وصيتي
WASIYYATA
WASIYYATA
Godiya ta tabbata ga Allah, tsira da aminci su tabbata ga Manzon Allah, bayan haka:
Ni (............................................................) Lambar katin ɗan ƙasata:
Na yi wasiyya, ni ina cikin hayyacina abin lura a shari'a na cikakken hankalina da kuma kyakkyawan riskata, cewa ni ina shaidawa cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah Shi kaɗai yake, ba Shi da abokin tarayya, kuma cewa (Annabi) Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa ne, kuma cewa (Annabi) Isa bawan Allah ne kuma ManzonSa ne kuma kalmarSa ce wacce Ya jefata zuwa ga Nana Maryam kuma rai ne daga gareShi, kuma cewa aljanna gaskiya ce kuma alƙiyama mai zuwa ce babu kokwanto a cikinta, kuma cewa Allah Zai tashi waɗanda ke cikin ƙaburbura.
Ina yi wa iyalan gidana wasiyya cewa idan mutuwa ta ta zo mini da (ina musu wasiyya da) haƙuri da yarda da kuma miƙa wuya.
Kuma ina yi musu wasiyya da kada su yi tarukan da suka keɓanci ta'aziyya, su kuma yi kwaɗayi akan Sunnah.
Kuma ina yi musu wasiyya da abinda (Annabi) Ibrahim ya yi wa 'ya'yansa wasiyya da shi da kuma (Annabi) Ya'akub: (Ya ku 'ya'yana lallai Allah Ya zaɓar muku Addini to kada ku mutu sai ku kuna musulmai).
Kamar yadda nake yi musu wasiyya da tsoron Allah - Maɗaukakin sarki - da kuma yi masa muraƙaba a ɓoye da kuma a bayyane, kuma su kiyaye dokokin Allah su yi ruko da umarce-umarcenSa su nisanci hane-hanenSa kuma su kiyaye sallah domin ita ce ginshiƙin Addini.
Kuma ina yi musu wasiyya da rashin rarrabuwa da saɓani kuma su jiƙan junansu, kada su yanke zumunci kuma su sadar da zumuncinsu kuma su kiyaye dukiyoyinsu kuma su bada hakkin Allah a cikinta, kada su yi kasuwanci sai na halal, kuma su nisanci riba kaɗan ɗinta da mai yawanta kuma su yi taimakekeniya a tsakaninsu da abinda yake akwai gyara Addininsu da duniyarsu a cikinsa.
Kamar yadda nake yi musu wasiyya da abinda ke tafe:
Na farko: Gaggawar biyan basukan da suke cikin wuyayena da wuri, domin cewa: (Ran mumini abin ratayawa ne da bashinsa har sai an biya masa).
Su ne kamar yadda suke tafe:
Haƙƙoƙin Allah mai girma da ɗaukaka na (zakka da azimi da kaffarori da bakance) kuma sune:
...............................................................................................
Haƙƙoƙin mutane na (Basussuka ko ajiya da amanoni) kuma sune:
Adadi/Amana------———————— Mai bashin/Amana---————————----Adireshinsa--—————————----Lambar wayarsa------—————————---Kwanan watan biyan bashin/Biyan bashin
Na biyu: Tabbatar abinda yake haƙƙina ne na dukiyoyi da haƙƙoƙina a wajen wasu, su ne kamar abinda ke tafe:
Adadi-———--------Suna na wanda ake bi bashi---————————----Adireshinsa--———---Lambar wayarsa—————-----------Kwanan watan biyan bashin————————
Na uku: Tattaro dukiyoyina su ne kamar yadda yake tafe:
a- Dukiyoyi na kuɗin da suke a ajiye a cikin asusuna da banki, kuma bayaninsu shi ne kamar yadda yake tafe:
Sunan bankin--------Reshe-------Lambarsa--------Lambar asusu---------asusun da aka yi wa rijista da sunan---------wanda ya keɓanci
b- Abubuwan da aka mallaka na kadarori:
Ƙasar/fili da aka mallaka wacce aka bayyana bayaninta a abinda ke tafe:
Nau’i ƙasar----——————————--Lambar takardu-------Kwanan watansa-------An yi shi daga---------gari--------Unguwa
Na huɗu: Ina yin wasiyya daga dukiyata:
Tsabar kuɗi gwargwadan: ().
Mallakin ƙasata/fili hakan da mallakata wanda ke a unguwa.............A gari...............Da lambar takardun mallaka.......Kwanan watansa....................
Da kashin da gwargwadan: (%).
Na biyar: Wanda aka yi wa wasiyya akan dukiyar da aka yi wasicci da ita shi ne: (.......................) kuma lambar katin ɗan ƙasarsa (.......................) An yi masa wasiyya akan ragowar abinda aka bari har sai an raba, shi ne: (..........................) kuma lambar katin ɗan ƙasarsa (.....................)
Wanda na yi wa wasicci dan kula da 'ya'yana ƙanana dan tarbiyyantar da su tarbiyya mai kyau da kula da dukiyoyinsu da kuma haɓakata ta hanyar kasuwanci da ita shi ne: (..................) Lambar katin ɗan ƙasarsa (..........................) Wanda na yi wa wasicci akan ɗaura auren 'ya'yana mata shi ne: (........................) Lambar katin ɗan ƙasarsa (.....................)
Haka waɗanda ke bayansu daga wanda suka cika sharuɗɗan nan masu zuwa: Musulunci da shiriya, da amana da ƙarfi, da adalci da nagarta gwargwadan iko, kuma wanda aka yi wa wasicci yana da damar zaɓin wanda zai maye gurbinsa, haka nan dukkan wanda aka yi wa wasicci tare da wanda ke bayansa.
Na shida: Za'a bada ribar dukiyar da aka yi wasicci da ita a ayyukan alheri wanda daga cikinsu akwai:
Hanyoyin alheri na musamman: ..........................................
Idan ribar ta ragu sai abayar a ayyukan alheri na gamewa (Fagen ilimi - fagen zamantakewa da taimako - fagen Da'awa - fagen masallatai - fagen lafiya - fagen kafafen yaɗa labarai masu manufa). Makusanta sune mafi cancanta da yi wa alheri, a cikin halin samun wata buƙata ana gabatar da mafi kusa.
A ƙarshen wannan wasiyyar ina fatan zaku yi mini afuwa ga abinda ya zo daga gareni na kuskure ko kasawa, kuma babu wani da zai iya kuɓuta daga hakan, Allah ne wanda ake neman taimakonSa, bana mantawa da in yi muku wasicci da yawan yi mini addu'a, kuma ina roƙon Allah Ya yi albarka ga makusantana kuma Ya kyautata cikawata Ya gafarta mini da mahaifana Ya kuma ɗaukaka darajata a lahira da mahaifana da kuma musulmai, kuma na yi izinina ga wanda zai yi shaida akan hakan. Allah ne Mafi alherin masu shaida.
An fitar da wannan wasiyyar a ranar.......................wadda ta yi daidai da / / 143 bayan Hijira, kuma ta shfe abinda ke gabaninta.
Tsira da aminci su tabbata ga annabimmu Muhammad da alayansa da sahabbansa ka yi aminci amincewa.
Siffa---------- Suna -------------- Kwanan wata ----------- Lambar katin ɗan ƙasa --------- Sa hannu
Mai yin wasiyyar:
Mai shaida na farko
Mai shaida na biyu
Faɗakarwa: Wannan taƙaitacciyar wasiyya ce wacce ta dace ga dukkanin musulmai dan ƙarin bayani ka tuntuɓemu, kamar yadda zaku iya rubuta wasiyyoyinku da kuma samun shawarwari kyauta daga cibiyar Waƙif ƙwararrun masu wasiyya da kuma waƙafai ta hanyar manhaja (application) na wasiyya.
"Bai da ce ga mutum musulmi ba yana da wani abin da zai yi wasiyya da shi, ya zauna kwana biyu face sai wasiyyarsa ta kasance a rubuce tare da shi" Bukhari - za'a ɗorashi akan bango
Wani dare bai taɓa wuce min ba tun da na ji Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana faɗin haka sai wasiyyata tana wurina a rubuce. Abdullahi ɗan Umar - za'a ɗora shi akan bango
Mai arziƙi shi ne wanda idan numfashinsa ya yanke, amma ayyukansa ba su yanke ba. Ibnu Ƙudama - za'a ɗora shi a ƙarshen shafi a cikin wasiyyar
Sassauƙar wasiyya ga dukkanin musulmai - za'a ɗora shi akan bango