يومي الأول في الإسلام
RANATA TA FARKO A MUSULUNCI
RANATA TA FARKO A MUSULUNCI
Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.
GABATARWA
Dukkan godiya ta tabbata ga Allah, wanda ya aiko Annabin Sa Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - rahama ga talikai, ina shaidawa cewa babu abin bautawa da gaskiya sa Allah, Shi kaɗai yake, ba Shi da abokin tarayya, Ubangijin jama'ar farko da na ƙarshe, kuma ina shaidawa cewa (Annabi) Muhammad bawan Sa ne, kuma Manzan Sa ne, cikamakin AnnabAwa da Manzanni - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - aminci mai yawa har zuwa ranar sakamako, bayan haka:
Mutane gaba ɗaya suna bincike akan farin ciki mai bada nutsuwa, daga cikin su, akwai wanda yake zatan cewa, tsira yana cikin tara dukiya, daga cikin su akwai wanda yake bincike game da shi ƙarƙashin haskake-haskaken shahara, daga cikin su akwai wanda yake ganin sa a wagen samun matsayiyyika maɗaukaka, ko wanin hakan, daga jin daɗin rayuwa, sai dai abin da ke faruwa a aikace, yana shaida cewa da yawa daga waɗanda suka samu waɗan nan abubuwan basu samu farin ciki mai bada nutsuwa da suke nufi ba.
Lallai wannan farin ciki mai bada nutsuwa bazai yiwu ya tabbata garemu ba, sai lokacin da muka shiriya zuwa ga Addinin gaskiya, wanda Mahaliccin 'yan Adam gaba ɗaya Ya zaɓa mana shi, kuma mu Addinantu da shi, mu kuma tafi dai dai da koyarwar sa, da wannan ne kawai zamu samu tsira da rayuwa mai daɗi a duniya, da kuma tsira madawwami a lahira, Allah - maɗaukakin sarki - Yana cewa:
{Na'am! Wanda ya sallama fuskarsa ga Allah, alhãli kuwa yana mai kyautatãwa, to, yana da ijãrarsa, a wurin Ubangijinsa, kuma bãbu tsõro a kansu, kuma ba su zama suna baƙin ciki ba}.
[Al-Bakara: 112].
Kuma Yana cewa:
{Wanda ya aikata aiki na ƙwarai daga namiji kõ kuwa mace, alhãli yanã mũmini, to, haƙĩƙa Munã rãyar da shi, rãyuwa mai dãɗi. Kuma haƙĩƙa Munã sãkã musu lãdarsu da mafi kyãwun abin da suka kasance sunã aikatãwa}.
[Surat Al-Nahl: 97].
Kai da zarar ka shiga Musulunci - ya kai ɗan uwana mai girma- zaka kasance haƙiƙa ka ɗora diddigen ka akan hanyar shiriya da haske, da tsira da farin ciki, to yana kamata ka zama akan amincewa cewa ranar musulintar ka ba kamar kowace rana ce a cikin rayuawar ka ba, lallai cewa ita ranar sabuwar haihuwa ce gare ka!
Idan har ka kasance, ranar da aka haifeka ka fita daga duhun mahaifar mahaifiyar ka, tare da ƙuncin sa, zuwa hasken duniya da yalwar ta, to kai a yau zaka fita daga duhun kafirci zuwa hasken imani, haka kuma daga ƙuncin ɓata zuwa yalwar shiriya, Allah - maɗaukakin sarki - Yana cewa:
{Shin, kuma wanda ya kasance matacce sa'an nan Muka rãyar da shi, kuma Muka sanya wani haske dõminsa, yanã tafiya da shi, yanã zama kamar wanda misãlinsa yanã cikin duffai, shĩ kuma ba mai fita ba daga gare su?}
[Al-An'am: 122].
Barka da zuwa farfajiyar Musulunci, kuma karɓi wannan ɗan ƙaramin littafin, wanda yake tattaro wasu al'amura muhimmai, da asalai masu girma waɗanda yake kamata ka san su a ranar farko daga musuluntar ka.
MASHIGA:
MUSULUNCI SHINE ADDININ GASKIYA:
Addinin Musulunci, shine Addinin gaskiya, wanda Allah - maɗaukakin sarki - Ya yarda da shi - ga mutane baki ɗaya, shine Addinin da ba'a karɓar wanin sa a wurin Allah, Allah - maɗaukakin sarki - Yana cewa:
{Lallai Addini A wurin Ubangiji shine Musulunci}
[Aal Imran: 19].
Kuma Allah - mai girma da ɗaukaka - Yana cewa:
{Kuma wanda ya nẽmi wanin Musulunci ya zama addini, to, bã zã a karɓa daga gare shi ba. Kuma shi a Lãhira yana daga cikin mãsu hasãra}.
[Aal Imran: 85].
Wanda ya rungumi Addinin Musulunci, kuma yayi riƙo da shi, to shi zaiyi tafiya a hanyar haske da shiriya, hanya madaidaiciya mabayyaniya wacce zata sadar zuwa ga Allah wanda ya halicci ɗan Adam, kuma Ya samar da shi a wannan rayuwar.
Haƙiƙa Addinin Musulunci yazo da gyara halin mutum da sashi nutsuwa da farin ciki a cikin rayuwar sa ta duniya, hakanan azirtar sa da kuma rabautar sa a cikin rayuwar lahira bayan mutuwa, lokacin da Allah - maɗaukakin sarki - zai shigar da shi Aljanna sai yaji daɗi da abin da ke cikin ta na ni'ima madawwamiya.
Ya na wajaba akan kowane mutum yayi bincike game da Addinin gaskiya, wanda shine Musulunci, kuma ya nemi sanin sa, ya kuma shiga cikin sa yana mai bada gaskiya da shi, kuma ya lazimci koyarwar sa da hukunce-hukuncen sa, dan ya samu alheran duniya dana lahira.
TA YAYA MUTUM ZAI SHIGAMUSULUNCI?
Mutum yana shiga Musulunci, idan ya ce; (Ina shaidawa cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma lallai cewa Annabi Muhammad Manzon Allah ne), da gaskiya da sakankancewa da kuma sanin abin da take nuni akan sa, duk wanda ya faɗi wannan kalmar, yana sane da ma'anar ta yana mai gaskiya a faɗinta mai sakankancewa mai jawuwa ga abinda tayi nuni akan sa, to haƙiƙa ya shiga Musulunci, sannan ya wajaba a kansa ya nemi sanin ragowar ayyukan Musulunci, kuma yayi aiki dasu gwargwadan ikonsa, duk lokacin da iliminsa ya ƙaru to imanin sa zai ƙaru, kuma ladan sa zai girmama a wajen Allah - maɗaukakin sarki -.
Ma'anar Shaida biyu (Ina shaidawa cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma (Annabi) Muhammadu Manzon Allah ne):
Haƙiƙa ka shiga Musulunci da zarar faɗinka: (Ina shaidawa cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma Muhammadu Manzon Allah ne), kana mai bada gaskiya da ita, kuma mai gasgatawa, to shin kasan haƙiƙanin ma'anarta?
Ma'anar Shaidawa cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah: Shine ƙudircewa da tabattarwa cewa, babu wani Ubangijin da ya cancanci bauta da biyayya sai Ubangiji ɗaya, shine Allah - tsarki ya tabbatar masa Ya ɗaukaka -, Mahaliccin kasantacce, kuma Mai jijjuya al'amarin sa.
Ma'anar shaidawa cewa Annabi Muhammad Manzon Allah ne: Shine ƙudircewa da tabbatar da cewa (Annabi) Muhammad bawan Allah ne, kuma ManzonSa ne cikamakin Anmnabawa, abin aikowa zuwa ga mutane gaba ɗaya,da kuma aiki da abin da hakan ya ƙunsa, ta hanyar yi masa biyayya a cikin abin da yayi umarni, da gasgata shi a cikin abinda ya bada labari, da nisantar abin da yayi hani gareshi kuma ya tsawatar, kuma kada a bautawa Allah sai da abin da Ya shara'anta.
ALBISHIRDIN KA DA MUSULUNCI:
Dan uwana mai girma, lallai cewa ranar shigar ka Musulunci, itace mafi alherin kwanukan ka a sake, haƙiƙa ya tabbata cewa Annabin mu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce:
"Musulunci yana rusa abin da (ya wuce) a gaban sa".
Muslim ne ya rawaito shi.
Wato lallai cewa Musulunci yana shafe dukkanin abin da ya faru daga gareka kafin musuluntar ka, na kafirci da sharrika da kurakurai da laifuffuka, to kayi farin ciki da gafarar Allah - maɗaukakin sarki -, kai a yau za'a tsarkakeka daga kurakurai, za'a buɗe maka farin shafi a cikin rayuwar ka, dan ka dawo a tsarkake kamar ranar da babarka ta haife ka, zaka fara sabuwar rayuwa wacce alheri ya cikata, kuma zaka tafi a hanyar haske da tsira da kuma farin ciki.
FARIN CIKI DA NI'IMAR MUSULUNCI:
Lallai cewa farin ciki mai girma wanda kaji yayin shigar ka Musulunci yana wajaba ya wanzu yana mai lazimtar ka tsawon rayuwar ka, to ni'imar shiriya tana daga mafi ɗaukakar ni'imomi, kuma mafi girman baiwowin da Allah - maɗaukakin sarki - Yayi baiwa da ita ga bayin Sa, itace mafi girma daga ni'imar iska da ruwa da abinci da abin sha, kuma mafi girma daga dukiya da matsayi da alfarma, itace mafi girman ni'ima kai tsaye, to ta yaya bazakayi farin ciki da ita ba? Allah - maɗaukakin sarki - Yana cewa:
{Ka ce: "Da falalar Allah da rahamarSa. Sai su yi farin ciki da wannan." Shĩ ne mafi alhẽri daga abin da suke tãrãwa}.
[Surta Yunus: 59].
To ba makawa da kadinga jin falalar Allah a gareka ka, cewa Ya zaɓeka tsakanin miliyoyin mutane dan ka shiga Musulunci, Allah - maɗaukakin sarki - Ya ce:
{Wanda Allah Yayi nufin shiryar da shi zai buɗe ƙirjin sa ga Musulunci}
[Surat Al'An'am: 125].
Wannan ni'imar mai girma tana buƙatuwa zuwa godiya mai yawa, to ya wajaba gareka ka yawaita yabon Allah - maɗaukakin sarki - da godiyar Sa da yabo gare Shi - Ya girmama Ya ɗaukaka - cewa Ya shiryar da kai ga ingantaccen Addini.
WASU TUSHEN DA BABU MAKAWA SAI AN SANSU:
Idan kashiga Addinin Musulunci to lallai cewa akwai wasu al'amuran da yake wajaba akanka ka nemi sanin su, da kuma sanin su, daga wannan akwai sanin amsar tambayoyi uku muhimmai waɗanda za'a tambayi kowane mutum akansu bayan mutuwa, waɗanda suke iyakance makomar sa ta dindindin, ko dai zuwa Aljanna ko kuma zuwa wuta, sune:
Waye Ubangijin ka?
Menene Addinin ka?
Waye Annabin ka?
TUSHE NA FARKO: WAYE UBANGIJIN KA?
Ubangiji na (Shine ) Allah.
Musulmi yana ƙudire cewa ubangijin sa Shine (Allah) wanda Ya halicci wannan kasantaccen da dukkanin abin da ke cikin sa, kuma Ya halicci mutum.
Mu idan mukayi tinani a cikin wannan kasantaccen mai girma, da abin da ke cikin sa daga Majarrat masu girman gaske (wani wurine a sama a cikin sa akwai taron taurari), da abin da ta tattaro na biliyoyin masaukan taurari da kuma taurarin, idan muka lura da wannan ƙasar wacce muke rayuwa akan ta da abin da ke cikin ta na sarari da duwatsu, da busashshe da koguna da ƙoramai, da abin da ke cikin su na abubuwan mamaki kasantattu a cikin zurfin koguna, haka nan a cikin sahara da dazuzzuka, idan muka lura da mamakin yin mutum da wanin sa daga kasantattu, to lallai cewa tinanin mu zai kaimu zuwa sakamakon da babu maguda gare shi, cewa shi babu makawa daga samuwar wani Mahalicci Mai girma Masani, Mai iko kuma Gwani, Ya halicci wannan kasantaccen sai Ya ƙayatar da shi, to bazai yiwuba a samu waɗan nan ababen halittar ba tare da samuwar wani Ubangiji mahaliccin da ya samar da su ba, kuma Ya tsara al'amarin su, Ya kyautata aikin su da abin da zai rinjayi hankula, wannan al'amarin Allah - mai girma da ɗaukaka - Ya bayyana shi a bayyane ga kowane mai hankali in da Ya ce:
{shin, an halitta su ne bã daga kõme ba, kõ kuwa sũ ne mãsu yin halitta?}
[Surat Al-Dur: 35].
To waɗan nan kasantattun ba su samar da kansu ba, kuma ba'a samar da su ba ba tare da mai samarwa ba, to wannan korarrene a wurin masu hankali!
Allah Shine macancanci ga bauta Shi kaɗai:
Wannan Ubangijin Shine Allah macancanci ga bauta Shi kaɗai؛, domin cewa Shine Mahalicci Mai jujjuya dukkanin abin da ke cikin wannan kasantaccen, kuma Mai azirta dukkanin wanda ke cikin sa, to shine wanda Ya halicci dukkanin mutane, kuma Ya samar da su a wannan ƙasar, kuma Ya basu sabubban rayuwa, Allah - maɗaukakin sarki - Yana cewa:
{Wancan ne Allah Ubangijinku. Bãbu wani abin bautãwa fãce Shĩ, Mahaliccin dukan kõme. Sabõda haka ku bauta Masa kuma Shi ne wakĩli a kan dukan, kõme}.
[Surat Al-an'am: 102].
To yana wajaba akan kowane mutum, ya bautawa Allah Shi kaɗai, kuma kada ya tarayya wani abu da Shi a cikin bautar Sa, Allah - maɗaukakin sarki - Yana cewa:
{Yã ku mutãne! Ku bauta wa Ubangjinku, Wanda Ya halicce ku, kũ da waɗanda suke daga gabãninku, tsammãninku ku kãre kanku!}
[Suarta Al-Baƙara:21].
Kuma tsarki ya tabbatar maSa Yana cewa:
{Ku bautawa Allah kar ku hada shi da komai}
[Surat Al-Nisa: 36].
KIRAN ANNABAWA ZUWA KADAITA ALLAH - MADAUKAKIN SARKI -:
Duk da bayyanar wannan al'amarin, sai dai cewa Allah - mai girma da ɗaukaka - da falalar Sa da karamcin Sa, da kuma rahamar Sa a gare mu, Bai haliccemu ba kuma Ya barmu muna faɗawa can da can a rayuwa, kai Ya aiko mana wasu Manzanni gare mu kuma Ya saukar da wasu littatattafai a tare da su dan su sanar damu Shi kuma su shiryar damu zuwa gare Shi, Allah - maɗaukakin sarki - Ya ce:
{Lalle Mũ Mun aike ka da gaskiya, kanã mai bãyar da bushãra kuma mai gargaɗi. Kuma bãbu wata al'umma fãce wani mai gargaɗi yã shũɗe a cikinta}.
{Surat Faɗir: 24}.
Uban mutane Adam - aminci ya tabbata a gare shi -, da Annabawa dukkanin su, daga cikin su akwai Nuhu da Ibrahim da Musa da Isa da wasun su daga Annabwa, tuƙewa da Annabin mu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata a gare su - sun haɗu akan wani tushe mai girma, shine kiran mutane zuwa imani da Allah - maɗaukakin sarki -, da kaɗaita Shi da kaɗaita Shi da bauta, da barin bautar wanin Sa daga ababen bauta, daga mutane da duwatsu da bishiyoyi da taurari da masaukan taurari da wasun su, Allah - maɗaukakin sarki - Yana cewa:
{Haƙiƙa mun aiko ga kowacce Al’umma Manzo da cewa ku bautawa Allah ku kuma guji bautawa Dagutu}
[Surat Al-Nahl: 36].
Kuma Allah - mai girma da ɗaukaka - Yana cewa:
{Kuma ba Mu aiki wani Manzo ba a gabãninka fãce Munã yin wahayi zuwa gare shi, cẽwa "Lalle ne Shi, bãbu abin bautãwa fãce Nĩ, sai ku bauta Mini}
[Surat Al-anbiyaa: 25].
DAGA SUNAYEN ALLAH DA SIFFOFIN SA:
Allah-maɗaukakin sarki- Yana da kyawawan sunaye da siffofi maɗaukaka, yayin da muke ƙoƙarin sanin su to muna ƙara sanin Ubangijin mu - tsarki ya tabbata maSa Ya ɗaukaka -, kuma muna ƙara son Sa, da tsoron Sa, da ƙaunar falalar Sa da karamcin Sa, Allah - maɗaukakin sarki - Yana cewa:
{Allah bãbu abin bautãwa fãce Shi. Yanã da sunãye mafiya kyau}.
[Surat Daha: 8].
Da kuma sunayen Sa masu shiryarwa a bisa siffofin Sa masu yawa, yana daga sunayen Allah - maɗaukakin sarki -:
Mai rahama Mai jin ƙai: Allah - maɗaukakin sarki - Ya ce:
{Kuma Ubangijinku Ubangiji Guda ne. Bãbu wani Ubangiji fãce Shi, Mai rahama, Mai jin ƙai}
[Surat Al-Bakara: 163].
To Shine mai yalwatacciyar rahama mai girma, wacce ta yalwaci dukkan komai, ta kuma game dukkanin ababen halitta, haƙiƙa rahamar Sa ta tattaro duniya da dukkanin halittar Sa, daga dabbobi da mutane musulmai da waɗanda ba musulmai ba, Allah - maɗaukakin sarki - Ya ce:
{Kuma rahama Ta ta yalwaci dukkan komai}
[Surat Al-A'a raf: 156].
To Shine Yake azairata su gaba ɗayan su, kuma Yake basu lafiya da abinci da 'ya'ya da wanin wannan, amma rahamar Sa a lahira to bata kasancewa sai ga muminai daga bayin Sa, masu bin Annabawa da Manzannin Sa, to waɗan nan suna da cikakkiyar rahama mai sadarwa zuwa tsira na dindindin.
$ Mahalicci: Allah maɗaukakin sarki - Ya ce:
{Allah shi ne Mahaliccin komai}
[Surat Al-Zumar: 62].
Shine wanda Ya halicci sammai da ƙasa da abin da ke tsakanin su, kuma Ya halicci kowane abu daga ƙwaya zuwa Majarra, da abin da ke mafi yalwa daga hakan, kuma halittar Sa ta kasance da hikima, da iko, da kyautatawa, bazaka taɓa ganin tawaya ko ɓaci a halittar Sa ba.
$ Mai Yawan gafara: Wanda Yake gafarta zunubai gaba ɗaya ga wanda ya tuba yana mai gaskiya, duk yanda yazo da ayyukan da suka rigaya, kai yana yin afuwa daga yawa daga halittar Sa dan karamci daga kan Sa - ban da shirka a cikin bautar Allah - maɗaukakin sarki -, to Shi baya gafartawa sai da tuba -, haƙiƙa Allah Ya buɗe hanyoyi ga dukkanin halittar Sa dan neman gafarar Sa, da tuba, da neman gafara, da imani, da aiki na gari, da kyautatawa zuwa halittar Allah, Allah - maɗaukakin sarki - Ya ce:
{Kuma lalle Nĩ haƙĩƙa Mai gãfara ne ga wanda ya tũba kuma ya yi ĩmãni, kuma ya aikata aikin ƙwarai, sa'an nan kuma ya nẽmi shiryuwa}.
[Surat Al-Najm: 82].
$ Mai yawan azirtawa: Allah - tsarki ya tabbatar maSa - Shine sarkin da mallakin kowane abu yake a hannun Sa, Shine Mawadaci, kuma daga falalar Sa cewa Shi Mai yawan kyauta ne, babu wani abin halitta sai arziƙin sa yana ga Allah, Allah - maɗaukakin sarki - Ya ce:
{Kuma Ban halitta aljannu da mutãne ba sai dõmin su bauta Mini}
{Bã Ni nufln (sãmun) wani arziki daga gare su, Bã Ni nufin su (yi Mini hidimar) ciyar da Ni}
{Lalle Allah, Shĩ ne Mai azurtãwa, Mai ĩkon yi, Mai cikakken ƙarfi}
[Surat Al-Zariyat: 56-58].
$ Assalam: Abin girmamawa abin tsarkakewa daga aibuka da kuma siffofin tawaya gaba ɗayan su, wanda yake da siffofin cika da ɗaukaka da kyau, wanda yake son yaɗa sallama daga bayin Sa da faɗa da kuma aiki, Allah - maɗaukakin sarki - Yana cewa:
Shi ne Allah ,wanda babu wani abin bautawa da gaskiya sai Shi sarki tsarkakkke amintacce}
[Surat Al-Hashr: 23].
$ Mai yawan sani: Allah - maɗaukakin sarki Masani ne, Mai gani ne, kuma Masani ne, sanin Sa ya kewaye dukkanin komai, Shi yana sanin abin da ke bayyane, da abin da ke ɓoye, da abin da ƙiraza suka ɓoye, kuma Yana sanin abin da ya kasance a lokacin da ya wuce, da abin da ya kasance a yanzu, da abin da zai kasance a nan gaba, Shine mai kiyayewa wanda Yake tsinkaye akan ayyukan bayi, biyayyar masu biyayya bata ɓoyuwa gare Shi, ko saɓon masu saɓo, ko buƙatar raunana, ko muryoyin masu addu'a, Allah - maɗaukakin sarki - Ya ce:
{Lallai Allah masani ne da dukkanin komai}
[Surat Al-Baƙara: 231].
Shi - tsarki ya tabbatar maSa - Ubangijin talikai ne, wanda Ya kyautata haliattar kowane abu, kuma dukkanin kyau da cika a wannan duniyar, to shi yana daga alamomin cikar Sa - tsarki ya tabbatar ma Sa -.
TUSHE NA BIYU; MENENE ADDININ KA
Addinina shine Musulunci:
Musulunci: Shine miƙa wuya ga Allah, da kaɗaitawa, da jawuwa gare Shi da biyayya, da kuma kuɓuta daga shirka.
Musulmi shine wanda yake shiga Addinin Musulunci, kuma yake miƙa al'amarin sa ga Allah - maɗaukakin sarki -, yana mai imani da samuwar Sa da kuma kaɗaitakar Sa, mai jawuwa ga umarnin Sa, mai nisantar abin da Yayi hani a kansa, Allah - maɗaukakin sarki - Yana faɗa a cikin Al-ƙur'anin Sa mai girma:
{Kuma wãne ne ya fi kyau ga addini daga wanda ya sallama fuskarsa ga Allah, alhãli kuwa yanã mai kyautatawa kuma ya bi aƙidar Ibrãhĩm, Yanã mai karkata zuwa ga gaskiya? Allah Yã riƙi Ibrãhĩm badãɗayi}
[Surat Al-Nisa'a: 125].
Kuma Yana cewa:
{Kuma wãne ne mafi kyau ga magana daga wanda ya yi kira zuwa ga Allah, kuma ya aikata aiki na ƙwarai kuma ya ce: "Lalle nĩinã daga mãsu sallamãwar al'amari zuwa ga Allah?}
[Surat Fussilat: 33].
YANA DAGA KYAWUN ADDININ MUSULUNCI:
Musulunci Addinin adalci ne: Yana umarni da adalci tare da na kusa da na nesa, da maƙiyi da aboki, da mumini da kafiri, Allah - maɗaukakin sarki - Yana cewa:
{Allah Allah Yana umarni da adalci}
[Surat Al-Nahl: 90].
Allah - mai girma da ɗaukaka - Mai hukunci ne, kuma Adali ne, ba'a zalintar wani ɗaya a wurin Sa, maɗaukakin sarki Yana faɗa game da ranar Al-ƙiyama:
{Yau anã sãka wa kõwane rai a game da abin da ya aikata, bãbu zãlunci a yau}
[Surat Ghafir: 17].
Musulunci Addinin rahama ne: Allah - maɗaukakin sarki - Yana cewa:
{Kuma ba Mu aike ka ba fãce dõmin wata rahama ga talikai}
[Surat Al-anbiya: 107].
Kuma Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - yana cewa:
"Masu jin ƙai Allah Yana jin ƙan su, kuji ƙan mutanen dake bayan ƙasa wanda yake sama zaiji ƙanku".
Abu Daud ne ya ruwaito shi.
Musulunci Addinin soyayya ne da haɗuwa da sabo: Annabi Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - yana cewa:
"Dayanku ba zaiyi imani ba har sai ya sowa ɗan uwan sa abin da yake sowa kan sa".
Bukhari ne ya rawaito shi.
Musulunci Addinin sauƙi ne: Koyarwar Musulunci a cikin sa akwai sauƙaƙawa da ɗauke ƙunci dukkanin wanda yake tsinkaye akan koyarwar sa zai san shi, Allah - maɗaukakin sarki Yana cewa:
{Allah Yana nufin sauki gare ku, kuma baya nufin tsanani gare ku}
Kuma Yana cewa:
{Allah baya nufin sanya wani ƙunci gare ku}
[Surat Al-Ma'idah: 6].
Kuma Yana cewa:
{Allah baya ɗorawa wata rai sai abin da zata iya}
[Surat Al-Baƙara: 286].
Musulunci Addinin ilimi ne: Farkon ayar da ta fara sauka a Al-ƙur'ani ita ce:
{Ka yi karatu da sunan Ubangijin ka, wanda Ya yi halitta}
[Surat Al-Alaƙ: 1].
Musulunci yana kwaɗaitar da kowane musulmi namiji da musulma mace akan neman ilimi da neman ƙarin ilimi, Allah - maɗaukakin sarki - Ya ce:
{Kuma ka ce Ya Ubangiji ka ƙara mini ilimi}
[Surat Daha:114].
Mai neman ilimi yana da mafi ɗaukakar darajoji, tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka Yana cewa:
{Allah yana ɗaga darajojin waɗanda sukai imani daga cikin ku kuma da waɗanda aka bawa Ilimi}
[Suratu Al-Mujadalah: 11].
GAMEWAR ADDININ MUSULUNCI (DUK DUNIYA):
Musulunci Addinine na duniya, bai keɓanci wani bigire a ƙasa banda waninta ba, ko wasu jama'a banda wasun su, ba Addinin larabawa bane su kaɗai, kaɗai shi Addinin kowaɗane mutune ne, Allah - maɗaukakin sarki - Ya faɗa Yana mai magana da Annabin Sa Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - a cikin Al-ƙur'ani mai girma:
{Ka ce: "Yã kũ mutãne! Lalle ne nĩ manzon Allah nezuwa gare ku, gabã ɗaya. (Allah) Wanda Yake Shĩ ne da mulkin sammai da ƙasa; Bãbu wani abin bautawa fãce Shi, Yanã rãyarwa, kuma Yanã matarwa, sai ku yi ĩmãni daAllah da ManzonSa, Annabi, Ummiyyi, wanda yake yin ĩmãni da Allah da kalmominSa; ku bĩ shi, tsammãninku, kunã shiryuwa}
[Surat Al-A'araf: 158].
Kamar yanda cewa shi, ba abin keɓancewa bane da wani zamanin da ya wuce, kai shi Addini ne na gaskiya daga aiko Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - zuwa ranar Al-ƙiyama, Allah - maɗaukakin sarki - Ya ce:
{Kuma wanda ya nẽmi wanin Musulunci ya zama addini, to, bã zã a karɓa daga gare shi ba. Kuma shi a Lãhira yana daga cikin mãsu hasãra}
[Surat Aal Imran: 85].
TATTAROWAR ADDININ MUSULUNCI:
Musulunci shine hanyar rayuwa ga musulmi ɗaya, da kuma jama'ar musulmai, da kuma al'umma musulma, a cikin kowane sasanni da fage, a siyasa ne da tattalin arziƙi da ilimin zamantakewa da wasun su.
Musulunci aƙida ne da shari'a: Shi mai tattarowa ne akan inagntattun aƙidu, da ibadu masu girma, da mu'amaloli masu hikima, da ɗabi'u masu kyau, da tsararran hali.
Koyarwar Musulunci da hukunce-hukuncen sa suna kyautata alaƙar mutum da Ubangijin sa, da alaƙar mutum da kan sa, da laƙar mutum da wanin sa daga mutane, kai har alaƙar sa da dabbobi da kuma sandararrun abubuwa.
Koyarwar Musulunci ta tattaro abin da yake rataya da gyara rai da jiki.
A dunƙule dai: Musulunci ya zo da abin da abin da a cikin sa akwai mafi alheri ga mutane da gyaran su da kuma arziƙin su a duniya da lahira.
GINSHIKUN AKIDUN MUSULUNCI (RUKUNAN IMANI):
Ginshiƙun aƙidar Musulunci suna misaltuwa a cikin imani da gasgatawa a yanke da abubuwa shida, ana ambatan su da sunan (Rukunan imani), sune:
1- Imani da Allah - maɗaukakin sarki -: Wato imani da samuwar Allah, kuma cewa Shi Shi kaɗai yake Mahalicci Mamallaki Mai jujjuya kasantacce dukkanin sa da dukkanin abin da ke cikin sa, kuma cewa Shi Shine wanda Yake cancantar bauta Shi kaɗai baShi da abokin tarayya, kuma cewa Shi Mai siffantuwa ne da siffofin kyau da ɗaukaka, kuma cewa Shi cikakke ne abin tsarkakewa daga kowane aibi da tawaya, kuma cewa Shi babu wani tamkar Sa.
2- Imani da Mala'iku: Su wata halitta ne daga halittun Allah - maɗaukakin sarki -, Ya halicce su dan bautar Sa, da cikakkiyar jawuwa ga umarnin Sa, da tsayuwa da zartar da abin da aka wakilta su akan sa na ayyuka, to muna imani da samuwar su a dunƙule, kamar yanda muke imani da sunaye da siffofi da ayyukan waɗanda wahayi ya bamu labarin su a rarrabe, kamar jibril wanda Allah Yake aiko shi da wahayi zuwa Annabawa da Manzanni, da Mika'il wanda aka wakilta da ruwa da tsirrai, da Israfil abin wakiltawa da busa ƙaho, da Mala'ikan mutuwa wanda yake ɗaukar rayukan mutane, da Malik mai tsaron wuta.
3- Imani da littattafai: Sune littattafan da Allah Ya saukar da su ga Manzannin Sa, dan rahama ga halitta, da shiryar da su؛ dan su sadu zuwa azirtar duniya da lahira, sai muyi imani da su a dunƙule, kuma muyi imani da abin da muka san sunan sa ta hanyar wahayi a rarrabe, kamar Al-ƙur'anin da aka saukar ga (Annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, da Injila wacce aka saukar ga (Annabi) Isa - aminci ya tabbata a gare shi -, da Attaura wacce aka saukar da ita ga (Annabi) Musa - aminci ya tabbata a gare shi -, da Zabura wacce aka bada ita ga (Annabi) Dawud - aminci ya tabbata a gare shi -, da takardun da Allah Ya saukar da su ga (Annabi) Ibrahim - aminci ya tabbata a gare shi -.
4- Imani da Manzanni: Su mutane ne Allah - maɗaukakin sarki - Yayi musu wahayin shiriyu, kuma Ya aiko su zuwa ga mutane dan su isar da Addinin Sa, na farkon su shine (Annabi) Nuhu - aminci ya tabbata a gare shi -, na ƙarshen su shine (Annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, sun kasance akan cika Addini da ɗabi'u, mafi muhimmancin manufar wanda Ya aiko su shine kiran mutane zuwa kaɗaita Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - da ibada, kuma su bar shirka da bautar wanin Sa, kuma su aikata alheri, su bar sharri.
Sai muyi imani da cewa Allah Ya aiko Manzanni daga mutane, kuma Ya wajabtawa bayi gasgata su cikin abin da suka bada labari da shi da biyayyar su da bin abin da aka umarce su da shi, kuma musan cewa daga cikin su akwai waɗanda Allah Ya bamu labari da sunayen su da kuma ƙissoshin su, tare da mutanen su misalin: Idris, da Nuhu, da Ibrahim, da Musa, da Isa, da Hudu, da Salihu, da Shu'aibu, daga cikin su akwai waɗanda Allah Bai bamu labarin sunayen su ba, Allah - maɗaukakin sarki - Ya ce:
{Kuma lalle haƙĩƙa, Mun aika wasu Manzanni daga gabãninka, daga cikinsu akwai wanda Muka ƙissanta maka lãbãrinsa kuma daga cikinsu akwai wanda ba Mu ƙissanta lãbãrinsa ba a gare ka. Bã ya yiwuwa ga wani Manzo ya jẽ da wata ãyar mu'ujiza fãce da iznin Allah. Sa'an nan idan umurnin Allah ya jẽ, sai a yi hukunci da gaskiya, mãsu ɓãtãwa sun yi hasara a can}
[Surat Gafir: 78].
5- Imani da ranar lahira: Itace ranar Al-ƙiyama, wacce Allah Zai tashi mutane a cikinta, dan yin hisabi da sakayya akan ayyukan su, waɗanda suka aikata su a duniya, ta in da mutane suke rabuwa gida biyu: Sai muminai su tabbata a Aljanna suna madawwama a cikinta har abada, kuma kafirai su tabbata a wuta suna madawwama a cikinta har abada, wanda ya kasance mumini sai dai yana aikata laifuka, ko dai Allah - maɗaukakin sarki - ya gafarta masa, ko Ya azabtar dasu tsawon wani lokaci sannan Ya shigar da su Aljanna.
6- Imani da ƙaddara alherin Sa da sharrin Sa: Sai musulmi yayi imani da cewa Allah Yana sanin abin da ya kasance, da abin da zai kasance, kuma cewa Allah Ya rubuta abubuwan ƙaddarawar halittu kuma Ya nufe su sai Ya samar da su, wani abu bazai afku ba a cikin kasantacce sai da sanin Sa, da rubutawar Sa, da abinda yaso shi, da halittar Sa, idan ya kasance alheri ne to shi daga rahamar Allah ne - maɗaukakin sarki - da shi, idan ya kasance wanin hakan to shi jarraba ne daga Allah - maɗaukakin sarki -, ko uƙuba ne, kuma ya gudana da hikimar Allah Ya ɗaukaka da adalcin Sa, wacce mutum bazai kewaye ba da su dan girman su da kuma cikar su, idan bawa yayi imani da ƙaddara alherin Sa da sharrin Sa zuciyar sa zata nutsu ransa zai huta, zai miƙa al'amauran sa dukkanin su ga Allah - maɗaukakin sarki -؛ domin cewa shi yana sanin kowane abu yana hannun Allah Shi kaɗai, abin da Yaso zai kasance, abin da Bai so ba bazai kasance ba.
RUKUNAN MUSULUNCI:
Rukunan Musulunci sune ginshiƙen sa waɗanda aka gina shi akan su, su rukunai biyar ne, yana wajaba ga musulmi tsayuwa da su:
1- Shaidawa cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma Annabi Muhammad Manzon Allah ne: Itace shaidar da za'a faɗa da harshe, kuma zuciya zata dace da ita, da cewa Allah Shine abin bauta na gaskiaya Shi kaɗai yake, baShi da abokin tarayya, kuma cewa Annabi Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - shine Manzo mai iasarwa daga Allah.
2- Tsaida sallah: Yana wajaba akan musulmi, yayi salloli biyar a yini da dare, sallar da take da tsayuwa da ruku'u da sujjada؛ dan girmamawa ga Allah - maɗaukakin sarki -, kuma tana da lokuta da ake ambatan su da sunan su, sune: Sallar Asuba, da sallar Azahar, da sallar La'asar, da sallar Magariba, da sallar Issha'i, acan akwai wasu sallolin daban ba wajibai bane.
3- Bada Zakka: Wato musulmi wanda yake da dukiya, ya fitar da wani gwargwado mai sauƙi abin iyakancewa daga dukiyar sa, ya bada shi zuwa waɗanda suka cancance shi, daga mabuƙata da miskinai, da wasun su daga waɗanda ake bawa zakka.
4- Azimtar Ramadan: Wato musulmi ya kame daga abinci, da abin sha, da jima'i, da makamacin su daga masu karya Azimi, daga ɓullowar Alfijr zuwa faɗuwar rana a cikin watan Ramadan؛ dan bauta ga Allah - maɗaukakin sarki -.
5- Ziyarar ɗakin Allah mai alfarma: Shine tafiyar musulmi zuwa Makka abar girmamawa؛ dan bauta ga Allah - maɗaukakin sarki - da tsayawa da alamomin Hajji, ko da sau ɗaya ne a rayuwa, ga wanda ya sami ikon hakan.
IBADA A MUSULUNCI:
Ibada: Itace kaɗaita Allah - maɗaukakin sarki - da neman kusanci zuwa ga Allah da dukkanin abin da Yake sonsa kuma Ya yarda da shi daga maganganu da ayyuka na sarari da na ɓoye.
Daga maganganu: Akwai karatun Al-ƙur'ani, da Addu'a, da Ambaton Allah - maɗaukakin sarki -, da koyar da ilimi mai amfani, da gabatar da nasiha ga wasu, da sauran su.
Daga ayyuka kuma: Akwai tsarki da sallah, da Hajji, da kai ka wo a cikin buƙatun mutane, da wasun su.
Na bayyane kuma: Sune ayyukan da ake bayyanar da su kuma ake ganin su, ko ake jin su da makamancin hakan, kamar sallah da Hajji, da karatun Al-ƙur'ani, da kira zuwa ga Allah, da sada zumuncin 'yan uwa.
Na baɗini kuma: Sune ayyukan da suke kasancewa a cikin zuciya, kamar son Allah - maɗaukakin sarki - da ƙaunar Sa, da tsoron Sa, da ƙanƙar da kai, da dogaro ga Allah - maɗaukakin sarki -.
MUHIMMANCIN IBADA A MUSULUNCI:
Bautar Allah - maɗaukakin sarki - itace matuƙar wacce saboda inae Allah Ya halicci mutane, Allah - maɗaukakin sarki - Ya ce:
{Kuma Ban halitta aljannu da mutãne ba sai dõmin su bauta Mini}
[Surat Al-Zariyat: 56].
Haƙiƙa an shara'anta ibada dan hikimomi masu girma, da maslahohi masu yawa da suke tabbata a cikin rayukan mutane da rayuwar su, daga falalolin ibada cewa, ita tana tsarkake rayuka, tana tsarkake su, kuma tana ɗaukaka su zuwa mafi ƙololuwar darajojin cika na mutum.
Mutum mabuƙaci ne zuwa bauta mafi girman buƙata, kamar yanda jikinsa yana cikin buƙata zuwa abinci da abin sha, to haka nan zuciyar sa da ran sa suna cikin buƙata zuwa fuskantowa zuwa ga Allah da ibada, rai baya nutsuwa sai da ambaton Allah da bautar Sa, zuciya bata azirta, ƙirji baya buɗewa sai da neman kusanci zuwa ga Allah - maɗaukakin sarki - da kyakykayawar alaƙa da shi, ma'abota ibada na gaskiya sune mafi azirtar mutane, kuma mafi buɗewar su ƙirji, wanda yake son azirta to ya lazimci bakin ƙofar bauta ga Allah Shi kaɗai.
TATTAROWAR IBADA A MUSULUNCI:
Ibada a Musulunci ta tattaro dukkanin ayyuka na gari waɗanda Allah Yake son su, kuma waɗanda muke neman kusanci da aikata su zuwa gare Shi - mai girma da ɗaukaka, ita ta tattaro:
- Alamomi na bauta: Kamar sallah, da Zakka, da Azimi, da Hajji, da karatun Al-ƙur'ani, da Addu'a, da ambaton Allah - maɗaukakin sarki -, da wasunsu.
- Da kyakykayawr mu'amala: Kamar biyayya ga iyaye, da sada zumunci, da kyakykyawar mu'amala tare da mata da 'ya'ya, da kyakykaywan siye da siyarwa, da kyautata yin ayyuka, da kyautatawa maƙota, da taimakon miskinai, da kyautatawa dabbobi, da wanin hakan.
- Hakanan ta tattaro ɗabi'u masu kyau: Kamar gaskiyar zance, da dawo da amana, da cika alƙawarurruka, da murmushi, da kalma mai daɗi, da kunya, da wanin hakan daga ɗabi'u.
Musulmi yana bautawa Allah a dukkanin halayen sa, yana bautawa Allah a cikin masallaci, a cikin gida, a wurin aiki, a kowane wuri, rayuwar sa gaba ɗayan tana ga Allah ne - maɗaukakin sarki -, Allah - maɗaukakin sarki - Ya ce:
{Ka ce: "Lalle ne sallãta, da baikõna, da rãyuwãta, da mutuwãta, na Allah ne Ubangijin tãlikai}
[Surat Al-An'am: 162].
TUSHE NA UKU: WAYE ANNABIN KA?
Annabi na Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -.
Annabin mu shine: Muhammad ɗan Abdullahi ɗan Abdul Muɗɗalibi ɗan Hashim, nasabar sa tana komawa zuwa ga Annabin Allah Isma'il ɗan Annabin Allah Ibrahim - tsira da aminci ya tabbata gare su da Annabin mu -.
Allah Ya aiko shi a Makka abar girmamawa alhali shekarun sa arba'in, kuma Ya saukar masa da Al-ƙur'ani, sai ya kira mutane zuwa tauhidi da Addinin Musulunci, sai mutanen sa suka cutar da shi mafi tsananin cutarwa, suka azabtar da sahabban sa, suka kashe wani adadi daga cikin su, sannan yayi hijira zuwa Madina Yasriba (Sannan sunan ta ya zama Madinar Annabi), bayan shekara goma sha uku, acan ya tsaida daular Musulunci, ya kafa al'ummar musulmi, ya wanzu a cikinta shekara goma yana shiryarwa yana fuskantarwa yana sanarwa, ya zarce akan haka har sai da shari'a ta cika, sai Musulunci ya cika da hakan ya kuma cika Addini, faɗin Allah - maɗaukakin sarki - ya sauka:
{Kuma yaune muka cika muku Addininku kuma muka cika muku ni'amarku kuma muka yarje muku Musulun a matsayin Addini}
[Surat Al-Ma'ida: 3].
Sannan - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya rasu bayan yayi farin ciki da ganin mutane suna shiga Addinin Allah dan soyayya da biyayya, kamar yanda Allah - Ya girmama Ya ɗaukaka - Ya ce:
{Idan taimakon Allah ya zo da cin nasara}
{Kuma ka ga mutane suna shiga addinin Allah, ƙungiya ƙungiya}
{To, ka yi tasbihi game da gõde wa Ubangijinka, kuma ka nẽme Shi gafara, lalle Shi (Ubangijinka) Ya kasance Mai karɓar tũba ne}
[Surat Al-Nasr: 1-3].
ANNABIN RAHAMA:
Annabin mu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - shine Annabin rahama, rahama bata rabu da shi ba a dukkanin tarihin sa, da kuma dukkan matakan rayuwar sa da halayen sa, Alla - maɗaukakin sarki - Ya ce:
{Kuma ba Mu aike ka ba fãce dõmin wata rahama ga talikai}
[Surat Al-anbiya: 107].
Yana daga rahamar sa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - cewa shi mai tsananin kwaɗayi akan shiriyar mutanene, da fitar da su daga duffan kafirci da jahilci da ɓata zuwa hasken imani da ilimi da shiriya, yayin da mutanen sa basuyi imani ba ya kusa ya halaka kan sa dan baƙin ciki da ɓacin rai abisa rashin imanin su, Allah - maɗaukakin sarki - Ya ce:
{To, kã yi kusa ka halaka ranka a gurabbansu, wai dõmin ba su yi ĩmãni da wannan lãbãri ba sabõda baƙin ciki}
[Suart Al-Kahf: 6].
Hakanan ma'anonin rahamar sa take bayyana a cikin kwaɗayi ga muminai, da tausayin sa ga su, Allah - maɗaukakin sarki - Ya ce:
{Lalle ne, haƙĩƙa, Manzo daga cikinku yã je muku. Abin da kuka wahala da shi mai nauyi ne a kansa. Mai kwaɗayi ne sabõda ku. Ga muminai Mai tausayi ne, Mai jin ƙai}
[Surat Al-Taubah: 128].
A cikin kwaɗayin sa ga sauƙaƙawar Addini da rashin ɗorawa al'aummar sa abin da zai wahalar da su, da abin da baza su iya tsayuwa da shi ba, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: "Ku sauƙaƙa kada ku tsananta, kuma kuyi albishir kada ku kore". Bukhari da Muslim ne suka ruwaito shi.
Haƙiƙa ran Manzo mai girma ta cika da rahama, ya kasance mafi jin ƙai, ga mata da 'ya'ya, ɗaya daga sahabban sa ya ce, shine Anas ɗan Malki - Allah Ya yarda da shi -; "Ban taɓa ganin wani ɗaya ba da ya kasance mafi jin ƙai ga iyali fiye da Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ba -" Muslim ne ya ruwaito shi.
Rahamar sa bata tsayaba - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ga mutane ba, kai ta ƙetara zuwa dabbobi, sai yayi kira zuwa kayautata musu ya gargaɗar abisa cutar da su, ya bayyanawa sahabban sa cewa, wata mata karuwa ta shayar da wani kare sai Allah Ya gafarta mata Ya shigar da ita Aljanna, kuma wata mace ta shiga wuta domin cewa, ita ta tsare wata mage bata ciyar da ita ba har ta mutu.
MANZANCIN SA MAI GAMEWA NE GA DUKKANIN MUTANE:
Annabawa da Manzannin da suka rigaya - tsira da aminci ya tabbata a gare su - sun kasance ana aiko su ne zuwa mutanen su akeɓance, amma Annabi Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - to Manzancin sa mai gamewa ne, ga dukkanin mutane a kowane zamani da wuri.
Allah - maɗaukakin sarki Ya ce:
{Bamu aiko ka ba sai zuwa ga mutane baki daya Mai gargaɗi kuma Mai bushara}
[Surat Saba'i: 28].
Allah - maɗaukakin sarki - Ya ce:
{Ya ku mutane ni manzon Allah ne zuwa gare ku baki ɗaya}.
[Surat Al-A'araf: 158].
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce:
"Annabi ya kasance ana aiko shi zuwa ga mutanen sa a keɓance, ni kuma an aiko ni zuwa mutane baki ɗaya".
Bukhari ne ya rawaito shi.
To yana wajaba akan kowane mutum, tun daga aiko shi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - a cikin wannan zamanin, har zuwa tashin Al-ƙiyama bin sa, da gasgata abin da ya zo da shi, da shiga cikin Addinin sa, haƙiƙa Allah Ya cika saƙonnin sama da shi, kuma Ya wajabta biyayyar sa, wanda ya bishi ya azirta a duniya, zai shiga Aljanna a lahira, wanda ya saɓa masa ya taɓe a duniya, kuma zai shig wuta a lahira, Allah - maɗaukakin sarki - Ya ce:
{Wanda yabi shiriyata to ba zai ɓata ba kuma bazai taɓe ba} (123)
{Kuma wanda ya bijire daga ambatõNa (Alƙur'ãni) to, lalle ne rãyuwa mai ƙunci ta tabbata a gare shi, kuma Munã tãyar da shi a Rãnar ¡iyãma yanã makãho}.
[Surat Daha: 123 - 124].
MANZO TSIRA DA AMINCIN ALLAH SU TA BBATA A GARE SHI - A CIKIN GIDAN SA KUMA TARE DA IYALAN SA:
Gidan mutum shine gurin da yake bayyana kyan ɗabi'un sa, da kuma cikar ladabin sa, da tsarkin mu'amalar sa, lokacin da mutum ya kasance tare da matar sa ko 'ya'yan sa da almajirin sa to cewa shi yana aiki ne akan ɗabi'ar sa batare da ɗorawa kai wata wahala ba.
Wanda ya lura da halin Manzon al'ummar Musulunci kuma jagaoran ta malamin ta - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - a cikin gidan sa, zai samu cewa shi ya gabatar da mafi kyan misalai, ga abin da yake kamata mutum mai hankali ya zama a cikin gidan sa, kuma tare da iyalin sa da 'ya'yan sa.
Ancewa A'isha matar Annabi - Allah Ya yarda da ita -: Me Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kasance yakeyi a gidan sa? Ta ce:
"Ya kasance a cikin hidimar iyalin sa - tana nufin hidimar iyalin sa - idan sallah tazo sai ya fita zuwa sallah".
Muslim ne ya rawaito shi.
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kasance mafificin mutane ga iyalin sa da matan sa, yana gabatar da wasu surori masu ƙayatar wa, a cikin kyakkyawar mu'amala, da taushin gefe, da sanin kwaɗayin zuciya da rai ga matar sa, kuma yana amfani da lokutan da suka da ce dan shigar da nishaɗi gare ta da sata walwala, A'isha - Allah Ya yarda da ita - tana cewa:
"Haƙiƙa naga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - wata rana a ƙofar ɗakina alhali mutanen Habasha suna wasa a cikin masallaci, Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - yana kareni da mayafin sa, ina kallon wasan su".
Bukhari da Muslim ne suka ruwaito shi.
Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kasance yana son 'ya'yan sa mata kuma yana girmama su, haƙiƙa ya kasance idan 'yar sa Faɗima ta shigo gurin sa sai ya miƙe gareta ya sumbaceta ya kuma zaunar da ita a majalisin sa, kuma ya kasance yana ziyarar 'ya'yan sa mata kuma yana bibiyar halayen su.
Yana daga wasiyyoin sa - tsira da aminci su tabbata a gare shi - ga al'ummar sa faɗin sa:
"Ku yi wasiccin alheri ga mata".
Bukhari da Muslim ne suka ruwaito shi.
Yana daga ɗabi'un Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -:
Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kasance mafificin mutane a ɗabi'u, kuma mafi kyan su a ladabi, haƙiƙa Allah - maɗaukakin sarki - Ya siffanta shi da faɗin sa:
{Kuma, lalle haƙiƙa kana a kan hãlãyen kirki, manya}
[Surat Al-ƙalam: 4].
Ya kasance yana jin daɗi da cika a cikin ɗabi'un sa, wanin sa bai kaishi ba, yayin da aka tsare shi daga kowane tawaya, kuma ya tattaro cika daga dukknin falala, ɗabi'un sa sun kasance Al-ƙur'ani ne mai girma, da yake ladabtuwa da shi, kuma yake ladabtar da mutane da shi, daga ɗabi'un sa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -:
- Lallai cewa shi ya kasance mafi haƙurin mutane, mafi adalcin su, mafi kamewar su, mafi kyautar su, kuma mafi karamcin su.
- Ya kasanace mafi tsananin mutane a kunya.
- Ya kasance mai ƙanƙar da kai, yana amsa kira daga kowane mutum, kuma yana karɓar kyauta ko da tayi ƙaranci, kuma yana sakayya akan ta.
- Ya kasance yana gaida marasa lafiya, yana halartar jana'izoji, yana zama da talakawa, yana cin abinci tare da miskinai, yana girmama ma'abota falala da ɗabi'u, kuma yana jawo hankalin ma'abota ɗaukaka.
- Ba wani ɗaya da zaizo masa sai ya tsaya akan buƙatar sa, bai kasance mai kausasawa ba, ko mai kaurin magana, bai kasance yana saka mummuna da mummuna ba, sai dai yana afuwa yana kau da kai, sai dai idan an keta alfarmar Allah, to a lokacin zaiyi fushi sabo da Allah ba dan kan sa ba.
- Ya kasance daga ɗabi'un sa, yana farawa wanda ya haɗu da shi sallama, ya kasance idan ya haɗu da ɗaya daga sahabban sa yana fara yi masa musafaha.
- Ya kasance yana bawa duk wanda ya zauna dashi rabonsa na fuskar sa, da jin sa, da zancen sa, da tattausan kyautatawar sa da fuskantar sa.
- Ya kasance mafi rangwamin mutane, kuma mafificin mutane, kuma mafi amfanawar mutane ga mutane.
- Yana kakaci amma baya faɗa sai gaskiya, mai yawan murmushi ne, yana dariya ba tare da kyakyatawaba, yana tsere da matan sa yana tausasa musu.
- Ya kasance yana cin abin da yazo, baya dawo da abin da ya samu, baya aibata abinci ko sau ɗaya, idan ya samu dabino sai ya ci shi, idan kuma ya samu nama zai ci shi, idan ya samu gurasar alkama ko wake zai ci ta, idan ya samu abu mai zaƙi ko zuma zai ci shi, idan ya samu nono ba tare da gurasa ba sai ya isu da shi, idan ya samu kankana ko ɗanyen dabino sai ya ci shi.
- Ya kasance yana sanya abin da ya samu, wani lokaci mayafi, wani lokaci sufi, abin da ya samu na abin da aka halatta sai yasa.
- Ya kasance yana hawa abin da sawwaƙa gare shi, wani lokaci doki, wani lokaci kuma raƙumi, wani lokaci alfadari, wani lokaci jaki, ko ya tafi akan digadigan sa.
Ya kasance wani lokaci baya shuɗewa gare shi batare da wani aiki ga Allah - maɗaukakin sarki - ba, ko a abin da babu makawa gare shi, na gyaran kan sa da iyalan gidan sa.
Zuwa wanin haka, daga ɗabi'u mafifita da tsarkakikkiyar mu'amala.
KAMMALAWA
Musulunci Addinin ne mai girma, yana tabbatarwa musulmin - da yake lazimtar koyarwar sa - hutu da rayuwa mai daɗi da gyara hali a duniya, da tsayayyiyar ni'ima da arziƙi madawwamiya a lahira, haka nan yana tabbatarwa da al'ummar musulmi wanda ya lazimci koyarwar sa ɗaukaka, da ci gaba, da tsarkaka, da ƙaruwa, da haɗuwar kan al'umma, da aminci, da amincewa.
Farin ciki ya tabbata gareka, ya kai mai shiryuwa zuwa Musulunci da wannan ni'imar mai girma, ya san aƙidar sa da shari'ar sa, da koyarwar sa da hukunce-hukuncen sa, da ɗabi'un sa, da ladubban sa, yayi riƙo da hakan a ransa, ya lazimce shi a dukkanin sasannin rayuwar sa gwargwadan ikon sa, domin cewa shi zai ga gurbin Musulunci a gareshi, kuma ta yaya zai maida shi mutum na gari, da yake farin ciki a kansa, kuma dukkanin wanda ke gefen sa ya tsirira da shi, daga mahaifa ne da mata da 'ya'ya, da makusanta da maƙota da abokanai, da dukkanin wanda yake hulɗa tare da musulmin da Allah Ya girmama shi da shiga cikin Addinin Sa, da tafiya a cikin hanya mai sadarwa zuwa gare Shi.
Wannan ɗan ƙaramin littafin, shine farkon hanyar ka a cikin neman sanin hukunce-hukuncen Addinin ka, sannan ya wajaba akan ka bayan sa kayi ƙoƙari a neman ƙarin ilimi mai amfani da aiki na gari da tsarkake ranka, da gyara zuciyar ka, a duk lokacin da ilimin ka ya ƙaru da Musulunci da aikin ka da abin da ka sani sai kusancin ka ga Ubangijin ka mai girma - Ya buwaya Ya ɗaukaka - ya ƙaru, to ka fuskanto ga karatun Alƙur'ani da neman sani da karatu da bibbiyar ayoyin sa, ka tsinkaya ga tarihin manzon Allah Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - da sunnar sa, shine koyin ka da zakayi koyi da shi a cikin rayuwa, shi kaɗai ne wanda Allah Ya umarce ka ka karɓi dukkanin abin da yazo da shi, amma wanin sa daga mutane duk yanda matsayin su yakai to zancen su ana karɓar abin da ya dace da Al-ƙur'ani da sunnah daga gare shi ne, ana maida abin da ya saɓa musu, kashedin ka da jayayya a Addini, ka nisanci musu da saɓani da jayayya tare da 'yan uwan ka musulmai.
Muna roƙa mana Allah mu da kai dacewa da tabbata akan wannan Addinin, har mu haɗu da shi alhali shi yana mai yarda da mu, godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai, tsira da aminci su tabbata ga Annabin mu Muhammad da alayen sa da sahabban sa gaba ɗaya, da wanda ya bishi zuwa ranar sakayya.