رسالتان موجزتان في الزكاة والصيام
TAƘAITATTUN SAƘONNI BIYU A KAN ZAKKA DA AZUMI
TAƘAITATTUN SAƘONNI BIYU A KAN ZAKKA DA AZUMI
Shehin Malami
AbdulAzeez Bn Abdullahi Bn Baaz
Allah - Maɗaukakin sarki - Ya yi masa rahama.
SAƘO NA FARKO
A kan wasu bincike-bincike masu muhimmanci akan zakka.
Da sunan Allah Mai rahama Mai jin ƙai
Godiya ta tabbata ga Allah Shi kaɗai, tsira da aminci su tabbata ga wanda babu wani annabi a bayansa, da alayen sa da sahabban sa, bayan haka:
Abinda yasa aka rubuta wadannan bayanan shi ne, yin nasiha da tinatarwa akan wajibcin zakka, wacce mafi yawancin musulmai suka yi sakaci da ita, ba su fitar da ita ta hanyar da aka shara'anta ba, tare da girman sha'aninta, da kuma kasancewarta ɗaya daga cikin rukunan musulunci biyar, waɗanda gininsa ba ya daidaituwa sai akansu; saboda faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: «An gina musulunci akan abubuwa biyar: Shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma lalle (Annabi) Muhammad Manzon Allah ne, da tsaida sallah, da bada zakkah, da azumin Ramadan, da Hajjin (ziyartar) ɗaki». Bukhari da Muslim sun haɗu akan ingancinsa. [1] Bukhari ne ya fitar da shi. a lamba ta (8) da Muslim, a lamba ta (16).
Kuma wajabcin zakka akan musulmai, yana daga mafi bayyanar kyawawan Musulunci, da kuma kulawarsa ga sha'anin waɗanda suka karɓe shi; saboda yawan fa'idojinta, da kuma tsananin buƙatuwar talakawan musulmai zuwa gareta.
Daga cikin fa'idojinta: Tabbatar da igiyar soyayya tsakanin madawaci da talaka; domin cewa rayuka an ɗabi'antar da ita ne akan son wanda ya kyautata musu.
Yana daga cikinsu: Tsarkake rai da nisantar da shi daga ɗabi'ar ƙwauro da rowa, kamar yadda Alƙur'ani mai girma ya yi nuni zuwa ga wannan ma'anar a cikin faɗinSa Allah - Maɗaukakin sarki -: (Ka karɓi sadaka (zakka) daga cikin dukiyoyinsu, wacce za ta tsarkake su kuma ta gyara musu halayensu da ita) [al-Taubah: 103].
Daga cikinsu: Sabawa musulmi siffar kyauta da karamci da tausayawa mabuƙaci.
Kuma yana daga garesu : Jawo albarka da ƙaruwa, da kuma maye gurbi (Allah Ya maye gurbin mafi alheri daga abinda mutum ya bayar) ga Allah, kamar yadda (Allah) Maɗaukakin sarki - Ya ce: (Abinda kuka ciyar na wani abu, to Shi ne Mai maye gurbinsa, kuma Shi ne mafi alherin masu azirtawa) [Saba'a: 39], da kuma faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a cikin ingantaccen Hadisi: Allah yana cewa: «Yakai ɗan Adam, ka ciyar zamu ciyar gareka...», Zuwa wanin haka, daga fa'idoji masu yawa. [2] Muslim ne ya fitar da shi, a lamba ta (993).
Haƙiƙa narko mai tsanani ya zo a cikin haƙƙin wanda ya yi rowa da ita, ko ya rage a wurin fitar da ita, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: (Waɗanda suke taskance zinare da azirfa, kuma basa ciyar da su a tafarkin Allah, to ka yi musu bushara da azaba mai raɗaɗi. 34. A Rãnar da ake ƙõna shi a kanta a cikin wutar Jahannama, sai a yi lalas da ita ga gõshinansu da sãshinansu da bãyayyakinsu, (a ce musu): "Wannan ne abin da kuka taskace dõmin rãyukanku. To, ku ɗanɗani abin da kuka kasance kunã sanyãwa a taska) [al-Taubah: 34- 35], Dukkan dukiyar da ba'a bada zakkarta, to ita taska (kanzu) ce, wacce za’a yi wa mai ita azaba a ranar Alƙiyama, kamar yadda ingantaccen Hadisi daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya yi nuni akan hakan cewa shi ya ce: «Babu wani ma'abocin zinare ko azirfa, da ba ya bada haƙƙinsu, sai a ranar alƙiyama ya kasance za'a ƙerasu a siffar farantai na wuta*, sai a ƙona shi a kansu a cikin wutar Jahannama, sai a yi wa sasanninsa da goshinsa da bayansa lalas, duk lokacin da suka ƙone, sai a dawo da su, a cikin wani yinin da gawargwadansa shekara dubu hamsin ne, har sai an yi hukunci tsakanin bayi, sai ya ya hanyarsa: Ko dai zuwa aljanna ko kuma zuwa wuta». [3] Muslim ne ya fitar da shi, a lamba ta (987).
Sannan Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ambaci mai raƙuma da shanu da tumakai, wanda ba ya bada zakkarsu, kuma ya bada labarin cewa za’a yi masa azaba a ranar Alƙiyama saboda su.
Kuma ya inganta daga Manzon Allah -tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi- cewa shi ya ce: «Wanda Allah Ya ba shi dukiya, bai bada zakkarta ba, za'a kamanta masa wani maciji mai kora, yana da alamomi biyu, za'a rataya masa shi a ranar Alƙiyama, sannan ya kama gyaffan bakinsa, sanna ya ce: Nine dukiyarka, nine taskarka», sannan Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya karanta faɗinSa - Allah Maɗaukakin sarki -: (Kada waɗanda suke yin rowar abinda Allah Ya ba su na falalarSa kar su yi zatan cewa hakan alheri ne garesu, a'a hakan sharri ne gare su za’a yi musu saƙandami da abinda suka yi rowa da shi a ranar alƙiyama) [Aal- Imran: 180]. [4] Bukhari ne ya fitar da shi a lamba ta (1338).
Zakka tana wajaba a kan nau’uka huɗu: Abinda yake fita daga ƙasa na ƙwayoyi da 'ya'yan itatuwa, da dabbobin ni'ima masu kiwo, da zinari da kuma azirfa, da hajojin kasuwanci.
Kuma kowanne daga waɗannan nau’ukan guda huɗu suna da nisabinsu abin iyakancewa, zakka ba ta wajaba a abinda bai kai shi ba. Nisabin ƙwayoyi da 'ya'yan itatuwa shi ne: Ausuƙi biyar, wasƙi shi ne: Sa'i (kwano) sittin da Sa'in Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, na dabino da zabibi da alkama da sha'ir da makanatansu (shi ne) sa'i ɗari uku da sa'in Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, shi ne cikin tafi huɗu na hannun mutum madaidaicin halitta idan hannuwansa sun kasance a cike.
Kuma wajibi (wato abinda yake zakka) a cikin hakan shi ne ɗaya bisa goma, idan dabinan da kuma shukokin sun kasance ana shayar dasu ne ba tare da wata wahala ba, kamar ruwan sama da na ƙoramai da idanun ruwa masu gudana da makamancin haka.
Amma idan sun kasance, ana shayar da su ne da ɗawainiya, da kuma wahala: Kamar abubuwan shayarwa da injina masu ɗago ruwa, da makamancin haka, to wajibi a cikinsu shi ne, rabin ushuri (rabin daya bisa goma) kamar yadda Hadisi ya inganta da hakan, daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -:
Amma nisabin masu kiwo cikin raƙuma da shanu da tumakai, to a cikinsa akwai bayanai daki-daki a cikin Hadisai ingantattu, daga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -, mai kwaɗayin saninsa, yana da ikon tambayar ma'abota ilimi game da hakan, kuma da badan nufin taƙaitawa ba, da mun ambace shi dan cikar fa'ida.
Amma nisabin azurfa, to shi ne awon ɗari da arba'in, kuma gwargwdaansa da dirhamai na larabawan Sa'udiyya, shi ne riyal hamsin da shida.
Nisabin zinare shi ne awo ashirin, kuma gwargwadansa daga Junaih na Sa'udiyya, shi ne Junaih goma sha ɗaya da ukun subu'in (daya bisa bakwai na) Junaih, a awon Gram kuwa shi ne Gram casa'in da biyu, kuma wajibi (wato zakka) a cikinsu shi ne rubi'in ɗaya bisa goma akan wanda ya mallaki nisabi daga gare su, ko daga ɗayansu, kuma shekara ta kewayo akaansa.
Riba mai bi ce ga asali, dan haka ba'a buƙatuwa zuwa ga sabuwar shekara, kamar yadda abinda dabba mai kiwo ta haifar to mai bi ne ga asalinsa dan haka ba'a buƙatuwa zuwa ga wata sabuwar shekarar, idan asalinsa ya kasance nisabi ne.
Dan gane kuma kuɗi na takarda waɗanda mutane suke mu'amala da su a yau, to suna cikin hukuncin zinare da azirfa, daidai ne an ambacesu dirhami ne, ko zinare, ko dala, ko wanin haka na daga sunaye, idan ƙimarsu ta kai nisabin azirfa ko zinare, kuma shekara ta kewayo akansu, to zakka ta wajaba a kansu.
Kayan ado na mata na zinare ko azirfa a keɓance ana riskar da su ga kuɗi, idan sun kai nisabi kuma shekara ta kewayo a kansu, to lallai a cikinsu akwai zakka koda an tanadesu ne dan amfani ko aro, a cikin mafi inagncin maganganun malamai biyu; saboda gamewar faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: «Babu wani ma'abocin zinare ko azirfa da ba ya bada zakkarsu, sai an maida su farantai na wuta gare shi a ranar alƙiyama». Har dai zuwa ƙarshen Hadisin da ya gabata. [5] Muslim ne ya fitar da shi, a lamba ta (987).
Kuma saboda abinda ya tabbata daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - cewa shi, ya ga awarwaro biyu na zinare a hannun wata mace sai ya ce: «Shin kina bada zakkar wannan?». ta ce: A'a. Ya ce: «Shin kina son Allah Ya maida miki su awarwaro biyu na wuta a ranar Alƙiyama!» sai ta jefar da su, kuma ta ce: «(Na bada su) ga Allah da kuma ManzonSa». [6] Abu Dawud ya fitar da shi, a lamba ta (1563) da Nasa'i, a lamba ta (2270) da isnadi mai kyau.
Kuma ya tabbata daga Ummu Salama - Allah Ya yarda da ita - cewa ita ta kasance, tana sanya wasu kayan ado na zinare, sai ta ce Ya Manzon Allah: Shin su taska (kanzu) ne? Sai ya ce: «Abinda ya kai a yi masa zakka to sai aka fitar da zakkar to ba taska ba ne». Tare da wasu Hadisan daban a cikin wannan ma'anar. [7] Abu Dawud ne ya fitar da shi, a lamba ta (1564).
Amma hajoji, su ne hajojin da aka tanada dan siyarwa, to su ana yi musu ƙima a ƙarshen shekara kuma ana fitar da rubu'in ushurin ƙimarsu, daidai ne ƙimar ta su ta kasance kwatankwacin kuɗinsu ne ko sama da haka, ko ƙasa da hakan; saboda hadisin Samura ya ce: «Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance yana umartarmu mu fitar da zakka daga abinda muke tanadarsa dan siyarwa», [8] Abu Dawud ne ya fitar da shi, a lamba ta (1562).
Filayen da aka tanada dan siyarwa suna shiga cikin hakan, da kuma gidaje, da motoci, da injina da suke ɗago ruwa, da wanin haka, daga nau'ikan hajojin da aka tanada dan siyarwa.
Amma manyan gidajen da aka tanada dan haya, ba dan siyarwa ba, to zakka ta tabbata a cikin kuɗin hayarsu, idan shekara ta kewayo a kansu, amma zatinsu to babu zakka a cikinsu; saboda kasancewarsu ba'a tanadesu ne dan siyarwa ba, haka nan motocin da aka ware dan hawa da kuma haya, babu zakka a kansu idan ba'a tanadesu dan siyarwa ba, kawai mai su ya saye su ne dan amfani.
Idan kuɗin da suka kai nisabi suka haɗu ga mai motar haya, to ya wajaba ya fitar da zakkarsu idan shekara ta kewayo musu, daidai ne ya kasance ya tanadesu ne dan ciyarwa, ko dan aure, ko dan siyan gidaje da filaye, ko dan biyan bashi, ko dan wanin haka na manufofi; saboda gamewar dalilai na shari'a masu nuni akan wajabcin zakka a kan misalin wannan.
Ingantaccen zance daga maganganun malamai shi ne cewa, bashi ba ya hana zakka saboda abinda ya gabata.
Haka nan dukiyoyin marayu da mahaukata zakka tana wajaba a cikinsu, a wajen mafi yawa daga malamai, idan sun kai nisabi, kuma shekara ta kewayo musu, kuma yana wajaba akan waliyansu su fitar musu da ita da niyya a maimakonsu, yayin cikar shekara; saboda gamewar dalilan, misali faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a cikin hadisn Mu'azu - Allah Ya yarda da shi - lokacin da ya aike shi zuwa Yaman: «Lallai cewa Allah Ya wajabta musu sadaka (zakka) a cikin dukiyoyinsu, za'a karɓa daga mawadatansu, za'a dawo da ita ga talakawansu». [9] Bukhari ne ya fitar da shi, a lamba ta (1395) da Muslim, a lamba ta (19).
Zakka haƙƙin Allah ce muhaba da ita (shi ne: Keɓantar wani da ita alhali bai cancanci a ba shi ita ba) ba ya halatta ga wanda bai cancanceta ba, ko kuma mutum ya jawowa kansa wani amfani da ita, ko tunkuɗe wata cuta, ko kuma ya kare dukiyarsa daga zargi da ita ko kuma ya tunkuɗe zargi daga gareta, kai yana wajaba akan musulmi ya bada zakkarsa ga waɗanda suka cancanceta, dan kasancewarsu suna daga ma'abotanta, ba dan wata manufar daban ba, tare da daɗin rai da ita, da tsarkake niyya saboda Allah a cikin hakan; har sai wuyayensa ya kuɓuta, kuma ya cancanci gwaggwaɓan sakamako da kuma maye gurbi.
Haƙiƙa Allah - tsarki ya tabbatar maSa - Ya bayyana a cikin littafinSa mai girma nau’ukan waɗanda ake bawa zakka, Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: {Abin sani kawai, dũkiyõyin sadaka na faƙĩrai ne da miskinai da mãsu aiki a kansu, da waɗanda ake lallãshin zukãtansu, kuma a cikin fansar wuyõyi, da wadanda bashi ya yi wa yawa, da a cikin hanyar Allah da ɗan hanya (matafiyi). Farilla daga Allah. Kuma Allah ne Masani, Mai hikima} [al-Taubah: 60].
A rufe ƙarshen wannan ayar mai girma da waɗannan sunayen biyun masu girma, akwai faɗakarwa daga Allah - tsarki ya tabbatar maSa - ga bayinSa akan cewa Shi - Allah tsarki ya tabbatar maSa - Shi ne Masanin halayen bayinSa: Wanda ya cancanci sadaka daga cikinsu, da kuma wanda bai cancanceta ba, kuma Shi ne Gwani a cikin shari'arSa da ikonSa dan haka ba Ya sanya abubuwa sai a bigiren da ya dace da su, koda wasu daga cikin sirrikan hikimarSa sun ɓuya ga wasu daga cikin mutane; dan bayi su natsu da shari'arSa kuma su miƙa wuya ga hukuncinSa.
Allah muke roƙo Ya datar da mu da musulmai ga fahimtar AddininSa, da kuma gaskiya a cikin mu'amalantarSa, da tsere zuwa ga abinda zai yardar da Shi, da kuma kariya daga abubuwan da suke wajabta fushinSa, lallai cewa Shi Mai yawan ji ne kuma Makusanci!
Allah Ya yi tsira da aminci ga bawanSa kuma ManzonSa Annabimmu Muhammad da alayensa da sahabbansa.
Babban shugaba gaba ɗaya na gudanar da bincike-binciken ilimi
da bada fatawa da kuma da'awa da shiryarwa
Babban malami: Sheikh Abdul’Aziz ɗan Abdullah ɗan Baz
SAƘO NA BIYU
A kan cikin falalar azimin watan Ramadan, da tsayuwarsa, tare da bayanin wasu hukunce-hukunce masu mihimmanci, waɗanda zasu iya ɓoyuwa ga wasu cikin mutane
Da sunan Allah Mai rahama Mai jin ƙai.
Daga Abdul'aziz ɗan Abdallah ɗan Baz, zuwa ga wanda yake ganinsa daga cikin musulmai, Allah Ya shigar da ni da kuma su tafarkin ma'abota imani, kuma Ya datar da ni da su ga fahimtar Sunnah da kuma Alƙur'ani, ameen!
Aminci ya tabbata a gareku da rahamar Allah da albarkataunSa
Bayan haka: Wannan taƙaitacciyar nasiha ce da ta kunshi falalar azimin watan Ramadan, da kuma tsayuwarsa, da falalar rigegeniya a cikinsa da ayyuka na gari, tare da bayanin hukunce-hukunce masu muhimmanci waɗanda zasu iya ɓoyuwa ga wasu daga cikin mutane.
Ya tabbata daga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - cewa shi ya kasance yana yi wa sahabbansa bushara da zuwan watan Ramadan, kuma tsira da aminci su tabbata agare shi- yana basu labarin cewa shi ne watan da ake buɗe ƙofofin rahama da ƙofofin aljanna a cikinsa, kuma ake kulle ƙofofin wutar Jahannama a cikinsa, kuma ake ɗaure Shaiɗanu a cikinsa, kuma yake cewa: «Idan farkon daren watan Ramadan ya zo, za'a buɗe ƙofofin aljanna ba za'a kulle wata ƙofa daga cikinsu ba, kuma za'a kulle ƙofofin wuta ba za’a buɗe wata ƙofa daga cikinsu ba, kuma za'a ɗaure Shaiɗanu, mai kira zai yi kira, ya mai neman alheri ka fuskanto, kuma ya mai neman sharri ka taƙaita, Allah Yana da waɗanda Yake 'yan tawa daga wuta, kuma hakan a kowanne dare ne». [1] Tirmizi ya fitar da shi, a lamba ta (682) da Ibn Majah, a lamba ta (1642).
Kuma mai tsira daminci yana cewa: «Watan Ramadan ya zo muku, watan albarka, Allah Yana zakke muku a cikinsa: Sai Ya saukar da rahama kuma Ya share kurakurai, kuma Ya amsa addu'a, Allah Yana kallon rigaye-rigayenku (gasarku) a cikinsa, sai Mala'ikunSa su yi alfahari da ku; ku nunawa Allah alheri daga kawunanku; domin cewa taɓaɓɓe shi ne wanda aka haramta masa rahama a cikinsa». [2] Ɗabarani ne ya fitar da shi a Musnaɗinsa, a lamba ta (2238).
Kuma mai tsira daminci yana cewa: «Wanda ya azimci Ramadan yana mai imani da neman lada, za'a gafarta masa abinda ya gabata daga zunubinsa, wanda kuma ya yi tsayuwar Ramadan, yana mai imani da neman lada za'a gafarta masa abinda ya gabata na zunubinsa, wanda ya yi tsayuwar daren Lailatul ƙadri yana mai imani da neman lada, za'a gafarta masa abinda ya gabata na zunubinsa». [3] Bukhari ne ya fitar da shi, a lamba ta (2014) da Muslim, a lamba ta (760).
Kuma mai tsira daminci yana cewa: «Allah Yana cewa dukkan aikin Ɗan Adam nasa ne, kyakkyawa ɗaya da kwatankwacinsa goma, har zuwa ninki ɗari bakwai, sai azimi lallai shi nawa ne, kuma Ni zan yi sakayya da shi; ya bar sha'awarsa da abincinsa da abin shansa saboda Ni, mai azimi yana da farin ciki biyu: Farin ciki a lokacin buɗa bakinsa, da kuma farin ciki alokacin haɗuwa da Ubangijinsa, kuma bashin bakin mai azimi shi ne mafi daɗi a gurin Allah daga ƙanshin almiski». [4] Ibnu Majah ya fitar da shi, a lamba ta (1638).
Hadisai a cikin falalar azimin watan Ramadan da tsayuwarsa da kuma falalar jinsin azimi suna da yawa.
To yana kamata ga mumini, ya ribaci wannan damar, ita ce : Abinda Allah Ya yi masa baiwa da ita na riskar watan Ramadan; sai ya yi gaggawar yin ayyukan ɗa'a, kuma ya kiyayi munanan ayyuka, ya yi ƙoƙari a yin abinda Allah Ya wajabta a kansa, musamman ma dai salloli biyar; domin cewa ita ginshiƙin Musulunci ce, kuma ita ce mafi girman farillai bayan shahada biyu, to wajibi ne akan kowanne musulmi namiji da musulma mace kiyayewa a kanta da kuma yinta a lokacinta da kushu'i da kuma nutsuwa.
Daga mafi muhimmancin wajibanta a haƙƙin maza shi ne, yin ta a cikin jama'a a cikin ɗakunan Allah (masallatai) waɗanda Allah Ya yi izini a ɗaukaka su, kuma a ambaci sunanSa a cikinsu kamar yadda Ya ce: (Ku tsaida sallah ku bada zakka kuma ku yi ruku'u tare da masu ruku'u) [al-Baƙara: 43], Kuma (Allah) - Maɗaukakin Sarki - Ya ce: (Ku tsare lõkatai a kan sallõli da sallah mafificiya. Kuma ku tsayu kuna mãsu ƙanƙan da kai ga Allah) [al-Baƙara: 238], Kuma Ya ce: (Lalle ne, Mũminai sun sãmi babban rabõ 1 Waɗanda suke a cikin sallarsu mãsu tawãli'u ne 2) [al-Muminun: 1-2] har zuwa inda Ya ce: (Su ne waɗanda suke kiyaye sallolinsu, waɗannan su ne magada, waɗanda suke gadan (aljannar) Firdausi alhali su suna madawwama a cikinta) [al-Mua'Minun: 9-11] Kuma Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Lallai alƙawarin da ke tsakanin mu da su (shi ne) sallah, wanda ya barta, to, haƙiƙa ya kafirta». [5] Tirmizi ne ya fitar da shi a lamba ta (2621), da Ibn Majah a lamba ta (1079).
Kuma mafi muhimmancin farillai bayan sallah shi ne, bada zakka kamar yadda (Allah) Ya ce: (Kuma ba a umarce su da kome ba fãce bauta wa Allah, suna mãsu tsarkake addinin gare Shi, mãsu karkata zuwa ga addinin gaskiya, kuma su tsaida sallah su bãyar da zakka, kuma wannan shi ne addinin waɗanda suke a kan hanyar ƙwarai) [Al-Bayyinah: 5], Kuma (Allah) - Maɗaukakin Sarki - Ya ce: (Ku tsaida sallah ku bada zakka, kuma kubi Manzo tsammaninku za'a jiƙanku) [Al-Nur: 56].
Haƙiƙa Littafin Allah mai girma ya yi nuni da kuma Sunnar ManzonSa mai girma, sun yi nuni akan cewa wanda bai bada zakkar dukiyarsa ba, za’a yi masa azaba da ita a ranar alƙiyama.
Kuma mafi muhimmancin al'amura bayan sallah da zakka da azimin Ramadan, kuma shi ɗaya ne daga cikin rukunan Musulunci biyar, waɗanda aka ambata a cikn faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: «An gina musulunci akan abubuwa biyar: Shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma lalle (Annabi) Muhammad Manzon Allah ne, da tsaida sallah, da bada zakkah, da azumin Ramadan, da kuma Hajjin ɗaki». [6] Bukhari ya fitar da shi, a lamba ta (8) da Muslim, a lamba ta (16).
Kuma yana wajaba akan musulmi ya kiyaye aziminsa da tsayuwar darensa, daga abinda Allah Ya haramta akansa, na maganganu da ayyuka; domin cewa abin nufi da azimi shi ne yi wa Allah - tsarki ya tabbatar maSa - biyayya da girmama alfarmominsa, da yaƙar rai akan saɓawa son ranta a kan biyayya ga Ubangijinta, da kuma saba mata da haƙuri daga abinda Allah Ya haramta, kuma abin nufi bai zama mujarradin (kawai) barin abin ci da abin sha da sauran abubuwan da suke ɓata azimi ba; saboda haka ya inganta daga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - cewa shi ya ce: «Azimi garkuwa ne, idan yinin azimin ɗayanku ya kasance, to kada ya yi kwarkwasa, kuma kada ya yi zancen banza, idan wani ya zage shi ko ya yi faɗa da shi, to ya ce azimi nake yi», Kuma ya inganta daga gare shi - tsira da amincin Allah su tabbata gareshi - cewa shi ya ce: «Wanda bai bar faɗin ƙarya ba, da kuma aiki da ita da wauta ba, to Allah ba Shi da wata buƙata akan ya bar abincinsa, da kuma abin shansa». Ta hanyar waɗannan nassosin da ma wasunsu sai aka san cewa, wajibi akan mai azimi shi ne ya kiyaye daga dukkan abinda Allah Ya haramta akansa, da kuma kiyayewa akan dukkan abinda Allah Ya wajabta a kansa, da haka ne ake ƙaunar rahama gare shi, da kuma 'yantuwa daga wuta, da karɓar azimi da kuma tsayuwar dare. [7] Bukhari ne ya fitar da shi, a lamba ta (1904) da Nasa'i, a lamba (2537).) [8] Bukhari ne ya fitar da shi, a lamba ta (1804) da Abu Dawud, a lamba ta (2362).
Kuma akwai wasu al'amura waɗanda zasu iya ɓoyuwa akan wasu daga cikin mutane.
Daga cikinsu: Cewa wajibi akan musulmi ya yi azimi dan imani da neman lada, badan riya ko jiyarwa ba, ba kuma dan koyi da mutane ba, ko bin iyalansa ko mutanen garinsa, kai wajibi akansa ya zama abin da ya sashi yin azimi shi ne, imaninsa da cewa Allah Ya wajabta masa hakan, da kuma neman sa ga lada a wurin Ubangijinsa a cikin hakan, haka nan tsayuwar Ramadan yana wajaba akan musulmi ya aikatata dan imani da neman lada, ba dan wani dalilin daban ba; saboda haka ne tsira da aminci su tabbata agare shi ya ce: «Wanda ya azimci Ramadan yana mai imani da neman lada, za'a gafarta masa abinda ya gabata daga zunubinsa, wanda kuma ya yi tsayuwar Ramadan yana mai imani da neman lada za'a gafarta masa abinda ya gabata na zunubinsa, wanda ya yi tsayuwar daren Lailatul ƙadri, yana mai imani da neman lada, za'a gafarta masa abinda ya gabata na zunubinsa». [9] Bukhari ya fitar da shi, a lamba ta (2014) da Muslim, a lamba ta (760).
Yana daga cikin al'amuran da hukuncinsu zai iya ɓoyuwa ga wasu daga cikin mutane shi ne: Abinda yake bijirowa mai azimi na ciwo, ko haɓo, ko amai, ko shigar ruwa ko kananzir zuwa ga maƙogwansa, ba tare da zaɓinsa ba, to dukkanin waɗannan al'amuran basa ɓata azimi, sai dai wanda ya yi gangancin yin amai, to aziminsa ya ɓaci; saboda faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: «Wanda amai ya zo masa (ya rinjaye shi) to babu ramuwa akansa, wanda kuma ya jawo amai, to ramuwa ta wajaba akansa». [10] Tirmizi ne ya fitar da shi, a lamba ta (720) da Ibn Majah a lamba ta (1676).
Daga hakan akwai: Abinda yakan bijirowa mai azimi, na jinkirin yin wankan janaba har zuwa ɓullowar alfijir, da kuma abinda yake bijirowa wasu daga cikin mata, na jinkirin yin wankan al’ada ko biƙi, har zuwa ɓullowar alfijir, idan ta ga tsarki kafin alfijir, to azimi ya lazimce ta, kuma babu wani hani akan jinkirta wanka har zuwa bayan ɓullowar alfijir, sai dai ba ya halatta gareta ta jinkirta shi har zuwa bayan ɓullowar rana, kai yana wajaba akanta ta yi wanka ta sallaci Asuba kafin ɓullowar rana. Haka nan mai janaba ba ya halatta a gare shi ya jinkirta wanka, har zuwa bayan ɓullowar rana, kai yana wajaba akansa ya yi wanka ya sallaci Asuba kafin ɓullowar rana, kuma yana wajaba akan namiji ya yi gaggawa da yin hakan har ya riski sallar Asuba tare da jama'a.
Daga cikin al'amuran da basa ɓata azimi: Diban jini, da yin allurar da ba ta ciyarwa ba ce, sai dai jinkirta hakan har zuwa dare ya fi , kuma ya fi tsare azumi idan hakan ya sawwaƙa; saboda faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: «Kabar abinda kake kokwantansa, zuwa abinda baka kokwantansa». [11] Tirmizi ne ya fitar da shi, a lamba ta (2518).
Da kuma faɗinsa - tsira da aminci su tabbata agare shi -: «Wanda ya kiyaye shubuhohi to ya kuɓutar da Addinisa da kuma mutuncinsa». [12] Bukhari ne ya fitar da shi, a lamba ta (52) da Muslim, a lamba ta (1599).
Kuma daga cikin al'amuran da hukuncinu yake ɓoyuwa ga wasu daga cikin mutane: Rashin nutsuwa a cikin sallah, daidai ne ta kasance sallar farilla ce ko ta nafila, haƙiƙa ingantattun hadisai daga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sun yi nuni akan cewa, nutsuwa rukuni ce daga cikin rukunan sallah, sallah bata inganta ba tare da ita ba, ita ce ƙanƙar da kai a cikin sallah, da kuma rashin yin gaggawa har sai kowanne ƙashi ya koma bigirensa, kuma da yawa daga cikin mutane suna yin sallar ashan a cikin watan Ramadan sallar da ba ya yin ta cikin hankali, kuma ba ya nutsuwa a cikinta, kai yana yin caccaka acikinta caccaka, kuma wannan sallar akan wannan siffar ɓatacciya ce, kuma mai yinta mai saɓo ne, ba za'a ba shi lada ba.
Kuma yana daga cikin al'amuran da hukuncinsu yakan ɓoyu ga wasu daga cikin mutane: Zatan sashinsu cewa, sallar ashan ba ya halatta a rageta daga raka'a ashirin, kuma wasu daga cikinsu suka yi zatan cewa ba ya halatta ayi ƙari a cikinta akan raka'a goma sha ɗaya, ko raka'a goma sha uku,, to wannan dukkansa zato ne, ba'a bigiransa ba, kai kuskure ne ya saɓawa dalilai.
Haƙiƙa ingantattun Hadisiai daga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - sun yi nuni akan cewa, sallar dare akwai yalwa a cikinta, bata da wani iyakar da ba ya halatta a saɓa masa, kai ya tabbata daga gare shi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - cewa ya kasance yana yin sallar dare raka'a goma sha ɗaya, wani lokacin ma ya yi sallah raka'a goma sha uku, kuma ba mamaki ya yi sallah ƙasa da haka a cikin watan Ramadan da waninsa, lokacin da aka tambaye shi game da sallar dare sai ya ce: «(Raka'a) biyu-biyu ne, idan ɗayanku ya ji tsoron Asuba (ta riske shi) sai ya sallaci raka'a ɗaya zata zame masa wuturi ga abinda ya sallata». Bukhari da Muslim sun haɗu akan ingancinsa. [13] Bukhari ne ya fitar da shi, a lamba ta (946) da Muslim, a lamba ta (749).
Kuma bai iyakance wasu raka'o'i ababen ayyanawa ba, ba'a watan Ramadan ba haka kuma ba'a waninsa ba, saboda haka ne sahabbai suka yi sallah a lokacin Umar - Allah Ya yarda da shi - a wasu daga cikin lokuta raka'a ashirin da uku, a wasu lokutan kuma raka'a ashirin da ɗaya, dukkanin wannan ya tabbata daga Umar - Allah Ya yarda da shi - haka kuma daga sahabbai a lokacinsa.
Wasu daga cikin magabata ya kasance, yana yin sallah a watan Ramadan raka'a talatin da shida, kuma yana yin wutiri da uku, waninsu kuma yana yin sallah raka'a arba'in da ɗaya, babban malamin musulunci Ibnu Taimiyyah da waninsa daga ma'abota ilimi sun ambaci hakan daga garesu, kamar yanda - Allah Ya yi masa rahama - ya ambaci cewa, al'amarin akwai yalwa a cikin hakan, kuma ya ambaci cewa abinda ya fi ga wanda ya tsawaita karatu da ruku'u da sujjada shi ne ya ƙaranta adadin, wanda kuma ya sawwaƙa karatu da ruku'u da sujjada sai ya ƙara adadin wannan shi ne ma'anar maganarsa - Allah Ya yi masa rahama -.
Wanda ya lura da sunnarsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - zai san cewa abinda ya fi a cikin wannan dukkaninsa shi ne sallah raka'a goma sha ɗaya, ko goma sha uku a cikin watan Ramadan dama waninsa; saboda kasancewar hakan shi ne wanda ya dace da aikin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a galibin halayensa, kuma cewa hakan ya fi sauƙi ga masallata, kuma ya fi kusa ga kushu'i da nutsuwa, wanda kuma ya ƙara to babu laifi kuma ba'a ƙi hakan ba kamar yadda ya gabata.
Kuma abinda ya fi ga wanda ya yi sallah tare da liman a tsayuwar dare cewa, kada ya fita sai tare da liman; saboda faɗin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi -: «Lallai cewa mutum idan ya tsaya tare da liman har sai da ya idar, Allah Zai rubuta masa tsayuwar dare». [14] Tirmizi ne ya fitar da shi, a lamba ta (806) da Abu Dawud, a lamba ta (1375).
Kuma an shara'antawa musulmai su yi ƙoƙari a cikin nau'ikan ibada a cikin wannan watan mai girma na sallar nafila, da karatun Alƙur'ani, ta hanyar tadabburi (bibbiyarsa) da fahimta da yawaita tasbihi da hailala da tahmidi da kabbara da istigfari da addu'o'in da aka shara'anta, da horo da aikin alheri, da kuma hani daga abin ƙi, da kira zuwa ga Allah, da taimakon talakawa da miskinai, da yin ƙoƙari a biyayya ga mahaifa da sada zumunci, da girmama maƙwabci, da gaida mara lafiya, da wanin haka na nau’ukan alheri; saboda faɗinsa - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - a cikin Hadisin da ya gabata: «Allah Yana duba zuwa ga gasarku a gare shi, sai Ya yi wa Mala'ikunSa alfahari da ku, dan haka ku nunawa Allah alheri daga kawunanku, domin cewa mara arziƙi shi ne wanda aka haramta masa rahamar Allah a cikinsa». [15] Ɗabarani ne ya fitar da shi a cikin Musnadinsa, a lamba ta (2238).
Da kuma abinda aka ruwaito daga gare shi - tsira da aminci su tabbata agare shi - cewa shi ya ce: «Wanda ya nemi kusanci a cikinsa, da wata ɗabi'a daga cikin ɗabiun alheri, to ya kasance kamar wanda ya bada wata farilla ce a cikin watan da ba shi ba, wanda kuma ya yi wata farilla a cikinsa, to ya kasance kamar ya yi farilla saba'in ne a cikin waninsa» [16] Ibnu Khuzaimah ne ya fitar da shi a cikin Sahihinsa, a lamba ta (1887).
Da kuma faɗinsa - tsira da aminci su tabbata agare shi - a cikin ingantaccen Hadisi: «Umarah a cikin Ramadan ta yi daidai da Haji - ko cawa ya yi: Da Hajji tare da ni». [17] Bukhari ne ya fitar da shi, a lamba ta (1863).
Hadisai da abinda aka ruwaito daga sahabbai masu nuni akan halaccin rigegeniya a cikin nau'ikan alheri a cikin wannan watan mai girma suna da yawa.
Allah Shi ne wanda ake roka Ya datar da mu da sauran musulmai ga dukkan abinda a cikinsa akwai yardarsa, kuma Ya karɓi aziminmu, da tsayuwarmu, kuma Ya gyara halayenmu, Ya kuma tsaremu daga fitintinu masu ɓatarwa, kamar yadda muke roƙonSa - tsarki ya tabbatar maSa - Ya gyara jagororin musulmai, kuma ya haɗa kalmarsu akan gaskiya, lallai cewa Shi Majiɓincin haka ne kuma Mai iko ne akansa.
Aminci ya tabbata a gareku da rahamar Allah, da kuma albarkokinSa.