shi daga hadisin Ka'abu bn Ujra - Allah Ya yarda da shi -, a lamba ta (3370).

{"Yã Ubangijinmu! Ka bã mu mai kyau a cikin dũniya da mai kyau a cikin Lãhira, kuma Ka tsare mana azãbar Wuta!"} ([99]) [al-Baƙara: 201].

An so a wannan wurin mai girma, mahajjaci ya maimaita abinda ya gabata na zikirai da addu'o'i, da abinda ke cikin ma'anoninsu na zikiri da addu'a da salati ga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbbata agare shi -, kuma ya yi na ci a cikin addu'a, ya roƙi Ubangijinsa alherin duniya da lahira, Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance idan zai yi addu'a yana maimaita addu'ar sau uku, to yana kamata a yi koyi da shi a cikin hakan tsira da aminci su tabbata agare shi.

Kuma a wannan matsayar musulmi ya zama mai ƙanƙar da kai ga UbangijinSa - tsarki ya tabbatar maSa -, yana mai tawali'u gareShi, mai ƙanƙar da kai ga janabinSa, mai karairaya a gabanSa, yana kwaɗayin rahamarSa da gafararSa, kuma yana jin tsoron azabarSa da fushinSa, kuma yayiwa kansa hisabi, ya sabunta tuba tsarkakakke; domin wannan yini mai girma ne, kuma matattara ce mai girma, Allah Yana kyauta a cikinsa ga bayinSa, kuma Ya na yiwa mala'ikunSa alfahari da su, kuma 'yantuwa daga wuta yana yawaita a cikinsa, kuma Shaiɗan bai taɓa ganin wani abu a cikin wani yini mafi koruwa daga rahama gareshi ba kuma mafi ƙasƙanta kuma mafi wulaƙanta gareshi daga yinin Arfa, sai dai abinda aka nuna masa a ranar Badr; hakan kuwa saboda abinda ya gani na kyautar Allah ga bayinSa da kuma kyautatawarSa garesu da yawan 'yantawarSa da gafararSa.

Ya zo a cikin Sahihu Muslim daga Nana A'isha - Allah Ya yarda da ita - cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi - ya ce: «Babu wata rana wacce Allah Yafi 'yanta bayi daga wuta, kamar ranar Arfa, kuma lallai Shi wallahi Yana kusantowa, sannan Yana wa Mala'iku alfahari da su, yana cewa: Me waɗannan suke so? ([100])». [77] Muslim ne ya rawaito shi daga hadisin Nana A'isha - Allah Ya yarda da ita -, a lamba ta (1348).

To, yana kamata ga musulmai su nunawa Allah alheri daga kawunansu, kuma su wulaƙantar da maƙiyinsu Shaiɗan, su baƙanta masa rai da yawan zikiri da addu'a da lazimtar tuba, da neman gafara daga dukkanin zunubai da kurakurai. Mahajjata ba zasu gushe ba a wannan matsayar suna masu shagaltuwa da zikiri da addu'a da ƙanƙar da kai, har sai rana ta faɗi, idan rana ta faɗi, sai su juya zuwa Muzdalifa da nutsuwa da tabbata, su yawaita talbiyyah suyi gaggawa a al-Muttasa; saboda aikin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, kuma barin Arfa baya halatta kafin faɗuwar rana; domin cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbta a gare shi - ya tsaya har sai da rana ta faɗi, kuma ya ce: «Ku riƙi ibadunku (na Hajji) daga gurina ([101])». «Ku riƙi ayyukan ibadunku (na Hajji da Umra) daga gare ni [78]». [78] Fitar da shi ya gabata.

Idan sun isa Muzdalifa, sai su sallaci Magariba raka'a uku a nan da Issha'i raka'a biyu a tsarin sallar jam'i (a haɗe) da kiran sallah ɗaya, da iƙama biyu, daga lokacin da suka isa gareta; saboda aikin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, daidai ne sun isa Muzdalifa a lokacin Magariba ne ko bayan shigar lokacin Issha'i.

Amma abinda wasu daga cikin gamagarin mutane suke aikata shi, na tsintar tsakwankwani tun isarsu Muzdalifa kafin sallah, da kuma ƙudircewar mafi yawa daga cikinsu cewa hakan abin shara'antawa ne to shi galaɗi ne bashi da asali. Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - baiyi umarni da a tsintar masa da tsakuwa ba, sai bayan juyowarsa daga Mash'aril haram zuwa Mina, a duk gurin da ya tsinci tsakuwa, to hakan ya isar masa, kuma tsintar sa daga Muzdalifa bai ayyana ba, kai tsintar yana halatta daga Mina, sunna shine tsintar bakwai a wannan ranar da zai jefi babbar Jamra (babban shaiɗan) da su; dan koyi da Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, amma a kwanuka uku, sai ya tsinci tsakwankwani ashirin da ɗaya da zai jefi Jamrori (shaiɗanu) ukun da su.

kuma ba'a son wanke tsakuwa, bari dai yayi jifa da ita ba tare da wankewa ba; domin cewa hakan ba'a cirato shi daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ko sahabbansa ba, kuma kada yayi jifa da tsakuwar da akayi jifa da ita.

Mahajjaci yana kwana a cikin wannan daren a Muzdalifa, kuma ya halatta ga raunana daga mata da yara ƙanana da makamancinsu, su tafi zuwa Mina a ƙarshen dare; saboda hadisin Nana A'isha da Ummu Salamah da wasunsu. Amma wasunsu daga mahajjata to yana ƙarfafuwa a cikin haƙƙinsu su zauna a nan har sai sun yi sallar Asuba, sannan su tsaya a Mash'arul haram sai su fuskanci Alƙibla su yawaita ambatan Allah da girmamaShi da addu'a har sai gari ya yi musu fatsi-fatsi sosai. An so ɗaga hannaye a nan a lokacin addu'a, kuma a duk inda suka tsaya a Muzdalifa to hakan ya isar musu, kuma kusantar Mash'aril haram (Masallacin Muzdalifa) ko hawansa ba ya wajaba a kansu; saboda faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: «Na tsaya a nan - yana nufin akan Mash'aril haram - kuma Muzdalifa dukkanta gurin tsayawa ne ([102])» Muslim ne ya ruwaito shi cikin Sahih ɗinsa, Jma kuma: Itace Muzdalifa. [79] Muslim ne ya ruwaito shi daga hadisin Jabir - Allah Ya yarda da shi -, a lamba ta (1218).

Idan gari yayi haske sosai, sai su juya zuwa Mina, kafin ɓullowar rana, kuma su yawaita Talbiyyah a cikin tafiyarsu, idan suka isa Muhassir, an so suyi gaggawa kaɗan.

Idan suka isa Mina, sai su yanke talbiyyah a Jamratul aƙabah (babban shaiɗan), sannan suyi jifa da su daga isarsu da tsakwankwani bakwai a jere, yana ɗaga hannunsa a lokacin jifan kowace tsakuwa yana yin kabbara, kuma an so ya jefesu daga cikin kwarin, ya sanya Ka'aba a hagunsa, Mina kuma a damansa; saboda aikin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -. Idan ya jefe su ta wasu ɓangarorin daban ya isar masa idan tsakwankwanin sun faɗa cikin inda ake jifan, kuma ba'a sharɗanta wanzuwar tsakuwar a cikin wurin jifan ba kawai abinda aka sharɗanta shine faɗawarsa a cikinsa, da ace tsakuwa zata faɗa a cikin wurin jifan sannan ta fita daga cikinsa, to ta isar a zahirin zancen ma'abota ilimi, daga cikin waɗanda suka bayyanar da hakan ɓaro-ɓaro: Al-Nawawi - Allah Yayi masa rahama - a cikin (Sharhul Muhazzab), kuma tsakwankwanin jifan su zama kwatankwacin tsakuwar da ake harbi da ita, ita tafi wake girma da kaɗan.

Sannan bayan yayi jifa zai soke hadayarsa, kuma an so a lokacin da zai soke ko zai yanka ya ce: «Da sunan Allah, kuma Allah ne Mafi girma, Ya Allah, wannan daga gareKa ne, kuma naKa ne», kuma ya fuskantar da shi zuwa ga alƙibla. Sunnah itace: Soke raƙumi alhali yana tsaye, hannunsa na hagu a ɗaure, da kuma yanka shanu da tumakai ta ɓangarensu na hagu, da zaiyi yanka bai kalli alƙibla ba, to ya bar sunnah kuma yankansa ya isar masa; domin cewa fuskantarwar zuwa alƙibla a yayin yanka sunnah ne ba wajibi ba ne, kuma an so yaci daga hadayarsa, yayi kyauta yayi sadaka; saboda faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Sai ku ci daga gare su, kuma ku ciyar da matsattse matalauci"} ([103]) [al-Hajj: 28], kuma lokacin yankan yana zarcewa har zuwa faɗuwar ranar yini na uku cikin kwanukan Tashriƙ a cikin mafi ingancin maganganun ma'abota ilmi, sai kwanakin yankan su zama ranar babbar sallah da kuma kwanaki uku a bayanta.

Sannan bayan soke hadaya, zai aske kansa ƙwal-ƙwal ko ya saisaye shi, amma aski ƙwal-ƙwal ya fi; domin cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi wa masu askin ƙwal-ƙwal addu'ar rahama da gafara (sau uku) masu saisaye kuma sau ɗaya, kuma aske sashin kai ba ya wadatarwa, kai babu makawa sai an saisaye shi dukkaninsa kamar aski ƙwal-ƙwal, mace kuwa tana rage gwargwadan ɗan yatsa ko ƙasa da haka daga kowanne kitso.

Bayan jifan Jamratul Aƙabah (Babban Shaiɗan) da aski ƙwal-ƙwal ko saisaye to an halattawa mai harama dukkan abinda ya haramta gare shi sai mata kawai, ana kiran wannan Tahallulin da: Tahalluli na farko, kuma bayan wannan Tahallulin an sunanta masa turare da nufatar Makka dan ya yi Ɗawafin Ifada; saboda hadisin Nana A'isha - Allah Ya yarda da ita - ta ce: «Na kasance ina shafawa manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - tirare dan yin haramarsa kafin ya yi harama, haka ga warware haraminsa, kafin ya yi ɗawafi a ɗaki ([104])». Bukhari da Muslim ne suka fitar da shi. [80] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (1539), da Muslim, a lamba ta (1189).

Kuma ana ambatan wannan Ɗawafin: Ɗawafin Ifada, da Ɗawafin ziyara, kuma shi rukuni ne daga cikin rukunan Hajji, Hajji ba ya inganta sai da shi, kuma shi ne ake nufi a cikin faɗinSa - Allah Mai girma da ɗaukaka -: {"Sa'an nan kuma sai su ƙãre ibãdarsu da gusar da ƙazanta, kuma sai su cika alkawuransu kuma sai su yi ɗawãfi (sunã gẽwaya) ga Ɗãkin nan 'yantacce"} ([105]). [al-Hajj: 29].

Sannan bayan ɗawafi da sallah raka'a biyu a bayan Maƙamu Ibrahim zai yi Sa'ayi tsakanin Safa da Marwa idan ya kasance mai Tamattu'u ne, wannan sa'ayin na hajjinsa ne, Sa'ayin farko kuma na Umararsa ne.

Sa'ayi ɗaya baya isuwa a cikin mafi ingancin maganganun malamai; saboda hadisin Nana A'isha - Allah Ya yarda da ita - ta ce: «Mun fita tare da manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -» sai ta ambaci hadisin, kuma a cikinsa sai ya ce: «Wanda ya kasance a tare da shi akwai hadaya, to sai yayi niyyar Hajji tare da Umra, sannan bazai warware haramarsa ba, har sai yayi Tahalluli (kammalawa) daga garesu baki ɗaya»... ...har zuwa inda ta ce : «Sai waɗanda sukayi niyyar Umra sukayi ɗawafi a Ɗaki, da kuma Safa da Marwa, sannan suka warware haramarsu, sannan sukayi wani ɗawafin daban don Hajjinsu bayan sun dawo daga Mina don Hajjinsu ([106])» Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi. [81] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (1556), da Muslim, a lamba ta (1211).

Da faɗinta - Allah Ya yarda da ita - game da waɗanda sukayi niyyar Umra -: "Sannan sukayi wani ɗawafin daban bayan sun dawo daga Mina don Hajjinsu" tana nufi da shi: Ɗawafi tsakanin Safa da Marwa, akan mafi ingancin maganganu a cikin tafsirin wannan hadisin. Amma faɗin wanda yace: Tayi nufin ɗawafin Ifadah ne da hakan, to ba ingantacce ba ne; domin cewa ɗawafin Ifadah rukuni ne a haƙƙin kowa da kowa alhali kuwa sun riga sunyi shi, kawai abin nufi da hakan: Abinda ya keɓanci mai tamattu'i, shine ɗawafi tsakanin Safa da Marwa karo na biyu bayan dawowa daga Mina don cika Hajjinsa, kuma hakan a bayyane yake da godiyar Allah, kuma shine maganar mafi yawancin ma'abota ilimi.

Abinda Bukhari ya ruwaito shi a cikin Sahih Mu'allaƙi wanda yake a yanke, yana nuni a bisa ingancin haka, daga Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su - cewa shi an tambaye shi game da Mut'atul Hajji, sai ya ce: «Muhajirun da Ansar da matan Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sunyi niyya, a cikin Hajjin bankwana, muma munyi niyya, lokacin da muka gabato Makka sai Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: Ku maida niyyarku ta Hajji ta koma Umra, sai dai wanda ya ratayo hadaya, sai mukayi ɗawafi a Ɗaki da Safa da Marwa, muka zowa mata, muka sanya tufafi, kuma yace: Wanda ya ratayo hadaya, to shi ba zai warware haraminsa ba har sai hadaya ta kai bigirenta, sannan ya umarce mu muyi niyyar Hajji a yammacin Tarwiyyah, idan mun gama ibadun hajji sai muzo muyi ɗawafi a Ɗaki da Safa da Marwa»([107]). Abinda ake nufi daga gare shi ya ƙare, kuma shi a bayyane yake a cikin Sa’ayin wanda yake Tamattu'i sau biyu ne (na farko dan Umarah na biyu kuma Don Hajj). Allah ne Mafi sani. [82] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (1572).

Amma abinda Muslim ya ruwaito daga Jabir - Allah Ya yarda da shi - «Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ko sahabbansa ba suyi ɗawafi tsakanin Safa da Marwa ba, sai ɗawafi ɗaya»([108]). Ɗawafinsu na farko abin ɗauka ne akan wanda ya koro hadaya daga sahabbai; domin cewa su sun wanzu akan haramarsu tare da Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - har sai da suka warware haramarsu na Hajji da Umra baki ɗaya, kuma Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yayi niyyar Hajji da Umra kuma ya umarci wanda ya koro hadaya, da cewa yayi niyyar Hajji tare da Umra, kuma kada ya warware haramarsa har sai ya gamasu baki ɗaya; Mai yin ƙirani (gwamna Hajji da Umarah), babu wani abu a kansa, sai Sa'ayi ɗaya, kamar yadda hadisin Jabir wanda aka ambata ya yi nuni a kansa da waninsa cikin hadisai ingantattu. [83] Muslim ne ya ruwaito, a lamba ta (1215).

Haka nan wanda yayi Ifradi ya kuma wanzu a cikin haramarsa har zuwa ranar babbar sallah, babu komai a kansa, sai Sa'ayi ɗaya. Idan mai ƙirani da mai Ifradi sukayi Sa'ayi bayan Ɗawafil ƙudum, to hakan ya isar musu daga Sa'ayi bayan Ɗawafin Ifadah, wannan shine haɗawa tsakanin hadisin Nana A'isha da na Ibnu Abbas da kuma hadisin Jabir wanda aka ambata, da haka ne karo zai gushe, kuma a samu damar yin aiki da hadisan gabaɗayansu.

Daga cikin abinda zai ƙarfafi wannan haɗawar cewa hadisai biyu na Nana A'isha da Ibnu Abbas hadisai ne ingantattu, alhali kuma sun tabbatar da Sa'ayi biyu a cikin haƙƙin wanda ya yi Tamattu'i, kuma zahirin hadisin Jabir yana kore hakan, kuma mai tabbatarwa shi ake gabatarwa akan mai korewa, kamar yadda yake tabbatacce a cikin ilmi biyu na Usulu da Musɗalahul hadis, Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Shi ne Mai datarwa zuwa ga daidai, babu wata dabara babu wani ƙarfi sai ga Allah.

FASALI

A cikin bayanin mafificin abinda Maniyyaci zai aikata shi ranar babbar sallah

Abinda yafi ga mahajjaci shine, ya jeranta waɗannan al'amurra huɗun a ranar babbar sallah, kamar yanda muka ambata: A farko sai ya fara da jifan Jamratul Aƙabah (Babban Shaiɗan), sannan yanka, sannan aski ƙwalƙwal ko saisaye, sannan Ɗawafi a Ɗaki da kuma Sa'ayi a bayansa ga mai Tamattu'i, haka nan ga mai Ifradi da mai ƙirani, idan ba suyi Sa'ayi tare da Ɗawafil ƙudum ba, idan ya gabatar da sashin waɗannan al'amuran akan wasu, to ya isar masa; saboda tabbatar sauƙi daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - a cikin hakan, kuma gabatar da Sa'ayi akan Ɗawafi shima ya shiga cikin hakan; domin cewa shi yana daga cikin al'amurran da ake aikatasu a ranar babbar sallah. Sai ya shiga cikin faɗin sahabi: ba'a tambaye shi game da wani abu da aka ƙaddamar ko aka jinkirtar a wannan ranar ba sai ya ce: «Ka aikata babu wani laifi ([109])» , kuma saboda hakan yana daga abinda mantuwa da jahilci suke afka masa, sai shigarsa a cikin wannan gamewar ya wajaba; saboda abinda ke cikin hakan na sauƙaƙawa da sahhalewa. [84] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (83), da Muslim, a lamba ta (1306).

Haƙiƙi ya tabbata daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - cewa an tambaye shi game da wanda yayi Sa'ayi kafin yayi ɗawafi, sai ya ce: «Babu wani laifi ([110])» Abu Dawud ne ya fitar da shi, daga hadisin Usama ɗan Sharik da Isnadi inagntacce, sai shigarsa cikin gamewar ya bayyana, ba tare da wani kokwanto ba. Allah ne Mai datarwa. [85] Abu Dawud ne ya rawaito shi, a lamba ta (2015).

Al'amurran da cikakken Tahalluli yake tabbata ga mahajjaci da su abubuwa ne uku sune: Jifan Jamratul Aƙabah (Babban Shaiɗan), da aski ƙwalƙwal ko saisaye, da Ɗawaful Ifadah tare da Sa'ayi a bayansa saboda abinda aka ambata ɗazu. Idan ya aikata waɗannan abubuwa ukun, to dukkan abinda ya haramta a kansa da harama ya halatta gare shi, na daga mata, da tirare da wanin haka, wanda kuma ya aikata biyu daga cikinsu, to dukkan abinda ya haramta a kansa da harama ya halatta gare shi, sai mata, kuma ana ambatan wannan da: Tahalluli na farko.

Kuma an so ga mahajjaci yasha ruwan Zamzam ya ƙoshi da shi, da kuma yin addu'a da abinda ya sawwaƙa na addu'a mai amfani, da kuma «Ruwan Zam-zam dan abinda aka sha gare shi ne([111])», kamar yanda aka rawaito daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a cikin Sahihu Muslim daga Abu Zarr: Cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya faɗa a sha'anin ruwan Zam-zam: «Lallai shi abinci ne (Abinci mai wadatarwa ne daga dukkanin abinci)» ([112]). Abu Dawud ya ƙara: «Kuma waraka ne daga masassara ([113])». [86] Ibnu Majah ne ya rawaito shi daga Jabir bn Abdullahi - Allah Ya yarda da shi -, a lamba ta (3062). [87] Muslim ne ya ruwaito shi, a lamba ta (2473). [88] Yana nufin: Abu Dawud al-Ɗayalusi alhali ya fitar da shi a cikin hadisin ƙissar musuluntar Abu Zarr - Allah Ya yarda da shi -, a duba Musnad na Abu Dawud al-Ɗayalusi a lamba ta (459).

Bayan Ɗawafin Ifada (wato Dawafin Wajibi) da Sa'ayi ga wanda a kansa akwai Sa'ayi mahajjata za su dawo zuwa Mina sai su zauna a nan kwana uku da dararensu, su jefi Jamrori uku a kowace rana daga kwanuka ukun, bayan karkacewar rana, kuma jeranta jifan nasu wajibi ne.

Sai ya fara da Jamra ta farko (Karamin shaiɗan): Itace wacce take bin masallacin Khaif, sai ya jefeta da tsakwankwani bakwai a jere, yana mai ɗaga hannunsa a kowace tsakuwa, kuma an sunnanta ya gabaceta, ya sanyata a hagunsa, ya fuskanci alƙibla, ya ɗaga hannayensa, kuma ya yawaita addu'a da ƙanƙar da kai.

Sannan ya jefi Jamrah ta biyu (Shaiɗan na tsakiya) kamar ta farko, kuma an sunnanta ya gabato kaɗan, bayan ya jefeta ya sanyata a damansa, ya fuskanci alƙibla, ya ɗaga hannayensa sai yayi addu'a mai yawa.

Sannan ya jefi Jamrah ta uku (Babban Shaiɗa) kuma kada ya tsaya a wurinta.

Sannan ya jefi Jamrorin a yini na biyu daga cikin kwanukan Tashriƙ bayan zawali , kamar yadda ya jefesu a yini na farko, kuma ya aikata a ta farko da ta biyu kamar yadda ya aikata a yini na farko; dan yin koyi da Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -.

Jifa a yini biyun farko daga cikin kwanukan Tashriƙ wajibi ne daga cikin wajiban Hajji, haka nan kwana a Mina a dare na farko da na biyu, wajibi ne sai dai ga masu shayar da ruwa da kuma makiyaya da makamantansu to baya wajaba akan su .

Sannan bayan jifan Jamarat a kwanuka biyun da aka ambata, to wanda ya so ya yi gaggawar dawowa daga Mina, to hakan ya halatta gare shi, kuma ya fita kafin faɗuwar rana, wanda kuma ya jinkirta kuma ya kwana a dare na uku kuma ya jefi Jamarorin uku a yini na uku, to shi ya fi kuma Ya fi girman lada, kamar yadda Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma ku ambaci Allah a cikin kwanuka ƙidayayyu. To, wanda ya yi gaggawa a cikin kwana biyu, to, bãbu laifi a kansa, kuma wanda ya jinkirta, to, bãbu laifi a kansa, ga wanda ya yi taƙawa} ([114]). [al-Baƙara: 203]. Kuma saboda Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi rangwame a gaggautowar, amma shi bai gaggauto ba, kai ya tsaya a Mina har sai da ya jefi Jamarat ɗin a yini na goma sha uku bayan zawali, sannan ya tafi kafin ya sallaci Azahar.

Kuma yana halatta ga waliyyin yaron da ya kasa yin jifan, ya jefi Jamratul Aƙabah ɗin da ma ragowar jamarorin ga shi yaron, bayan ya yi wa kansa jifan, haka nan ƙaramar yarinya wacce ta kasa yin jifan waliyyinta zai yi mata jifan; saboda hadisin Jabir - Allah Ya yarda da shi - ya ce: «Munyi Hajji tare da Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, alhali a tare da mu akwai mata, da ƙananan yara, sai muka yiwa ƙananan yaran Talbiyyah, kuma mukayi musu jifa ([115])». Ibnu Majah ne ya fitar da shi. [89] Tirmizi ne ya ruwaito shi, a lamba ta (927).

Kuma ya halatta ga wanda ya kasa yin jifa saboda rashin lafiya ko yawan shekaru, ko juna biyu ya wakilta wanda zai yi masa jifan; saboda faɗin Allah - Maɗaukakin sarki -: {Sai ku bi Allah da taƙawa gwargwadon abin da kuka sãmi ĩko} ([116]). [al-Tagabun: 16]. Waɗannan ba zasu iya cunkoso da mutane a wurin Jamrorin ba, kuma zamanin jifan mai wucewa ne, kuma ba'a shara'anta ramashi ba, sai ya halatta garesu, su wakilta (wani) saɓanin waninsa daga ibadu, to baya halatta ga mai harama ya wakilta wanda zaiyi masa, koda Hajjinsa na nafila ne; domin cewa wanda yayi harama da Hajji ko Umra - koda sun kasance na nafila ne - to ya lazimce shi ya cika su; saboda faɗin Allah - Maɗaukakin Sarki -: {Kuma ku cika Hajji da Umra dōmin Allah} ([117]). [al-Baƙara: 196], kuma loakacin Ɗawafi da Sa'ayi ba ya wucewa saɓanin zamanin jifa.

Amma tsayuwa a Arfa, da kwana a Muzdalifa da Mina, to babu kokwanto cewa lokacinsu yana wucewa, sai dai samuwar gajiyayye a waɗannan wuraren mai yi wuwa ne, ko da tare da wahala ne, saɓanin yin jifansa, kuma saboda jifa haƙiƙa wakilci a cikinsa ya zo daga magabata na gari a cikin haƙƙin wanda keda uzuri saɓanin waninsa.

Ibadu a tsaye suke ba ya halattta ga wani ya shara'anta wani abu daga garesu, sai da hujja, kuma yana halatta ga wanda zai yi wakilci ya yi wa kansa jifa sannan ya yi wa wanda yake wakilta a dukkanin Jamrorin uku, alhali shi yana wuri ɗaya, kuma ba ya wajaba a gare shi ya cika jifan Jamrori ukun ga kansa, sannan ya dawo ya yi jifa ga wanda yake wakilta a cikin mafi ingancin maganganun malamai biyu; saboda rashin dalili mai wajabta hakan, kuma saboda abinda ke cikin hakan na wahala da ƙunci, Allah - tsarki ya tabbatar amSa Ya ɗaukaka - Yana cewa: {Alhãli kuwa (Allah )bai sanya wani ƙunci ba a kanku a cikin addĩni} ([118]). [al- Hajj: 78]. Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Ku sawwaƙa, kada ku tsananta ([119)». Kuma domin cewa hakan ba'a ruwaito daga sahabban manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ba lokacin da suka yi wa ƙananan yaransu da wanda ya kasa daga cikinsu jifa ba, da ace sun aikata hakan, to da an ruwaito; domin hakan yana daga cikin abinda himmomi suka jerantu akan ruwaito shi. Allah ne Mafi sani. [90] Bukhari ne ya ruwaito shi, daga hadisin Anas - Allah Ya yarda da shi -, a lamba ta (69).

FASALI

A kan wajabcin jini (yanka) akan mai tamattu'i da mai ƙirani.

Kuma jini (wato yanka) yana wajaba akan mahajjaci, idan ya kasance mai Tamattu'i ne ko mai ƙirani - kuma bai zama daga mazauna masallaci mai alfarma ba, jinin shi ne: Akuya, ko ɗaya bisa bakwai na taguwa ko ɗaya bisa bakwai na saniya, kuma hakan yana wajaba ya zama daga dukiyar halal da nema na halal; domin cewa Allah - Maɗaukakin sarki - tsarkakakke ne ba ya karɓa sai mai tsarki.

Kuma yana kamata ga musulmi ya kame daga roƙon mutane hadaya ko waninsa, daidai ne sun kasance sarakuna ne ko wasunsu, idan Allah Ya yassare masa abinda zai yi wa kansa hadaya da shi daga dukiyarsa, kuma ya wadace shi daga abinda ke hannun mutane; saboda abinda ya zo a cikin hadisai masu yawa daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a kan zargin roƙo da aibinsa, da kuma yabon wanda ya bar shi.

Idan mai Tamattu'i da mai ƙirani suka kasa yin hadaya, to ya wajaba a kansa ya yi azumin kwana uku a cikin Hajji da kuma kwana bakwai idan ya koma ga iyalansa, kuma an ba shi zaɓi a kan azumtar kwana uku, idan ya so ya azimcesu kafin ranar babbar sallah, idan kuma ya so ya azimce su a cikin kwanukan Tshriƙi uku, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Wanda ya ji dãdi da umra zuwa haji, sai ya biya abin da ya sauƙaƙa daga hadaya, sa'an nan wanda bai sãmu ba, sai azumin yini uku a cikin haji da bakwai idan kun kõma, waɗancan gõma ne cikakku. Wancan yana ga wanda iyãlinsa ba su kasance mazaunan Masallãci Tsararre ba} ([102]). [al-Baƙara: 196]. Karanta har ƙarshen ayar.

A cikin Sahihul Bukhari, daga Nana A'isha da Ibnu Umar - Allah Ya yarda da su - sun ce: «Ba'ayi rangwami ayi azimi a kwanukan Tashriƙ ba, sai dai ga wanda bai samu hadaya ba (121)», Wannan yana cikin hukuncin hadisi Marfu'i zuwa ga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, amma abinda yafi ya gabatar da azumin kwanuka ukun akan ranar Arfa, don a ranar Arfa ya zama bakinsa a buɗe yake; domin cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya tsaya a ranar Arfa alhali yana mai buɗe baki, kuma ya yi hanin azimtar ranar Arfa ga wanda yake a Arfa, kuma domin cewa buɗe baki a wannan ranar yafi nishaɗantarwa gareshi ga zikiri da kuma addu'a. Yana halatta a azimci kwanuka ukun da aka ambata a jere ko a rarrabe, haka nan azimin kwanuka bakwan jerantawa a cikinsu baya wajaba, bari dai yana halatta a azimcesu a tare ko a rarrabe; domin cewa Allah - tsarki ya tabbatar maSa - bai sharɗanta jerantawa a cikinsu ba, haka nan manzonSa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, abinda yafi, jinkirta azumin kwanuka bakwan har sai ya koma ga iyalansa; saboda faɗinSa - Maɗaukakin Sarki -: {Da (kwanuka) bakwai idan kun koma} ([122]) [al-Baƙara: 196]. [91] Bukhari ne ya ruwaito shi, a lamba ta (1998).

Azimi ga wanda ya kasa hadaya, yafi roƙon sarakuna da wasunsu hadayar da zai yankawa kansa, wanda aka bawa hadaya ko waninta ba tare da roƙo ba, ba kuma tare da nuna kai ba, to babu laifi da shi, ko da mai yiwa waninsa Hajji ne, wato: Idan waɗanda ya ke yiwa basu sharɗanta masa siyan hadaya daga kuɗin da suka bashi ba. Amma abinda wasu daga cikin mutane suke yi na roƙon gwamnati ko waninta wani abu na hadaya, da sunan wasu mutanen da zai ambace su alhali shi maƙaryaci ne, to wannan babu kokwanto a haramcinsa; domin cewa shi yana daga cikin ci da ƙarya, Allah Ya kare mu da musulmai daga hakan.

FASALI

A kan wajabcin horo da aikin alheri akan mahajjata da wasunsu

Daga cikin mafi girman abinda yake wajaba akan mahajjata da wasunsu, horo da aikin alheri da kuma hani daga abin ƙi, da kuma kiyayewa akan salloli biyar a cikin jam’i, kamar yadda Allah Ya yi umrani da hakan a cikin LittafinSa, da kuma harshen AnnabinSa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -.

Amma abinda mafi yawancin mutane suke aikatawa daga mazauna Makka da baki na yin sallah a cikin gidaje da barin masallatai, to wannan kuskure ne ya saɓa wa shari'a, dan haka ya wajaba a hanu daga gare shi, da umartar mutane da kiyaye sallah a cikin masallatai; saboda abinda ya tabbata daga gare shi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - cewa shi ya cewa Ibnu Ummu Maktum - Allah Ya yarda ad shi - lokacin da ya nemi izininsa akan ya yi sallah a gidansa; saboda kasancewarsa makaho kuma gidansa nesa yake da masallaci: «Shin kana jin kiran sallah? ya ce: Eh, ya ce: To ka amsa ([123])», A cikin wata riwayar: «Bazan iya sama maka rangwami ba ([124])». Annabi- tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Haƙiƙa nayi niyyar inyi umarni da yin sallah, sai ayi iƙamar sallar, sannan in umarci wani mutumin sai yayiwa mutane limanci, sannan in tafi zuwa ga wasu mutanen da basa halartar sallah, in ƙona musu gidajensu da wuta ([125)». A cikin Sunan na Ibnu Majah da waninsa da kyakkywan Isnadi, daga Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su -, cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: «Duk wanda ya ji kiran amma bai zo mata ba, to bashi da sallah sai da uzuri ([126])», a cikin Sahihu Muslim, daga Ibnu Mas'ud - Allah Ya yarda da shi - ya ce: "Duk wanda yake so ya gamu da Allah gobe (alƙiyama) yana musulmi, to ya kiyaye waɗannan sallolin a duk inda aka kira su, domin Allah Ya shara'antawa Annabinku sunnonin shiriya, kuma lallai su suna daga cikin sunnonion shiriya, da ace za kuyi sallah a cikin gidajenku, kamar yanda wannan mai saɓawar yake yin sallah a cikin gidansa, to da kun bar sunnar Annabinku, da kuma kun bar sunnar Annabinku, to da kun ɓata. Babu wani mutumin da zaiyi tsarki sai ya kyautata tsarkin, sannan ya nufi wani masallaci daga cikin waɗannan masallatan, face Allah Ya rubuta masa kyakkyawan lada da dukkanin wani takun da ya taka, kuma Allah zai ɗaukaka masa daraja da ita, kuma Ya sarayar masa da mummuna da ita. Haƙiƙa na ganmu babu wanda yake ƙin halartarta sai munafiki, wanda aka san shi da munafunci, kuma haƙiƙa mutum ya kasance ana zuwa da shi, ana kakkamoshi tsakanin mutum biyu har sai an tsaida shi a cikin sawu" ([127]. [92] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (2420), da Muslim, a lamba ta (651). [93] Muslim ne ya rawaito shi daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi -, a lamba ta (653). [94] Abu Dawud ne ya rawaito shi daga Abdullahi bn Ummu Maktum, a lamba ta (552). [95] Muslim ne ya ruwaito shi, a lamba ta (654). [96] Abu Dawud ne ya rawaito shi daga Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su -, a lamba (551).

Kuma yana wajaba akan mahajjata da wasunsu, su nisanci abubuwan da Allah - Maɗaukakin sarki - Ya haramta, da kiyaye aikata su; kamar zina da luwaɗi, da sata, da cin riba, da cin dukiyar maraya, da algus a cikin mu'amaloli, da ha'intar amanoni, da shan kayan maye, da shan taba, da sakin tufafi har ƙasa, da girman kai, da hassada, da riya, da giba (yi da wani), da annamimanci, da yiwa musulmai izgili, da amfani da kayan kaɗe-kaɗe; kamar kasakasan garaya, da goge, da molaye, da garayu, da makamantansu, da kuma jin waƙe-waƙen garayu, da kayayyakin shagalta na radio da waninta, da wasa da ludo da darar shanu, da yin caca, da zana hotunan 'yan Adam masu rai da wasunsu, da kuma yarda da hakan. Domin lallai dukkan waɗannan suna daga cikin abubuwan ƙi, waɗanda Allah Ya haramta su akan bayinSa a cikin kowane zamani da wuri, to yana wajaba mahajjata su kiyayesu, kuma mazauna Ɗakin Allah mai alfarma sune mafi yawa (a kiyayewa) daga wasunsu; domin cewa saɓo a wannan garin amintacce laifinsa shine mafi tsanani kuma ukubarsa itace mafi girma.

Haƙiƙa Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma wanda ya yi nufin karkatar da gaskiya a cikinsa da zãlunci zã Mu ɗanɗana masa daga wata azãba mai raɗadi} ([128]) [al-Hajj: 25]. Idan Allah Ya kasance haƙiƙa Ya yi alƙawarin narko ga wanda ya yi nufin yin wata fanɗara a cikin harami da wani zalinci, to yaya uƙubar wanda ya aikata? babu kokwanto cewa, ita ce mafi girma kuma mafi tsanani, dan haka kiyayewa yana wajaba akan haka da ma sauran saɓo.

Kuma Hajji kuɓutacce da gafarta zunubai ba sa samuwa sai da kiyayewa daga waɗannan saɓon da wasunsu cikin abinda Allah Ya haramta musu, kamar yadda yake a cikin hadisi daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - cewa shi ya ce: «Wanda ya yi Hajji bai yi jima'i ba, kuma bai yi fasiƙanci ba, zai dawo kamar ranar da mahaifiyarsa ta haife shi ([129])». [97] Bukhari ne ya rawaito shi, daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi -, a lamba ta (1521), da Muslim, a lamba ta (1350).

Kuma mafi tsanani daga waɗannan munanan ayyyukan kuma mafi girma daga garesu: Kiran matattu, da neman agajinsu, da yin bakance saboda su, da yanka saboda su; dan kwaɗayin su ceci mai kiransu a wurin Allah, ko su warkar masa da mara lafiyansa, ko su dawo masa da wanda ya ɓata da wanin haka.

Wannan yana daga cikin babbar shirka, wacce Allah Ya haramtata, kuma hakan addinin mushrikan Jahiliyya ne, kuma Allah Ya aiko da manzanni, kuma Ya saukar da littattafai dan yin inkarinsa da kuma hani daga gare shi.

To yana wajaba akan kowane mutum daga mahajjata da wasunsu ya kiyaye shi, kuma ya tuba zuwa ga Allah daga abinda ya wuce daga hakan, idan ya kasance wani abu ya rigaya daga gare shi, kuma ya sake wani sabon aikin Hajjin bayan ya tuba; domin cewa shirka babba tana ɓata ayyuka gabaɗayansu, kamar yadda Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma dã sun yi shirki dã haƙĩƙa abin da suka kasance sunã, aikatãwa yã lãlãce.} ([130]) [al-An'am: 88].

Yana daga nau’ukan shirka ƙarama: Rantsuwa da wanin Allah; kamar rantsuwa da Annabi da kuma Ka'aba da kuma amana da makamancin hakan.

Yana daga hakan: Riya da jiyarwa, da kuma faɗin: Allah Ya so kaima ka so, da badan Allah da kai ba, wannan daga Allah ne da kai, da makamancin hakan.

To, yana wajaba a kiyaye daga waɗanannan munanan abubuwan na shirka, da kuma yi wa juna wasicci da barinsu; saboda abinda ya tabbata daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - cewa shi yace: «Wanda ya rantse da wanin Allah, to haƙiƙa ya kafirta ko ya yi shirka ([131])» Ahmad ne ya fitar da shi, da Abu Dawud da Tirmizi da kyakkyawan Isnadi. [98] Abu Dawud ne ya rawaito shi, a lamba ta (3251).

Kuma a cikin Sahih daga Umar - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira daa mincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Duk wanda zai rantse, to ya rantse da Allah, ko yayi shiru ([132])», Kuma Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: «Wanda ya rantse da amana, to baya daga cikinmu ([133])», Abu Dawud ne ya fitar da shi. [99] Abu Dawud ne ya rawaito shi, a lamba ta (3253). [100] Bukhari ne ya rawaito shi daga Abdullahi, a lamba ta (2679), da Muslim, a lamba ta (1646).

tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: «Abu mafi tsoratarwa dana ke ji muku tsoro: shi ne ƙaramar shirka, sai aka tambaye shi mece ce ita, sai ya ce: Riya ([134])», Annabi- tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Kada ku ce : Allah Ya so, wane ma ya so, saidai ku ce: Allah ne Ya so, sannan wane ma ya so ([135])», kuma Nasa'i ya fitar, daga Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su - cewa wani mutum ya ce: Ya Manzon Allah, Allah Ya so kuma kaima ka so, sai ya ce: «Shin ka sanyani kishiya ga Allah, a'a, Allah Ya so Shi kaɗai ([136])». [101] Ahmad ne ya ruwaito, a lamba ta (5/428). [102] Abu Dawud ne ya rawaito shi, a lamba ta (4980). [103] Ibnu Majah ne ya rawaito shi, a lamba ta (2117).

Waɗannan hadisan, suna nuni akan kariyar da Annabi - tsira da amincin Allah su tabbara agare shi - ya bayar a abinda ya shafi tauhidi, da kuma gargaɗar al'ummarsa daga shirka babba da ƙarama , da kuma kwaɗayinsa akan tsaftar imaninsu, da kuma tsirarsu daga azabar Allah da kuma sabubban fushinSa, Allah Ya yi masa mafificin sakamako, haƙiƙa ya isar ya yi gargaɗi, ya yi wa Allah nasiha da kuma bayinSa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - salati da aminci madawwama har zuwa ranar sakamako.

Wajibi akan ma'abota ilimi daga mahajjata, da mazauna garin Allah amintacce da birnin ManzonSa mai girma - tsira da aminci su tabbata a gare shi - shine su sanar da mutane abinda Allah Ya shara'anta musu, kuma su gargaɗar da su abinda Ya haramta musu, na nau'ikan shirka da saɓo, kuma su shimfiɗa hakan da hujjoji, su bayyana shi bayani mai warkarwa; don su fitar da mutane da hakan daga duffan zalinci zuwa haske, kuma da haka ne za su bada abinda Allah Ya wajabta a kansu na isarwa da kuma bayani. Allah - tsarki ya tabbatar maSa - Ya ce: {Kuma ka tuna lokacin da Allah Ya yi alƙawari da waɗanda aka baiwa littafi cewa zaku bayyana shi ga mutane, kuma ba zaku ɓoye shi ba.} ([137]) [Āli- Imran: 187].

Abin nufi daga haka: Malamai su gargaɗi wannan al'ummar daga shiga mashigar azzalumai daga mazowa littafi (Yahudu da Nasara) a cikin ɓoye gaskiya; don zaɓin duniya akan lahira, alhali haƙiƙa Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya ce: {Lalle ne waɗanda suke ɓõyẽwar abin da Allah Ya saukar da ga hujjõji bayyanannu, da shiriya, daga bãyan Mun bayyana shi ga mutãne, a cikin Littãfi (Alƙur'ãni), waɗannan Allah Yana la'anar su, kuma mãsu la'ana suna la'anar su}. {Sai waɗanda suka tũba, kuma suka gyãra, kuma suka bayyana, to waɗannan Ina karɓar tũba a kansu kuma Nĩ ne Mai karɓar tũba, Mai jin ƙai }([138]) [al-Baƙara: 159-160]. Haƙiƙa ayoyin Alƙur'ani da hadisan Annabi sunyi nuni akan cewa: kira zuwa ga Allah - tsarki ya tabbatar maSa - da shiryar da bayi ga abinda aka halicce su saboda shi, to yana daga mafifitan ayyukan kusanci, kuma mafi muhimmancin wajibai, kuma cewa sune hanyar manzanni da mabiyansu har zuwa ranar alƙiyama, kamar yanda Allah - tsarki ya tabbatar maSa - Ya ce: {Kuma wãne ne mafi kyau ga magana daga wanda ya yi kira zuwa ga Allah, kuma ya aikata aiki na ƙwarai, kuma ya ce: "Lalle nĩinã daga mãsu sallamãwar al'amari zuwa ga Allah?} ([139]), [Fussilat: 33]. Fadin Allah maigirma da Daukaka: {Ka ce: "Wannan ce hanyãta; inã kira zuwa ga Allah a kan basĩra, nĩ da waɗanda suka bĩ ni, kuma tsarki ya tabbata ga Allah! Nĩ kuma, ban zama daga mãsu shirki ba.} ([140]) [Yusuf: 108].

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Duk wanda ya shiryar akan wani aikin alheri, to, yana da kwatankwacin ladan wanda ya aikata shi ([141)» «Allah Ya shiryar da mutum ɗaya saboda kai, shine mafi alheri gareka daga jajayen raƙuma ([142])». Ayoyi da hadisai da suka zo da wannan ma’anar suna da yawa. [104] Muslim ne ya ruwaito, a lamba ta (1893). [105] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (3009), da Muslim, a lamba ta (2406).

To, ya cancanta ga ma'abota ilimi da imani, su ninka ƙoƙarinsu a cikin kira zuwa ga Allah - tsarki ya tabbatar maSa -, da shiryar da bayi zuwa dalilan tsira, da gargaɗar da su daga dalilan halaka, musammanma dai a cikin wannan zamanin wanda soye-soyen rayuka suka rinjaye shi, mafarar abubuwa masu rusawa da alamomi masu ɓatarwa suka yaɗu a cikinsa, masu kira zuwa ga shiriya sun ƙaranta, kuma masu kira zuwa ga ilhadi da 'yan ibahiyya (halatta abubuwan da aka haramta) sun yawaita, Allah ne abin neman taimako, babu dabara babu ƙarfi sai da (taimakon) Allah Maɗaukaki Mai girma.

FASALI

A cikin son guzuri daga ayyukan biyayya

An so mahajjata su lazimci ambaton Allah, da yi maSa ɗa'a, da aiki na gari, tsawon zamansu a Makka, su yawaita sallah da ɗawafi a Ɗaki; domin cewa kyawawan ayyuka a cikin harami ana ninka su, munana kuma a cikinsa masu girma ne masu tsanani, kamar yanda aka so a yawaita salati da sallama ga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -.

Idan mahajjata sukayi nufin fita daga Makka, to ya wajaba a kansu suyi ɗawafin bankwana a Ɗaki; don ƙarshen alƙawarinsu ya zama Ɗaki ne, sai dai mai haila ko mai nifasi (jinin biƙi), to babu bankwana a kansu; saboda hadisin Ibnu Abbas - Allah Ya yarda da su - ya ce: «An umarci mutane da su sanya ƙarshen alƙawrinsu shine Ɗakin, sai dai anyi sauƙi ga mace mai haila ([143])» [106] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (1755), da Muslim a lamba ta (1328).

Idan ya gama yiwa Ɗaki bankwana kuma ya so fita daga masallaci, ya zarce ta gabansa har sai ya fita, kuma baya kamata gare shi, ya tafi ta baya (rubos); domin cewa hakan ba'a cirato daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ba ko daga sahabbansa, kai shi yana daga cikin bidi'o'in da aka farar da su, alhali haƙiƙa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Duk wanda ya yi wani aiki wanda babu umarninmu a cikinsa, to wannan aikin abun mayarwa ne ([144])». Annabi- tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Na haneku da fararrun abubuwa, saboda kowane fararren abu bidi'a ne, kuma kowace bidi'a ɓata ce ([145])» [107] Fitar da shi ya gabata. [108] Muslim ne ya fitar da shi, daga Jabir bn Abdullahi - Allah Ya yarda da shi, a lamba ta (867).

Muna roƙon Allah tabbata akan AddininSa, da kuɓuta daga abinda ya saɓa masa, lallai cewa Shi Mai yawan kyauta ne Mai karamci.

FASALI

A cikin hukunce-hukuncen ziyara da ladubbanta

An sunnanta ziyarar masallacin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - kafin Hajji ko bayansa; saboda abinda ya tabbata a cikin Sahihain (Bukhari da Muslim) daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Sallah a cikin masallacina wannan (ita ce) mafi alheri daga sallah dubu a cikin waninsa, sai dai masallaci mai alfarma ([146])» Daga ibn Umar - Allah Ya yarda da su - cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Sallah a cikin masallacina wannan (ita ce) mafi alheri, daga sallah dubu a cikin waninsa, sai dai masallaci mai alfarma ([147])» Muslim ne ya rawaito shi. Daga Abdullahi ɗan Zubair - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Sallah a cikin masallaci na wannan yafi daga sallah dubu a cikin wanda bashi ba, sai dai masallaci mai alfarma, kuma sallah a cikin masallaci mai alfarma, tafi salloli ɗari a cikin masallaci na wannan ([148])». Ahmad ne ya fitar da shi, da Ibnu Khuzaimah, da Ibnu Hibban. [109] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (1190), da Muslim, a lamba ta (1394). [110] Muslim ne ya ruwaito, a lamba ta (1395). [111] Ahmad ne ya ruwaito, a lamba (4/5).

Daga Jabir - Allah Ya yarda da shi - cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Sallah ɗaya a cikin masallaci na wannan, tafi sallah dubu a waninsa, sai dai masallacin harami, kuma sallah a cikin masallacin harami tafi sallah dubu ɗari a waninsa ([149])» Ahmad ne ya fitar da shi, da Ibnu Majah, kuma hadisan da sukazo da wannan ma'anar suna da yawa. [112] Ibnu Majah ne ya rawaito shi, a lamba ta (1406).

Idan mai ziyara ya isa masallaci, an so ya gabatar da ƙafarsa ta dama a lokacin shiga, kuma ya ce: «Da sunan Allah, tsira da aminci su tabbata ga Manzon Allah, ina neman tsarin Allah Mai girma da fuskarSa mai girma da sarautarSa daɗaɗɗiya daga Shaiɗan abin jefewa, Ya Allah, Ka buɗe mini ƙofofin rahamarKa»

Kamar yanda zai faɗa a yayin shigarsa ragowar masallatai, kuma babu wani keɓantaccen zikiri dan shiga masallacinsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, sannan yayi sallah raka'a biyu, sai ya roƙi Allah abinda ya so na alherin duniya da lahira a cikinsu. Idan ya sallace su a cikin raudah maɗaukakiya to shi yafi; saboda faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: «Tsakanin gida na da munbari na, dausayi ne daga cikin dausayan aljanna ([150])». Sannan bayan sallah, ya ziyarci ƙabarin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, da ƙabarirrikan sahabbansa biyu: Abubakar da Umar - Allah Ya yarda da su -, sai ya tsaya fuskar ƙabarin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - da ladabi da ƙasa-ƙasa da murya, sannan yayi masa sallama - tsira da aminci su tabbata a gare shi - yana mai cewa: "Aminci ya tabbata a gareka ya Manzon Allah da rahamar Allah da albarkarSa"; saboda abinda yake cikin Sunan Abu Dawud da kyakkyawan Isnadi, daga Abu Hurairah - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Babu wani mutum da zai yi mini sallama, har sai Allah Ya dawo mini da raina har sai na mayar masa da sallamar (151)». Idan mai ziyarar yace a ciki sallamarsa: "Aminci ya tabbata a gare ka ya Annabin Allah, aminci ya tabbata a gareka ya zaɓin Allah daga halittarSa, aminci ya tabbata a gareka ya shugaban manzanni kuma jagoran masu tsoron Allah, ina shaida cewa haƙiƙa ka isar da saƙo ka bada amana, ka yiwa al'umma nasiha, ka yi yaƙi saboda Allah haƙiƙanin yaƙi", to babu laifi da hakan; domin cewa wannan gabaɗayansa yana daga cikin siffofin sa - tsira da amincin Allah su tabbaba a gare shi -. Ya yi kuma salati a gare shi - tsira da amincin su tabbata agare shi - ya yi masa addu'a; saboda abinda ya tabbata a cikin shari'a daga halaccin haɗawa tsakanin salati da sallama agare shi; don yin aiki da faɗinSa - Maɗaukakin Sarki -: {Lalle, Allah da malã'ikunSa sunã salati ga Annabi. Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku yi salãti a gare shi, kuma ku yi sallama dõmin amintarwa a gare shi.} ([152]) [al-Ahzab: 56]. Sannan ya yi sallama ga Abubakar da Umar - Allah Ya yarda da su -, ya yi musu addu'a, ya nema musu yardar Allah. [113] Bukhari ne ya rawaito shi daga Abdullahi bn Zaid al-Mazini, a lamba ta (1195), da Muslim, a lamba ta (1390). [114] Abu Dawud ne ya rawaito shi, a lamba ta (2041).

Ibnu Umar - Allah Ya yarda da su - ya kasance idan zai yi sallama ga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - da sahabbansa biyu, galibi baya ƙarawa akan faɗinsa: "Aminci ya tabbata a gareka ya Manzon Allah, aminci ya tabbata a gareka ya Abukar, aminci ya tabbata agareka ya babana" Sannan ya juya.

Wannan ziyarar an shara'antata ne kawai a haƙƙin maza a keɓance, amma mata ba'a shara'anta musu ziyarar wani abu daga ƙaburbura ba, kamar yanda ya tabbata daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - cewa shi «Ya la'anci mata masu yawan ziyarar ƙaburbura da masu mariƙon su masallatai da fitilu ([153])». [115] Abu Dawud ne ya rawaito shi, a lamba ta (3236).

Amma nufin Madina don yin sallah a cikin masallacin Manzo - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, da kuma addu'a a cikinsa, da makamancin haka daga abinda aka shara'anta a cikin ragowar masallatai, to an halatta shi a haƙƙin kowa da kowa; saboda abinda ya gabata na hadisai a cikin hakan.

Kuma an sunnatawa mai ziyara, yayi salloli biyar a cikin masallacin Manzo - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, kuma ya yawaita zikiri da addu'a da sallar nafila a cikinsa; don cin ribar abinda ke cikin hakan na gwaggwaɓan lada.

An so ya yawaita sallar nafila a cikin Raudah maɗaukakiya; saboda abinda ya gabata na ingantaccen hadisi a cikin falalarta, shine faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: «Tsakanin gidana da mumbari na, dausayi ne daga cikin dausayan aljanna ([154])». [116] Fitar da shi ya gabata.

Amma sallar farilla, to yana kamata ga mai ziyara da waninsa, ya gabato gare su, kuma ya kiyaye akan halartar sawun farko gwargwadan iko, duk da ya kasance akwai ƙarin lada a sawun gaba; saboda abinda ya zo a cikin ingantattun hadisai daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - na kwaɗaitarwa da zaburarwa a cikin sawun farko, misalin faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: «Da mutane sun san abin da ke cikin kiran sallah da sahun farko, sannan ba za su samu ba sai sun yi ƙuri'a a kan sa; to, da sunyi ƙuri'ar». Bukhari Da Muslim suka rawaito shi. Da misalin faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ga sahabbansa: «Ku gabato, kuyi koyi da ni kuma waɗanda ke bayanku suyi koyi da ku, mutum ba zai gushe ba yana jinkirin sallah, har sai Allah ya jinkirtar da shi ([156])». Muslim ne ya fitar da shi. [117] Muslim ne ya ruwaito daga Abu Sa'id al-Kudri - Allah Ya yarda da shi -, a lamba ta (438). [118] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (615), da Muslim, a lamba ta (437).

Kuma Abu Dawud ya fitar daga A'isha - Allah Ya yarda da ita - da sanadi mai kyau, cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Mutum bazai gushe ba, yana jinikiri daga sawu na gaba, har sai Allah Ya jinkirta shi a cikin wuta ([157])», kuma ya tabbata daga gare shi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - cewa shi ya faɗawa sahabbansa: «Shin bakwayi sawu ba kamar yanda mala'iku sukeyin sawu a wajen Ubangijinsu ba!? Suka ce: Ya Manzon Allah, yaya mala'iku sukeyin sawu a gaban Ubangjinsu!? Ya ce: Suna cika sawun farko, kuma suna kafuwa a cikin sawun ([158])» Muslim ne ya ruwaito shi. [119] Muslim ne ya ruwaito daga Jabir bn Samura, a lamba ta (430). [120] Abu Dawud ne ya rawaito shi a lamba ta (679) kuma lafazinsa: "wasu mutane ba zasu gushe ba suna jinkirtuwa daga sawun farko har sai Allah Ya jinkirta su a cikin wuta".

Hadisai a cikin wannan ma'anar suna da yawa, kuma su sun game masallacinsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - da waninsa kafin ƙari da bayansa, haƙiƙa ya inganta daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - cewa shi ya kasance yana kwaɗaitar da sahabbansa akan sawun dama, kuma abin sani cewa sawun dama a cikin masallacinsa na farko a wajen Raudah yake, sai aka sani da hakan cewa kulawa da sawun farko da na dama abin gabatarwa ne akan kulawa da Raudah maɗaukakiya, kuma kiyayewa a kansu shi yafi daga kiyayewa akan yin sallah a Raudah. Wannan a bayyane yake ga wanda ya lura da hadisan da suka zo a cikin wannan babin, Allah ne Mai datarwa.

Baya halatta ga wani ya shafi ɗaki, ko ya sumbaceshi, ko yayi masa ɗawafi; domin cewa hakan ba'a cirato daga magabata na gari ba, kai shi bidi'a ne ma abin ƙi.

Kuma baya halatta ga wani ya tambayi Manzo - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - biyan buƙata, ko yaye baƙin ciki, ko warkar da mara lafiya, ko makamancin haka; domin hakan gabaɗayansa ba'a nema sai ga Allah - tsarki ya tabbatar maSa -, kuma nemansa daga matattu shirka ne kuma bautar wanin Allah ne, kuma Addinin musulunci an gina shi ne akan asali biyu:

Ɗaya daga cikin su: Kada a bauta wa kowa sai Allah Shi kaɗai.

Na biyu: Kada ayi bauta sai da abinda Manzo - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya shara'anta shi.

Wannan shine ma'anar shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma cewa (Annabi) Muhammad Manzon Allah ne.

Haka nan baya halatta ga wani ya nemi ceto daga Manzo - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - domin cewa shi (ceton) mallakin Allah ne, saboda haka ba'a nemansa sai daga gareShi, kamar yanda - Maɗaukakin Sarki - Ya ce: {Ka ce: "Cẽto gabã ɗaya ga Allah yake} ([159]) [Al-zumar: 44]. Sai kace: "Ya Allah Ka bawa Annabinka ceto na, Ya Allah Ka bawa mala'ikunKa ceto na, da bayinKa muminai, Ya Allah Ka bawa mmagatana ceto na", da makamancin haka. Amma matattu ba'a neman komai daga gare su, ba'a neman ceto ko waninsa, daidai ne sun kasance Annabawa ne ko wasun annabawa; domin cewa hakan ba'a shara'anta shi ba, kuma domin cewa mamaci aikinsa ya yanke sai dai abinda mai shara'antawa ya toge shi.

Ya zo a cikin Sahihin Muslim daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - daga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Idan mutum ya mutu aikin sa ya yanke, sai dai daga abu uku: Sadaka mai gudana, ko wani ilimi da ake anfanuwa da shi, ko ɗa na gari da ya ke masa addu'a ([160])». [121] Muslim ne ya rawaito shi daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi -, a lamba ta (1631).

Kaɗai neman ceto yana halatta ne daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - a cikin rayuwarsa da ranar alƙiyama, saboda ikonsa akan haka, domin shi zai iya gabatowa ya roƙawa mai nema Ubangijinsa, amma a duniya to sanannen abu ne, hakan bai keɓance shi ba, kai mai gamewa ne gare shi da waninsa, dan haka yana halatta ga musulmi ya cewa ɗan'uwansa: Ka nemawa Ubangijina cetona a abu kaza da abu kaza, da ma'anar: Ka roƙa mini Allah ga wanda ake faɗawa haka ya roƙi Allah ya nemawa ɗan'uwansa ceto idan abin neman yana daga abinda Allah Ya halatta neman sa ne.

Amma a ranar alƙiyama, to wani ba zaiyi ceto ba, sai bayan Allah - tsarki ya tabbatar maSa - Yayi masa izini, kamar yanda Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Wane ne wanda yake yin cẽto a wurinSa, fãce da izninSa?} ([161]) [al-Baƙara: 255].

Amma halin mutuwa, to hali ne keɓantacce, riskar da shi baya halatta da halin mutum, kafin mutuwa ko da halinsa, bayan tashin alƙiyama da taruwa, don yankewar aikin mamaci da kuma jinginar da shi da aikinsa, sai dai abinda mai shara'antawa ya togance shi, kuma neman ceto daga matattu bai zama daga abinda mai shara'a ya togance shi ba, don haka baya halatta a riskar da shi da hakan. Babu kokwanto cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - bayan wafatinsa rayayye ne irin rayuwar barzahu mafi cika daga rayuwar shahidai, sai dai cewa ita bata daga cikin jinsin rayuwarsa kafin mutuwa, ko jinsin rayuwarsa a ranar alƙiyama, kai wata rayuwa ce babu wanda yasan haƙiƙaninta da yanayinta sai Allah - tsarki ya tabbatar maSa -, saboda haka ne faɗinsa ya gabata a cikin hadisi Maɗaukaki - tsira da aminci su tabbata a gare shi -: «Babu wani mutum da zai yi mini sallama, face Allah Ya dawo mini da raina har sai na mayar masa da sallamar ([162])».

Sai hakan yayi nuni akan cewa shi mamaci ne, kuma cewa ransa ya rabu da jikinsa, sai dai cewa shi yana dawo masa a lokacin sallama, kuma nassosin da suka yi nuni akan mutuwarsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - daga Alƙur'ani da sunnah sanannu ne, kuma shi wani al'amari ne wanda aka haɗu a kansa tsakanin ma'abota ilimi. Sai dai cewa hakan baya hana rayuwarsa ta barzahu, kamar yanda cewa mutuwar shahidai bata hana rayuwarsu ta barzahu, wacce aka ambata a cikin faɗinSa - Maɗaukakin Sarki -: {Kada ka yi zaton waɗanda aka kashe a cikin hanyar Allah matattu ne. A'a, rãyayyu ne su, a wurin Ubangijinsu. Ana ciyar da su.} ([163]) [Āli- Imran: 169]. [122] Abu Dawud ne ya rawaito shi, a lamba ta (2041).

Kaɗai mun yawaita magana ne a cikin wannan mas'alar, don buƙatuwa zuwa gareta, saboda yawan wanda yake rikicewa a cikin wanna babin, yana kira zuwa ga shirka da bautar mamata koma bayan Allah. Muna roƙa mana Allah mu da dukkanin musulmaix, kuɓuta daga dukkan abinda yake saɓawa shari'arSa, Allah ne Mafi sani.

Amma abinda wasu daga cikin masu ziyara suke aikatawa, na ɗaga murya a ƙabarinsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, da tsawaita tsayuwa a nan, to shi ya saɓawa shari'a; domin cewa Allah - tsarki ya tabbatar maSa - Ya hana al'umma ɗaga muryoyinsu sama da muryar Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, da kuma bayyanawa gare shi da magana, kamar yanda sashinsu ke bayyanawa sashi, da kuma kwaɗaitar da su akan ƙanƙar da sauti a wurinsa a cikin faɗinSa - Maɗaukakin Sarki -: Yã kũ waɗanda suka yi ĩmani! Kada ku ɗaukaka saututtukanku bisa sautin Annabi, kuma kada ku bayyana sauti gare shi a magana, kamar bayyanãwar sãshenku ga sãshe, dõmin kada ayyukanku su ɓãci, alhãli kuwa kũ ba ku sani ba. {Lalle waɗanda ke runtsẽwar saututtukansu a wurin Manzon Allah waɗannan ne waɗanda Allah Yã, jarrabi zukãtansu ga taƙawa. Sunã da wata irin gãfara da ijãra mai girma.} ([164]) [al-Hujurat: 2-3].

Kuma domin cewa tsawaita tsayuwa a ƙabarin sa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, da yawaita yi masa sallama, yana sa cunkoso da yawan hayaniya da ɗaga muryoyi a ƙabarin sa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, to hakan ya saɓawa abinda Allah Ya shara'antawa musulmai shi a cikin waɗananan ayoyin masu kyawun ma'anoni, kuma shi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - abin girmamawa ne halin kasancewarsa a raye ko a mace, dan haka baya kamatuwa ga mumini ya aikata abinda ya saɓawa ladabin shari'a a ƙabarin sa.

Haka nan abinda wasu daga masu ziyara da wasunsu suke aikatawa na kintatar addu'a a ƙabarinsa, yana mai fuskantar ƙabari yana mai ɗaga hannaensa yana yin addu'a, to dukkanin wannan ya saɓawa abinda magabata na ƙwarai suke a kansa daga sahabban manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - da masu binsu da kyautatawa, kai shi yana daga bidi'o'in da aka farar, kuma haƙiƙa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Na hore ku da sunnata da kuma sunnar halifofi shiryayyu a bayana, kuyi riƙo da ita, kuma ku riƙeta da fiƙoƙinku, kuma na haneku da fararrun abubuwa; saboda kowane fararren abu bidi'a ne; kuma kowace bidi'a ɓata ce ([165])». [123] Abu Dawud ne ya rawaito shi, daga hadisin Irbad bn Sariyah, a lamba ta (4607).

Annabi- tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Duk wanda ya farar da wani sabon abu a cikin wannan Addinin namu wanda ba ya ciki, to shi abun juyarwa ne ([166])». «Duk wanda ya yi wani aiki wanda babu umarninmu a cikinsa to wannan aikin abun juyarwa ne ([167])». [124] Fitar da shi ya gabata. [125] Fitar da shi ya gabata.

Kuma Aliyu ɗan Husain Zainul abidin - Allah Ya yarda da shi - ya ga wani mutum yana addu'a a ƙabarin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, sai ya haneshi daga hakan, kuma ya ce: Shin bana zantar da kai wani hadisin da na ji shi daga babana ba, daga kakana, daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - cewa shi ya ce: «Kada ku riƙi ƙabarina a matsayin idi, haka kuma gidajenku su zama ƙaburbura ba, kuyi mini salati, domin sallamarku tana isar mini a duk inda kuke ([168])» [126] Riwayar Zainul abidin, al-Sheikh al-Hafiz al-Maƙdasi ya danganta ta kuma ya fitar da hadisin ba tare da ƙissar ba, da Ahmad a cikin al-Musnad (2/367).

Haka nan abinda wasu daga masu ziyara suke aikata shi a lokacin yi masa sallama - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, na ɗora hannun damansa akan na hagunsa a saman ƙirji ko ƙarƙashinsa, kamar siffar mai yin sallah, to wannan siffar bata halatta a lokacin yin sallama gare shi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, ko yayin sallama ga waninsa daga sarakuna da shugabanni da wasunsu; domin cewa ita siffa ce ta ƙasƙanci da ƙanƙanr da kai da ibadar da bata halatta sai ga Allah, kamar yanda al-Hafiz Ibnu Hajar - Allah Yayi masa rahama - ya hakaito a cikin al-Fathu daga malamai, kuma al'amarin a cikin hakan a bayyane yake ga wanda ya lura da matsayin kuma hadafinsa ya zama bin shiriyar magabata na ƙwarai.

Amma wanda ta'assubanci da son rai da makauniyar biyayya suka rinjaye shi, da kuma mummunan zato ga masu kira zuwa ga shiriyar magabata na ƙwarai, to al'amarinsa yana ga Allah, muna roƙon Allah shiriya ga mu da shi da dacewa don fifita gaskiya akan waninta, lallai cewa Shi - tsarki ya tabbatar maSa - Shine Mafificin abin tambaya.

Haka nan abinda wasu daga cikin mutane suke aikata shi na fuskantar ƙabari maɗaukaki daga nesa da mommotsa leɓɓansa don yin sallama ko addu'a, to dukkanin wannan yana daga jinsin abinda ke kafin shi, na fararrun abubuwa, kuma baya halatta ga musulmi ya farar da abinda Allah baiyi izini da shi a cikin Addininsa ba, kuma shi da wannan aikin yafi kusa da yi masa wauta akan yi masa biyayya da tsarkakewa. Haƙiƙa Imam Malik - Allah Ya yi masa rahama - yayi musun wannan aikin da mai kama da shi, kuma ya ce: "Babu abinda zai gyara ƙarshen wannan al'ummar sai abinda ya gyara farkonta". [126] Igāsatul lahfan fi masāyid Shaiɗān (1/363).

Kuma abin sani cewa, abinda ya gyara farkon wannan al'ummar shine tafiya akan tafarkin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - da halifofinsa shiryayyu da sahabbansa ababen yarda da mabiyansu da kyautatawa, kuma babu abinda zai gyara ƙarshen wannan al'ummar sai riƙonsu da hakan, da kuma tafiyarsu a kansa.

Allah Ya datar da musulmai ga abinda a cikinsa akwai tsiransu, da azirtarsu, da ɗaukakarsu a duniya da lahira, lallai Shi Mai yawan kyauta ne Mai karamci ne.

Fadakarwa

HUKUNCIN ZIYARAR ƘABARIN ANNABI - TSIRA DA AMINCI SU TABBATA A GARE SHI -

Ziyarar ƙabarin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ba wajiba ba ce ba kuma ba sharaɗi ba ce a cikin Hajji, kamar yanda wasu daga gamari da wasunsu suke zato, kai ita mustahabba ce a cikin haƙƙin wanda ya ziyarci masallacin Manzo - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ko ya kasance kusa da shi.

Amma na nesa daga Madina, to baya a kansa ɗaura sirdi don ziyarar ƙabari, sai dai an sunnanta masa ɗaura sirdi dan nufin masallaci mai alfarma. Idan mai ziyara ya isa can, to ya ziyarci ƙabari maɗaukaki da ƙabarin sahabbansa biyu, kuma ziyarsa - tsira da aminci su tabbata a gare shi - da ƙabarin sahabbansa ta shiga don bi ga ziyarar masallacinsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, hakan saboda abinda ya tabbata a cikin Sahihain, cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Ba'a ɗaura sirdi, sai zuwa masallatai uku: Masallaci mai alfarma, da wannan masallacin nawa, da msallacin al-Aƙsa ([169])». [128] Bukhari ne ya rawaito shi daga Abu Huraira, a lamba ta (1189), da Muslim, a lamba ta (1397).

Da ce ɗaura sirdi don nufatar ƙabarinsa - tsira da aminci su tabbata a gare shi - ko ƙabarin waninsa ya kasance abin shara'antawa, da ya nunawa al'umma shi, kuma ya shiryar da su ga falalarsa; domin cewa shine mafi nasihar mutane, kuma mafi saninsu ga Allah, kuma mafi tsananinsu tsoro gareShi. Haƙiƙa ya isar isarwa mabayyaniya, kuma ya shiryar da al'ummarsa akan kowane alheri, kuma ya gargaɗar da su daga kowane sharri, ta yaya, kuma haƙiƙa yayi gargaɗi daga ɗaura sirdi ga wanin masallatan nan uku, kuma ya ce: «Kada ku riƙi ƙabarina idi, haka kuma gidaddajinku ƙaburbura, kuyi mini salati, domin cewa salatinku zai isar mini a duk inda kuke ([170)». [129] Fitar da shi ya gabata.

Kuma magana da shara'anta ɗaura sirdi dOn ziyarar ƙabarinsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - yana kaiwa zuwa ga riƙarsa idi, da kuma afkuwar abinda ake gudu wanda Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - yake jin tsoronsa; na wuce gona da iri, kamar yanda mafi yawa daga mutane suka faɗa cikin hakan saboda ƙudircewarsu cewa ɗaura sirdi dOn ziyarar ƙabarinsa - tsira da aminci su tabbata a gare shi - ya halatta.

Amma abinda wanda yake kafa hujja da halaccin ɗaura sirdi zuwa ƙabarinsa - tsira da aminci su tabbata a gare shi - yake ruwaitowa a cikin wannan babin na hadisan da yake kafa hujja da su, to su hadisai ne masu raunin isnadi, kai na ƙarya ne ma, kamar yanda hafizan hadisi suka faɗakar akan rauninsu; kamar al-Daruƙuɗni, da al-Baihaƙi, da al-Hafiz Ibnu Hajar da wasunsu. To baya halatta ya bijirar da su ga hadisai ingantattu masu nuni akan haramcin ɗaura sirdi ga wanin masallatan nan uku.

Ya kai mai karatu ga wani abu daga hadisan na ƙarya a cikin wannan babin; don ka sansu kuma ka kiyaye ruɗuwa da su:

Na farko: «Wanda yayi Hajji bai ziyarce ni ba, to haƙiƙa yayi mini wauta».

Na biyu: «Wanda ya ziyarce ni bayan mutuwata, to kamar ya ziyarceni ne a halin rayuwata».

Na uku: «Wanda ya ziyarce ni kuma ya ziyarci babana Ibrahim a cikin shekara ɗaya zan lamunce masa aljanna ga Allah».

Na huɗu: «Wanda ya ziyarci ƙabarina, to cetona ya wajaba gare shi».

To, waɗannan hadisan da masu kama da su babu wani abu da ya inganta daga garesu daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -.

Al-Hafiz Ibnu Hajar ya faɗa a cikin (al-Talkhis) - bayan ya ambaci mafi yawancin riwayoyin -: Hanyoyin wannan hadisin dukkansu masu rauni ne.

Kuma al-Hafiz al-Uƙaili ya ce: Wani abu baya inaganta a cikin wannan babin.

Kuma Shehul Islam Ibnu Taimiyyah - Allah Yayi masa rahama - ya yi yanke akan cewa waɗannan hadisan dukkansu na ƙarya ne, kuma ya isheka iliminsa da haddarsa da kuma muɗala'arsa.

Da ace wani abu daga garesu ya zama tabbatacce, da sahabbai - Allah Ya yarda da su - sun riga mutane zuwa ga aiki da shi, da kuma yiwa al'umma bayanin hakan da kiransu zuwa gare shi; domin cewa sune mafifitan mutane bayan Annabawa, kuma mafi saninsu da iyakokin Allah da kuma abinda Ya shara'anta shi ga bayinSa, kuma mafi nasiharsu ga Allah da kuma halittarSa, lokacin da ba'a cirato wani abu daga hakan daga garesu ba, sai hakan yayi nuni akan cewa shi ba'a shara'antashi ba.

Kuma da ace wani abu daga cikinsu ya inganta, da ɗaukar hakan akan ziyara ta shari'a, wacce babu ɗaura sirdi don nufin ƙabari shi kaɗai ya wajaba; don haɗawa tsakanin hadisan. Allah - Mai tsarki da ɗaukaka - ne Mafi sani.

FASALI

A CIKIN SON ZIYARTAR MASALLACIN ƘUBA DA BAƘI'A

An so ga mai ziyarar Madina ya ziyarci masallacin ƙuba kuma yayi sallah a cikinsa; saboda abinda ke cikin Sahihain daga Hadisin Ibnu Umar - Allah Ya yarda da su -, ya ce: «Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance yana ziyartar masallacin ƙuba akan abin hawa, haka ma a ƙasa, kuma yana yin sallah a cikinsa raka'a biyu (171)». [130] Bukhari ne ya rawaito shi, a lamba ta (1193), da Muslim, a lamba ta (1399).

Daga Sahlu ɗan Sa'ad - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Duk wanda ya yi tsarki daga gidansa, sannan ya taho masallacin Ƙuba, sai yayi sallah a cikinsa, to yana da ladan Umra ([172])». [131] Ibnu Majah ne ya rawaito shi, a lamba ta (1412).

Kuma an sunnata masa ziyartar ƙaburburan Baƙi'a, da ƙaburburan shahidai, da ƙabarin Hamza - Allah Ya yarda da shi -; domin cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance yana ziyartarsu, kuma yanayi musu addu'a, kuma saboda faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: «Ku ziyarci ƙaburbura domin cewa zasu dinga tuna muku lahira ([173])» Muslim ne ya fitar da shi. [132] Muslim ne ya ruwaito shi, a lamba ta (976).

Annabi - tsira da aminciin Allah su tabbata a gare shi - ya kasance yana koyawa sahabbansa idan sun ziyarci ƙabarurruka (maƙabarta) da su ce: «Amincin Allah ya tabbata a gareku ya ku mazaunan wannan gida na muminai da musulmai, muma in Allah Ya so masu riskuwa ne da ku, muna roƙon Allah rangwame ga mu da ku ([174) Muslim ne ya fitar da shi, daga hadisin Sulaiman ɗan Buraidah daga babansa. [133] Muslim ne ya ruwaito shi, a lamba ta (975).

Kuma Tirmizi ya fitar daga Anas - Allah Ya yarda da su - ya ce: Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya wuce ƙaburburan Madina, sai ya fuskantosu da fuskarsa, sai ya ce: «Aminci ya tabbata a gareku yaku ma'abota ƙaburbura, Allah Ya yi mana gafara mu da ku, kune marigayanmu mu kuma muna nan tafe ([175])». [134] Tirmizi ne ya ruwaito, a lamba ta (1035).

Daga waɗannan hadisan ne ake sanin cewa, ziyara na shari'a ga ƙaburbura, ana nufin tuna lahira daga garesu ne, da kyautatawa mamata, da yi musu addu'a da nema musu rahama.

Amma ziyararsu, da nufin yin addu'a a ƙaburburansu ko lazimta a wurinsu, ko roƙonsu biyan buƙatu, ko warkar da marasa lafiya ko roƙon Allah saboda su, ko saboda alfarmar su da makancin haka, to wannan ziyarar bidi'a ce abar ƙi, Allah ko manzonSa basu shara'antata ba, haka kuma magabata na gari basu aikatata ba - Allah Ya yarda da su -,bari dai ita tana daga mummunan zance da Manzo - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yayi hani daga gare shi, inda ya ce: «Ku ziyarci ƙaburbura, kada ku faɗi mummunan zance ([176])». [135] Muslim ne ya rawaito shi, daga Buraidah daga babansa a lamba ta (977).

Waɗannan al'amurran da aka ambata sun haɗu akan kasancewarsu bidi'a ne, sai dai cewa su sun banbanta a matakai, wasu daga cikinsu bidi'a ne ba shirka ba ne; kamar kiran wanin Allah - tsarki ya tabbatar maSa - a wajen ƙaburbura, da kuma roƙonSa da haƙƙin mamaci da kuma alfarmarsa da makamancin hakan, wasu daga cikinsu kuma babbar shirka ne, kamar kiran matattu da neman agajinsu, da makamancin haka.

Haƙiƙa bayanin wannan ya gabata a rarrabe a cikin abinda ya gabata. Sai ka lura ka kuma kiyaye, ka roƙi Ubangijinka dacewa da shiriya ga gaskiya, domin cewa Shi - tsarki ya tabbatar maSa - Mai datarwa ne kuma Mai shiryarwa ne, babu wani abin bautawa da gaskiya sai Shi, kuma babu wani Ubangiji in ba Shi ba.

Wannan shine ƙarshen abinda mu kayi nufin shifatarsa, godiya ta tabbata ga Allah a farko da ƙarshe, Allah Ya yi daɗin tsira ga bawanSa kuma ManzonSa, kuma abin zaɓinSa daga halittarSa (Annabi) Muhammad da alayensa da sahabbansa, da waɗanda suka bisu da kyautatawa har zuwa ranar sakamako.