العقيدة الصحيحة

العقيدة الصحيحة

AƘIDA INGANTACCIYA

Language: lang_ha
Prepared by: Kwamitin ilimi a ƙarƙashin jagorancin harkokin Addini a Masallacin Harami da Masallacin Annabi
Version: 1.1
Translations 10
English Spanish Persian French +6
Attachments 7
PDF
Audio
Video
+3

AƘIDA INGANTACCIYA

Kwamitin ilimi a ƙarƙashin jagorancin harkokin Addini a Masallacin Harami da Masallacin Annabi.

Da sunan Allah Mai rahama Mai jin ƙai.

Dukkan yabo ya tabbata ga Allah Ubangijin talikai, ina shaida cewa babu abin bautawa bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai Yake ba Shi da abokin tarayya, kuma ina mai shaida cewa (Annabi) Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa ne, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, tare da alayensa da sahabbansa, da waɗanda suka biyo bayansu da kyautatawa har zuwa ranar sakamako.

Bayan haka;

Lallai Allah - Maɗaukakin sarki - Ya halicce mu a wannan rayuwar ta duniya don wata manufa mai daraja da ɗaukaka; wato ita ce: Bauta maSa Shi kaɗai, da kuma tabbatar da tauhidi gare Shi, kamar yadda tsarki ya tabbatar maSa Ya ce: {Kuma Ban halitta aljannu da mutãne ba sai dõmin su bauta Mini. 56 Bã Ni nufln (sãmun) wani arziki daga gare su, Bã Ni nufin su (yi Mini hidimar) ciyar da Ni. 57 Lalle Allah, Shĩ ne Mai azurtãwa, Mai ĩkon yi, Mai cikakken ƙarfi.} 58 [al-Zariyāt: 56-58].

Wannan ita ce manufar halitta, wacce saboda ita ne Allah Ya halicci halitta, kuma Ya saukar da littattafai, kuma Ya aiko Manzanni, kuma Ya halicci aljanna da wuta, kuma Ya raba mutane zuwa ƙungiyoyi biyu: Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {...Wata ƙungiya tanã a cikin Aljanna kuma wata ƙungiya tãna a cikin Sa'ĩr.} [al-Shurā: 7].

- Tauhidi shi ne asalin Addini, wanda Allah ba Ya karɓar wani Addinin daga mutanen farko da na ƙarshe in ba shi ba, kuma shi ne sirrin Alƙur'ani, kuma tsantsar imani.

- Kuma Tauhidi shi ne Addinin Musulunci, shi ne imani da shiriya, shi ne tsoron Allah da aikin alheri.

Allah Ya sanya maSa suna Musulunci, sai (Allah) - tsarki ya tabbatar maSa - Ya ce: {Lalle Addini a wurin Allah, Shi ne Musulunci...} [Āl- Imrān: 19], Kuma (Allah) - tsarki ya tabbatar maSa - Ya ce: {Kuma wanda ya nẽmi wanin Musulunci ya zama Addini, to, bã zã a karɓa daga gare shi ba. Kuma shi a Lãhira yana daga cikin mãsu hasãra. 58} [āl Imrān: 85].

Ya kuma kira shi imani, sai (Allah) - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku yi ĩmãni da Allah da ManzonSa...} [al-Nisā': 136], Kuma Ya ce: {Kuce: "Mun yi ĩmãni da Allah, da abin da aka saukar zuwa gare mu...} [al-Baƙara: 136].

Kuma (Allah - Maɗaukakin sarki - ) Ya kira shi shiriya, sai Ya ce: {...Alhãli kuwa shiriya daga wajen Ubangijinsu, ta jẽ musu.) [al-Najm: 23].

Kuma Ya ambace shi tsoron Allah, (Allah) - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku bi Allah da taƙawa...} [al-Baƙara: 278], Kuma Ya ce: {Ya ku mutãne! Ku bi Ubangijinku da taƙawa...} [al-Nisā': 1].

Kuma Ya kira shi aikin alheri, sai (Allah) tsarki ya tabbatar maSa Ya ce: {...Amma Addini shi ne ga wanda ya yi ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira...} [al-Baƙara: 177].

- Shaidawa da Tauhidi shine abu na farko wanda bawa zai shiga cikin Musulunci da shi, sai ya ce: Ina shaida cewa babu abin bautawa da cancanta sai Allah, kuma ina shaida cewa (Annabi) Muhammad Manzon Allah ne.

- Kuma da tauhidi ne Allah Ya aiko dukkanin Manzanni, (Allah) - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma ba Mu aiki wani Manzo ba a gabãninka fãce Munã yin wahayi zuwa gare shi, cẽwa 'Lalle ne Shi, bãbu abin bautãwa da cancanta fãce Nĩ, sai ku bauta Mini. 25} [al-Anbiyā': 25], Kuma Ya ce: {Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun aika a cikin kõwace al'umma da wani Manzo (ya ce): 'Ku bauta wa Allah, kuma ku nĩsanci ɗãgũtu...'} [al-Nahl: 36]. Kuma (Annabi) Nuhu -Amincin Allah a gare shi - ya cewa mutanensa: {...Ku bauta wa Allah. Bã ku da wani abin bautãwa waninSa...} [al-A'arāf: 59], Kuma haka ma (Annabi) Hudu da Salihu da Shu’aibu da sauran su suka ce wa mutanensu.

- Kuma tauhidi shi ne wahayin Allah ga ManzanninSa masu daraja, (Allah) -tsarki ya tabbatar maSa - Ya ce: {Yanã sassaukar da malã'iku da Rũhi daga umurninSaa kan wanda Yake so daga bãyinSa, cẽwa ku yi gargaɗi cẽwa: Lalle ne shĩ, bãbu abin bautãwa da cancanta fãce Ni, sabõda haka ku bĩ Ni da taƙawa. 2} [al-Nahl: 2].

Ruhi shi ne wahayi, kuma an ce shine: Annabci.

- Kuma Ya sanya hakan wajibi ga ManzonSa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - har zuwa mutuwa, kamar yadda Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma ka bauta wa Ubangijinka, har mutuwa ta zo maka. 99} [al-Hijr: 99].

- Tauhidi shine asalin aikin ƙwarai, kuma shi ne sharaɗin karɓar aiki: Allah - tsarki ya tabbatar maSa - ba Ya karɓar aiki ko ibada sai idan an cika sharuɗɗa biyu: Tsarkake aiki ga Allah Shi kaɗai, da bi da kuma dacewa da shari'a, Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya ce: {...Sabõda haka wanda ya kasance yanã fãtan haɗuwa da Ubangijinsa, to, sai ya yi aiki na ƙwarai. Kuma kada ya haɗa kõwa ga bauta wa Ubangijinsa.} [al-Kahf: 110].

A cikin hadisi: «Allah - alherinSa ya yawaita Ya girmama - Ya ce: Ni ne Mafi wadatar abokanan tarayya daga shirka, duk wanda ya aikata wani aiki ya haɗa Ni da wani a cikinsa to Zan bar shi da shirkarsa». Muslim ne ya ruwaito shi.

- Kuma duk wani aiki da bai da alaƙa da Tauhidi; ba shi da wani nauyi, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Waɗancan ne waɗanda suka kãfirta da ãyõyin Ubangijinsu, da kuma haɗuwa da Shi, sai ayyukansu suka ɓãci. Sabõda haka bã zã Mu tsayar musu da awo ba a Rãnar ƙiyãma. 105} [al-Kahf: 105].

- Tauhidi shi ne haƙƙin da Allah - Mai girma da ɗaukaka - Ya wajabta a kan bayi, wanda idan suka zo da shi tsantsa zasu rabauta, idan kuma suka gauraya shi da shirka to zasu halaka, Allah - Maɗaukakin sarki - Yace: {Kuma an yi wahayi zuwa gare ka da kuma zuwa ga waɗanda suke a gabãninka, 'Lalle idan ka yi shirki haƙĩƙa aikinka zai ɓãci, kuma lalle zã ka kasance daga mãsu hasãra. 65} [al-Zumar: 65].

Kuma a cikin hadisin Mu'az - Allah Ya yarda da shi -: «Lallai cewa haƙƙin Allah a kan bayi shi ne: Su bauta maSa kada su haɗa wani abu da Shi, kuma haƙƙin bayi a kan Allah shi ne: Ba zai azabtar da wanda bai haɗa wani abu da Shi (a bauta) ba». Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi.

- Tauhidi yana kankare zunubai da kusakurai, (ya zo) a cikin hadisi Ƙudsi: «Ya kai ɗan Adam, lallai da zaka zo min da kusakurai kwatankwacin yawan ƙasa [Wato: Da kwatankwacinta da abin da ya kusance ta], sannan ka haɗu da Ni baka haɗa Ni da komai (a ibada) ba, tabbas, zan zo maka da gafara kwatankwacin yawanta.». Tirmizi ne ya rawaito shi kuma Al-Albani ya ce shi Hasan ne li gairihi.

- Tauhidi shine ƙofar aljanna wacce babu wanda zai shiga aljanna sai daga gareta, Kuma wanda ya yi shirka da Allah to haƙiƙa ya rufe wannan ƙofar, kamar yadda Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {...Lalle ne shĩ, wanda ya yi shirki da Allah, to, lalle ne, Allah Yã haramta masa Aljanna. Kuma mãkõmarka ita ce Wuta...} [al-Mā'ida: 72].

Allah - Maɗaukakin sarki - ba Ya gafartawa shirka idan mai yinta ya mutu a kanta, kamar yadda Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Lalle ne, Allah ba Ya gãfarta a yi shirki da Shi, kuma Yana gãfarta abin da yake bãyan wannan, ga wanda Yake so...} [al-Nisā': 48].

A cikin hadisi: «Duk Wanda ya gamu da Allah ba ya yi maSa shirka ba to zai shiga aljanna, kuma duk wanda ya gamu da shi alhalin yana yi maSa shirka to zai shiga wuta». Muslim ne ya ruwaito shi.

- Tauhidi shine wanda yake hana mai shi dawwama a cikin wuta, idan a cikin zuciya akwai ƙasa da ƙwayar komayya daga gareshi, (ya zo)a cikin hadisi: «Lalle Allah Ya haramtawa wanda ya ce La’ilaha illallahu wuta alhali yana mai neman yardar Allah da hakan». Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi.

- Tsintsar tauhidi shine wanda yake haifar da cikakken aminci a duniya da lahira, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Waɗanda suka yi ĩmãni, kuma ba su gauraya ĩmãninsu da zãlunci ba, waɗannan sunã da aminci, kuma sũ ne shiryayyu. 82} [al-An'ām: 82].

- Kuma da tauhidi ake samun ceton Manzo - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, (yazo) a cikin hadisi: «Mafi rabautar mutane da cetona a ranar alƙiyama shine wanda ya ce: La'ilaha illallahu, yana mai tsarkakewa daga zuciyarsa ko daga ransa». Bukhari ne ya rawaito shi.

- Kaɗaita Allah shine tafarkin da dukkan wannan kasantacce, mai rai da marar rai, suke bi, dukkansu suna miƙa wuya ga Allah da kaɗaita Shi, kuma suna tasbihi gare Shi, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Sammai bakwai da ƙasa da wanda yake a cikinsu sunã yi Masa tasbĩhi. Kuma bãbu wani abu fãce yanã tasbĩhi game da gõde Masa, kuma amma ba ku fahimtar tasbĩhinsu. Lalle ne shĩ, Ya kasance Mai haƙuri ne, Mai gãfara. 44} [al-Isrā': 44].

Gaba ɗaya dai... kalmar tauhidi kamar yadda Imam Ibnul Qayyim - Allah ya jiƙansa - ya faɗa a cikin littafinsa "Zadul Ma'ad": "Wata kalma ce wacce da ita ne ƙasa da sammai suka tsayu, kuma saboda ita ne aka halicci dukkan halittu, kuma da ita ne Allah - Maɗaukakin sarki - Ya aiko ManzanninSa, kuma Ya saukar da littattafanSa, kuma Ya shar'anta dokokinSa.

Saboda ita ne aka kafa ma'aunai, kuma aka sanya littattafai, kuma kasuwar Aljanna da Wuta suka tsayu, kuma saboda ita ne halitta ta kasu zuwa muminai da kafirai, da salihai da fajirai. Saboda haka ita ce asalin halitta da umarni, da sakamako da azaba, Kuma ita ce gaskiyar da aka halicci halitta dominta, kuma a kanta da haƙƙoƙinta ne tambaya da hisabi (suke), kuma a kanta ne ake samun lada da azaba. A kanta ne aka saka alƙibla, kuma a kanta aka assasa Addini, kuma saboda ita aka fito da takubban jihadi, Ita ce hakƙin Allah a kan dukan bayi, ita ce kalmar Musulunci, kuma mabuɗin gidan aminci.

Kuma daga gareta ne za a tambayi na farkon da na ƙarshe, don haka digadigan bawa a gaban Allah ba zasu gushe ba har sai an tambaye shi game da tambayoyi guda biyu: Me kuke bauta wa? Kuma da me kuka amsa wa manzanni? Amsa ta farko ita ce da tabbatar da cewa: "Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah", tare da sanin ma’anarta, da kuma tabbatarwa, da kuma aiki da abin da take nunawa, Amma amsar ta biyu tana tabbatuwa da cewa: "(Annabi) Muhammad Manzon Allah ne", da sanin hakan da kuma tabbatarwa, da miƙa wuya da kuma yi masa biyayya.

Rukunan imani guda shida ne:

Ka sani ya kai musulmi mai tauhidi cewa imani yana tsayuwa ne a kan rukunai guda shida, imani baya cika sai da su; idan wani rukuni daga cikinsu ya faɗi, to mutum ba zai zama mumini ba kwata-kwata; domin ya rasa wani rukuni daga cikin rukunan imani.

Waɗannan rukunan sune waɗanda suka zo a cikin mashhurin Hadisin nan na Jibril - aminci ya tabbata a gare shi -, lokacin da ya tambayi Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: «To ka bani labari game da imani, ya ce: Ka bada gaskiya da Allah, da Mala'ikunSa, da littattafanSa, da ManzanninSa, da ranar lahira, kuma ka yi imani da ƙaddara alherinta da kuma sharrinta». Muslim ne ya ruwaito shi.

IMANI DA ALLAH

Muna imani da Rububiyyar Allah - Maɗaukakin sarki - wato: Shi ne Ubangiji Mahalicci, Mamallaki, Mai jujjuya dukkan al'amura.

Muna imani da Uluhiyyar Allah Ta'ala; wato cewa: Shi ne Allah na gaskiya; babu wani abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma duk wani abin bautawa wanda baShi ba to ƙarya ne.

Muna imani da sunayenSa da siffofinSa; wato: Cewa Yana da sunaye kyawawa da kuma siffofi cikakku maɗaukaka.

Muna imani da kaɗaitakar Allah - Maɗaukakin sarki - a cikin hakan; wato: Ba Shi da abokin tarayya a cikin RububiyyarSa, haka a cikin UluhiyyarSa, haka a cikin sunayenSa da kuma siffofinSa.

Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Shi ne Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãnin su. sai ka bauta Masa, kuma ka yi haƙuri ga bautar sa. Shin kã san wani takwara a gare shi? 65} [Maryam: 65].

Kuma (Allah) - tsarki ya tabbatar maSa - Ya ce: {...Wani abu bai zama kamar tamkarSa ba, kuma Shĩ ne Mai ji, Mai gani.} [al-Shurā: 11].

Muna imani cewa Shi - (Allah) Maɗaukakin sarki - Ya daidaita akan Al'arshinSa, Yana sane da halayenmu, Yana jin maganganunmu, Yana ganin ayyukanmu, Yana jujjuya al'amuranmu, Yana azurta matalauci, Yana gyara wanda ya karye, Yana bayar da mulki ga wanda Ya ga dama, Yana ƙwace mulki daga wanda Ya ga dama, Yana ɗaukaka wanda Ya ga dama, Yana ƙasƙantar da wanda Ya ga dama, a hannunSa alheri yake, kuma Shi ne Mai iko akan komai.

Kuma wanda wannan shi ne sha'aninsa, to Shi - tsarki ya tabbatar maSa - da Ma'iyyarSa ta musamman Yana tare da bayinSa da waliyyanSa muminai da taimako da goyon baya, da Ma'iyyarSa mai gamewa Yana sane da dukkan halittarSa da yanayinsu, kuma Yana jin maganganunsu, Masani da abin da zukatansu ke ɓoyewa da wanin haka, kuma Shi - tsarki ya tabbatar maSa - Yana saman Al'arshinSa kamar yadda Ya sanar game da kanSa: {Mai rahama, Ya daidaita a kan Al'arshi. 5} [Ɗāha: 5], kuma kamar yadda ya dace da ɗaukakarSa - tsarki ya tabbata maSa -: {...Wani abu bai zama kamar tamkarSa ba, kuma Shĩ ne Mai ji, Mai gani.} [al-Shurā:11].

Muna imani da tabbatar da dukkan abin da Allah Ya tabbatarwa kanSa ko ManzonSa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya tabbatar maSa da shi na sunaye da siffofi, kuma muna nisantar manyan abubuwa guda biyu masu hatsari; su ne:

Kamanceceniya: Mutum ya faɗa da zuciyarsa ko da harshensa: Siffofin Allah - Maɗaukakin sarki - kamar siffofin halittu ne.

Tambayar ya ya: Shine mutum ya faɗa da zuciyarsa ko da harshensa: Yadda siffofin Allah - Maɗaukakin sarki - suke kaza da kaza ne.

Kuma muna imani da kore dukkanin abin da Allah Ya korewa kanSa ko ManzonSa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kore maSa, kuma wannan korewar tana ƙunshe da tabbatar da cikar kishiyarSa, Allah Ya korewa kanSa zalunci saboda cikar adalcinSa, kuma mu yi shiru daga abin da Allah da ManzonSa suka yi shiru daga gare shi.

IMANI DA MALA'IKU

Muna imani da Mala'ikun Allah - Maɗaukakin sarki -, kuma cewa su: {...bãyi ne mãsu daraja. 26 Bã su gabãtarSa da magana, kuma su da umurninSa suke aiki. 27} [al-Anbiyā': 26-27].

Allah - Maɗaukakin sarki - Ya halicce su daga haske, kuma sun yi masa bauta kuma sun miƙa wuya ga yi masa biyayya, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {...bã su yin girman kai ga ibãdarSa. kuma bã su gajiya. 19 Sunã tasbĩhi dare da rãnã, bã su yin rauni. 20} [al-Anbiyā': 19-20].

Allah Ya shamakance su daga gare mu ba za mu gan su ba, kuma wataƙila Ya bayyana su ga wasu daga cikin bayinSa.

Muna imani cewa mala'iku suna da ayyuka da aka ɗora musu: Daga cikinsu akwai Jibril wanda aka wakilta da wahayi, yana saukowa da shi daga wurin Allah zuwa ga wanda Yake so daga cikin AnnabawanSa da ManzanninSa.

Kuma daga cikinsu akwai Mika'ilu wanda aka wakilta shi ga ruwan sama da tsirrai.

Kuma daga cikinsu akwai Israfil wanda aka wakilta da busa ƙaho a lokacin mutuwa da tashin alƙiyama.

Da cikinsu akwai Mala'ikan mutuwa wanda aka wakilta da ɗaukan rayuka a lokacin mutuwa.

kuma daga cikinsu akwai Mala'ikan duwatsu wanda aka wakilta shi da su.

Akwai kuma wasu Mala'ikun da aka wakilta su da kula da jarirai a cikin mahaifa, wasu kuma da aka wakilta su da kiyaye 'yan Adam, wasu kuma da aka wakilta su da rubuta ayyukansu, kowanne mutum yana da mala'iku biyu, Allah ya ce: {...daga dãma, kuma daga hagu akwai wani (malã'ika) zaunanne. 17 Bã ya lafazi da wata magana fãce a lĩƙe da shi akwai mai tsaro halartacce. 18} [Qāf: 17-18].

Wasu kuma an wakilta su da tambayar mamaci bayan an gama binne shi.

IMANI DA LITTATTAFAI

Muna imani cewa Allah - Maɗaukakin sarki - Ya saukar da littattafai ga ManzanninSa, hujja akan talikai kuma bayyananniyar hanya ga masu aiki. Imani da su gaba ɗayansu wajibi ne, kafircewa da ɗaya daga cikinsu; kafircewa ne da su gaba ɗayansu; Allah - Maɗaukaki - Ya ce: {Manzon Allah yã yi ĩmãni da abin da aka saukar zuwa gare shi daga Ubangijinsa, da mũminai. Kõwanensu yã yi ĩmãni da Allah, da mala'ikunSa, da littattafanSa, da manzanninSa. Bã mu rarrabẽwa a tsakãnin ɗaya daga manzanninSa. Kuma (mũminai) suka ce: "Mun ji kuma mun yi ɗa'a; (Muna nẽman) gãfararKa, yã Ubangijinmu, kuma zuwa a gare Ka makõma take. 285} [al-Baƙara: 285].

Allah - Maɗaukakin sarki - Ya saukar da littafi tare da kowane Manzo; kamar yadda Allah - tsarki ya tabbata a gare Shi - Ya ce: {Haƙĩƙa, lalle Mun aiko Manzannin Mu da hujjõji bayyanannu, kuma Muka saukar da Littãfi da sikẽli tãre da su dõmin mutãne su tsayu da ãdalci...} [al-Hadid: 25].

Kuma daga cikin waɗannan litattafan akwai:

Attaura: wacce Allah - Maɗaukakin sarki - Ya saukar da ita ga (Annabi) Musa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, ita ce mafi girman Littattafan Banu Israeel, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Lalle ne Mu, Mun saukar da Attaura, a cikinta akwai shiriya da haske...} [al-Mā'ida: 44].

Al-Injil: Wanda Allah Maɗaukakin sarki - Ya saukar da shi ga bisa (Annabi) Isa - aminci ya tabbata a gare shi -, kuma mai gasgatawa da Attaura kuma mai cikawa gareta, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma Muka biyar a kan gurãbansu da Ĩsa ɗan Maryama, yãnã mai gaskatãwa ga abin da yake a gaba gare shi daga Attaura, kuma Muka bã shi Injĩla a cikinsa akwai shiriya da haske, yanã mai gaskatãwa ga abin da yake a gaba gare shi daga Attaura, kuma shi shiriya ne da wa'azi ga mãsu taƙawa. 46} [al-Mā'ida: 46].

Da Zabura: Da Allah - tsarki ya tabbatar maSa - Ya bawa (Annabi) Dawud - aminci ya tabbata a gare shi -, Allah - tsarki ya tabbatar maSa - Ya ce: {...Kuma Mun bai wa Dãwũda zabũra.} [al-Isrā': 55].

Littaffan Ibrãhĩm da Mũsã - tsira da amincin Allah su tabbata a gare su - Allah - Mai tsarki - Ya ce: {Lalle ne, wannan yanã a cikin littafan farkon. 18 Littaffan Ibrãhĩm da Mũsã. 19} [al'Aalā: 18-19].

Alkur'ani mai girma: Wanda Allah Ya saukar ga AnnabinSa Muhammad cikamakin Annabawa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, (Allah) Maɗaukakin sarki Ya ce: {...shiriya ga mutãne da hujjõji bayyanannu daga shiriya da rarrabẽwa...} [al-Baƙara: 185]. Saboda haka ya kasance mai gasgatawa ga littattafan da suka gabata, kuma mai hukunci a kansu; (Allah) - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma Mun saukar da Littãfi zuwa gare ka da gaskiya, yanã mai gaskatãwa ga abin da yake a gaba gare shi daga Littãfi (Attaura da Injĩla), kuma mai halartãwa a kansa...} [al-Mā'ida: 48].

Allah Ya soke dukkan shari'o'in da suka gabace shi, kuma Ya lamunce kiyaye shi daga ɓarnar masu ɓarna da karkatar masu karkata, (Allah) Maɗaukakin sarki Ya ce: {Lalle Mũ ne, Muka saukar da Ambato (Alƙur'ãni), kuma lale Mũ, haƙĩƙa, Mãsu kiyayẽwane gare shi. 9} [al-Hijr: 9]; Saboda zai kasance hujja a- kan halittu gaba ɗaya har zuwa ranar Alƙiyama.

Amma sauran litattafan da suka gabata; an ƙayyade su da wani lokaci wanda zai ƙare da saukar abin da zai shafe su; Allah Ya wakilta kiyayesu ga malaman su da masu bauta daga cikinsu amma ba su kiyaye su ba; don haka canje-canje da ƙari da ragi suka shiga cikinsu, (Allah) - Maɗaukaki - Ya ce: {Daga waɗanda suka tũba (Yahũdu), akwai wasu sunã karkatar da magana daga wurãrenta...} [Surat al-Nisā': 46], Kuma (Allah) - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {To, bone ya tabbata ga waɗanda suke rubũta littãfi da hannuwansu sa'an nan kuma su ce wannan daga wurin Allah yake, dõmin su sayi kuɗi kaɗan da shi, sannan bone ya tabbata a gare su daga abin da hannayensu ke rubũtãwa, kuma bone ya tabbata a gare su daga abin da suke sanã'antãwa. 79} [al-Nisā': 79]

Imani da Manzanni.

Muna imani cewa Allah - Maɗaukakin sarki - Ya aiko manzanni daga cikin mutane zuwa ga halittunSa, (Allah) - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Manzanni mãsu bãyar da bushãra kuma mãsu gargaɗi dõmin kada wata hujja ta kasance ga mutãne a kan Allah bãyan Manzannin. Kuma Allah yã kasance Mabuwãyi, Mai hikima. 165} [al-Nisā': 165].

Wanda ya kafurta da wani Annabi ɗaya to haƙiƙa ya kafurta da dukkan Manzanni, domin babu bambanci tsakanin Manzo da Manzo; saboda da'awarsu ɗaya ce wato bautar Allah Shi kaɗai, don haka wanda ya kafurta da saƙon (Annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - zuwa ga mutane duka to haƙiƙa ya kafurta da dukkan Manzanni, har ma da Manzon da yake iƙirarin cewa yana imani da shi kuma yana bin sa; saboda fadinSa (Allah) - Maɗaukakin sarki -: {...Bã mu rarrabẽwa a tsakãnin daya daga manzanninSa...} [al-Baƙara: 285], kuma da faɗinSa: {...bã mu rarrabẽwa a tsakãnin kõwa daga gare su...} [al-Baƙara: 136]. Ma'ana: A'a, muna imani da dukkaninsu, ka yi la'akari da maganar Allah - Maɗaukakin sarki -: {Mutãnen Nũhu sun ƙaryata Manzanni. 105} [al-Shu'arā': 105]; Sai Allah Ya sanya su masu ƙaryatawa ga dukkan Manzanni, tare da cewa babu wani Manzo da bai gabaci (Annabi) Nuhu ba!

Kuma (Allah) - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Lalle ne, waɗanda uke kãfirta da Allah da ManzonSa kuma sunã nufin su rarrabe a tsakãnin Allah da manzanninSa, kuma sunã cẽwa: "Munã ĩmãni da sãshe, kuma munã kãfirta da sãshe." Kuma sunã nufin su riƙi hanya a tsakãnin wannan. 150 Waɗannan sũ ne kãfirai sõsai, kuma Mun yi tattali, dõmin kãfirai, azãba mai walãkantarwa. 151 Kuma waɗanda suka yi ĩmãni da Allah da manzanninSa, kuma ba su rarrabe a tsakãnin kõwa ba daga gare su, waɗannan zã Mu bã su ijãrõrinsu, kuma Allah Yã kasance Mai gãfara, Mai jin ƙai. 152} [al-Nisā': 150-152].

Muna imani cewa na farkonsu shi ne (Annabi) Nuhu, kuma na ƙarshensu shi ne (Annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata a gare su duka -. {Lalle ne Mu, Mun yi wahayi zuwa gare ka, kamar yadda Muka yi wahayi zuwa ga Nũhu da Annabãwa daga bãyansa...} [al-Nisā': 163].

Kuma mafificinsu shi ne Annabi Muhammad, sai Annabi Ibrahim, sai Annabi Musa, sai Annabi Nuhu, da Annabi Isa ɗan Maryama, su ne waɗanda aka keɓance su a cikin faɗinSa - Maɗaukakin sarki -: {Kuma a lõkacin da Muka riƙi alkawarin Annabawa daga gare su, kuma daga gare ka, kuma daga Nũhu da Ibrãhĩm da Mũsa da kuma Ĩsã ɗan Maryama, kuma Muka riƙi wani alkawari mai kauri daga gare su. 7} [al-Ahzab: 7].

Muna imani cewa dukkanin Manzanni 'yan Adam ne ababan halitta, ba su da wani abu da ya keɓanci Ubangijintaka, dukkansu bayin Allah ne - Maɗaukakin sarki -, Ya girmama su da risala kuma Ya siffanta su da bauta, kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya umarci (Annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - wanda shi ne na ƙarshe kuma mafi alherinsu da ya ce: {Ka ce: "Bã ni mallaka wa raina wani amfãni, kuma haka ban tunkuɗe wata cũta, fãce abin da Allah Ya so...} [al-A'araf: 188].

IMANI DA RANAR LAHIRA

Muna imani da ranar lahira, wacce ita ce Ranar Alƙiyama babu wata rana a bayanta, lokacin da za a tashi mutane suna masu rayuwa madawwamiya, ko dai a gidan ni'ima ko kuma a gidan azaba mai raɗaɗi.

Muna imani da tashi; shi ne: Allah - Maɗaukakin sarki - zai raya matattu lokacin da Isrāfil zai yi busa ta biyu a cikin ƙaho: {Kuma aka busa a cikin ƙaho, sai waɗanda ke a cikin sammai da ƙasã suka sũma sai wanda Allah Ya so (rashin sumansa), sa'annan aka hũra a cikinsa, wata hũrãwa, sai gã su tsaitsaye, sunã kallo. 68} [al-Zumar: 68], Sai mutane su tashi daga ƙaburburansu ga Ubangijin talikai, marasa takalma, tsirara babu sutura, marasa kaciya, {...kamar yadda Muka fãra a farKon halitta Muke mãyar da ita. Wa'adi ne a Kanmu. Lalle ne Mun kasance Mãsu aikatãwa.} [Al-Anbiya': 104].

Muna imani da sahifan ayyuka za a ba da su ga masu imani ta hannun dama ko daga bayan bayansu ta hannun hagu ga kafirai, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma kõwane mutum Mun lazimta masa abin rekõdinsa a cikin wuyansa, kuma Mu fitar masa a Rãnar ¡iyãma da littãfi wanda zai haɗu da shi buɗaɗɗe. 13 Karanta Littãfinka. Ranka ya isa ya zama mai hisãbi a kanka a yau. 14} [al-Isrā': 13-14]; Kuma (Allah) - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {To, amma wanda aka bai wa littãfinsa da damansa. 7 To, za a yi masa hisãbi, hisãbi mai sauƙi. 8 Kuma ya jũya zuwa ga iyãlinsa (a cikin Aljanna), yanã mai raha. 9 Kuma amma wanda aka bai wa littãfinsa, daga wajen bãyansa. 10 To, zã shi dinga kiran halaka! 11 Kuma ya shiga sa'ĩr. 12} [al-Inshiƙāƙ: 7-12].

Muna imanin da ma'aunan da za a aza a Rãnar Alƙiyama, sabõda haka ba a zãluntar rai da kõme, kamar yadda (Allah) - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma Munã aza ma'aunan ãdalci ga Rãnar Alƙiyama, sabõda haka ba a zãluntar rai da kõme. Kuma kõ dã ya kasance nauyin ƙwãya daga kõmayya ne Mun zo da ita. Kuma Mun isa zama Mãsu hisãbi. 47} [al-Anbiyā': 47], Kuma (Allah) - Maɗaukakin sarki -Ya ce: {To, waɗanda sikẽlinsu ya yi nauyi, to, waɗannan sũ ne mãsu babban rabo. 102 Kuma waɗanda sikẽlinsu ya yi sauƙi, to, waɗannan ne waɗanda suka yi hasãrar rãyukansu sunã madawwama a cikin Jahannama. 103} [al-Mu'Munān: 102-103].

Muna imani da babban ceto na Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - musamman a cikin rabe hukunci tsakanin halitta da kuma a shigar 'yan aljanna aljanna, da ceto ga waɗanda suka shiga wuta daga cikin muminai don su fito daga cikinta, kuma wannan ceto na Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ne da sauran Annabawa da muminai da Mala’iku.

Muna imani da tafki, da siraɗin da aka kafa akan Jahannama, mutane zasu wuce ta kansa gwargwadan ayyukansu.

Muna imani da dukkan abin da ya zo a cikin littafi da sunnah na labaran wannan rana da tsoratarwarta, Allah Ya taimake mu a kansu, kuma muna imani da cewa aljanna da wuta suna nan a yanzu haka, kuma ba za su gushe ba har abada; domin aljanna gidan ni'ima ce da Allah - Maɗaukakin sarki - Ya tanadar wa muminai masu taƙawa, kuma wuta gidan azaba ce da Allah - Maɗaukakin sarki - Ya tanadar wa kafirai azzalumai, Allah Ya faɗa game da azabar jama'ar Fir'auna a cikin ƙabari da kuma a lahira: {...kuma mummunar azãba ta wajaba ga mutãnen Fir'auna. 45 Wutã, anã gitta su a kanta, sãfe da maraice, kuma a rãnar da Sa'a take tsayuwa, anã cẽwa, 'Ku shigar da mutãnen Fir'auna a mafi tsananin azãba. 46} [Ghāfir: 45-46], Kuma (Allah) - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Kuma lalle Munã ɗanɗana musu daga azãba, mafi ƙasƙanci, kãfin a kai ga azãba mafi girma, dõmin fãtan za su kõmo. 21} [al-Sajda: 21].

Kuma ya wajaba a kan mumini ya yi imani da dukkanin abin da ya zo daga littafi da sunnah na waɗannan al'amuran gaibu, kuma kada ya bijirar da su saboda abin da yake gani a duniya; domin al'amuran lahira ba a auna su da al'amuran duniya; saboda bayyanar bambanci mai girma a tsakaninsu.

IMANI DA ƘADDARA ALHERINTA DA SHARRINTA

Muna imani da ƙaddara alherinta da sharrinta, kuma ita ƙaddarawar Allah ne - Maɗaukakin sarki - ga halittu bisa ga abin da ya gabatar da saninSa da kuma abinda hikimarSa ta buƙata.

Ƙaddara tana da matakai huɗu:

Ilimi: Muna imani da cewa Allah - Maɗaukakin sarki - Masani ne da dukkan komai, Ya san abin da ya kasance da abin da zai kasance da yanda zai kasance - tsarki ya tabbata a gare Shi -.

Rubutu: Muna imani da cewa Allah - Maɗaukakin sarki - Ya rubuta dukkan kasantaccen abu a cikin Luhul mafuz har zuwa ranar Alƙiyama, (Allah) - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Ashe, ba ka sani ba, lalle ne Allah Yanã sanin abin da yake a cikin sama da ƙasa? Lalle ne wancan yanã cikin Littafi lalle wancan ga Allah mai sauƙi ne. 70} [al-Hajj: 70].

Mashī'ah: Muna imani da cewa babu wani abu da zai kasance sai da mashi'ar Allah, abin da Allah Ya so ne yake kasancewa, abin da kuma bai so ba to ba zai kasance ba, Allah - Maɗaukkain sarki - Ya ce: {Kuma Ubangijinka Yanã halitta abin da Yake so kuma Yake zãɓi...} [al-Kasas: 86].

Halitta: Muna imani cewa Allah ne Mahaliccin kowane abu, (Allah) - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {Allah ne Mai halitta dukan kõme, kuma Shĩ ne Wakĩli a kan kõme. 62 Shĩ ke da mabũɗan sammai da ƙasã...} [al-Zumar: 62-63].

Duk wani abu da bayin Allah suke yi na maganganu ko ayyuka ko barin aikatawa, duk yana cikin sanin Allah - Maɗaukakin sarki -, kuma an rubuta shi a wurinSa, kuma Allah - Maɗaukakin sarki - Ya so su kuma Ya halicce su.

Amma duk da haka muna imani cewa Allah - Maɗaukakin sarki - Ya sanya wa bawa zaɓi da iko, da su ne ake yin aiki; don haka babu wata hujja ga mai laifi a kan laifinsa da ƙaddarar Allah - Maɗaukakin sarki -; domin mai laifi yana aikata laifi da zaɓinsa ba tare da ya san cewa Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ƙaddara shi a kansa ba; domin babu wanda ya san ƙaddarar Allah - Maɗaukakin sarki - sai bayan faruwar abin ƙaddarawar, Allah - Maɗaukakin sarki - Ya ce: {...kuma wani rai bai san abin da yake aikatãwa a gõbe ba...} [Luƙmān: 34].

Muna roƙon Allah - Maɗaukakin sarki - ya datar da mu da ilimi da aiki, kuma Ya sanar da mu abin da zai amfane mu, kuma Ya amfane mu da abin da Ya sanar da mu, Ya kuma ƙara mana ilimi, kuma Ya kiyaye mana Addininmu, kuma Ya karɓi kyawawan ayyukanmu, kuma Ya nisantar da mu daga kuskure, amin.

Dukkan yabo ya tabbata ga Allah Ubangijin talikai

Allah Ya yi tsira da aminci ga Annabinmu Muhammad, da alayensa da sahabbansa baki ɗaya.